Download Now ZURFIN CIKI KASHI NA 2 BIYU
:-2**** ta dafa kafadata tana cewa kayi haquri mubarak na sani kana son nabeelah sannan itama tana sonka,sai dai kuma kayi kuskuren rashin bayyana soyayyarka gareta a sanda ta bukaci hakan,nayi kokarin dai- daita tsakaninku amma naji tsoron kada mutane suyi tunanin na aurar da nabeelah ga d'ana ba bisa son ranta ba sai dai bisa dole kasancewar ta girma a hannuna.......haka kuma yanzu bazan saka kaina cikin wannan matsalar taku ba amma zan goya muku baya bisa dukkan shawarar da kuka yanke,idan kuna nemana ku sameni a fallow*** na kalli nabeelah idona cike da hawaye na fara magana kamar haka'nabeelah ina sonki,kuma ina kaunarki, sai dai na kasance cikin irin mutane da sukan boye sirrin zuciyarsu,kiyi haquri ki gafarceni,nasan nayi miki laifi...nagode ki tashi ki tafi allah ya bada zaman lafia sannan allah yasa shine mafi alkhairi gareki........na miqe zan fita daga motar,ta kamo hannuna ta zaunar dani tana magana hade da wani kuka mai tsuma zuciya gami da sa tausayi kamar haka'yamubarak da farko na yarda kana sona amma yanzu na gane cewar soyayyar batayi tasiri a zuciyarka ba tunda har ka yarda zaka haqura dani kan wani ya aura,lallai na yarda baka kishina baka tausayina irin zaman da zanyi tare da wani namiji wanda ba kaiba,ka sani cewar zuciya ba zata aminci rabuwa da kaiba,jikina na haramtashi ga dukkan wani d'a namiji idan ba kaiba dan haka na qudiri niyyar mallakarka ka ta wane hali,yamubarak kayi kokari ka soni kamar yanda nake sonka,yamubarak kada ka bani kunya'*** na share hawayen dake zuba kan kuncinta,na kama hannayenta na kwantar da ita bisa kirjina,nabeela h ki amince da soyayyata gareki kada ki zargeni da komi sai alkhairi,nabeelah ina sonki kuma nine mijinki da yardar allah,da sauri ta tashi daga kan kirjina ta dafa kafaduna tana kallon fuskata,ta sumbaci goshina sannan ta rungumeni kan kirjinta tana cewa hakika farincikina ya karu,burina ya cika sannan alheri ya tabbata gareni.....amma *menene mafita? *da wane zance zamu tunkari abba? *sannan kuma lokaci yana da karanci garemu.... Na kalli nabeelah dake kan kirjina nace zaifi sauki muje wurin kawu aminu mu shaida masa halinda muke ciki...ni nasan me zan fada masa kuma zai yarda. *kai tsaye na tuka motar zuwa gidan kawu na tarar ya gama cin abinci yana gindin bishiya yana hutawa..bayan mun gaisa ya cigaba da magana kamar haka'lallai daga ganinku akwai matsala dan naga alamun damuwa gareku, shin ko baki son auren ne? Ya tambaya' na fara da cewa gaskiya kawu ita nabeelah ba wanda take son za'a bata ba,kawu yace wannan zancen banza ne dama shi yasa suke boye min to wallahi wannan maganar babu ita,ku tashi mu tafi gidan.... Na tuka mota har kofar gidan muka shiga shi kuwa kawu tun daga kofar gida yake ta fada..yana shiga su mama suka fito suna gaisuwa amma ko amsawa bayyiba ya cigaba da cewar'maganar auren nabeelah babu na soketa yanzu zata fada mana wanda take so kuma goben zan daura mata aure dashi...nabeelah ta kada baki tace'ya mubarak nake so' kawu yayi dariya yace au to ai shikenan ta kwana gidan sauki kuda dan iskanci abin na gidane ma kuke bata lokaci,to ai ni yanxu xan daura auren idan yaso kuje chan kuyi ta bikinku,sannan baba ya shigo yaji meke faruwa amma ba yanda zaiyi da kawu dan yasan halins doe qura ya zama waliyina shi kuma waliyin yamubarak aka daura auren*** take yamubarak ya daukeni muka tafi gidan kunshi daga nan ya kaini nayi kitso muka wuce gidan aunty nafeesat nayi wanka na saka rigar atamfa kaina ba dankwali na fito gareshi,wow nabeelah amma kinyi kyau,ya kamo hannu daga inda yake zaune gefen gadon,ya sumbaceni har saida numfashina ya dauke,ya kwantar dani kan gadon ya fara cire kayan dake.......hakika ban taba sanin haka yamubarak ya iya soyayyaba sai yau,lallai da tuni nayi asar miji,haka muka kasance cikin nuna kaunar juna har zuwaN CIKI book 2 part 1
ZURFIN CIKI book 2 part 1
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:05
Abba kwance kan gado,dare yayi nisa amma shi
ya kasa bacci sam.saboda matsalar da yake ciki
yanzun. domin kuwa matar shi in yaga bazai iya
ba sai ya sawwake mata,amma maganar auran
ummi koda Alhaji bai goya mishi ba bazai iya guje
mata ba. "yanzun menene mafita?"ya tambayi
kansa,wata zuciyar ta ce, "kayi shiru tamkar baka
ga wannan takarda ba,tunda ba wanda yasan ka
gani." a fili ya ce,"haka ne." ya ci gaba da
tunanin kila ma yanxun ya janye kudirinshi,tunda
yaga ummin bata da kan gado. don yaga rubutun
yayi shi ne tun ranar da aka haifi ummi,ko kuma
ranar sunanta. tunda gashi har da sunan ummi a
jiki.mafita kenan yayi shiru.wata zuciyar ta ce,"in
ko kayi haka kayiwa Alhaji da ummanka adalci?
koda yar su ba yar adam ba ce bai kamata ka
gujeta ba.ko don albarkacin son da suka nuna
maka. shin da ummi ta kasance mai jin magana
da nutsuwa,kuma mai tsananin kyau zaka
gujeta? Kada kayi zaton Alhaji yayi kudurin aura
maka yarsa ne don yasan zata zama mara ji,kayi
nazari. haka Abba yayi ta tunani har asubah
tayi,amma hukuncin da ya yanke shine yayi shiru.
sai dai ya janye batun rabuwa da matar shi,don
yasan yana sakinta zai zama mijin ummi,kai
batun nan hadiye ma cikinshi shine mafi dacewa.
dunkuna masu kyau yayi wa matarshi saboda cin
suna.haka yayi wa dan siyayya daidai karfinshi,ya
kawo ma umma. Taji dadi sosai nan ahj ya iske
su, shima ya shiga dakin umman ya xauna ya ce
a dauko masa abinci nan xai ci yau.ya dubi abba,
babana nayi sautun raguna xuwa qauye nace xa
a siyo nmanya.abba ya ce biyu?umma tace
hakan yayi.abba ai tuwan girma miyarsa nama,
aja rago daya xiqal a shiga wannan gida da shi?
abba yace,me xai hana tunda ban musu qaryar
arxiki ba sun san mu talakawa ne.ahj yace
xancanka dutse bacna,amma maganar ummanka
ita xa a bi, sannan xa a sai buhun shinkafa da
cefane a kai musu.ana gobe suna abba da
abokansa suka dira gidan da ragunan da kayan
mai jego da na yaro sannan ga kayan abinci. sun
samu anty a gidan,ta musu tarbar mutunci.da
yake abba xana waya da ita,ya fada mata komai
ta sani.hjy zainu da taji kukan raguna ta fito,anty
tace dan Allah momy kada ki musu magana,kin
ga shi da abokansa ne.da qar ta samu ta turata
sashin ahj,shi kuma murna yayi yace aje a daure
su.zainu tace ahj menene na numa farin ciki sai
kace ba ma cin nama?can ba xa a ka kada ba
dan kawai shagalin sunan, sannan tace harda
shinkafa suka kawo sai kace muna yunwa? nana
take ya hade rai tare da cewa,zainu kada dai ki ce
min kin sa an dawo da yarinyar nan gidan ne dan
ki kashe mata aure?tace haba dai. ya ce to hir
dinki dan bansan in kuma jin irin xantukan nan
yayi ma matarsa daidai arxikinsa. mu kuma mu
ma yarmu da jikanmu gwargwadan arxikinmu,in
ya fito daga gun mai jegon ki turo min shi,sbd mu
ji in da xa a yi sa sunan.tace ina xa ayi in ba nan
ba?ya dube ta an taba haka?ki dai turo minshi.ta
taba baki sannan ta wuce.lkcn da ta leqa dakin
abba da abokansa suna xaune,abba yana ta fama
da danne dannen waya,domin tun da suka shiga
ya qi ko kallan inda bishira take bare danta.tace
bishira ki eada musu in sun fito ahj na san
magana da su.ta wuce ba tare da jiran jin amsa
ba,ko amsa gaisuwan da abokan abba suke mata
bata yiba.bishira ta kalli abba wanda tana
hankalce da shariyan da yayi mata,tace kaji abin
da momy tace?sai lkcn ya dubeta me tace? yayi
maganar ne cikin tsare gida.dadynmu yana san
ganin ku. bai amsa ba,sai kurun ya tura mata
jakar kayanta,ki duba,ta xaxxage dinkuna ne na
gani na fada masu kyau,duk da xannuwan ba
masu tsada ba ne kala uku atamfa daya shaea
daya sai kuma leshi.sai ko kayan yaron.ta dube
shh an riga an sai mana kayan fitar
sunanmu.ahmad ya dube ta wannan din baki so?
tace ni bance ba.abba yace ku tashi muje.tace
ina san magana da kai.ya ce kiyi
maganarki.muktar yace kuxo mu fita ta dauki
yaran tare da miqa mashi ta ce ina lura da kai
rabon da ka dauke shi tun randa aka
haifeshi,alhalin mu kuma yana nan yana hana mu
baccin dare.kai kana can kana baccin ka.ta fadi
haka ne cikin sanyin murya.ya amshi dan tare da
cewa ai gara ya hanaku bacci tunda kunqi ku
kaishi gurin babanshi.ya tsura ma yaran ido,wata
qaunan dan ce take shigarsa.ta matso
jikinshi.abba ya kalli furkarta,ita ma kallansa
take,ta ce yanxu ko dan murmushin ka bana
gani.yace,in da kina san gani da baki dawo ghda
ba.yaci gaba da cewa na sha mamakinki
bishira,da har xa ki yarda ki dawo gidanku ba da
ixinina ba. kuma tun kafin ki haihu sai da na fada
miki ba za ki zo gida ba.Ta ce To Abba mony ce
ta ce sai an zo. Ya ce shi kenan ku zauna. ya
mike mata yaron ta amshe shi ta kwantar ta
kama mishi hannu. Abba wane suna ka sa masa?
ya ce Sunan Alhj babba. Da sauri ta saki
Hannushi . Sunan 'yan da? ya kalle ta Na zaci
zaki ce suna mara ma'ana,tund da ne da sauki.
ya fice. Haushin hali irin na Bishira ya ke ji.dn
son shi yasan tana matukar sonshi,amma bata
son yin biyayya ga abn d yake so. Ya samu su
Mktr sannan suka shiga gurin Alhj ya tambaye su
in d za a sa sunan,Abba ya ce a masallaci kusa d
gidn babnshi ne za a yi addu a. Amma tuni an sa
wa yaro suna Sulaiman.sunan babana. Alhj ya ce
Madalla Allah ya raya mana shi, ba sai mun zo
ba dn yanayin sanyi ne. Nan dai Abba d
abokansa suka tafi suna yabn Alhjn. An ci sunan
shima Abba shi d abokansa sun yi walima da
Azahar. matar abokinshi Bala ita ce suka bai wa
girkin ta yi masu. Mai jego taci gaba d wnk. Abba
kan leka su lkc zuwa lkc,kusan dk lkcn d yaje ba
su cika rabuwa d dadi ba sbd mgnr d hjy zainu kn
datsa mishi. Umma shi ma bata yi fushi ba tana
leka su dk d rashin sakar mata fuska d mai jegon
tare d mahaifiyar keyi. Ummi tana tafe tana 'yan
tsince-tsincenta,kmr yadda ta saba,sai ko taga
sim,take ta yarda dk wani abu d t samu t dauki
Sim din. Gefen zaninta t samu ta kulle,sannan ta
tafi,cikin jakr mkrntrta t saka.wata rana ta dauki
wayar umma ta shige daki,ta bude wayar ta cire
sim din ta saka wanda ta tsinto a cikin zani ta
soke wayar ta fito soro.Jikin dakin yaya Abba a
bakin kofar ta dauki lamar Abba da ya rbt sbd
masu zuwa nemanshi tana kira taji wayr tana
ringing. Ta kashe tana ta dry,hk tayi ta yi wa
Abba Flashing dg nan tayi gidn du Amina
kawarta,tana ba wa Amina lbrn abn d ta ke wa
Abba. Ta ce Amina nsn yanzun hk yana cn yana
jin haushi,shi yasa ki ka ga ina murna.Ta ce in ya
gane fa?Ummi ta ce Ai tsintar sim din nayi,Umma
kuwa ba za ta san na dauki wayarta ba,domin
yaya Abba da Alhjnmu kawai suke kiranta. Amina
ta ce Yadda za a yi ki kira shi ne in ya dauka sai
ki make murya ki canza suna. Ummi ta ce Tab,dn
in ci duka. Amina ta ce Dalla cn gane ki zai yi?
suka kira ya daga ummi ta sirantr d muryarta
tana fadin "Hello! Abba ya ce Ke wace ce ki ke
kiran layina? Ta ce Sunana '"Suhaila. ya ce
Menene ki ke kirana?Ina ma ki ka samu lambata?
Ta ce Gani nayi ni ma a cikin wayr. Tsaki yaja
Sannan ya kashe.Suka dinga tsuntsira dry. Amina
ta ce Sake kiranshi ki ce ma ke a kaduna ki ke.
Ummi ta ce Kai yin waya akwai dadi ni ina son
buga waya. Ta sake kira cikin Zafin rai ya ce Ke
lfy??kin dame ni fa!Ummi ta ce To tsaya mana
kaji ina son mu gaisa ne ni ina kaduna ne. Ya ce
To na gode. Sai ma ya kashe wayar gaba daya
suka yi ta kira a kashe. Tun daga ranar Ummi ta
samu in umma tana aiki ko tana bacci sai ta sace
wayar ta cire sim tasa nata ta kira Abba. Tun
yana kyararta hr ya daina ya koma rokon ta
daina kiranshi,dk a banza. Daga baya sai Abba ya
soma sauraronta, ranar kuma ta kira shi ne
misalin dayan dare,ranar taki zuwa dakin
Tsohuwa ta kwanta a dakin umma. umma kuma
dama dakin Alhj take kwana. A dai-dai lkcn ya
kwanta kadaici ya dame shi,ga garin yanayin
sanyi. wayar ta katse tunaninshi d yake yi na
matarshi zuwa yanzu ya haddace lambar Suhaila.
Ya daga ya ce "Hello ya ce Ke wai me ya hana ki
bacci?Ta ce Ni ba sunana ke ba,Ni sunana
Suhaila,kai fada min sunanka. Ya ce Abba Ta
danne dryr d taso kwace mata ta ce Abba ba
suna bane,Fada mn sunanka n gsky. Ya ce "Idris
Yadda ya fadi sunan sai da ta dage kwarai
sannan ta maida dryrta. Ya katseta d cewa Ina
ku ke a kaduna?tayi dim,dn dai bata san ko ina
ba a garin kaduna ba,ba ta ma ta6a zuwa ba.
Take ta tuno Amina sun ta6a zuwa unguwar
Sarki,dn hk ta ce "Unguwar Sarki. Ya ce, wai
shekaranki nawa? Ta ce Sha takwas. Ta sheka
masa karya.Ya ce Amma shi ne a ka ba kiwaya?
ta ce ta ka san wanene Babana? Ya ce A"a ta ce,
To shi ne mai bawa Gwamna shawara a jihar
kaduna. Abba ya ce Lallai, ki ce in nazo kawo
miki ziyara ba zan samun ganinki ba? Ta ce za
ka ganni mana. Ya ce To zan zo. Ta ce To, Ya
ce,Amma fa ina d mata ta haihu ne ta tafi
wankan gida. . Ummi ta ce Lallai to sai da safe.
Ya ce, Wa ke zuba miki kudi ne cikin waya?Ta ce
Babana mana. ita sai lkcn ne ma ta tuna cewa
ana saka kudi tunda ta ke kira bai taba kin zuwa
ba,aranta ta ce kila wannan ba a sa kudi. Sunyi
Sallama babu dadewa,wayar ta sake daukar
tsuwwa. Ga zaton Ummi Abba ne sai da ta daga
sannan taji muryar wani. Ya ce Da wa nake
waya? ta ce wa ka ke nema?Ya ce Me wayr. ta
ce Ummata ce kuma tayi bacci. Ya ce Yallabai
nake nema. Ta ce Ban san wani yallabai ba,kada
ka dame ni Ta kashe wayar tare da jan tsaki.
Sannan ta cire layin ta maida na umma Wasa-
wasa cikin kwanakin Abba ya soma damuwa da
lamarin Suhaila kaduna, lokuta da dama ya kan
kira layinta amma sai ya ji shi a kashe. Sam ba
ya samunta sai lkcn d ta kira shi,ko da ya yi
mata korafin hk,sai ta ce "Eh ita ce ke kashe
layin sbd ana damunta. Sun yi jarabawar (J. S.
C.E.)sakamako suke jira. dn hk yanzu tana gida
ko yaushe tsokana kuwa bata fasa ba. Kullum ita
d Amina cikin shirya yadda za su yi wa Abba
waya suke, kudin cikin layin ya kare,Abba shi ke
tura kati yanzun. Duk lkcn d Abba yazo gidansu d
ya ga ummi ya hade rannan yana muzurai,ita km
sai ta yi ta sheka dry,dmn tana tuno yadda yake
kwantat d murya a waya. Wata rana hr duka ya yi
mata sbd dryr d ta dinga yi daga sallamrshi a
gdn. Tsohuwa kam ranar yini tayi fada,wai ita za
ta bar gidan.Cin kashin d ake yi wa ummi ya yi
yawa. A ce rashin 'yancin yakai ko dry ba a son
tayi. Da kyar umma ta sha kanta t hkr. Wannan
ta kaicin dukn yasa ummi tace ita kam sa tasa
shi wahala. dn hk ranar gdn su Amina taje. suka
shirya yadda in ta kira shi zata ce yaxo Kd ta
ganshi, ummi ta ce mugu dama in yaje ya 6ace in
huta. Hakn kuwa ta fada mishi, a ranar d suna
waya. Ta ce '"Idris.dn Allah yaushe za ka zo ne?
Ya ce Tun yaushe Suhaila nake cewa zan zo
amma kin ki,to yanzun yaushe zanzo? ta ce kazo
Juma'a ya ce A"a zan dai zo Asabar,Juma'a
rabin rana ce. Ta ce,To sai kazo.Nan d kwana 4
kenan?ya ce Insha Allah,sannan ina son ki toro
min da adireshin dn gdnk,sannan ranar d zan zo
ki bar wayarki a kunne. Ta ce To." Ranar Asabar
misalin goma na safe Abba ya shigo cikin sabbin
kaya,ya yi matukar kyau tamkar sabon Ango.
Umma ta ce za ka je gurin su Maigida ne?Ya ce
A"a umma koda yake zan bi ta can.Kd zan je.
Umma ta rike baki "Kd,? Me a ke yi?ya ce sai na
dawo za ki ji.Ummi d ke wanke-wanke ta kwashe
da dry. Umma ta dirma mata dundu tare d
cewa,Ke wai ciwon dry ne y kama ki?Abba ya
dubeta cike da tsana. Ummi ba za ki shiga
hnklnki da ni ba?ta sunkuyar da kai tare d maida
dryrta ciki. Sannan ta ce Yaya Abba dn Allah ka
siyo min biredi,wlh biredin Kd dadi ne da shi.
Lkcn d Amina suka dawo ta sammin. Ya galla
mata harara,tare d fadin an ce miki nima bakauye
ne irinki?In ma ki ka sake min mgn sai na gabje
ki. . Ya kalli Umma Kada ki ce ma Alhj nayi tafiya
amma in na dawo zan fada masa. ta ce ,To" Allah
ya tsare. Abba ya fita. Ummi tana gama wanke-
wanke ta shige daki dn yin gyaran gado. Umma
na shiga kicin itama ta fito falo ta ciri wayr a caji
taje ta saka sim. Take kuwa kiranshi ya shigo, ta
daga ta matse murya kamar yadda ta saba, ka
taso ne? ya ce Ina mota mun kusa tasowa. Ki
turo mn adireshin. Ta ce Ba fa wahala,d kun
sauka tasha sai ka ce a kawo ka unguwar sarki
gidn mai ba Gwamna shawara. Ya ce Suhaila ma
su ba Gwamna shawara d yawa Ta ce Um to ai a
nan unguwar Sarki shi daya ne. Ya ce Ya sunan
layin?ta ra sa me zata ce,gabnta y shiga
faduwa.Ta samu kanta da cewa, Abuja Ya ce
Abuja kuma Suhaila?ko dai Abuja road? Ta ce Eh
gida mai lamba 6. ya ce To zan ci gaba da kiran
layin. ummi ta ce To," Ta zauna tana sauke
numfashi. Tab da ya dogata d ta bani,Sannan ta
saka dry murna take yau yaya Abba zai sha
wahala. Jefi-jefi ya kan kira ya ce sun zo gari,dk
lkcn d ya kira in ta ji ringing sai tayi bayi da
gudu, har Tsohuwa da suke zaune tare ta ce, ke
takwara gudawa ki ke ko atini ne? Ta yamutsa
fuska, sannan ta ce Bacin ciki ne. Tsohuwa ta ce,
To taso uwarki ta baki magani. Ummi ta ce ya yi
min sauki ma. Can kuma masu kiran layin suka
kara kira. Ummi tayi kofar gida ta daga wayar a
ka ce ke ina ki ka samu wannan wayar? Ta ce
Oho 'yan rainin wayau kada ku sake kirana. Ta
kashe wayar ta koma gida. Lokacin da Abba ya
ce sun shiga KD har ma sun kusa sauka, sai ta
cire layin ta ci gaba da harkokin gabanta ta
manta ma da labarin wani yaya Abba. KADUNA
Abba suna sauka a tashar kawo, ya sauka ya
shiga raba ido yana kallon garin kaduna. Yau ce
rana ta 2 d ya ta6a zuwa KD, daman sun zo
daurin auran wani abokin su bara waccan. Ya
kalli wani dan aca6a sannan ya yafito shi da
hannu. Ya iso yana cewa Ina za ka? ya ce
Unguwar Sarki. Dan aca6a ya ce Wane layi? Abba
ya ce Abuja Road. Ya dubi Abba Rigasa kenan,
unguwar Sarki babu layi mai wannan sunan.
Abba ya ce, Ina zuwa, bari dai in kirata. Koda ya
kira layin Ummi sai ya ji shi a kashe, yana ta kira
a kashe. Ya dubi dan aca6a ya ce, Kasan gidn
Mai ba Gwamna shawara? Dan aca6a ya ce, Hau
dai muje sai mu tambaya. Abba ya hau mashin
yana mai ci gaba da nemn layin Suhaila. Sun
zagaye unguwar Sarki layi-layi suna tambayar
masu gadi da 'yan dai-daikun mutanen da ke
giftawa kasancewar unguwa ce ta manyan
mutane, daga karshe dan aca6a yaba Abba
shawar ya tafi gida kawai. Don haka sun gama
zagayen unguwar Sarki har da makotanta, amma
ba su samu ba. Gida daya ne aka ce musu da
akwai Suhaila, amma yarinya ce ta goye. Kusan
karfe 3 sannan suka koma tasha,ya biya dan
aca6a, sannan yaje ya yi sallah. Zuciyarsa cike
da takaici sai yanzu yake Sallah. gashi ya kasa
samun layin Suhaila. kila ma tana sane ta kashe
wayr dn kawai ta tazarta shi. Ya tuna d zagin d
wani mu2m ya masa lkcn d suka tambaye shi ko
ya san ina ne gidan mai ba wa Gwamna
shawara? Mutuminya ce,mai ba Gwamna
shawara a kan me? Ma su ba da shawara suna
da yawa, ya sunan layin da ka zo? ya sunan mai
gidan? kama ina lambarsu? Abba ya ce, Lambr
kadai gare ni,km taki shiga.Mutumn ya ce,"Amma
kai soko ne,gashi kmar wayayye.Ya ja tsaki ya
wuce. Shi kanshi sai yanzu yaga wautarshi. ko
me ya kawo shi gurin yarniyar?Shida dai ba za
ya ce sonta ya keba,km ba ya ce ba sonta yake
ba. Wani ma ya zaci dn kudi ubanta yazo,shi kam
in ya koma shiru zai yi ko abokanshi zai ce musu
bai gane ba kawai,dn yabi ya fada musu lbrn
Suhaila,sun km san d batun zuwanshi gurinta
sarai,km yasan hlinsu za su maida abn na
tsokanarshi. Cikin matukar takaici suke tafe cikin
motar kaduna zuwa kani,sun zo kwanar Dangora
tsautsayi ya akfa musu. in da tayar motarsu guda
ta fashe. . Nan take motar ta bar hannunta ta
mulmula da su suna ta salati,nan aka kwashe su
xuwa asibiti.wasu sun mutu take,wasu sun yi
dogon suma.masu waya ta cikin wayarsu aka yi
ta kiran yan uwansu,shi ma abba a cikin wayarsa
aka kira lambar ummanshi da alhj da sauran su
aka shaida musu cewa mai wannan layin sun
samu hadari,kuma an kawo su asibitin mlm
aminu kano yanxu.iyakan rudewa su umma sun
rude,tsohuwa kam take cikinta ya kada ta soma
xagawa bandaki tana kuka tana face
majina.ummi bata gidan tana can gidan su amina
suna ta hira suna cin dariya ,tace bari in je in
qara sa layin in ya kira sai ince wayata chaji ne
sai yanxu nayi.sadaf sadaf ta shige daki,kan
kujera taga wayar,ta dauka ta saka sim din ta
cire wancan. tana kunnawa sakuna suka soma
shigowa. kafin ta bude ta duba sai ta jiyo muryar
tsohuwa cikin kuka tana cewa wannan yaro ashe
ajalh ne ya kira shi,ko me xashi yi kaduna?ni ban
sani ba.ummi ta fito da sauri tana cewa,tsohuwa
me ya faru?tace ba kina can gun yawanki na
tsiya ba.Mai sunan mlm da ya tafi kd sun tafka
hadari, yanxun haka suna asibitin mlm. ana xatan
shi ma ya mutu.ummi ta saki ihu,sam bata san
ta damu da dan uwan ta abba ba sai yau,ko tana
kukan ita ce sila?oho.kafin kice haka,lbr ya watsu
a unguwa abba ya mutu.cikin kuka ummi ta
tambayi tsohuwa ina ummata? tace tare suka
nufi asibitin da ummarku.taqi yarda ta jira
su.ummi tana jiyo ihun kukan umman bashir ta
xaga gidan.gidan ya rincabe da kuka,ummi fa
hankalinta ya qara tashi.matarsa ta iso da kuka
da yan uwanta a motoci.yayyantamaza suka nufa
asibitin.can kusan qarfe takwas su alhj suka
shigo.alhj ya ba mutane haquri,ya ce bai mutu ba
dogm suma yayi.kuma Allah yayi taimako ba
karaya.likitocin sunce xast duba shi xuwa gobe
su gani.nan ko jama'a suka dinga fadin
alhamdulillah.ummi ma tadan ji dadi a
ranta,sanna fa kowa ya tafi dama wasu sunce xa
stje yin sallah su dawo.saida suka koma sannan
suka taho da umma,ummi cikin kuka tace umma
da gaske bai mutu ba, umma tace eh bai mutu
ba,muyi magana dashi. . Umma tace in sha Allah
gobennan xai dawo gida. ummi tace to,umma
tace kinga wayata? gaban ummi ya fadi ta tashi
da sauri ta shiga neman waya,taci sa'ar ganin
wayar,sai dai bata san inda ta saka sim din ba
sai wanda ta tsinto ne a ciki.ummi dai tayi shiru
ta miqa ma umma waya. kusan qarfe goma sha
daya wayar abba da umma ta taho da ita ta
soma qara,umma ta dauka.alhj ne ya ce ina
wayarki ina ta kira ana cemin a kashe?una tace,
a ku6e take gata ma a hannuna.yace to inata
kira.tace qila faduwan da tayi daxu ne ta samu
matsala.yace to dama zance ne ki dafa masa
ruwan xafi a xuba a flask dan uwan matansa xai
kawo mu yanxun a mota xai amsa ya kai.ta ce to
alhj wayn xai kwana gunsa?yace bashir na nan
kuma matarsa anyi anyi ta qi tafiya shi yasa na
haqura xan dawo dan ba na xauna gun su ba ko?
umma tace amma yaya jikin nashi?ya ce da sauqi
yanxu ma yana son shan tea ne.tace to xan hada
harda wayar tasa inya so ma dunga kiran shi
kafin gari ya waye.ya ce yauwa ki
bada.Alhamdulillah abba jiki ba matsala. Don hk a
ka sallamo shi zuwa gd.kai tsaye gdn su umma a
ka wuce d shi. A salin dakinsa a ka gyara a cikin
kwana nan 3 ya yi ras sannan ya koma shago.
Bishira kuwa lkcn mahaifinta ya ce maza ta koma
dakinta,tunda ga abn d ya samu mijinta.Sun
dawo hr da tafkeken injin Janareto wai yaron ba
ya son duhu. Sannan ga kayan kallo d
saraunsu.TabbasAbba ya ji dadin dawowar
iyalanshi,dn dama yana cike d bukatarsu. Ranar
yini suka yi gyaran gd ita da 'yan uwanta,sai byn
magrib sannan ya shigo d tsarabobi.madara
tatacciya da kaji. Ya dauki dansa cikin jin dadi
yana kallonta cike da so da kauna,Nayi missing
din ku da yawa.URFIN CIKI book 2 part 3
ZURFIN CIKI book 2 part 3
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:08
Ai bama shiri. shi ne fa ya kawo ni mkrntr kwana
dn kawai baya son ganina. Suka yi ta mamaki.
Can jimawa ya dawo, sun fito rakiyar 'yan
uwansu Safiyya da na Khadija, suka ganshi tsaye
yana danne- dannen waya. Ya taho ya gaida
iyayensu duka,sannan suka koma gefe d ummi,
ya ce Ni ma zan tafi. Ta ce, Ya Abba ko fa
gaisawa ba mu yi ba. Ta karkatar da kai,Cikin
raunin murya tamkar mai shawagaba,ta ci ga ba
da cewa Ya Abba su Umma ba wanda ya ce a
gaishe ni? Sai hawaye suka soma zuba.
Hankicinshi da ke hannunta tasa tana sharar
kwalla.Abba yana da matukar tausayin mace. Don
haka duk da tsanar da ya yi wa Ummi sai da ya
tausaya mata.Ya tausasa Murya. Sun ce in
gaishe ki sosai, za ki ga gyada mai gishiri,
Tsohuwa ta ce a ba ki.Umma ta miki miya, ta
kuma daka miki yaji. Ta ce Na gode, Alhj me
yasai min?ya ce kayan tea ne da lemun kwali. Ta
ce Na gode. Tana ci gaba da share hawaye. Ya
mike Zan tafi. yasa hannu cikin aljihu ya ciro kudi
ya mika mata, ta ce A'a ya Abba ka bar kudinka.
Ya ce Ba ni ne na baki ba,Alhj Karami ne ya ce in
ba ki. Ta sa hannu 2 ta amsa tare d godiya.Sun
raka shi kusa da Gate ita da su khadija,sai kuka
Ummi ke yi. Bayan sun dawo dakinsu ne ta zauna
tana duba kayan da ya lissafo mata,duk ta gani.
Sai kuma saitin sabulun wanka da manshi da
turaransa da hodarsa duk na (Aloe vera.) Shi
kuma bai fada mata ko daga wa ba,ko ba komai
ta dai yi murna sobada tana da 'yan kuraje a
fuska,tasan kuma za su mutu. Sai kuma audagar
mata,tayi dan murmushi. . Tunda Umma taji
sallamar Abba ya shigo dakin ta bar komai tazo
ta zauna tana son jin lbrn Ummi. Abba ya fahimci
Haka,dn haka sai ya boye mata cewa, Ummi na
kuka hr yanzun. Ya nuna mata ai Ummi ta
kwantar da Hankalinta,km tayi hnkl dn ya bincika
ya ji ana ta yabonta. Umma taji dadi Sosai,Sai da
ya fara zuwa gurin Ummu,sannan ya je gida.Ya
samu Bishira tana zaune tana aikin nata,wato
Kallo. Tun da ta dawo daga wankan gida tazo da
janareto da kayan kallo,shi kenan ta sanu abn
yi.Kullum tana gabn (TV)da ta shi da safe in ta
kokarta shi ne ta dafa ruwan tea ko wanka ba za
ta yi wa dan ba,sai lkcn d man injin ya kare. Ya
nufi gurin injin ya kashe,dif din da ta ji komai ya
tsaya shi ne yasa ta zabura ta mike tana fadin
Ba dai har man nan ya kare ba? Ta fito da niyar
dubawa.Abba ta gani tsaye gabn injin yana bn
tsakar gidan da kallo cikin takaici. Ta ce Baban
Walid kashe min injin kayi??Ya ce Eh na kashe dn
Allah dubi gidanki?kalli wanke-wanke kuda na bi
dubi tulin wankin kayan Fitsarin yaronki. Dubi
kicin dinki,kuma ko da bn shiga dakinki da
wannan falon da ki ke kallo ba.na tabbata da
wanda ki ka dauke ko tsinkw a cikin sa.Kila ma
ba ki yi Sallah ba. Ta ce Dan karashe ne fa ya
rage min in gama kallon in zo in yi aikin.Haushi
ya sake kana shi,Sai kurum ya shige daki.
Tsakuwar da ya dora kafa a kai tasa tsigar
jikinshi tashi,sam ya tsani ya shiga daki ya dora
kafa kan datti. Ya dawo yasa takalmanshi ya
shiga da su,Walid yana kwance tun kayan da ya
bar shi da su da safe sune a jikinshi yana ta
bacci cikin fitsarin da ya shafka wanda ba wata
leda da zata hana katifar ta jike. Ko wankan safe
ma ba a mishi ba kenan.A fili ya ce,",Inna lillahi
wa'inna ilaihinr raji'un. ya juya ya nufi shagi. Ita
kam sai ta kunna injinta ta karasa kallonta,
sannanta tashi ta dora girki.sai lkcn ta ma Walid
wanka. Ta dan dauraye kwanukan da za su ci
abnci,wai ta gaji sauran wanke-wanken sai gobe.
Fati ta shigo,Bishira ta ce Yauwa Fatima naji
dadin zuwanki.shuga dakina ki gyara min gado,ki
dan yo min shara. Fati ta ce To. Ta shiga ita ma
duk shegiyar darin ce gurin kuiyar aikin,dn haka
ta dan birbira ta fito ta ce ta gama. Bishira ta ce
Yauwa dan dauraye min kaya can na Walid. Nan
ma tasan sama ta shanya. Bishira ta ce Yauwa
ta ga abnci nan kici.sai ki dauki na Ummarku ki
kai mata. Har Fati ta kai waje,Bishira ta kwala
mata kira. ta ce,Zo ki tafi da wannan galan din
na man fetir kije shagon Babn Walid kice ya taho
mana da shi,dn man ya kare. Koda Fati ta same
shi da galan ta fada mishi sako ya ce Ba zan siya
ba,Maida mata galan din. Ta tafi,Shi kuma ya ci
gaba da mita a zcyrshi. Yana fadin Na daina
sayan man tunda ba za a bari sai dare a kunnan
ba.Gidan Ummanshi yaje,ba ta nan ma taje
barkar Haihuwa. Ko dakin Tsohuwa bai shiga
ba,ya zauna nan falonta.Ya za kula ya zuba
abncinshi ya ci.sannan ya dan huta sai ya fita
zuwa gidan su Ahmad. Cam ya samu wasu daga
cikin abokanshi suka shiga hira. Ranar dai Abba
bai je gida ba sai misalin sha daya ko daya shiga
bai nemi matar gidan ba,ya dibi ruwa ya yi wanka
sannan ya shiga dakin. Ya lalibo makunnan wuta
ya kunna,dn Nefa sun kawo wuta. Tana kwance
irn banzan kwanciyarta da ta iya,dakin sai tashin
wani irin wari yake kamar na ruma,kamar na
fitsari ko na datti.Ya kalli ko'ina kullin kaya ne na
wanki ne,na gaga ne ciki da guri.Ranshi ya
baci,Ya kuma dubanta ga wata kiba da ta tafka.
Tun da ta haihu ta zama rusheshiya,gashi bata
son kama jikinta.Tsaki yaja,sannan ya dauki fiko
ya fita. kan doguwar kujera ya jefa filo,ya kwanta
a gajiye.Amma me?sai ya ji dora gadon bayansa
acikin lema.Da sauri ya mike ya kunna wuta.Duk
fitsarin yaron ne a kan kujerun dakin,dn haka sai
ya nufi dakin da takw aje tarkace ya kunna
wuta,shi ma dai duk shirgi. . Ya share Ya
shimfida ta barma ya kwanta,a ranar ya dauri
aniyar maida dakin ya zama nashi din-din-dn.
Don haka washegari yasa a ka zo a kayi masa
fenti,ya siyo kati fa ya yar da zanin gado,dk wani
abu nashi sai da ya kwashe su. Kafin wata guda
ya maida dakinshi cikakken daki,ya zuba dk wani
abu da yake bukata. kafin ya fita kullum sai ya
gyara dakinsa fes. ita kuma sam bata zuwa
dakin,sai dai in yana da lalura yaje can ya sauke
ya dawo. kazantarta kam ta kai in da ta kai,tunda
hr kayan kashi tana zube su a cikin daki. Ya gaji
yaje ya samu Anty ya fada mata,hr gidan Anty
tazo ta zazzageta,ta tasata suka gyara gidan,
amma ko a jikinta.Washegari ta ci gaba da in da
ta tsaya. Sam babu wanda zai ganta ya ce
haihuwarta daya. ¤¤¤¤¤¤ ¤¤¤¤¤¤ UMMI yau
ba wanda ya kaita murna,domin yau dai an basu
hutu..Sai dai tunaninta zata ko iya kai kanta
gida? Sunyi ban kwana bata da kudin mota, dan
duk tayi taba su safiya kudin gurinta, amma ta ce
yau ko da qafa ne xata gida.sun fito wajan mkrt
wata maryam tana cema,ki tsaya mota xato da
xata kaimu cikin kn.ummi tace baxan jira ba.sai
ga abba kamar daga sama,tsoro ya kamata karya
ce ta xauna gidan abokin sa da yace.hanka linta
ya tashi cikin in ina ta gaida shi ya amsa.ya
shiga mkrtn jim kadan ya dawo.hakan ta sha
alwashin yau ko da shiya saita je gida.shi kam
ma ya manta yai mata wannan maganan ma.ya
sabi akwatinta suka je suka shiga mota. abba
mamakin natsuwan ummi yake yi, ko da yake
baxai ce ta natsu ba, qila lafawa tayi.tundaga
soro ta saki jakanta da bokin tayi ciki da
gudu,cikin kuka tana kiran ummanta.umma ta
share do min tsohuwa tana cikin gida,kada tace
tayi rashin kara,sai tsohuwa ne ta tashi da sauri
tana fadin oyoyo takwara.suka qungume juna
tace to menene kuma na kuka?umma ta fito nan
fa ummi taje ta rungume ta.sai umma ta doje
tace bubi shirme,sakar ni ni.tsohuwa tace haba
suwaiba yarinya tana dokin, . Tsohuwa tace haba
suwaiba yarinya tana dokin ganinki amma ki
gwasale ta? abba ya ce daman nasan ba
natsuwan da yarinyan nan tayi,har ina
yabonta.dubi yanda ta xubarda kayan a soro.to
xaki debo su.tsohuwa tace bari ni in debo mata
tunda kai baka da tausayi.laile umma taga
canji,do min ummi dai tunda ta dawo ko qofar
gida bata fita ba,sai ko in an aike ta.sannan
yanxu ba gudu da tsalle tsalle bare tsokana.ga
aiki har girki ita kema umma komai.alhj yana
shan shayi da safe,ummi ta yi sallama ta shiga.
can gefen su umma ta xauna,sannan ta gaida alhj
ta gaida umma wanda ta saka alhj agaba tana
masa fira.wannan qa'idan umma ne bata barin
mijinta shi kadai,in har yana gida.alhj yace
suwaiba kinga ummina ko?laile abba yayi namijin
qoqari. yarinya ta natsu.umma tace Allah ya
amsa addu'an mu ka duba tsayuwan daran da
muka dunga yi bayan tafiyan ta kan cewa Allah
ya kintsa mana ita.alhj yace hakane,ummi dai na
jinsu tana murmushi.can tace alhj anjima xanje
gidan inna saratu in gaishe ta. qanwan sahura ce
da ke aure a kabuga.ya ce to ummi, xanba
umman ki kudin mota ko? ummi ta ce,to na
gode.ta miqe ta fita ta bar mahaifanta cikin farin
ciki jin dadin natsuwarta, suna godiya ga Allah
mai shirya bayinsa.lkcn da ta shirya dan xuwa
kabuga.sai umma tace ki kwana dan bana san ta
fiyan yamma,kabuga da nisa.tace to sannan ta
dauki kayanta kala guda, sannan ta fito.har xata
wuce sai ta shiga gidan alhj qarami,sahura na
ganinta ta hade rai,daman daqar take amsa
gaisuwan ummi tunda ta dawo.ummi ta gaisheta
a ciki ta amsa,sam ummi bata damu ba,tace
umma ina fati?ta yatsine baki tace tana gidan
abba,tace to inta xo ki ce mata naje kabuga sai
gobe xan dawo.umman bashir tayi tsaki,tare da
cewa ni yar aiken ki ne?ita dai ta wuce.tun
dawowan ummi suke shiri da fati kamar me,ko
yaushe suna tare suna fira.ummi tana mata
labarin mkrtn su.ita kuma fati tana bata lbrn
saurayin da tayi fahad,da irin son da take
masa.ummi tace tab,ni ko xanyi saurayi nafi san
irin ya abba...... . fati ta dubeta da al'ajabi kina
nufin ya abba kike so?ummi ta xabura tana fadin
tir, ko a mafarki Allah ya kyauta.ina nufin mai irin
hirarsa da tsafta.fati ta qyalqyale da dariya tare
da cewa ai na xaci shi kike cewa,inko ya ji kici
duka ummi ta ce,ai ni ba ma da shi nake ba
tab,shi da yayi auran so?kusan ko yaushe
yanayin hiran tasu kenan.ummi tana tafe
wadansu samari suka yi ta binta, sun shawo
kanta ta tsaya da kyar,kuma har ta masu
kwatancen gidansu. kwanaki uku bayan haka tana
ki shingide kan kujeran dakin umma,misalin
takwas saura ma dare.krtn wani littafi take yi na
hausa da fati ta ara mata,sam ita bata taba krnt
irin littafin ba,amma fati ta ce mata ta karanta da
dadi sunan littafin NAGA TA KAINA na
(sodangi).kasance wan wannan ne karo na farko
da ta taba krnt lbrn soyayya,sai abin ya
birgeta.amma nata ganin gwarxon sojan nan xai fi
dacewa a ce abba ne, jefi jefi takan kalli abba da
ke xaune kan kujera kusa da umma suna wani
xance da bata jiyo su. 'Amma tasan ko me suke
tattaunawa mai mahimmanci ne a gare
su.sallamar wani yaro ne ya katse su,umma da
abba suka amsa mishi a lkc gudu.yace wai ana
kiran ummi a waje inji wadansu.da sauri abba ya
kalla yaron,sam ba xai ce me yasa xance yaran
ya fadar masa da gaba ba.sai ya lumshe ido
sannan ya kalli ummi wadda kunya ta rufe
kasancewar yau ce rana ta farko da aka soma yin
sallama da ita.umma wadda kullum fatanta ummi
ta samu miji,sai tayi murmushi,sannanta ce da
yaron kace tana xuwa.abba ya dube ta da sauri,
umma kin san ko su waye?ta ce, a'a.yace ya
kamata a san ko su wanene dan kin san bata da
kan gado,kowa ma sai ta jajibo kuma ma duk
nawa ummin take da har xata soma tsayawa da
samari?umma tace,to abba ai gara ta kama
dahir, tana qare sakan dire ba sai ayi mata aure
ba?yace gaskiya umma gara ta dan taba krt,dan
yanxu xamani ne na krt.umma tace,tayi acan a
dakinta.ta dubi ummi tasgi kije.ummi ta miqe ta
fita.abba ya miqe shi ma,umma bari dai in gani
ma su kamun kai ne? umma tace to.., . Sun
gama gaisawa kenan sai ga abba ya fito.ganinsu
tsaye da ummi sai ya tsinci kanshi cikin wani
bacin rai.ya isa gun ya musu sallama, suka
amsa, sannan suka gaisa.yace daga ina kuke?
suka dube shi dayan ya ce lfy dai ko? ummi tayi
karaf ta ce yayana ne.anan suka sake gaida
abba.bai amsa ba, sai ma cewa yayi na tambeye
ku kai ma kana tambayana,wai lfy? suka ce,kayi
haquri,nan suka gabatar da sunansu.mai san
ummi shine nazir, abokinsa kuma sagir. sun 3a
masa cewa dukkansu daga kabuga suke.yace krt
kuke ko kasuwanci? sagir yace,eh krt muke,amma
muna taba kasuwanci a shagon mahaifinsa da ke
kwari.abba ya dan yi jim,sannan yace to kai ka
shirya aure ne?nazir yace eh to, nasan dai kafin a
tashi yi mata aure na shirya.abba ya ce, to ita
kam krt xata yi, kuma c ma buqatan ta hada krt
da soyayya. ya dubi ummi da fatan xaki sallame
su.ya juya gida.sagir ya ce, wannan wanki ne da
gaske? ummi tace qwarai kuwa. nazir ya ce to
yanxu ya kenan? kin ji abin da ya ce.ummi yayi
shiru tana tunani, ita fa basu kwanta mata rai,
tun randa ta hadu dasu,sam basu iya saka kaya
kalar yadda ya abba ke sawa ba.dan haka sai
tace, ina ganin xai fi mu haqura kada yaxo ni yayi
ta mun fada.nazir ya ce yanxun haka xaki ce?
ummi tace, um,sai da safenku.kada ku ja min
duka.sagir cikin jin haushi ya ce,ki xama
mangofak qarewan krt.sannan in kin gama wan
naki ya aure ki. ita dai ta shige gida.kusa da soro
ta iske umma da ya abba ta yo masa rakiya, tana
kuma ba shi aaki kan cewa yayi ta haquri,tace ina
fada maka ko yaushe ba fa fushi ko fada ne xai
saka matarka a hanya ba.lallashi da nashiha,ka
dunga koya mata giqki daka nutsu ka koya mata
ba gashi ka ce ta iya daidai gwargwado ba?abba
yace,hum lamarin yarinyan nan yayi nisa fa
umma,wankan jikinta ni xan koya mata? sallah fa
daga nake da ita.amma abin yaci tura.antynta
sau nawa tana xuwa tai mata fada duk a
cnxa,mkrtn ma ta qi xuwa.ni kuma da ce
ruwanta.umma cikin al'ajabi tace, sallah! sallai
ma bata san yi abba?abba yace umma baxan
mata sharri ba... Ta ce Tabdi,to kuwa ba kuwa
kazantarta ta wuce jiki hr d zcy. wannan ita ce
kazanta mafi muni. Don haka dole ne ka zage
damtse don ganin ta kama sallah,to menene
marabar arne d Muslmi in ba Sallah ba?Abba ya
ce Umma na mata nasiha na gaji. Ta ce To kasa
ta a mkrntr Islamiyya,kila ta ji tsoran Allah in
tana jin Wa'azi. Sannan ka dainga siyo mata
kasasuwan wa'azi.Abba ya ce Umma kaset nawa
na kawo mata bata sakawa,Kullum sai indiya da
Hausa fim,in naki sayan man fetur in tana da kudi
ta saya. In kuma ba a ta da shi sai ta dauki
ittafin Hausa ta dukufa.umma ta ce Allah ya
kyauta,kaje kayi ta hkr tare da addu'a. Ya kalli
Ummi,sannan ya ce ma umma,kada ta sake fita
gurin wadanan kananan yaran,sannan ya fita. A
daki umma take tambayar Ummi daga ina suke?
Ta ce um,Umma kyale su ni sam ma ba su min
ba. Umma ta ce to Allah dai ya miki za6i nagari.
Abba yana kwance a dakinsa ya yi lamo cikin
bargo,ya kasa amsa ma kanshi tarin tambayoyin
da ke yawo cikin kanshi. Haka tambayoyi suke
zuwa masa daya-bayan-daya ,me yasa ya damu
da lamarin Ummi??me yasa da a ka yi sallama da
ita ya samu kanshi cikin wani tashin Hankali? Me
ya sa ranar da zai je mata ziyara ya za6i ya sai
mata kayan kwalliya? A fili ya ce,don tana
kanwata.Zuciyarshi ta ki amincewa da haka. Me
yake shirin faruwa da ni ne? ya fada a fili. Ya yi
juyi zuwa rigingine,sannan ya dauki filo ya manna
a kirjinshi, ya ci gaba da magana shi daya. Bana
zaton cewa Son Ummi nake yi.don lkcn da na yi
tsananin Son Bishira bn ta6a samun kaina cikin
wannan yanayin ba. Kai Allah ya tsare ni da Son
ummi,wannan mahaukaciyar
yarinyar..........bugun kofarshi da a ke yi ne ya
katse shi. Murayar Bishira ce ta na cewa Babn
Walid!Babn Walid!! Ya bude kofar da sauri,ta ce
Walid ne ke ta amai. Ya fita ya dauki yaron daga
hannunta yana fadin Me zai hana shi amai,in ba a
ci sa'a ba har zawo sai ya yi,Saboda
kazantarki.Sam ba ki lura da me zai wawuro ya
tura bakinsa. Ta ce Yau fa bai ci komai ba,tun da
safe yake wannan aman.Ya ce shi ne ba ki sanar
da ni ba?Ya cire masa kayan jikinsa wadanda ya
ji suna ta doka karni.. . Ya isa igiyar shanya ya
ciri wasu yasa masa,sannan ya fita dashi.Wani
babban kyamis ya tafi da shi,mai kyamis din
likita ne,sai dai ba na yara ba ne,amma kowa
yazo sai ya duba shi.Nan dai ya masa bayani ya
ba su magunguna. Sha biyu dai dai ya dawo,tana
zaune tana kallo ya ce "A'uzubillahi,wai ke kallon
nan masifa ya zamarmiki ne?to ki sani na kusan
fita da kayan kallon nan. Ta ce,Tab,ka kaisu ina?
dadinta dai dafa gidan ubana a ka kawo su. Ya
ce ta za su koma gidan uban naki. Ta dafe kirji
"Zagina ka ke yi?ya dora mata dan a jiki "An
zage ki,ke din banza,kazama!yazube mata
maganguna ya fita. Ya jima zaune a kofar
gidanshi dafe da kai,yana tunanin shin wai shi
kadai ne bai yi sa'ar mata ba,ko kuwa duk maza
ne.Ya tuna abokanshi 2 da suka yi aure. Muktar d
Jamilu,sam ba su da wannan matsalar,duk lkcn
da yaje gidansu tsaf matansu,ga mutunci da
mutanta mutane. Shi kuma a cikin abokanshi
babu mai zuwa gidan sbd bata gainin kowa da
gashi. 'Yan uwanshi sai wanda ta za6a sannan
zata yi hulda da su. 'Yan garinsu kuwa can
¤ZAMFARA¤In suka zo kiri- kiri take nuna musu
kyama ga rowa,sam bata hulda da matan
abokanshi. Ya numfasa zai bi shawarar Umma ya
gani, amma gaskiya Bishira ba matar zama ba
ce. Tun da ya dawo sallarAsubahi dakinta ya
shiga tana ta shirga bacci. Walid kuma ya yi
faca-faca cikin kashi ya tausasa zuciyarshi ya ce
"Bishira! . Bishira!!Ya dan duki kafarta,sannan ta
tashi. Ya ce Ki tashi ki gyara masa jiki kiyi
sallah.Ta ce,Tab, me ya yi?ya ce, "kashi ya
yi.kurum sai ya ji ta ce Tab,wannan akwai dan
iskan yaro.Yanzun dan ubanka kashi ka min?
Sam bai san lkcn da ya watsa mata mari a baki
ba,cikin murya mai karfi ya ce "kada ki kuskura ki
sake ce ma dana dan iska!kar ki sake zagar min
yaro kada ki yi wa dana baki.Ba zan dauki
wannan ba. . Ta mike daga kan gadon tana kuka
Ni ka daka? wlh sai na rama. Kasancewar lebe
baya raina duka,sai jini.Nan da nan sai kumburi.
Ta cakumo shi,wlh sai na rama.Ya hankadata kan
gado ya bar gidan.cikin zcyrshi yana fadin
,"Wannan fitina da me tayi kama? Ita kam ruwa
ta dafa sannan ta wa yaron wanka, cukuikuiye
zanin gadon ta saka shi cikin baho,sannan tayi
kwaskwarima ta sabi danta baki suntum ta nufi
gida tana kuka. Mahaifinta bai nan yana
Abuja,Hjy Zainu ta kalle ta bayan ta gama kero
karyarta. Wai don yaro ya yi kashi ta ce yaron
bai kyauta ba shine ya hau ta da duka da zagi.
Hjy Zainu ta ce Amma wannan da muciya ya
dake ki ko?ta ce, Da hannu ne,nushina fa ya
dinga yi. Hjy Zainu ta ce Ai kin gani ba yadda ba
a yi ba ki tsaya kiyi karatunki kin ki,kin kafe sai
kin aure shi,wannan matsiyacin? Dama talaka
yana da wannan tsiyar.Yanzun za ki zauna mu
jiraZuwan Alhj,ba za ki koma ba.Ya dai baki
takardarki in yaso ki koma mkrnt.Su kuma su
dauki dan nasu. Bishira dai tayi shiru,zcyrta tana
jinjina rabuwa da Abba d kuma danata. Abba kam
gidansu ya nufa.Ummi ya soma cin karo da ita
tana sanye da doguwar rigar bacci,ta dora rigar
sanyu ta sakar ulu, a kai tana wanke baki da
busushi. Ta dube shi,mmkn ganinshi tayi a
wannan lkcn.Sai da ta dauraye baki sannan ta ce
masa sannu da zuwa,ya amsa a hnkl bai san mai
yasa ya kasa dauke idanunshi daga kanta ba,hr
ta gama alwala tayi addu a ta mike. Ta dube shi
da niyar yin magana,amma sai ta fasa don tana
tsoron kada ya daka mata tsawa. Ta daga
labulan dakin Umma zata shiga. Ya ce, "Ke!' ta
waiwayo cikin hada rai,domin ta tsani kiranta da
yake da ke!Ya ce Ummana fa?ta kalli dakin Alhj
Ba ta fito ba,,Ta shige ta zura hijabi ta tada
Sallah. Ya shiga dakin ya zauna,yana kallonta
tana Sallah zcyrshi tana nazarin Rayuwar
Ummarshi. Tun tasowarshi ya ke ganin kulawa da
kyautatawa da take yiwa Alhj Babba ga biyya,
sam bata wasa da dk wani abu nashi daga lkcn
da ya shigo gida ta gama sauraron kowa sai lkcn
da ya fita. Bai ta6a jin sunyi sa'in-sa ba bare ta
daga murya sama da tasa.Shin sauran matan ba
su fahimci irin wannan ladabi ba ne?Ummi tana
addu'a zcyrta cike da tunanin shi kuma ya Abba
me ya kawo shi da wannan sassafen? Muryar
Umma suka ji daga waje tana cewa,"Ummi in kin
idae ki fito ki share gidannan,ki wanke bayi,Ummi
ta ce To''. Sam Umma ba ta san Abba ya shigo
ba,dmn da ta ba Ummi umurni sai ta sake
komawa dakin mijinta, Ummi ta wanke bayi
kansu,sannan ta share ko ina na gidan, ta kunna
risho ta dora ruwan karyawa, sannan ta shiga
firar doya. Gyangyadi yake daga zaunw, Muryar
Ummanshi ce ta farkar da shi tana cewa, "A'aha!
ya bude ido cike da bacci.ZURFIN CIKI book 2 part 4
ZURFIN CIKI book 2 part 4
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:10
"A'aha! ya bude ido cike da bacci. Ya kalle ta tare
da yin mika,ta ce "Lafiya"? Ya ce,Umma lfyr
kenan.Ta zauna da sauri Me ya faru Kuma? Yayi
dan tsaki,umma na gaji da auran nan ina ga
wannan karan xan yar da qwallon mangwaro in
huta ta quda. umma ta ce abba! abba!! me yasa
baka da haquri? ban xace ka haka ba abba,ina ce
jiyannan ka min alqawarin kawo qarshen duk
wata matsala tsakaninka da matanka?shin ban
fada maka hanyoyin da xaka bi ka xauna da
matarka lfy ba?ya kamo hannun ta,umma ba na
san bata ranki, ban san yadda xanyi da halin
yarinyan nan ba ne. jiya fa ina kwance taxo tace
min yarona amai naje kai shi kyamis,ina dawowa
na samu ta xauna tana kallon,ina mata magana
ta hayayyaqo min da asuba na tashe ta
sallah,wai dan yayi kashi shine ta hau xagin
yaron nan,wai dan iska. ni ko na bige mata baki
har da cukume ni da dambe fa.umma tace kaine
harda duka abba? dukan mace?ta xuba tagumi
tana kallon shi,ya ce umma xaginshi fa tayi,kuma
kin san dai ba kyau uwa ta dinga xagin danta.dan
ba haka kikai min tarbiyya ba.kalli rashin ji irin na
ummi, amma ban taba jin kin ce mata yar iska
ba.tace to ba sai ka xaunar da ita cikin tsanaki
ba?? . Yayi shiru a xuciyarshi fadi yake umma ba
xata fahinta ba.tace, tashi kaje ka bata haquri, ka
lallasheta.matafa sai haquri,kasan da qashin
haqarqari aka yi su,dole ka ganta a karka
ce.saidai nasiha da lallashi,da xaran ka ce kan
dole xaka miqar da ita,sai ta karye.nan dai ta yi
ta ma abba fada, har sai da shi kanshi yaga
cewa eh,yayi saurin fushi.dan haka ya miqe ya
nufi gida da nufin bata baki.sai dai kuma kash!
lkcn da yaxo tuni tana gidansu.ya dawo ya sanar
da umma, tace to dole sai alhj yaji kenan.ta shiga
gun alhj yana shirin fita. yace yau dai suwaiba
akwai abin da ya dauke miki hankali daga kaina
ko? tace, me kagani? yace tunda kika fita ban
kuma jin duriyarki ba, hatta karin kumallo yau
uwata ce ta kawo min.ko taya ni shafa mai yau
ban samu ba, tace uhum, abba ne in gaya maka
na gani hankalinshi a duk tashe, matsala ce suka
samu da matarshi,wai ta yi yaji.alhj yace,yaji?
umma tace eh wai a ce kamar abba bai san
yadda xai yi haquri da mace ba, alhj yace ina
abban?ta ce yana daki yana karya wa. Ya ce kira
min shi.abba ya xauna ya xayyane ma alhj komai
duk abubuwan da ke faruwa wanda take
masa,hatta batun sallah da bata san yi duk ya
fadia.alhj yayi shiru,can ya ce in ko haka ne ba
qaramin haquri kake yi ba, amma kaje xamu je
gidan.abba ya ce, ni dama xa a baita can dana
huta.alhj yace ba xa ayi haka ba haquri dai xa ka
ci gaba da yi.xuwan su alhj biyu gidan amma ba
suyi dace ba ance musu mahaifinta baya nan.
antynta kuwa ta kira shi a waya ya ce yana nan
xuwa gidanta.da dare suka je da ahmad sun
same ta ita da mijnta,anty ta tare su cikin fara'a
aka kawo musu kayan shaye shaye.nan dai abba
ya fada mata komai.ya qara da cewa ban sani ba
ko dan ni talaka ne shi yasa bishira bata ji
maganata? anty tace dame ka gaxa mata?
iskancintane kawai, wai bishira har da rashin
sallah,xa ko taci qaniyarta gun alhj.mijin anty
yace,tabdi lalle kana haquri nan dai suka ci gaba
da hira har mijin antyn yayi mishi alqawarin cewa
ya kawo takardunshi.MD din gidan rediyon
tarayya na jihar kd, amininshi ne. Amininshi ne
tun da abn da ya karanta kenan za a sama mishi
aiki.Abba ya yi ta godiya. Bai san da wane baki
zai gode ma mijin anty ba,tun daga nemna auran
Bishira yake taimakoshi, darajar su shi da Anty
da Alhjn su Bishiran yake hkr da halayanta. Ya zo
ya sanar da su Umman,Sun yi murna hr Alhj ya
ce dole ne in in masa godiya. Umma ta ce To
Abba ka gani fa,ta dailin matarka gashi zaka
samu aiki,ka yi ta hkr fa. Abba ya ce Umma ba fa
ta dalilinta ba,in Allah ya rubuto zan samu ta
hanyarshi sai ki gani,ko ban santa ba Allah ya
kawo sila.Ta ce To yanzun dai ita ce Silar,Allah
yasa albarka.Sai dai ba zan ji dadin tafiyarka
garin Kd ka barni nan ba. Ya ce Umma ko ni
tunda ya ce kd ke kurum ni ke tunan.Umma tayi
Murmushi,Allah ya maka za6i na alkairi,dk in da
za ka je.Amin Ummata. Mahaifin Bishira ya dawo
kuma Alhj ya tasa Abba sun je in da aka kirata
gata ga shi ga kuma iyayensu. Abba ya jero duk
laifunkanta bai rage ko daya ba. Sannan ya ce,shi
ma yana son ta fadi tsakani ga Allah me yake
mata wanda ba ta So?Nan fa a ka ce ta fadan,
sai ta shiga Kame-kame, Wai in ya shigo gida sai
ya yi ta fadace-fadace sannan ba ya zama a gida
sai tayi bacci,km ga abnci ta dafa amma sai ya
amso na Ummarshi ya c. Alhjnta ya daka mata
tsawa."Yi min shiru,yaushe ki ka bar musulunci?
Ba kya sallah ko?sannan ki bude baki kina zagar
masa da a gabansa?Ya bige miki baki kin kwaso
kin taho gida,to a miki uban me?ya dubi Abba
"Idiris me yasa ma ka mata duka ba?Ai ke babu
abn da ya dace da ke irin duka. Maza ki kakkabe
mayafinki ki koma gidanki,bana son in sake
ganinki da sunan yaji a gidana, . Zan wulakanta
ki. Kuma game da batun sallah dk lkcn da bata yi
ba ka dakar min ita ni na saka,batun tsafta kuwa
kada tayi,ka nemi mata ka aura ka barta da
tsiyarta. kai dk lkcn da ka samu matar ma zan
biya maka sadakinta ko 'yar wanene.Sai a lkcn
Alhjn Su Abba ya yi magana. Hakuri za ka yi
ranka ya dade,Allah ya saka da Alkairi bisa
karamcin da a ka yi mana,kuma insha Allah ba za
su sake ba. Abba ma ya yi godiya,sannan suka
masa sallama.Ita ko Bishira mayafi ta dauko tana
kuka suka tafi. Hjy Zainu ranta ya 6aci,taso a
kashe auran don dama bata son Abba sam,kafin
zuwan iyayen Abba da shi kansa Abban ta
fadawa mijinta karairayi,kamu ransa ya 6aci. Ya
kuma daukar wa kansa alkawari in ya bincika ya
tarar haka ne dukanta da zaginta yake ba tare da
ta masa laifin komai ba?sai yasa an raba auran.
Amma da yaji batun Abba gata a gurin bata musu
ba,sai ranshi ya baci da ita, har dai batun sallar
nan.dn haka ya bincike yana da kyau ayi shi,kada
ka yanke hukunci da maganar gefe daya,wannan
shi ne adalci. Bayan sun dawo Abba ya rakata
gida ya zo gurin Alhj da ya ce ya dawo yana
jiranshi. Alhaji ya masa fada cewa dk in da tara
tayi to ya kansace a gida. Sannan fadan da ta ce
yana yi in ya shiga shi ma ya daina,haka ya
dinga zama yana cin abncin.Abba ya ce to.Umma
ma da ya shiga suyi Sallama nan dai ta kara
masa fada tare da nuna mishi hanyoyin da zai bi
ta ce kuma cikin satin nan yayo mata rijistar
Islamiya tunda da ita a kusa. Ya shiga ya same
ta zaune bakin gado tana ta fushi,ya zo ya zauna
kusa da ita.Yasa hannunshi ya kamo nata,sannan
ya kira sunanta bata amsa ba bata kalle shi ba
ya ci gaba da mgn. Kin san dai ina sonki ko??ta
dube shi Da ba kafin a zuga ka.Ya ce wa zai zuga
ni? ta ce Wa kuwa in ba Ummar taka ba. Ya yi
tsam ya ji haushin maganarta sosai,amma sai ya
danne kada ki zargi Ummata tana sonki kin ki
fahimta ne kawai.amma mu bar zancan kiyi hkr
akan abubuwa da nike miki. ki yafe min nima na
yafe miki. . Ya jawota zuwa jikinshi,hr gobe ina
sonki sosai.Ranta ya yi sanyi don mata na son
wannan kalma daga mazajensu. Ya kira sunanta
ta dube shi cikin ido suke kallon juna,ya ce kin ya
fe min?ta daga gira,kina sona hr yanzun?Ta kara
mannewa a jikinshi "Ina sonka sosai ma.Ranar
dakin shi suka kwana,kuma ranar ce rana ta
farko da suka soma kwana a dakin nasa. Washe
gari tunda ya dawo Masallaci ya soma akin share
gida,lungu-lungu ya gama ya wanke bayi kan su
sannan ya yako ta da kyar ta tashi ya ce tayi
sallah ta yiwa yaro wanka. Tayi Sallar,wankan ta
kuke wai akwai sanyu,sai ranar ta daga. Ya ce,To
t dafa musu ruwan zafi su karya.Shi kuma ya
fitar da wankinshi yana yi ya gama ya ce ta fito
da duk wankinsu ita da yaron.Tsawaya ya yi yana
kallon tilin kayan,amma gudun kada suyi rigima
sai ya yi shiru ya ci gaba da wanki. . Ya cire
kayan yaron da zannuwanta hr ma zanin gado
wadanda yaron ya yi kashi ta aje su suka
bushe,,wasu kayan hr da tsutsotsi. Ya kira ta ya
ce "To kalli kayanki hr da tsutsotsi,wanna n ya
dac fisabilillah?samo leda ki kwashe su,ba zan
iya wanke su ba,in kuma za ki wanke to. Nan ta
samo bako ta kwashe takai gurin bola,ya ce
Bishira tsafta cikin addini ce,Annabi (S.A.W)ya ce
Babu mai shiga Aljanna sai mai tsafta. Don Allah
ki dinga kula,ke kanki za ki ji dadi in har ki ka
tsaftace ko'ina na gidanki.Ta tura baki ta wuce.
Ranar haka ya yini wanki kayan yaron dk sun
dafe kaya masu tsada da kyau irin wadanda a ka
sai masa daga gidan iyayenta,ranar dai ko shago
bai je ba. Cikin satin dai babu laifi suna ta
shiri,kuma tana daurewa tana yin tsaftar
jikinta,haka nan yasa ta wanke kai tayo kitso. sai
dai ita gani take dk an takura mata,amma tana
jin dadin yadda ya sakar mata fuska kamar
farkonauresu. Mitar da take masa kullum ya
daina dadewa a waje,ita don Allah ya zauna a
gida suyi hira. Ranar dai saiya gwada zama tun
da ya dawo sallar Isha'i ya shigo gida. Tana
zaune ba riga ya ce,Wai Bishira kayan kwalliyarki
sun kara ne? ta ce,Me ka gani?ya ce,Rabon da in
ga kwalli a idonki tun kina amarya bare dan jan
baki. . Taja dan tsaki "kwalliyar me zan yi sai
kace wata budurwa?Da dai nayi.Ya ce kin ji wani
shirme kuma,ban da ke ai matar aure me miji a
hannu ita ce da yin kwalliya. Ta ce, To ko ma
nayi ba zama ka ke ba.Ya ce "To yau dai gani na
zauna,kuma ina son a sheka min kwalliya. Ta
dube shi Gsky sanyi ba zan iya yin wanka yanzun
ba.Shiru ya yi yana kallonta,can sai ta zame ta
kwanta,sai kuma bacci. Ya yi murmushi.Dubi
matar da ta ce wai ba na zama a gida. to yau na
zauna amma kalli yadda ta bingire tana shirgar
bacci. Ya mike ya fice.cikin takaici korafin banza
kenan take yi tunda ba ta san yadda za ta yi fira
da mijin ta ba. haka dai abba yayi ta hakuri don
baxai yiwu ya ce shi kadai zai dauke mata duk
aikin gidanta ba. sai dai yayi wanda zai iya,amma
duk wanda ya shigo gidan shi ko ba a fada ba
yasan matar gidan kazama ce ta bugawa a
jarida. ummi tana zaune gaban umma,fuska
shabe- shabe da hawaye.ta rikewa ummar
hannu."kinji don Allah umma kice wa ya Abba ya
dawo dani garin nan.wallahi bana son makarantar
kwana,ni dai bazan koma ba."umma ta ce "haba
ummi xuwa yanzu ya ci ace kin saba da
makarantar" ta ce,"umma bazan saba da rashinku
ba....."karaf a kunnen Abba. ya ce,"to sai ko ki
shirya sabawa,don wata rana ma aure zaki yi."
umma ta ce sosai kuwa. tsohuwa dake zaune a
kofarta,tana jinsu ta sako baki da cewa,"ku dai
lallasheta,karatun nan fa da ake ta matsanta
mata bana ganin manzo bane." Abba ya ce
mata,"in ji wa? kin ji ki,to ana neman aljanna da
karatun boko kuma ana neman wuta." ta ce,"kai
ni raba ni da shegiyar karya tunda bata so a
barta." Abba ya dubi ummi,"kada ma kiyi za ton
maganar tsohuwa za tayi wani tasiri,gara ma ki
shirya komai gobe da wuri zamu wuce." ta dube
shi,"don Allah ya abba." ya mike ki shirya da
yamma zanzo muje (sahad store). ya dubi umma
na tafi. . Ta ce,"abba bamu ko gaisa ba,ya mutan
gidan?" ya ce,"suna lafiya,sauri nake in karasa
wasu dinkuna,saboda gobe bana nan jibi litinin
zanje interview da gidan radiyo da talabijin na
(c.t.v) ta ce,"a'a ka samu anan din ne?" ya
ce,"eh bana fada miki ba da aka tura takarduna
can sai suka ce gurin da zasu saka ni akwai wani
wanda suke jin dadin aikinshi a gurin? don haka
zasu turo ni kano,suna ganin ana bukatar irina.to
shine mijin anty ya fada min to yanzu sun kirani
ranar litinin zasu min (interview).ummi dai na
jinsu bata ba kukanta ba.abba na ficewa umma
ta ce tashi kije kiyo kitso ummina,kin ji? dakyar
taje ta dawo.umma tana yankan kubewa wayarta
ta shiga ruri,ta dauka Abba ne.ya gaisheta ta
amsa,ya ce ummana ummi fa ta shirya? umma
takai duba cikin daki inda ta hango unmi nade
kan kujera tunda ta fito wanka. Tace can cikin
kujera,wai sanyi take ji.yace sanyin lfy kuma? ta
shirya ta sameshi gida,umma tace to gatanan
xuwa sukayi sallama.umma tace ke ummi fito
man in kin gama shirin.ummi tace umma nifa
sanyi nake ji,ina ganin xaxxabi ne xai
kamani.tace to ku biya ta kyamis kusai
magani.tsohuwa tace ke yi kwanci yanki, dole ne
fitan? umma ta miqe tana cewa, yanxu in ban je
ba da yaxo xai fara min masifan shi ne. ta shirya
ta fuce rai a bace.a nutse ta ke tafiya har daf da
qofan gidan ya abba. sallama taji anyi mata.wani
matashi ne suka gaisa, ya tambaye ta nanne
gidansu? tace a,a lafiya?ba tare da bata lkc ba ya
fara xayyane mata manu fanta,santa yake kuma
da aure,tace kaga mlm sai anjima.ta shige gidan
abba shiko ya kafe yaqi tafiya.da sallama ta
shiga gidan,qaran inji baisa aji sallaman ba,dan
haka ta jingina da rijiya tana kallan tsakar
gidan.mamakin daya yadda mace daya a gidan ta
kasa gyara gidan.sai kace gidan namiji, namijin
ma qaxami. . abba ne ya fita wanka sanye da
jallabiya fara.ya aje bokitin ya dube ta. yace ki
siga ciki mana, ai tana falo.tayi
sallama,bishiratana xaune da baso tana kalan tv,
ganin umma ta daga labule sai ta hada rai tare
da cewa lfy? ummi tace ina wuni. bishira tace
lau, nace lfy? ta fada hadi da xare ido. ummi tace
ya abba ne ya ce na xauna anan na jira shi. tace
baxa a xo nan adame ni ba, ehe dan kallo nakeyi.
ummi ta ja tsaki tare da sakin labulan, ta koma
ta jin gina da rijiya.bishira ta fito.ke sarkin rashin
kunya wa kike ma tsaki? ummi ko kallanta batayi
ba.sannan tace baki isa kixo min har gidana
ba,kice xakimin rashin kunyan da kika saba.abba
ya jiyo hargowanta ya fito, yana qoqarin saka t-
shirt baqa akan faran singiletin shi,wandan jeans
ne mai laushi blue.yace,menene? tace, wannan
mara kunyan yarinyan nanne xata sameni har
dakina tamin tsaki.oa dubi ummi dake kallan
qasa tamkar bata san me akeyi ba. yace ke
ummi, ta dube shi da sauri,xan bata maki rai
kinsan bana san raini ko? tace nifa ya abba
banfa yi mata komai ba kawai fa.ya daga mata
hannu,yace banasan ji. yace na fada maki dai
bana san raini. takaicin duniya ya isheta,ta
sunkuyad da kai cikin qunan rai.wanna shine
gaba kura baya damisa.bishiqa kam sai ci gaba
da mita take, shiko abba tuni ya koma dakinsa da
qarasa shiri. ya fito fes, sam baxaka ce mijin
bishira bane.qamshin turaransa ya karade gidan
ya daga labule.ni na fita. tace sai ina? xan kai
ummi ta sai duk abinda xata nema dan gobe xata
koma mkrt. ta tabe baki. ya dubi ummi wadda ke
cika tana batsewa,sannan ga sanyi alamun
xaxxabi yana damunta.yace muje ko? ta dube shi
sannan ta bishi.a qofar gida ya iske wannan
saurayin,yace lfy, ko kana jiran wanine? saurayin
ya ce wata yarin....sai ya hango ummi,dan haka
ya katse batun da cewa yauwa gatanan. . abba
ya kalleta ke uwar rore rore wannan ke yake jira
ko? ummi tace oho mashi, bina yake tayi.abba ya
ce, kayi haquri dan samari,ba aure xa a mata ba,
krt takeyi. yace nima din bawai ina nufin yanxu
bane.ya ce na fahince ka.to ka bari sai nan
gaba,ina nufin in auran yayi sai kaxo ko???? Ya
dubeta ranshi bace,ke kuma wuce muje.suka bar
shi nan tsaye yana kallansu.yaga kishi qarara a
idon abba.yace wannan ba wanta bane shima
santa yake.ya raya aransa shima yayi gaba abin
shi.shi kam abba suna tafe yana yi mata fada,wai
tabi ta sakar ma maxa fuska kowane gaja sai ya
xo yace yana santa.maimakon ta tsaya tayi
krtnt,xamani na ilimi,ita dai ta qi kula shi,har
yanxu takaicinta abin da matarshi ta mata,kuma
ya nuna ya goyi bayanta.wayarshi tayi ringing,ya
kalli ummi muje shago na mashin din
nacan.sannan ya daga wayar,ita tana tafe ne
amma sam bata jin dadi.da yake tafiyanta yanxu
tamkar tana jin tausayin qasa take yinta,sabanin
da da sai dai tayi gudu,shi da ke tafe yana waya
ya riga ta isa.gefe ta tsaya ya shiga shago bayan
ya gama amsa wayar.ahmad abokinsa yaxo xai
shiga shagon ya ganta tsaye.tace ina yini ya
ahmad? yace lfy lau yar daru.daman haka ya kan
ce mata.ya shiga shagon yana
waiwayanta,abbana barma yan shagon sallahu
wasu kayan da xa a xo dauka,ahmad ya shigo.
suka tafa,sannan suka gaisa.ahmad yace naxo ne
in fada maka anjima xamu shiga gidan su hafsa
dan gaida iyayenta,sai dai kuma ganin ummi ya
sani jin wani abu.anya ba xan dawo gida da
neman aurena ba?a rude abba ya ce wace ummi
kenan? ahmad ya ce qawarka mana.abba ya ce
dan Allah saki xancen nan kada ma ta jiyo ta
raina mu,me ka gani naso a gun ummi? dan Allah
kada ka cta min rai. . ahmad yace, allah in xai
yiwu, nutsuwan ta birge ni .abba ya ce to ba da
ni xa aci amanar hafsa ba.ummi kuwa dan Allah
ka bar xancenta.yaea ahmad yaga abba ya sha
mur ya tsare gida,dole ya saki batun.suka yi
sallama ya tafi,abba na cewa sai yaxo da
dare.yasa yaron shagon ya goge mashi mashin
din sannan ya tada,ya kalli ummi fuskarshi daure
xo ki hau.itama tata fuskar a daure take.tahau
suka tafi,iskar dake kadata tasa xaxxabin dake
san kamata ta qaru.ya kafe mashin dhn ya
kalleta,muje mana.ta bishi suka shiga cikin sahad
store din.tsaye tayi tana kallanshi yana diba
kaya.da alama na iyalanshi yake diba,dan taga ya
soma da pampas. Hannuwanta harde a qirjinta
tana kallan shi,kome nashi yana birgeta.ya
waiwayo ya dubeta, tsayuwarme kike yi a nan da
ba xaki dauki abinda ya kawo kiba? ta rasa me
xata dauka,sai kurun ta dauki makilin ta riqe a
hannu,ya gama diban abin da yake so,sannan ya
aje gaban masu amsar kudi.ya dubeta,bakya
buqatar komai kenan? ta nuna mishi makilin din
hannunta,tana murxa shi.ya harareta baxa ki
dauki komai ba,kina da kayan tea dasu complex?
tace a,a.y2e to ki tsaya kada ki dauka.ya soma
dibo mata saitin sabulan nan daya taba sai mata
na aloe vera,dan yaga duk kananan qurajen sun
mutu.sannan ya hada mata da audugar mata
guda biyu.ya kai table.lkcn ta dauki madara da
milo ta kawo.yace wawiya,dalla matsa ki bani
gu.yaje ya qara tsinto mata ,sanna akayi musu
total ya biya.suka fita.kafin sukai gida haqoranta
sun s6a haduwa,gashi tana ta takurewa,yace
lfy,wani irim xama kika yi haka?tace,sanyinake
ji.tana magana muryarta na makyarkyata.wani
dan asibiti ya nufa da ita nan kusa da unguwansu
aka dubata. Wurin allura,nan fa a ka soma
daga.Ta ce,ita kam bata san allura.Abba ya daka
mata tsawa da cewa,Allurar ce abn tsoro?Na
gane sam ba ki son ki koma mkrnt,a gobe ne
kuma sai kin koma duk abnki. Ta ce, Naji zan
koma amma yanzun kam dn Allah Ya Abba kada
amin allura.Nurse dai sai kallonsu take yi tana
dariya. kwai Ummi sai ta soma hawaye ita fa har
ga Allah bata son allura.Nurse ta ce,To ka rike ta
mana ko ba Amarya ba ce?Naga shagwabar tayi
yawa. Abba ya ce,Me? cikin tsawa ya yi
maganar,hr sai da Nurse din ta tsorata,ya ce
kanwata ce fa,kin ga wannan kucakar tayi kama
tayi kama da Amare? Nan take Ummi taji ta
muzanta,sannan km ta tsorata da irin tsawar da
ya yi,ba ta san lkcn da ta shige a ka yi mata
allurar ba. Ta fito tana sharar kwalla suka koma
gida. Sai dai tana hada kayanta a Jaka,Sannan ta
ga wadannan sabulun da kuma audugar,kenan shi
ne dama ya sai mata wancan?ko me yasa ya sai
mata kuma hr da augugar mata? . wata zuciyar
ta ce,kila dn yaga Umma bata san kan abubuwan
zamani ba sosai.A fili ta ce,kai umma tasan
audugar mana. Haka dai ta ci gaba da tufka tana
warwarewa,hr ta gama shirya kayanta. Yau kuma
a bayan Tsohuwa ta za6i kwanciya,da dn komai
ba sai dn suyi hirar yaushe gamo. Sai dai
Maimakon hira sai ta tsunduma a tunani,ta bar
Tsohuwa tana ta zance ita daya. Fitarsu da Ya
Abba ta tsaya mata a rai,ita tayi ta tunowa tana
murmushi.Sai dai bata Son tuna lkcn da ya yi wa
Nurse din nan tsawa dn ta ce ko ba amarya ba ce
kom me yasa zai mata Tsawa? ita kam kalamn
Nurse din nan sun birgeta,shi kuma daga ganin
yadda ya yi tsawar nan kalamn ba su masa dadi
ba.......... wai takwara bacci ki ka yi ne?Muryar
Tsohuwa ta katseta,ta ce,Idona biyu Tsohuwa.Ta
ce, Tunanin me ki ke yi ne haka?Ummi ta ce
"Um" ina tuna gobe yanzun ina can.Tsohuwa taja
tsaki,Ai mai sunan Malam ya san takan mugunta.
UMMI dai ta ce "Um.Tsohuwa kuwa sai yi take
da mai sunan Malam.Tun Ummi naji tana "Um",
hr zcyrta ta soma tsanar kalaman Tsohuwa. Sai
dai bata da damar ta katse Tsohuwa tunda dn ita
take yi,bata da mafita da ta wuce ta bar
dakin,don haka ta suri butar Tsohuwa,wai zata je
kewaye(bandaki). Shi ma Abban da ke kwance a
tsakar dakinshi kan kafet ya tada kai da
katifarshi,ban da tunanin fitarsu ta dazun ba abn
da ya keyi. Sai dai damuwarshi daya,me yasa
samari da dama suke kawowa Ummi hari?Me
yasa ya ke jin zafin haka?Zuciyarshita amsa da
cewa,ka so ko ka ki kana Son UMMI."a fili ya
furta "Haba dai so,Allah ya tsare ni." Tun misalin
tara Ummi ta gama shirinta tsaf,cikin kayan
mkrnt mai ruwan hoda,mai gida-gida.Da kuka ta
bar gidan yau ma. Haka nan kuka take hr suka
isa mkrnt,ta samu Khadija hr tazo,dn haka tare
suka kwashe kaya.Kafin Abba ya tafi sai da ya yi
mata fada kwantankwacn wnda Umma tayi
mata.Waton ta kula d kanta,kuma tayi abn da ya
kawo ta,waton krt.Sannan ba ya son tayi
kawance d yaketa shari'a.irin wanda wasu
watsatstsun yaran ke yi.(Allah ya shiryesu).
Sannan ya jadadda mata batun ibada,sannan ya
kawo kudi ya bata,ta ce Umma fa ta riga ta bani.
Ya ce,"Ki kara."ZURFIN CIKI book 2 part 5
ZURFIN CIKI book 2 part 5
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:12
Umma fa ta riga ta bani. Ya ce,"Ki kara."
Rayuwarta a mkrnta wannan karon ba laifi,sai dai
fa hr yanzun ta tunu da gida sai tayi kuka. Su
Safiyya suna mmkn yadda Habiba take da
matsanancin nacin gida. ******** Abba ya shigo
gidanshi dauke da ledajin kayan miya,da sauri ya
dire su kofar kicin ya nufi Bishira da ke kofar
bandaki tana shara amai. Ya kama ta,"lafiya?Me
ki ka ce? Sai da ta gama aman sannan ya karasa
da ita ta wanke baki da fuska a cikin bayin. Ya
ce,Ba ki d lfy ne?Ta soma Hawaye, Ka gani ko
Babn Walid,kila fa ciki ne da ni.Tun wancan Satin
ya kamata in ga al'aldata amma shiru. Ya ce, To
menene na kuka? Yi shiru,Allah ya inganta.Ta
harare shi Dana fa bai shekara ba.Ya ce,To dole
ne sai danki ya shekara sannan Allah zai baki
wata kyautar? Ta soma kuka,Ni dai zan je a
ciremin ne. ya hade fuska,Ban yarda da haka ba.
Ganin ta tada hnklnta tana cewa "Dama Hjyrsu ta
ce mata tabi a hankalu ta ki ji gashi nan yanzun
tana da wani ciki. Ya ce To kada ki damu kin ji?
Zamu je asibtin dn a tabbatar da cikin kafin a san
abnyi. Da za suje asibiti shi ne ya dage sai da
tayi wanka,dn d farko kaca-kaca ta dauko
mayafi, ya ce sai tayi wanka ta canza tufafi.
Gwajin farko ya tabbata tana da ciki,nan ta shiga
kuka. shi kanshi ya damu domin bai so ciki
yanzun ba.A son ranahi sai an yaye yaron kafin
wani cikin. Amma ba shi da ra'ayin
zubarwa,nashi ganin kyautar Allah ce,dn haka ya
amsa ya kuma gode. Ya lallashe ta da cewa,ta yi
hkr su amshi kyautar Allah dn haka wani na nema
da kudi bai samu ba. likita ya ce,Kada ta
damu,taci gaba da bai wa danta abnci tana hada
mishi da nonon,a hnkli zata yaye shi bana farat
daya ba. Bayan ya kaita gida ya kuma
lallashenta,saiya nufi gurin Umma. Bayan sun
gaisa,ta tambayi iyalanshi ya ce "Daga asibiti ma
muke da Bishira." Umma ta dube shi da
sauri,Waye ba lfy? ya ce, Ita ce.Sai kuka ma take
yi wai dn an ce tana da ciki. Umma ta ce, Ikon
Allah, to Allah ya inganta.Sai dai kuma kada
Walid ya sha ciki. Abba ya ce,likiya ma ya yi
mata bayanin yadda za ta yi masa,hr ta janye shi
daga nono cikin hikima.Umma ta ce, Da za ta
yarda ma an kawo mana shi nan. ya ce,Ai dama
nan zan kawo shi da zarar an yaye shi Umma.
Sam bai fada ma Bishira nufinshi na baiwa Umma
Walid ba,dn yasan ba zata ta6a laminta ba.Sai
dai itama tasan dole hakan zai yi. Don haka ta
garzaya gurin Umman Bashir ta shaida mata
cewa sunje asibiti,dk ta fada mata komai,sannan
ta ce ita danta take tunani kada ya dauka ya
kawo wa Ummarshi ita ma a mallake mata yaro.
Umman Bashir Ta ce Wannan a zaune take,sai
dai in ko ba a kai shi ba.Amma ki bari daga kin
kula ya daina damuwa da nonon ki janye shi,zan
zo in taho da shi wurina. Bishira taji dadi tare da
cewa, Hakan dai yafi. Sabuwar kazanta ta
samu,Bishira dk abn bi bangon daki an tofe da
yawu.Rashin wanka sabo,kai abn nata sai
addu'a. Ibada kuwa ba a mgn,domin dai tuni ta
aje Sallah a gefe,Azumi dai tana yi amma in ta
sha bata ramawa.Allah ya shirye wanda ya 6ata.
Abba ya dai yanzun tuni ya yafe abincin
gidansa,matsawar ba shi da kanshi ya girka
ba,don kuwa dama can shi mutum ne mai
kyankyani. In zata fita takan wanke kafafunta ta
dauki kaya ta saka,sai ka rantse tayi
wanka.Amma da zata matso kusa da kai,nan za
ka ji kauri na tashu da karni da kuma wari. Dole
ya hkr da laluranshi ta aure a gurinta,domin in
yaje shimfidarta ba zata ki ba,amma wari da
zarni suna hana shi yin komai cikin nutsuwa. In
kuma dakinshi ya kirata ko bata kwana ciki ba
har gari ya waye yana jin warin jikinta a
shimfidarshi don haka lokuta da yawa yake
hakura da ita. *********** . Ummi tana kwance
kan gadonta,yayin da Khadija da Safiyya suke
zaune bakin gadon Safiyyan wadda ke kallon
Ummi. Hirar masoyinta take basu,Safiyya bata ko
gajiya da zancensshi. Khadija ta ce,ita ma da
zata taho har kuka nata Saurayin ya yi. Sai lkcn
Ummi ta dube su,"kuka Khadija?Khadijata
ce,"Riris Kuwa. Ummi ta ce, Hu'um ba namijin shi
yasa nike da za6i a kan irin mijin da zan aura.
Safiyya ta ce,"ke banza,dk cikin so ne. Ummi ta
ce Ban damu da sai namiji yaso ni ba,in dai ya
tara abubuwan da nake so ga namiji to zan yi
amfani da kasantuwata 'ya mace in koya mishi
Sona. Khadija ta tashi ta dawo kusa da Ummi,Kin
san me ki ke fada?Koda yake sanar damu yadda
ki ke son mijinki ya kasance? Ummi ta ce "Na
farko mai son Addini,Mai Ilimi duka 2,mai hakuru
,sannan yana da saurin fushi,mai kuzari da
kwarjini. Ma"abocin tsafta da tsantseni,wandadk
tufafin da yasa sai sun kar6e shi,mai biyayya ga
iyayensa,sannanmai kula da gidansa,baki mai
tsare gida,ga yawan Ibada, Safiyya da khadija
suka kwashe d dry,Khadija ta ce, Ina za ki samu
dk mai wadannan lissafin da ki ka yi??? Safiyya
ta ce, Kuma fa bata gama lissafin ba ke ba ki ji
ana cewa dan Adam tara yake bai cika goma ba?
Ummi ta ce,Akwai shi,Ya Abbanmu haka
Halayansa suke. Yanzu ma da ni ke lissafin shi
na ke kallo a idona.Khadija ta ce,To ba dan
uwanki ba ne da shi kenan kin samu a gida.Ummi
ta ce,Wuu fitina Road,wannan ya mugun tsanata,
ina son dai me irin halayarshi ds
dabi'unsa.Khadija ta ce,Har da kamaninsa? Ummi
ta ce,sosai ma. Saitaga sun sa dry.Safiyya ta ce,
Malma shi ki ke so,kuma dk yanda a ka yi ba
shakikin ki ba ne,da aure a tsananinku. Umma
tayi Shiru tana kallonsu,Khadija ta ce,Habiba
kenan,wai har saurin fushinshi tana so. Ummi ta
6ata rai tare da cewa,Tunda kun kasa fahimtata
shi kenan.Ya zan yi in ce ina son Ya Abba yana
da matarsa? SAfiyya ta ce,ke dai in da aure
Tsakaninku kada ki tsaya "ZURFIN CIKI, kizo a
karshe kina da kin sani. Ummi ta ce,A bar
zancen. 32... Sai dai kuma a daran ranar ta
tsinduma duniyar tunani.Tabbas zuciyarta da
shisshiga take,tunda ta rasa wanda zata so sai
Ya Abba. Wanda ya yi mata muguwar tsana.Afili
ta ce,Duk kauce-kauce da kewaye-kewaye ba za
su kai ni ba,Ya Abba nake so. Hawaye Suka
soma sintiri daga idanunta. Wannan lkcn ziyarar
da yazo Abba da Umma d Tsohuwa da Alhj
Karami dk suka zo. Dadi ya kashe Ummi,ta rasa
jikin wanda zata fara fadawa don dadi. Alhj
karami ta soma kamkamewa sannan
Umma,Tsohuwa kam ai tana manne jikinta hr
suka zo tafiya.Shi ko Ya Abba yanzun kunyarshi
take ji,dn haka tunda suka gaisa mgn bata kara
hada su ba. Sai dai jife-jife suna satar kallon
juna,in sun hada ido sai ya dan daure
fuska.Safiyya da khadija sun gaisa da su sannan
sun yaba da yadda a ke ji da Ummi. Da za su tafi
kuwa Ummi kuka Tsohuwa kuka,sai da Abba ya
ce ba za a sake zuwa da su ba,Sannan Ummi tayi
shiru.Sun tafi sun barta d kewarsu,Kamar yadda
suma suka tafi suna kewarta. ********** . Bishira
da kanta ta dauki Walid ta kai ma Umman
Bashir,domin ta san zai kai ma Ummanshi ne.
Abba ya rufe ta da fada lkcn d y tambayi dan ta
ce ta yaye shi ta kai ma Umman Bashir. Ya ce To
je ki dauko mn yarona,dn ba can nayi niyyar kai
shi ba,Ta rike kugu,kaje mana da kanka,tunda ba
ka son zamn danka hannun mahaifiyarka to ni ba
zan yi saken da Mahaifiyarka tayi ba a ka raba ta
da danta ina fata ka fahimci karatuna? Kallo
kurum ya bita da shi,sannan yaja tsaki tare da
cewa,Dube ki kmr wata Bauna,jiki sai tsami yake.
Ta ce,Eh dk abn da zaka ce kace. Ya juya ya fita
rai 6ace. Umma ya Samu ya fada mata, ta ce, To
menene na bata rai Abba? Can din da nan ba dk
daya ba ne? ai ba za su cutar da shi ba. Ya ce, ki
fahimce ni Umma,ba ina nufin zai cutu ba
ne,amma can da yara kanana,nan kuma babu.
Sannan......... ...... Sai kuma ya yi shiru tare d
cewa,Shi kenan. Umma ta ce,Yauwa bana son
kana daga murya kan abn da bai kai ya kawo ba.
Allah ya raya mana shi ya kuma sauketa lfy.
Abba Ya ce Ameen. Gidan (T.V)sun kira Abba sun
masa (intervier)da kusan wata 2,dmn ya cire ran
samun akin, ko da yaje suka ce sun dauke shi
aiki. Abn d yasa suka yi jinkiri daukarshi,suna
canza tsarukan aikin ne sannan sun sake
tantance ma'aikatansu. Litinin Abba ya soma
zuwa aiki kmr yadda a ka bukata,dakin watsa
labarai a ka kai Abba. Sam bai samu matsala
ba,dk d shi na mai yawan surutu ba ne,amma a
cikin sati 1 ya goge da aikin,km an yaba da yadda
yake watso labarai. Yana yi da Hausa minti sha
biyar da turanci minti sha biyar,ana sakawa karfe
7 na yamma. Abba ya kama aiki cikin sa'a nan
da nam sai farin jini cikin abn d bai fi wata ba ya
nemi izinin a bashi fili koda mint 15 ne don
gabatar da wani fili da ya yi masu don matasa.
filin yana kiran shugabannin matasa na
unguwanni suna hira da su akan halin da matasa
suke ciki na shaye- shaye da sace-sace da kuma
rashin sana'a. Da turanci a ke shirin,sannan a kan
baiwa sauran matasa na gida su bugo waya su
fadi nasu ra'ayin,game da abin da ya kawo
hakan,da kuma hanyoyin da za a bi don magance
su. Haka nan ya kan samu lkc ya shiga cikin
matasan musamman ma su shaye-shayen da
marasa sana'a dn jin ra"ayoyinsu,da dalilan
fadawarsu cikin harkar. Kafin wani lkc filin ya yi
suna kuma kullum yakan tallata filin kan cewa ya
kamata Gwamnati ta dauki nauyi filin don yana
taimakawa mata wurin inganta rayuwar matasa.
Cikin ikon Allah sai gashi Gwamnati ta yaba da
filin,ta dauki nauyin shirin kuma an sa shi hr
fannin Radiyo. Lallai Abba ya shigo da kafar
dama,Sannan hukumar gidan Radiyo tayi Matukar
farin ciki da zuwan Idris Aminu Idris,wannan
Ma'aikata. Sannan sai Abba ya zama wani sabon
tauraro wurin Al'umma,dk in da a ka ganshi ya
zama abn kallo. Matsalar shi daya gidanshi,in ka
ganshi a waje Sam ba za a kayi tsammanin haka
zaka samu gidanshi ba,Dattin ya karu,musamman
da ya kasance yanzun ba shi da lkcn kanshi
ballatana ya yi sammakon share gidan. Wankinshi
mai kaiwa yake yi,haka nan nasu ya ce ta dinga
kaiwa makota gidan wanki. Amma kafin ta hada
ta kai aiki ne ita dai tayi kallo ko a shiga makota
hira. Sam Abba ko adreshin Zai bada ya
gwammace ya bada na gidansu Ummanshi dn ba
ya so aje gidanshi ************* . Kwanci tashi
Ummi suna ta fana da jarabawa zuwa (SS2) cikin
ikon Allah suka gama. ranar da aka yi musu hutu
kamar ta sani bata tsaya jiran Abba ba,Ta nufo
gida. Shi kuwa lkcn suna kici-kicin kai Bishira
asibiti zata haihu,amma yana sane da cewa yay
Ummi zata dawo kuma hnklinshi na can. Motar
wani Salis Abokin aikinsa ya aro ya kai su
asibitin ita d Ummanashi. Bayan ya ba d dk wani
abu da suke bukata ya ce Umma za shi dauko
ummi. Umma ta ce,Ka barta tukunna in matarka
ta sauka lfy gobe sai kaje tunda tana mkrnt ne.
Ya yi-ya yi Umma ta ki,dole ya hkr. sai bayan
la'asar sannan ta haihu,Nurse ce ta zo tayi musu
albishiri an samu 'ya mace. Bayan an kintsa
uwar,sannan a ka kaita dakin hutu,su kuma a ka
kawo musu 'yar.Nurse din da ta kawo 'yar ta ce
d Umma ke ce Mamanta? Umma ta ce,'Eh."Nursr
din ta ce "kazantar yarinyar tayi yawa,kafin ta
haihu sai da likita ya korata ta yi wanka,muka yi
mata aski ko'ina jinkinta datti. Gsky Mama
mijinta yana kokari,yanzun kuje ku dafa ruwan
dumi ku kawo mata tayi wanka. Abba ya yi tsaki
ya ce, kin ji ko Umma,Allah ya kara.Umma ta
ce,Yanzun kaje gida ka dauki babban filas dina ka
shiga wurin Umman Bashir ka ce Mata ta dafo
ruwan Zafi,daga nan ma sa ji haihuwar. Yana
shiga gidan tun daga zaure ya jiyo Muryar
Tsohuwa tana cewa,Naji shiru-shiru kin ga dai hr
yanzu. Yana saka kafa a tsakar gidan muryar
Ummi ta daki dodon kunnanshi.in da ta ce,Kila
kuma ta haihu yanzun. jinin jikinshi ya tsinke dn
jin Muryae. Ya nufi dakin.Tana zaune tana shan
rake. Ya dubeta, ita ma shi take kallo dn tunda ta
diro ba wanda take muradin Gani irin shi,cikin
sanyi murya ya ce,Ummi ke da wa ki ka taho? Ta
sunkuyar da kai,Ni da wasu 'yan mkrntrmu ne
muka dawo. Ya ce '"Good,tashi ki dafa ruwan zafi
ki zuba a babban flask. ya dubi Tsohuwa da take
ta tambayarshi ko mai dakin nashi ta sauka? Ya
ce, Eh ta haifi 'ya mace. Tsohuwa cikin takaici ta
ce,Sai yanzu kaga damar bani amsa?Dan
walakanci kawai? Kai mai sunan Malam ka gyara
halinka. Abba ya ce,Yi hkr Tsohuwa dk na gaji
ne,Nan kuma ina yi wa Ummi mgn. Ta ce kana
mata fadan ka dai. Ya ce,Tsohuwa wai ni hr
yanzun ba zan wanku a wurink ba game da
Ummi? ta ce, Ina fa zaka wanku?Har abada mai
sunan Malam kai ba me kaunar takwara bane. .
Yace to naji a bar maganar yanzu dai kishiyarki
ta haihu.an samu ya mace.tace Allah ya raya
mana. Yana jingine da bango yana kallon ummi
tana ta shige da ficen daura ruwan zafi.komai
cikin tsafta da natsuwa take yi. Sai da tasa
ruwan zafi ta wanke flask din kasancewar anjima
ba'ayi amfani dashi ba.ta tafasa ruwan tazo ta
bashi,ya ciro wayarshi ya mika mata. "sa min a
caji naga nepa sun kawo wuta" ummi ta jona
waya sannan ta ci gaba da girkin dare don tasan
Alhaji bai cika son wani abu da dare ba sabanin
tuwo. Ta gama wanka sannan tayi sallar
magariba tana kwance gadon tsohuwa tana
tunanin abba. Tsohuwa nata lazimi in tayi
magariba bata tashi sai tayi isha sannan taci
abinci.ummi ta tuna wayar da yaya abba ya bata
ajiya. Da sauri ta tashi tare da cewa "ke tsohuwar
nan anzo tayaki hira kin share mutane" ta mike
ta nufi daki ta dauko wayar ta kunna HEHE KIN
MANTA YAYA ABBA KENAN?" Sakwanni ne sukai
ta go slown shigowa sannan sai kira tashin farko
data daga wayar muryar mace taji, ta ce "dawa
nake magana" wadda ta kira ta ce "ina mai
wayar?" ummi tace "dq matarshi kike magana,ke
din wacece?" waccac n ta ce "in yazo ki
tambayeshi? yasan me lambar." nan da nan sai
ummi ta samu kanta yana juyawa,tayi tsakita
kashe.ta shiga duba sakonnin da yawansu na
mata ne masu sonshi,daidaikune na maza masu
nuna yabawar aikinsa.hankalin ummi ya tashi
ganin yadda mata suke farautar abinda take
tsananin so.ta kashe wayar cike da nadamar
kunnata Hankalin Ummi ta samu kanta yana
juyawa,tayi tsaki ta kashe.Ta shiga duba
sakonnin da yawansu na mata ne ma su
sonshi,dai-daiku ne na maza ma su nuna
yabawar aikinsu. Hankalin Ummi ya tashi,ganin
yadda mata suke farauta abnda take tsananin So.
Ta kashe wayar cike fa nadamar kunnata. Sintiri
ta dinga yi a tsakar dakin,Sallamarshi ce ta, katse
ta.Ta amsa ciki,sannan ta zauna ba tare da ta
kalle shi ba. Ya ce,Bani wayata da abinci 'yan
asibiti. Ta mike ta dauko masa abncin,sannan ta
bashi wayar.sai dai tana yin komai ne fuskarta
daure. Ya ce,Lafiya na ganki wani iri?ta dago ido
ta kalle shi,ta sake tsuke fuska. lfy lau.Ya ce,shi
kenan na tafi Sam bata tanka ba. Yana fita ta
mike a kujera,so takeyi a lkcn ta samu makanta
mafita,shin ko dai ta tare shi ne ta fada masa?
wata zuciyar ta ce,In ko ya dinga kwallo da ke
sai kin rasa mai cetonki. Ta tashi tare da
cewa,Bari kawai in fada ma Tsohuwa.Zuciyarta ta
sake rayawa.Tsohuwa fa ba zata yarda ba, domin
kullum tana bada shaidar tsanar da Ya Abba ya
mata,ta koma ta zauna. Sai ta samu kanta da
fashewa d kuka,tana fadin wannan wace irin fitina
ce ta same ni?me yasa zcyt ke son tozarta ni?
Me yasa zata so wanda ya tsane ta?Ta mike ta
shige uwar daka. Gado ta hau tana son ta lallashi
zcyrta,dn ta daina son Ya Abba. Shi kuma yana
tafe a mashin zcyrshi na mitar bata gaji da ganin
Ummi ba,yadda take ta kai kawo ya ke gani a
idonshi. Lkcn da ya kai musu abnci me jego ta
gyare,dama ta zubar d jini ne shi yasa suka ki
sallamarta,sukace sai da Safe. Ya samu kannanta
sun zo da wata 'yar Babnsu.Sun gaisa an yi 'yar
hira sannan suka ta fi lkcn ya dauki 'yar ya yi
mata kallon sosai. Ya dubi Umma kin san
yarinyar nan da wa take min kama?Ta ce,A'a.
Bishira ta tsare shi da ido,ya ce lkcn d Ummi na
karamarta sak wannan. Umma ta ce,Kana nufun
d Ummi take kama?ya ce,"Eh,Bishira ba kunya ta
ce,Allah ya kyauta ni 'yata bata kama da wata
can wai ummi. Umma tayi saurin cewa,Dama
zolayarki yake ba suyi kama ba.Shi kuma ya
kalleta.Ko ki so ko kada ki so yarinyar nan sak
take kama d Ummi. Ya mika ma Umma ita,yana
ci gaba da fadin Maman Walid kina bani
mmki,kina zaton zan ki raba 'ya'yanku d Ummi?
Ya girgiza kai"Sun hadu hr abada ,domin in kin
tsaga jikin 'ya'yanki dole za ki ga jinin Ummi. to
ya ya ma ki ke tsammanin zan so wanda ba ya
son Ummi? Ta ce, "Oho! Ni ba ka sona kenan?To
in da na gode ma Allah dk dyniya ta san cewa
Ummi bata kaunarka.dk da kana wanta.Ba ita ba
ce silar kariyarka?ko an kashe ka ma bata da
asara. Umma ta ce,'Abba jeka ban son in kuma
jin bakinka in na isa. / ZURFIN CIKI book 2 part 7
ZURFIN CIKI book 2 part 7
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:16
Ta samu an saka ranar auren fati da saurayinta
Fahat,nan fa Alhj ya ce dama ke ni ke jira uwata
ki dawo. A masu sonki ki fito da daya a hada
auranku da 'yar uwarki Fati. Hankalin Ummi ya yi
matukar tashi,ranar kasacin abnci tayi. Da suka
zauna da Umma a daran ta ce Umma baki fada
ma Alhj bani da tsayayyen saurayi ba?Umma ta
kalleta,ba shi yasa na ce Kitsada ba,amma ba kya
son fita. Duk kin bi kin kori masu sonki Abba na
daure miki gindi,kin san dai Alhj ba yarda zai yi ki
wani ci gaba ba,gara ma kin yi kokarin fidda miji
kafin lkcn da ya dibar miki,in ki ba haka ba ya
daki da mai rabo. Ummi tasa kuka ranar,kwana
tayi tunani hr ta yanke shawarar zata fada ma
Alhj Ya Abba take so. Da safen taje hr dakin Alhjn
ta gaishe shi,ya ce uwata naga kamar bakinki da
magana ko?Ta dube shi "Eh,a'a ba komai.Ta
mike,dakin Tsohuwa ta shiga ta haye gado ta
soma kuka. Tsohuwa ta dubeta a rude,Takwara
ke da waye,? Nasan ba zai wuce me sunan
Malam ba,dn shi ne kadai ke hana ki sukuni. A
ran Ummi ta ce,shi ne kam,amma ba irin wanda
ki ka sani ba. Amma a fili sai ta ce,Tsohuwa Alhj
ne wai in fito da miji,kuma abn da ke damuna ni
ba wanda na ke so. Tsohuwa ta ce, "Au, shi ne
abn kuka?To bari kiji bana ba zan goyi bayabki
ba,dn da ubanki ya ji ta tawa da yanzyn kina da
diya 2 in da rabo. Amma mai sunan Malam ya ce
za ki ci gaba da krt,yamzun ko tun da Allah ya
kawu mu angama wannan kaddararriyar mkrnt ba
sai aure ba? Ga Bunta nan hr an yi baiko, to rana
guda za a yi shi in muna cikin masu rai. FUU
Ummi ta fice,ta shiga dakin Umma tana tunanin
wa zata fada ma matsalarta?kamar an tsikareta
ta dauki mayafi zata fice. Umma ta ce, "Zo nan,
ina za ki? ta ce "Wurin Fati. Tana shiga Bashir
zai fito . Ya ce Yauwa Ummi ina son magana da
ke. Ta dawo baya ya fita kofar gida ita ma ta
fito,suka tsaya ya ce "Ummi gaskiya dama ba
wani abu ba ne, ni dai na tsinci kaina da sonki.
Ummi ta dafe kirji da sauri."Sona?" ya ce kwarai
kuwa, dn haka za ya ki ka gani?ta dube shi,sam
babu wata alama da ke nuna cewa dan uwan Ya
Abba ne. Ta girgiza kai "kayi hakuri kawai Ya
Bashir,wlhy zuciyata ta jima da kamuwa da son
waninka." ya ce, Me ki ke nufi?Kin fi son bare da
ni jininku? Ummi ta ce,"Ni dai na fada maka." Ya
ce, "To kin fada min,ni kuma zan fada wa su
Alhj." Gabanta ya fadi. Shi kuma ya yi tafiyarsa, .
Sabon tashin hankali kenan. Sai damuwa ta
lunku,bata ta6a marmarin zamn mkrntr kwana ba
sai ranar. Ta rasa me zata yi taji dadi,gida ta
koma cike da nadamar fitowa,ta zauna a falon
Umma ta soma kuka. Umman tana dakin mijinta
ya yi karin kummali. Sai da ya fita sannan Umma
ta maido hankalnta ga lamuran gidan, kan kujera
ta samu Ummi ta nata rera kuka. Umma ta ce
"Ke Ummi lafiyanki? Abun ya soma zama iya
shege,daga cewa ki fito da miji sai ki tsira kuka?
To ina ganin kwadantaki zamu yi muci. Ummi ta
ce, "Ni fa ba kukan da nike yi ba kenan,ni fa Ya
Bashir ne fa. Umma ta ce Bashir me,? kiranki aka
yi? Gara daya da ke ki. ta ce ba fa dukana ya yi
ba wai cewa yai wai fa yana sona. Tab,Allah ya
tsare ni. Umma dn Allah bana sonshi,gaban
Umma jikinta a mace ta ce "Tabdi,ai ko in Alhj ya
ji wannan zancan ta zauna. Ummi ta sake
firgicewa, cikin kuka ta ce Da na shiga 3 Umma,
ya ya zan yi ne don Allah?Umma ta ce,"Mafita
daya ce ki fidda wani kafin zancan yaje wurin
Alhj. Yinin ranar Ummi ta rasa mafita Addu'arta
daya,Allah ya turo mata ko ma waye a daran yau
ta ce ya turo iyayenshi. Wayar Umma tana
hannunta,ta rubuta text ta goge yafi sau 20 da
niyyar ta tura ma Ya Abba cewa tana
sonshi,amma da ta tuno da irin dukan da zai zo
gidan ya yi mata in ya karanta sai ta share. Ita
dai ta san shi kadai take so. Tayi Sallar Istihara
kusan sau 3,amma hr yau zcyrta na nan makale
da son Ya Abba. Don bayan Isha'i kuwa a ka aiki
kiranta, ai tare da dan aike suka fita. Wani
saurayi ne wai shi Sahabi,dan unguwar ne Kuma
sana'ar aca6a yake yi. Na dai manta. Suka gaisa
ya gabatar da kanshi sannan ya fada mata dalilin
zuwanshi ba tare da wani nazari ba,ta ce ta
amnice. suka yi sallama ta dawo gida,umma ta
tambaye ta wanene?Ta fada mata,sai dai Umma
bata gane shi ba. Can jimawa Bashir ya aiko
Kamal kaninsa wai Ummi tazo,ta ce kaje ka ce
masa ba zan zo ba,ya sake aiko shi cewa in bata
zo ba shi zai shigo. Umma ta ce mata tashi kije.
Ummi hr d kuka ta fita,dn a rayuwarta ta tsani
Bashir,sbd yanda ya raina Umma. Kuma ba ya
ganin kowa da gashi sannan tana ganin in hr ta
auri Bashir zai mata tsakani da auren Abba. Tana
zuwa ta same shi zaune a dakalin kaofar gida,ta
isa gurishin. Ya Bashir kiran me ka ke min? Ya
ce,kin sani kema. Ta ce Ya Bashir dn girmn Allah
ka bar ni ba,Usaina gidan kurma ce buduwarka
ba? Ya ce Da ba, ya ci gaba da cewa,Ummi ina
sonki so na hakika nayi mamakin yadda lkc daya
zcyta ta kamu da sonki,to wai dn Allah ni me
yasa ba ki sona? ta ce Ya Bashir ina da wanda
nake so tun farko..........kamar daga sama suka ji
muryar Abba yana cewa,Kai Bashir me ka ke
fada? ya ce sonta nake. Abba sai da wayarshi da
ke hannunshi ta kwace ta fadi don figici,bai bi
takan wayar ba ya isa gabn Bashir ya ce, In ka
kuma furta kalmar so ga Ummi sai na maka
matsiyacin duka,ke kuma hr da fitowa kin zo tadi
ko? kafin tayi magana ya ce,Bace min daga nan.
Bashir ya ce,Amma ai ba laifi ba ne don nace ina
sonta? Abba ya bige mishi baki tare da cewa In ji
wa ya ce maka ba laifi ba ne?Bashir ya ce,An
haramta aure tsakaninmu ne? Abba ya cakumo
wuyan rigarsa Ni ne nan na haramta haka,kuma
kar in kara jin wannan mgnr. Bashir ya fige ya
nufi gida yana fadin cewa Yau zan samu Alhj da
mgnr. Ina ruwanaka da zaka ce ka haramta min
sonta? . Abba jikinshi hr 6ari yake dn tashin
hankali, yasan in mgnr taje teburin Alhj to ta kullu
yanda yake mishi mgnr hada auran Ummi da Fat.
Har ya saka kafa a zauran gidan su Umma,sai
kuma ya fasa ya dawo ya nufi gidan su Bashir
din,yana saka kafa a zauren gidn Alhj Krm na
fitowa. Don haka sai yaja baya,Alhj ya fito ya
ce,A'a Abba ne? Abba ya ce "Eh ni ne. Ya gaida
Mahaifin nasa,sannan Alhj ya tambaye shi cewa
Babn naka yana gida? Gaban Abba ya yi
mummunan faduwa,ko dai Bashir ya fada wa
mahaifinsu ne? Alhjn ya ce ko ba ka ji ba?Abba
ya ce "Eh a'a ban riga na shiga gidan ba. Alhjn
ya ce To bari in ganshi. Nan jikin Abba ya jike da
zufa. Da azama ya shiga gidan. Mahaifiyarsu tana
alwala ya ce Umma ina Bashir? ta dube shi
Lafiya ba ko sallama? ya ce Nayi ba ki ji ba ne?
ta amsa sannan ta ce lfy ka ke nemanshi? ya ce
lfy lau. ta ce Yana daki,shima na ganshi ya shigo
a fusace. Abba ya nufi dakin. Bashir na zaune kan
katifar idonshi na kasa yana girgiza kafarshi ta
dama,Abba ya shiga ya ce,Bashir nazo ne in sake
gargadinka a kan Ummi,sai dai naga hr kayi
kuskuren fada ma Alhj krm ko,? Bashir ya mike
ya daga sauti Ban fada mishi ba,amma ina da
niyya. Ina sonta babu wanda kuma ya isa ya
hana ni sonta. Abba ya kashe masa fuska da
mari. Sai suka ji muryar Mahaifiyar tana cewa,
Kara mishi Abba,ka cika dana. Ta shigo dakin hr
gabn Bashir ta ce, Ni za ka tozarta? kayi kuskure.
Ai da in ga ranar aurenka da Ummi gara naga
gawarka kwance yafi min sauki. Abba da Bashir
suka dubeta a rude. Ta ci gaba da cewa Bashir
kai ma kasan ba zai ta6a sa6uwa ba ne in hada
jini da Suwaiba,kafi kowa sanin kin da nike
mata,zan iya daukar ranta ba don tsoron hukuma
ba. Kuma hr dny ta nade ba zan ta6a kaunarta
ba,kai ko fatan alheri ba zan ta6a mata ba. Ta
kalli Abba, Baka ta6a faranta min rai ba irin
yau,dama nasan cewa dole wata rana ka bayyana
dana in dai kai jinina ne,na gode Allah da yasa ka
zama mai kishina Kuma ka wanke dukkan
laifukan da ka min a baya da ka nusar da ni
Bashir na shirin jefa rayuwata a cikin garari,da ba
ka mishi mgn ba yaushe zan san yana shirin jefa
ni cikin bala'i. . Abn da Umma bata sani ba shi
ne,tuni Abba ya yi mutuwar tsaye,hnklshi ya
ninka na Bashir tashi,dn haka Bashir ya riga shi
fita daga dakin. Da kyar Abba ya dago ido ya kalli
Umma,ta ce Daina damun kanka shi ma din ko
ba don Allah ba zai dawo hanya,duku-dukayau
sati guda fa kenan da naje kauye na saida 'yar
Akuyata guda daya sannan na bada kaji 2 ga
Bokan kuka sbd a min akin da Ummi ba zata
samu miji ba. Sai kuma a ce ko satin bai rufe ba
dana na cikina ya zo ya ce yana sonta? Da sauri
Abba ya dafa kirji Umma Boka! Boka ki ka ce
Umma? Inna lillahi wa'inna ilaihin raji'un,Umma
kin san cewa zuwa gurin Boka shirka ne ga
Allah? kin san duk wanda ya mutu a shirka Allah
ya yi alkawarin kona shi a wuta?Umma kina cikin
hadari............ta kaste shi. Kai Abba!Ni ce nake
cikin hadari?Ni ce Allah zai kona a wuta? ya ce,
umma bana nufin haka, ina fada miki ne ki kiyaye
da zuwa gurin Bokaye makaryata,macuta 6arayin
Imanin Jama'a. Na ranste miki da girmn Allah
umma Bokaye 'yan wuta ne,matsawar ba su tuba
ba. Ta ce, Kai ni rufe min baki,da za ka ce karya
ne sau nawa suna min asirn kuma yana ci. Ba
gashi nan da ya min na kada Ummi ta riga Fati
samun miji baga Fatin ta riga samun ba? ummi
kuma ba ta d masoya. Abba ya ce, Umma kin ga
karya ko? wa ya fada miki Ummi bata d masoya?
ta ce, To me yasa ba wanda ya tsaya? Ya ce, Ni
dai Umma ki bar zancan nan a wurina, Bashie zai
bar Ummi ko yana so ko baya so,dn haka na
hada ki d girmn Allah kada ki koma gidan
mishieikin Bokan nan. Ta ce, Ba zan koma ba in
hr zaka raba Bashir da alakakai din yarnyar nan.
Ya ce Na miki Alkawari. ta ce, Shikenan. Ya fice
jiki babu karfi.URFIN CIKI book 2 part 8
ZURFIN CIKI book 2 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:18
Kasa shiga gidan su Umma ya yi,haka nan ya
manta sam da batun motar da yazo da ita a
kofar gidan Umma. Ko Bishira bata san cewa ya
shigo gidan ba,tana can jarabar kallonta na
tsiya,ya rufe gidan ya nufi dakinshi. Ranar mu2m
5 bacci sai dai 6arawo,Umman Bashir kwana tayi
saka da mugun zare. Umman Abban ma juyi
kurum take yi hr Alhj ya gaji ya ce,Yau dai sai
juyi ki ke yi. ta ce Na kasa bacci Alhj. Ya ce,
Tashi to kiyo alwala kizo ki kama sallah,in kina
da damuwa ne sai ki fada ma Allah. Umma bata
tsaya ba,ta tashi. shi ko Abba wani matsanancin
ciwon kai ne ya hana shi sallah. Ya dai yi
nasarar yin alwala da ya shiga daki sai jiri. Dole
ya kwanta rigingine tare da dafe kanshi da
hannuwa guda 2,sunan Allah yake ta kira dan
neman dauki. Ita ko Ummi dirshan ta zauna tana
kuka,hr sai da hawayenta suka kafe,idanunta
suka shiga zafi,kanta ya soma sarawa gefe daya.
Ita ma ringingine ta kwanta tare da lumshe
ido,Istigfari kurum take yi tare da hailala,shi ko
Bashir mafarkai ne suka hana shi bacci,dk
mafarkan na Ummi ne. Da safe da matsannancin
zazzabi ya farka,dn haka bai iya zuwa Masallaci
ba,da kyar ya yi alwala.yana idar da sallah ya
kundundune cikin bargo. Matsanancin ciwon kan
da Ummi ta tashi dashi ya firgita 'yan
gidan,Musamman Umma wadda ta same ta
kwance a tsakar daki da safe. Ganin fuskarta a
kumbure ya tsorata Umma,hr sai da ta kira
Alhj.Nan fa Alhj ya dauko wayarshi ya shiga kiran
Abba,kan cewa yazo ya kaita asibiti. Sai dai tayi
ringing ya kai sau 10 amma ba a daga ba. Alhj ya
ce Ina yaron nan ya shiga ne?kuma ga motarshu
a kofar gidan nan,na ganta da asubahi da na fita
Masallaci. Umma ta ce,Tao Allah yasa dai lfy.
Har karfe 8 Alhj na neman layin Abba shiru ba a
dauka ba,ga Ummi rike da kai tana ta salati
Umma ta ce,Alhj ko Bashir za ka sa ya duba shi?
Alhj ya koma daki ya dauki hula ya nufi gidan
Abba. Gidan a kulle ya same shi,dn haka ya dinga
bugawa.Abba na jiyowa amma ba zai iya tashi
ba,haka dk ringing din da wayarshi ke yi yana ji
ya kasa tashi ne. cikin bacci Bishira taji bugun
gida ya yi yawa,ta tashi ta bude. Da Alhj suka yi
ido 2,ya ce lfy ba ku tashi ba? Ta ce Mun tashi.
ya ce Ina maigidan naki? ta ce Ina ga ya fita,bari
in duba. Ta juya ta nufi ciki. Alhj ya cika da
mmk,ya za a ce wai mace bata san fitar mijinta
ba? Anya wannan matar tasan darajan mijin?
Tunaninshi ya katse lkcn da ta dawo tana cewa
Alhj yana kwance ba shi da lfy. Alhj ya bita yana
cewa Ba shi da lfy,amma ke ba ki sani ba?Wanna
wane irin zama ku ke yi ace kina matarsa amma
ba ki san cewa ya tashi ba lfy ba? Bishira ta ce
To ai shi ne bai kira ni ya fada min ba. Alhj ya ce,
Allah ya kyauta. ya nufi dakin. Abba na kwance
ya kundundune cikin bargo sai rawar sanyi yake
yi. Alhj ya yi Sallama ya shiga dakin ya rusuna ya
daga daidai fuskarshi ya janye bargon ya ce,
Abbana ba ka ji dadi ba? Abba ya bude
ido,idanunshi jajir,ya ce Abba kaina ne tamkar zai
6alle. Sai zazza6i tun daren jiya. Alhj ya ce,Ikon
Allah Yau kuma abn da na wayi gari da shi
kenan? Ummi ma na can kwance da ciwon kan,to
tashi. Shi yasa nake ta kiranka don ka kaita
asibiti amma da ka daga ba. Yanzu tashi in za ka
iya ka kira Ahmada abokinka sai ya kai ku
asibitin. Abba ya ce To Wayar Ahmada din a
kashe don haka sai Alhj ya ce "Af, na tuno da
Bashir,kintsa bari in je muzo naga mator can
kofar gidanmu ko?Abba ya lulubo makullin motar
yaba Alhj., Zani kawai Umma ta daura ma
Ummi,sai ta zura mata hijabi,suka shiga bayan
mota su 3 da Umma da Alhj,sukaje gidan Abba
suka dauko shi. Bishira taso zuwa amma suka ce
ba wuri ta bar shi kawai. Asibitin kudi ne kuma
likita guda ne ya duba su. Ummi dai hawan jini
ne don ita a ka fara dubawa. Gado likitan ya
bata,sannan Abba ya shiga shima likitan ya ce
jininsa ya hau,amma ba kamar nata ba. Nan ya
roki likitan cewa kada ya fada ma iyayensu abnda
ke damunsa,ya rubuta mishi magunguna kawai.
Likitan ya ce Ba komai. Amma me ya ke
damunku kai da sister dinka ciwonku iri daya
kuma ya kama ku a lkc daya? Abba ya ce Ba
komai lalura ce kawai a ka kaddara ta same su
lkc daya.Da Abba ya fito sai ya ce ma su Alhj
Zazza6i ne. sai dai shi kanshi ya ji mmkn
ciwonsu iri daya. Yana jingine da bango a dakin
da a ka ba Ummi gado,yayin da Bashir ya tsaya a
gabn gadon Umma tana zaune a kan kujera. Alhj
krm d Bbba suka shigo tare da Likitan ya kalli
Abba Yarona kana bukatar bacci ga. Abba ya ce
To yanzun zan tafi gida. Ya iso kan Ummi wadda
a ka daura ma ruwa,ya ce ku barta ta huta bata
bukatar hayaniya,don haka ku rage daga cikin
dakin. Alhji ya ce, To mun gode. Suka tafi suka
bar Umma. A mota Alhj ya ce da Abba,ka fada a
wurin ainkan? ya ce, Eh abokin aikina ya kira ni
kuma na fada masa. Alhj ya ce,To shi
kenan,yanzun sai muje can gidanmu zaka fi
hutawa... .Yanayin aikinku ne ba ka samun bacci
ko? eh kurum Abba ya ce,amma shi yasan
tunanin Ummi ne ya ke hana shi bacci da
matsalolin da yake hangowa. Yinin ranar yasha
bacci,sai kusan 4 ya tashi ya yi Sallah,ya ji dadin
jikinshi. Bishira tana gidan Umman Bashir wai ita
da tazo jinyar miji,tana bata lbrn wai Abba bai
fada mata ba shi da lfy ba,ya kira Alhj yazo yana
ta min surutai wai mijina ya fita ban sani
ba,meye- meye? Umman Bashir ta ce, Da Allah
kyale su,don wani sabon iskanci ma wai Bashi ne
ke son Ummi. Bishira ta mike zumbur tare da
cewa, Bashir fa ki ka ce Umma? Hu'um,lallai da
wani abu. Bashi da ya tsani Ummi shi ne zai ce
yana sonta? Umma ta ce, Sannu 'yar albarja,ashe
kin fahimta,? Tabbas nasan ke za ki fahimta,to in
gaya miki Bashir ko yau da safe fa sai da muka yi
ta dashi. Dubi yadda Bashir ke min biyayya amma
yau ina fada yana fada. wai hr da ce min shi bai
ga wani mugun halin Suwaiba da nike fada
ba,tana min alkairi amma ni kullum ina binta da
sharri. Kai dai jin wannan zancan ka san ba yin
Bashir ba ne,don haka na ce masa ba komai
nasan ba yin ka ba ne. Bishira ta ce,Tabdi,Umma
sai kin tashi tsaye. Ta ce ke dai bari ai ina cikin
wani hali shi kanshi miji naki sai na nema masa
taimako. Don wannan ciwon nashi ban yarda shi
ba, kuma lkcn daya. Fati ta shigo gidan da
sallama,ta shiga dakinsu ta canza kaya. Umma
ta ce,sai ina? ta ce Ya Abba ne ya ce in zo in
canza kaya zamu je asibiti wurin Ummi. Bishira
ta mike ya farka ne? Ta ce Eh hr ya yi wanka da
sallah Umma ta ce Bari in same shi bai gama jin
sauki ba zai tafi wurin wata can kema banza
mara kishi kin taho jiki Na 6ari,Fati ta ce,Umma
don Allah ki daina irin wannan abubuwan,wlh
Umman su Ummi bata yin haka Bishira ta fita
tana fadin Ai Ummi yanzun ita ce uwar Fati, don
bata jin mgnr kowa sai ta Ummi,tunda ta dawo
mkrnt. Sun samu Tsohuwa ma hr ta shiga
mota,shi kuma Abba yana jingine a jikin Motar
yana sanye da shadda (Sky blue) Rigar 'yar 3
Quarter kanshi da hula. Bishira ta ce,Babn Walid
hr ka tashi? ya dube ta,sannan ya kai idanunshi
kan fati Shiga muje. Bishira taja baya Ina ba in
da za ni. Ya kalleta ke Kuma ke da wa? Wa ya
fada miki da ke nake? yaja tsaki. Ta iso Ummar
tasu Abba ka hakura mana da wannan tafiyar. Ta
ce Naji sauki Umma. Tsohuwa ta ce, Mai sunan
Malam ka shiga don Allah mu tafi. cikin sauri ya
fada mota suka wuce. Yana yi wa Umman nuni
da Hannu wai yana zuwa. Tsohuwa ta
ce,Kinibibin banza ne da wannan matar taka mai
sunan Malam kana bukata kara aure,me a ke da
kazamar mace? Abba ya ce, Tsohuwa sha
kuruminki zan sake aure,ke ce ma za ki bani, Ta
ce, Ni a wa zan shiga maka ga . Bishira ta fita
tana fadin Ai Ummi yanzun ita ce uwar Fati, don
bata jin mgnr kowa sai ta Ummi,tunda ta dawo
mkrnt. Sun samu Tsohuwa ma hr ta shiga
mota,shi kuma Abba yana jingine a jikin Motar
yana sanye da shadda (Sky blue) Rigar 'yar 3
Quarter kanshi da hula. Bishira ta ce,Babn Walid
hr ka tashi? ya dube ta,sannan ya kai idanunshi
kan fati Shiga muje. Bishira taja baya Ina ba in
da za ni. Ya kalleta ke Kuma ke da wa? Wa ya
fada miki da ke nake? yaja tsaki. Ta iso Ummar
tasu Abba ka hakura mana da wannan tafiyar. Ta
ce Naji sauki Umma. Tsohuwa ta ce, Mai sunan
Malam ka shiga don Allah mu tafi. cikin sauri ya
fada mota suka wuce. Yana yi wa Umman nuni
da Hannu wai yana zuwa. Tsohuwa ta
ce,Kinibibin banza ne da wannan matar taka mai
sunan Malam kana bukata kara aure,me a ke da
kazamar mace? Abba ya ce, Tsohuwa sha
kuruminki zan sake aure,ke ce ma za ki bani, Ta
ce, Ni a wa zan shiga maka gaba a baka ku taru
kai da matarka ku halakata?Duk da Abba yana
jin jikinshi gim, sai da ya dar dara,sannan ya ce,
Sai ka ce ma su yankan kai? Tsohuwa kuma da
za ki ce na cika zcy yanzun ba ga mata nan ina
da ita ba tana kawo miki karan ina dukanta ne?
Tsohuwa ta ce Tabdi,ni yaushe ma wannan
guzumar matar taka zata zo guna da sunan kawo
min kara? Ban da ma haka ni bani shi da mara
kunya. Ya ce, sai Ummi ko? koda yake ita ai
takwararki ce shi yasa lkcn da tayi tata rashin
kunya ta zama 'yar lelanki. Tsohuwa ta ce ai
wannan ba kuciya ba ce? Yanzun ko kai ba ka fi
ta hankali ba.Abba da fati suka sa dry. suna isa
dakin suka samu Umma suna waya da Alhj,Ummi
kowa hr lkcn bacci take yi. Abba ya jingina da
bango yayin da Tsohuwa da Fati suka je suka
tsaya a gabn gadon. Sunyi Sallama da Alhj shi
ma ya kira ne ya ji ko Ummi ta farka. Ta ce
masa ba ta farka ba,kuma Likitan ya ce an fi son
tayi baccin. Nan suka gaisa tare da tambayar mai
jiki,Abba kallon Ummi yake,yau daya duk ta fyade
kmr ta yi sati,sonta da tsananin kaunarta ne
suka sake mamaye ko'ina na jikinshi. Ya kalli
Umma wadda ke tambayar nashi jikin, ya ce da
sauki. Sannan ya kalli Ummi tare da cewa Umma
wai dame Ummi ta fara? Umma ta ce kamar ya
ya? Ya ce mmkn ciwon Ummi nake,wai hawan
jini?Dama can bata da lfy ne? Tsohuwa ta amshe
da cewa, ko kai ai kasa mata hawan jini,irin
tsanar da ka mata Mai sunan Malam ai ta isa.
Abba ya ce Don Allah Tsohuwa ki daina mgnr
nan. Ya dubi Umma yana me kara maimaita
tambayarshi. Ta ce ko kusa ai kasan Ummi bata
cika laulayi ba ma,lalura ce dai yanzun bata ga
babba ba ta ga yaro,amma mafari daga yi mata
zancen aure shi kenan take ta kuka. Abba ya ce
to don Allah Umma ku barta da zancen nan,ina
krtn take so tayi kayanta,don gudun hawan jinin
nan kada yakw tashi akai-akai. Tsohuwa ta ce
Don kawai kada jinita ya hau sai a zura mata ido
kada tayi aure?ai ko lallai sai dai kada jininta ya
sauka. in ya hau,aure ya haifeta dole tayi shi,in a
kasarmu ce ta Zamfara wane ita. . Abba ya ce
Muje in kai ki gidan Tsohuwa. Ta ce ban tafiya,
sai naga dama Umma da fati suna ta musu dry.
Nan dai Abba ya fita yaje wurin likitan ya amshi
takardn maganin,dn da farko bai rubuta ba
magaungunan ba. Kwanan Ummi 3 a asibiti a ka
sallem ta. Abba ya kwashe su zuwa gida.
Saurayinta Sahabi zuwanshi 2, kuma sun je da
mahaifiyarshi. sai lkcn ne ma ta mishi kallon
tsaff,sam ita ba sonshi take yi ba,sai dai gara shi
da Bashir. Kuma ta lura Bashir din da gaske yake
yi. Domin kullum zai zo safe da yamma,haka nan
yakan dan tsaya hr yafi Abba wanda ke zuwa sau
daya hr tana cewa ina ma yadda Bashir ke nuna
tausayinshi a gare ta Abba ne. An shuri sati 2 da
sallamo ta kuma ta warke sarai,sai dai fa hr
yanzun Alhj yana nan kan bakanshi,ganin Bashir
na son takura mata sai ta daina fita. Abba ya
kira Basshir shagonshi wani yammaci,ya sake
fada masa ya rabu da Ummi sai dai yau da
lallashi yazo masa,. Ya ce Bashir ka ga
mahaifiyarmu bata sonka da ummi,dn haka ka
hkr ka nemi wata,na maka alwashin kashe ko
nawa ne dn yin hakan zai faranta ran Umma.
Bashir ya yi 'yar dry,sannan ya mike tsaye Ya
Abba kenan! kana tsammanin ni wawa ne?nasan
ba don Umma ka ke fafutukar in bar Ummi ba
kana yi ne don kana sonta. Gaban Abba ya
fadi,cikin saurin baki Abba ya ce,In ji wa ya fada
maka? Allah ya kiyaye. kai ka san Ummi kanwa
na dauke ta. Bashir ya kakki cikin idon
Abba,sannan ya ce,"Haba Malam,fadan da ka ke
da kalaman da ka ke furtawa suna nuna kishinka
ne karara. Dubi cikin idanunka,kishinUmmi ka ke
yi. don haka sai ka hkr ka bar min ita,domin ka
san ba wanda zai fi girgiza Umma tsakanina da
kai irin ka. Ya nuna Abba da yatsa, Za tafi bakin
ciki ka zama mijin Ummi fiye da ni. Abba ya daga
hannu ya falla mishi mari Bashir ya dafe wurin
sannan ya kalli sau 'yan shagon wadanda marin
ya janyo hankalinsu. Don farko ba su san abn da
a ke tattaunawa ba.Bashir ya ce, ka mare ni?
Abba ya ce, Zan kara maka,ko za ka rama ne?
Bashir ya ce, Ba zan rama ba,amma zan fada ma
su Alhj yau dinnan ina son Ummi. ya fita fuu.
Abba ya zauna ya rike kai yana huci. shi kam
Bashir ya kudurci niyyar fada wa iyayensu yau
dinnan. Abba ya kira wayar Umma ta daga suka
gaisa lkcn karfe 6 na yamma ya ce, Ummi fa? ta
ce Gata can kwance. Ya ce Ba dai jikin ba? ta ce
A" aikin karance-karancenta take. Ya ce, Ba ni ita
Umma. Umma ta kwala ma Ummi kira,ta mika
mata wayar tare da cewa "Yanyanki ne ke son
magana da ke. Yau ce rana ta farko da suka yi
waya a matsayin shi na Abba,ita kuma Ummi, in
an debe lkcn da suka yi waya a matsayin shi na
Abba ita kuma Suhailat. Tayi sallama cikin sanyi
murya can kasan makoshinta ya amsa tare da
runtse ido sakamakon tsigar jikinshi da ta tashi.
Ya ce "Ummi ta ce Na'am yaya. Ya ce "Kina son
Bashir? ta raunana murya. Yaya am sorry to say
bana son shin gsky. Ya ce To yau kam zai sanar
da su Alhj cewa yana sonki,in kina san kida
wanda ki ke so to ki gabatar da shi kafin shi ya
rigaki. Takaici ya kama ta, kamar ta ce, Ni kai na
ke so.......ya ce kina jina? ta ce,To Ya ce, kin san
in su Alhj suka ji ba ki da mafita,Ummi ta ce To
ni fa bani da wanda nake so shi ne ban san
yadda zan yi ba. Ya ce, shi kenan matsalarki ce.,
ya kashe wayar. Ummi tayi shiru tana tunanin
mafita,ko dai ta hkr ne ta aure Bashir din? kai a'a
to kuma gashi wanda take so ya ce matsalarta
ce. Can dai ta yanke yadda zata yi,don haka ta
kosa Alhj ya dawo. Tun kafin suje wurin cin abnci
ta same su a dakinshi su da Umma,ya yii wanka
yana kokarin fita sallar magriba. Ta ce Alhj dama
wanda ya ke zuwa gurina ne ya ce in fada muku
iyayenshi za su zo. Dadi ya kashe Alhj ya ce To
to dan nan unguwar ne? ta ce Eh ya ce To
madallah dama wannan yaron na sabon titi din
nan Suwaiba wanda kwanaki nake fada miki
nasan ubansa a kasuwarmu ya ke? Ta ce Naji
wanda ya soma zuwa wurin Ummi? ya ce Shifa,
Uban danai masa zancen naga dansa wurin 'yata
sai cewa ya yi auran gida za su yi masa,ko ni na
so hadin nan sai dai Allah bai so ba. Ya kalli
Ummi Yaushe za su zo? ta ce Ya dai ce in
tambaya ne. Alhj ya ce To Allah ya kawo su. Da
dare Sahabi yazo ta ce Sahabi an ce in maka
mgn ka turo ya ce Alhamdulillah, dama ina son in
miki mgn sai ina tsoron kada ki ce ya yi wuri don
haka gabe zan turo. Bashir yazo ya zauna gabn
Alhj suna cin abnci ya gaishe su. Suka amsa ya
yi shiru yana tunanin ta ina zai fara? Alhj Babba
ya ce ya ya Bashir akwai wata matsala ne?Ya ce
Am dama ina son in ce ni dai ina son Ummi ne.
Ummi kuma?Alhj karami?Ya ce Eh Alhj Babba ya
ce Ta amma ya aka yi kayi nauyin baki hr a ka
ba wani dama? Bashir ya ce Alhj Wanene? Alhj
karami ya ce Sai ka san shi? koda ba a tambaya
ba, ba zan ba da goyon baya a baka Ummii ba,
tashi ka bamu wuri. Abba ya ce, Bashir je ka ci
gaba da addu'a Allah yasa Ummi ta zam
rabinka,zan so haka dn na jima ina son zumuncin
nan. Iyayen Sahabi sun zo kuma an basu hr ma
an tsaida ranar daya fa ta Fati. Tun daga ranar
Ummi kullum cikin kuka take wanda iyayenta
suka kasa gane nufinta. Bashir bai daina cin
alwashin sai ya auri Ummi ba, dn haka kullum
cikin aiken kiranta yake. Ban da haka ma ya
maida hnkl kan sana'arshi tunda ubansa ya mishi
gorin wa zai ba shi mata ya ki tsayawa sana'a
nashi ganin in ya rike sana'a r za a ba shi. Abba
kuwa ya ji ya yi ma gidan wai don ya goge Ummi
a ranshi. Anya "ZURFIN CIKIN nan zai kai su? .
Sai mu hadu a littafi na Uku don jin yadda za a
kare. ZURFIN CIKI book 3 part 1
ZURFIN CIKI book 3 part 1
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:21
Na Halima Abdullahi K/Mashi 1... Abba ya fito
cikin suit bakake, yayi kyau matuka hatta
takalminshi sawu ciki baki ne, tamkar wani black
America. Igiyar wuyan ta zauna tsam, sai kamshi
yake. Dakin Bishira ya nufa ya daga labule, ta
dago ta kalle shi yayi matukar birgeta. Tana
alfahari da shi matsayin mijinta, ya ce "Kin
shirya?" ta ce,, "Zuwa ina?' Ya ce, "A'a, jiya fa na
sanar da ke ki shirya da wuri zamu je asibiti ki
gaida Ummi". Ta watso mishi wani kallo uku
saura kwata, tare da cewa "Ko garin nan ba a
sanyi ba zan fita gaida wata can Ummi ba bare
da sanyin nan." Ya ce, "Dalili ta mike tsaye "Ciwo
bai kai mutuwa ba, da mutuwa ya yi tazo ta min
gaisuwa?" Takaici ya turnu'ke Abba, da yake
sarkin dankara magana ne, sai ya ce "To ita ta
kashe shi da zata miki gaisuwa?" Ta kule da
bakin ciki ta zabga mishi harara "To ai kasan ni
na dora mata ciwon, don haka dole in je
gaisheta." Ahankali yake tukin, kira'ar Ahmed
Suleiman ce ke tashi wadda ya yi murya biyu
cikin sanyin murya. Wayarshi d ake gefe ta soma
ruri. Ya kali fuskar wayar, Hajiya Nina ce, don
haka ya ci gaba da tukinshi, kusan kira na bakwai
sannan ya daga. Ta ce, "Lokacinka ne za ka iya
yin duk yanda kaso, amma kafin kazo hannuna
wacce shawara ka yanke?" ya ce, "Ta me?" Ta
ce, "Au, ka manta kenan? To ba damuwa za ka
zo yau ne ko sai an dauko ka?" 2.... 'Yar dariya
ta kufce masa, "Ki sa a dauko ni sai ka ce wani
karamin yaro? In kin ci gaba da bibiyata za kiyi
nadamar hakan." Ta ce, "Ko kuma kai kayi ba, na
baka awa goma ka kawo kanka in ko ka 'ki, hum!
Za a kawo ka." Abba yaja tsaki "Yanda ki ke
zatona na wuce haka". Ta ce, "Idris Aminu Idris
raina ya biya da kai, kuma dole sai na cimma
hakan, jarumtarka din nan ta sake bige ni, kasan
dalilin da yasa na ce nan da awa goma? In ka
lissafa zai baka bakwai na yamma. Daidai lokacin
da ake watso mana labarai ina kwadayin ina tare
da kai, lokaci guda kuma ina kallonka cikin TV
kana feso turanci, kasan ina son muryarka ga shi
ka gwanance da iya tsara turanci, sai ka ce
yarenka. Kada in cika ka da surutu sai mun hadu
anjiman". Ta kashe wayarta. Abba yayi kokari ya
tsaida motar shi a gefen titi a hankali ya furta
"Allahumma ajir ni fi musibati..." ya kifa kansa a
jikin sitiyarin motar, yana tunanin wai shin ba za
ta sauya masa a halin da yake ciki ba? Wata
zuciyar ta ce in tasan kana cikin wani halin ko? A
haka ya isa gurin aikinsa, tunda suka shiga dakin
daukar labarai, abokanshi suka gane yana cikin
wani hali duk da bai kasance mai yawan magana
ba, amma yau ba kamar kullum ba. Salis ne ya
kasa hakuri, don haka bayan an gama daukar
labarai da kyar sun je su yi sallar Azahar suna
zaune wata Bafulatana da ke kawo musu fura ta
kawo. 3..... Dama shi Abba bai cika shan fura da
rana ba, yafi shanta da dare, don haka siyan
kurum yake yi. Bayan yaje gida sai yasha, amma
ranar ya ce mata ta bar shi kawai, ta jiya ma
tana nan bai sha ba. Da ta tafi Salis ya dube shi,
"Idris ba ka da lafiya ne?" Ya ce, "A'a me ka
gani?" Ya ce "Ba yanda ka saba ba, duk kwanakin
nan na lura kana cikin damuwa". Abba ya dube
shi amma ai kasan nayi rashin lafiya ko? Salis ya
ce dakata Idris kada kaga kamar na matsa maka
sai na ji cikinka, ko kusa ba haka ba ne. Ni
mutum ne mai saurin karantar duk dan Adam din
dana zauna kusa da shi na awa daya bare kai da
na zauna da kai tsawon lokaci, muna kuma ci
gaba da zama. Idris na fahimci kana da matukar
'ZURFIN CIKI' dalili kenan da yasa ban ta6a
damuwa da in tambaye ka matsalarka ba.
Sannan dalilin 'ZURFIN CIKIN' da naga kana da
shi ne yasa har kwanakin baya na kawo maka
matsalata da iyalina. Alhamdulillahi ka bani
shawara kuma nayi amfani da ita, kuma naga ci
gaba, matsalolina sun ragu". Abba yayi dan
murmushi. "Wai kana nufin saboda ina da
'ZURFIN CIKI' ne kaga ya dace ka sanar da ni
sirrinka?" Salis ya ce "Kusan haka ne, don me
Zurfin Ciki ya iya hadiye magana, sai dai a ganina
zurfin ciki wataran zai iya fadawa halaka, ko
wata gagarumar matsala". Abba ya dube shi,
"Wace irin halaka? Salis ya ce, "Me zurfin ciki sai
ciwon zuciya ya kama shi yana muku-muku da
matsalarshi, wani ma har ya mutu da ita ba
wanda ya sani. Amma in abu na cinka ka samu
wanda ka yarda da shi mai amana ka fada masa
zaka ji dan dadi". Abba ya ce, "To kai tunda baka
da zurfin ciki, kenan bai dace ka ji matsalar ba?"
4....Salis ya tuntsire da dariya, "Ta nan ka 6ullo?
Ai dama ka sani ba ina son yabon kaina ba ne,
a'a duk surutuna nasan abinda nake fadi". Abba
ya ce, "Salis na gode da kulawarka, matsalata ko
ka ji ta nasan shawarar da za ka bani bata wuce
ka ce in yi hakuri ba, ni kuma ba wannan ni ke
son ji ba. Salis ba komai nake yiwa 'ZURFIN CIKI'
ba, yawanci in ina da matsala nakan tunkari
Ummata ne kuma ta warware min komai. Saboda
na taso da wannan koyin da ta min, yanda na
shaku da ita ko su Alhajina ba mu shaku haka
ba". Salis ya ce, "To me ya hana ka fada mata
wannan karon?" Abba ya ce, "Ba zan iya ba, sai
dai in za ka samo min mafita ban da hakuri, to in
fada maka". Salis ya ce "In sha Allah ba za arasa
mafita ba". Nan Abba ya bai wa Salis labarinshi
da Ummi tun farko har zuwa yau. Salis ya
numfasa, sannan ya ce "Kaga illar 'ZURFIN CIKI'
ko? Ummin ma taka ce amma kana nema ka
rasata, ai ba mafitar da ta wuce ka samu
Ummarka ko Alhajinka ka fada musu muradinka".
Abba ya ce, "Tabbas haka ce mafita, sai dai idan
na aikata haka abu biyu za su faru, na farko na
zubar da mutuncin Alhajina, domin babu girma,
sun ba da 'ya ba tare da wani dalili ba ya ce ya
fasa. Sannan haramun ne neman aure cikin aure".
Salis ya ce, "Haka ne, to hakurin kawai zaka yi".
Abba ya ce "Ai mun yi ban da bada hakuri ko?"
Salis ya saki dariya, sannan ya ce "To kayi
addu'a". Abba ya mike tare da fadin "Ka tayani
da addu'a". Daga nan ya shiga dakin, Filin Don
Matasa na Hausa, don likkafar shirin tayi gaba
yanzu har na Hausa yana gabatarwa. Kullum
sake kar6uwa shirin yake a gurin Jama'a.
5......UMMI Tana kwance kan doguwar kujera,
yau kwana hudu kenan bata saka Abba a idonta
ba. Tamkar Umma ta san abinda ke ranta, sai ta
tsinkayi Umma na cewa "Yau kwana uku ne ko
hudu rabon Abba da gidan nan, sai dai ya kira mu
a waya. Alhaji dai ya ce, yana zuwa gunsa
kasuwa". Ummi ta ce, "Nima yanzun nake tunanin
haka". Ta miko ma Ummi wayarta da ke gefenta.
"Lalubo min shi in ji". Da ta soma /ringing/ sai ta
mika mata. Ya dauka suka gaisa ta ce "Abba ko
dai na maka laifi ne?" Ya ce, "Umma me a ka yi?"
Ta ce, "Tsaf, ka dauke min kafa, wanda kullum
komai saurinka sai ka biyo". Ya ce, "Ina nan
zuwa Ummata, kina raina duk inda nabi, harkoki
ne suka taru suka sa ni gaba". Ta ce, "Ni kuma
sai na ke ganin kamar don ba mu dauki
shawararka ba ne ta game da karatun Ummi shi
yasa ka". Ya ce, "Umma ba haka ba ne, zan shigo
da zarar na dawo". Ta ce. "To". Sam shi batun
shi yayi ba, sai dai baya son yazo ya ga Ummi
domin da ya ganta yake neman kwanciyar
hankalinsa ya rasa na tsawon lokaci. Amma
yanzun kalmar Salis ta karshe daya fafa masa da
za su rabu a gurin aiki ita yake tunawa. Dafa shi
ya yi tare da cewa "Miste Man shawara ta
karshe, ka nunawa kanwarka kana sonta a fili".
Ya ce "Tab, wannan shi ne me wahalar ai,
furtawa Ummi kalmar so. Zubar da kai kenan".
Ga shi ba sonsa take ba, duk yanda mace ke
girmamaka da zaran ka ce kana sonta shi kenan
ka zube a idonta. Musamman in kai ke sonta ita
ba ta sonka, wata ma har da rashin kunya zata
tsula maka, a fili ya ce, "Ina, ai ba zan ta6a gigin
bari ta san ina sonta ba". Daga kasan zuciyarshi
yaji an ce za ko ka sarata. Sai da ya yi sallar
Isha'i sannan ya yi wanka ya saka kananan kaya,
ya fito da nufin gidan su Ummarshi. Bishira ta
bishi da kallo, daga ganin fita zai yi ta fito da
saurinta tana cewa "Baban Walid! Baban Walid!!."
Ya tsaya, ta dube shi "Ina za ka?" Ya ce "Gidan
su Umma". Ta ce, "Ba wani gidansu Umma, kai
dai kurum tadi za ka je". 6.... Dariya ta su6uce
masa, sai da ya dara sannan ya ce "To in ma
tadin zan je ya za ki yi dani?". Ta ce, "Tab!, ai na
rantse maka kayi kadan. Kullum kuma ina 'kara
fada maka kai mijin mace daya ne rak!" Ya ce, "In
ji ki ko?" ta ce, "Eh." Ya ture ta gefe tare da cewa
"Da sauki tunda ba fadin Allah ba ne". Yayi
ficewarsa ya barta nan tana ta masifarta. Kan
dakalin kofar gidan, Ummi ce zaune da Sahabi
suna hira, duk da cewa Sahabin shi kadai ke ta
surutanshi Ummi na can duniyar tunanin abinda
zuciyarta ke so. Tun daga nesa ta shaki kamshin
turaransa, zaraf ta mike tsaye. So take ta kalli
fuskarshi amma ya dauke kanshi daga gare su.
Haka nan ya share sannun da zuwan da ta ke
mishi tare da shigewa cikin gida abinsa. Sahabi
ya ce, "Ya Abba na nan kuwa kwana biyu na rabu
da ganinshi?" Ta dauke kai sannan ta ce "Zan
tafi gida". Ya ce, "Haba Ummi, zuwana fa
kenan?" Ta dube shi. Ji take tamkar ta sheka
mishi mari, ta ce "To kaina ciwo yake yi, sannan
kuma ga Ya Abba yazo baya son ina dadewa a
waje". Ya ce, "To shi kenan sai gobe?" Ta ce,
"Don Allah kada kazo gobe, ka bari sai jibi". Ya
ce "Za ki azabtar da ni, ba zan iya kwana biyu
ban gan ki ba." Maimaikon taji dadin kalmar, sai
taji takaici ya mamayeta. A ranta ta ce,, "Tunda
ga gyatumarka ba". Ya ce, "In zo goben don
Allah?" Cikin muryar tausayi yake maganar, ta ce
"To shi kenan". Ta soma tafiya, ya dan tako ya
biyo ta tare da cewa "Sahibata mu kwana lafiya"
A kagare ta ce "Uhum". Ta samu Abba suna hira
da Umma, ta tura mishi kular birabisko tana
lallashinshi ya ci, tayi sallama Umma ce ta amsa.
Ta shiga idanunta kan Abba, ta zauna a kujerar
da ke fuskantarshi. Umma ta ce "Har Sahabin ya
tafi?" Ummi ta ce "Eh". Ta tsura ma Abba ido
tare da cewa, "Ina kwana Ya Abba?" Umma ta ce
"Wane irin kwana kuma Ummi da wannan daren?"
Ta ce, "Au, zan ce ina yini?" Ya amsa tare da
kallonta, "Lafiya". Ya mayar da dubanshi ga
Umma. "Umma Matar Ahmad fa ta haihu". Ta ce,
"Eh, ba jiya ka fada min ba a waya? Me ta samu
ne?" Ya ce, "Mace ta haifa, gashi ta sha wuya".
Umma ta ce, "Allah Sarki, to Allah ya raya mata,
zan je in dubota in mata barka gobe". Ya ce,
"Allah ya kai mu, ai Ahmad yayi dacen mata ba
kamar ni ba. A da Umma bana tunanin sake aure,
amma yanzun ina ganin dole sai nayi mata biyu".
Umma ta ce, "To ba dai yanzun ba duk nawa ka
ke kuma yaushe kayi wancan?" Ya ce, "Umma ke
dai ki min addu'a, ban samu irin macen data dace
da ni ba". Ta ce, "Ina maka addu'a, Allah ya
shirya maka matarka." Abba ya ce, "Ko ta shiryu
sai nayi aure insha Allahu". Ta ce, "Abba ni ko
gani nake ba ka san wadda za ka aure din ba
itama da nata kalar halin zata zo, sai su taru su
ruda ka". Ya kalli Ummi wadda ya lura da kallon
da ta tsare shi da shi kamar tana son jin abin da
yake fada ne. Ya maida idanunshi kan Umma.
"Na yarda da tarbiyar wannan yarinyar da nake
son aure yanzun, duk da yarinyar bata sona tana
girmamani". Umma ta ce, "Har ka samu kenan,
'yar gidan waye? Ummi kuwa tuni makoshinta ya
bushe, ta zaro idanu tana son ji wa kuma Abba
ke so? 7:....Ya kalli Ummi ganin yadda ta zaro
ido ya ce "Ke ni ke fadama wa ki ka zaro ido ki
ka tsare ni da su?" A hankali ta lumshe idanu
sannan ta maida kanta kan hannun kujera, ya
fuskanci Umma "Ba 'yar unguwar nan ba ce",
matsalar da yarinyar bata sona". Umma ta ce,
"To ka bar ta mana ka samu mai sonka? Yo in
haka ne ma ka ce gara matar taka ta gida, don
ita tana sonka". Yayi shiru zuwa can ya ce
"Umma in dai zan sameta zan aureta a haka".
Umma ta ce, "Kayi addu'a, ina ko mamakin mene
ne ta gani na 'ki a tare dakai Abba?" Ya ce cikin
'yar dariya "Umma ai ba dole ba ne sai ka birgke
kowa". Ummi ta mike jiri na dan dibanta ta shige
ciki. Zance ya dada watsewa, ta furta bayan ta
fada kan gado, ni ina son shi shi kuma ashe yana
can ya zarme da son wata. Ranar ta raba dare
tana kuka daga karshe ta soma ba kanta
shawarar ta samu Abba ta ce a fili dama
shisshigi ne irin na zuciyata Ya Abba ba irina
yake so ba. Shi kuwa zuciyarshi ta soma zargin
wani abu a kan Ummi, irin yanda ya ga tayi
kamar hankalinta ya tashi da batunsa. In ko haka
ne zai fi kowa murna, wata zuciyar ta ce ka sani
ko tsabar jin gulma ne yasa ta kafa maka ido duk
da haka yasha alwashin bibiyarta. Sun taso daga
sallar Juma'a shi da su Ahmad gidan budurwar
Tukur suka dosa, wayar Salis ta katse shi. Wani
aiki ne ya taso dole ya koma gurin aiki. Ya sauke
su a unguwar shi kuma ya nufi gurin aikinshi.
Karfe biyar ya baro gurin aikin da nufin yada
zango gidan Ummanshi. 8.... Yasan yau juma'a
duk yanda aka yi zai samu abinci na musamman,
don al'adarta ce girkinta na juma'a daban ne,
tana girmama ranar da abincin da ta san mijinta
zai yi farin ciki da shi. Haka nan ta kan yi
kwaliyyar musamman, shi yasa yake kara
kwadayin aura Ummi, ya san zata dauki wannan
tarbiyyar. Matasa guda uku a tsaye gefen titi cikin
fara'a da murna suka tsaida shi, ya saba kusan
kullum sai irin haka ta faru. Matasa kan tsaida
shi suna ma su nuna jin dadi da ganinshi, a gaisa
su wuce. Wasu kuma su amshi lambarshi har da
ma su son adireshinsa, yanzun ma sai ya tsaya
zai fito, tsum! Yaga sun bude motar sun shigo.
Biyu baya daya gaba, ya ba su hannu suka gaisa
su duka. Na gaban ya ce. "Mai matasa ai muna
jin dadin taimakon da ka ke mana. Ya kamata a
baka Sardaunan Matasa". Daya daga baya ya ce
"Sarkin Matasa gaba daya zamu ba shi, don yana
kokarin gurin binciko matsalolin matasa". Abba
ya yi murmushi tare da cewa, "Na Gode". Dayan
da bai yi magana ba sai ya ce "Amma mai
Matasa ka san da wannan matsalar?" Abba ya
waiwaya da nufin jin karin bayani, sai ko ya fesa
mishi wata farar hoda a fuska. Take nan atishawa
da tari suka tirnike shi. Ya soma mutsuka
idanunshi bakinshi na furta "Inna lillahi wa'inna
ilaihir raji'un". Kafin 'yar sakwanni kanshi yayi
din, kuma ya fita daga hayyacinsa. Suka tuka
motar suka tashi dashi. * Farkawa ya yi tamkar
wanda ya tashi daga bacci, a hankali ya bude ido
tangaran a kan silin, irin na masu hali. Kwan
lantarki irin na kasaitattun gidaje ya daki
hancinshi. Nan take ya shiga tunanin me ya kawo
shi nan? ba 6ata lokaci ya tuna duk abinda ya
faru, da sauri ya tashi zaune yana fadin "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raji'un". Ya ci gaba da kallon
dakin, cikin tangameme ne yana dauke da
tafkeken gado da sauran saitin shi. Sai kafet din
tsakar daki da kayan kallo, ga kuma kofofi guda
biyu. Ya tambayi kanshi da cewa me ya kawo ni
nan? me matasan suke nema a gurina?" Take
muryar Hajiya Nina ta fado masa, inda take cewa
"Za ka zo yau din ne ko sai an dauko ka?" ya
girgiza kai tare da cewa, Lallai wannan makirar
matar ce tasa aka mi shi haka". 9... Nan take ya
soma karanta addu'ar neman tsari. Daya daga
cikin kofofin ta bude, ya kure idonsa gurin da
kallo, matar ta shigo sanye cikin doguwar riga
baka mai ma6allai a gaba. Fara ce kyakkyawa,
shekarunta suna tsakanin Talatin da takwas zuwa
arba'in da biyar, domin kyawun nata sun 6oye
shekarunta, ta baza gashi a kafada. Tsura mata
ido yayi yana son tuna inda ya ta6a ganinta,
domin tabbas yasan fuskar. Muryarta ce ta katse
shi,"Dama nasan zuwa yanzun ka farko, kuma ka
gama nazarin yanda aka yi kazo nan. Kila ma
tunda kana da kamannin ma su basira ka hararo
wadda tasa a ka dauko ka". Ya ce, "Kwarai
kuwa". Lokacin ne ya tuno inda ya santa, wato
Hajiya Zabba'u ce matar shaharraran Attajirin nan
Alhaji Uzairu wadda a ke nuno ta a TV da Jaridu
tana taimakon talakawa da Marayu. Wadda ake
labarin tsoron Allahnta da gudun duniyarta,
wadda ta gina Masallatai da Makarantun Addini
ma su dama. Ya girgiza kai cikin matukar
mamaki, ta ce "Ka gane ni kenan?" Ya ce (Cikin
karfin hali) "Lallai mutum mugun ice. Wannan shi
ne Allah a baki shaidan a zuci". Ta ce "Kai ne na
biyu da ka furta wannan kalmar, sai dai bana fata
ka zama na biyu da ya bakunci inda na farkon ya
tafi. 10.... Ta tako a hankali ta dunfaro shi, ya
matsa baya cikin zuciyarshi yana korar shaidan,
'yar dariya tayi. "Nutsu Idris ko ince Abba. Ba
fyade zan maka ba". Ya dubeta da sauri, "Eh haka
nace, in na son hakan zan maka, amma ba
hakanne burina ba". Ta zauna bakin gadon, "Ka
zo mu daidaita, in kana tsoron ciwo zan baka
makari, sai dai ina so ka sani bana dauke da
wata cuta". Ya ce, "Karya ki ke, kina dauke da
mummunar cuta". Ta ce "In ka tashi daga dan
jarida ne, ka koma Likita zan baka dama ka
gwada ni". "Ya ce ba ki bukatar gwaji don ga
ciwonki nan a fili ciwon zuciya". Ta ce, "Sam ba
ni da ciwon a zuciyata, to in ma ina da shi me zai
dameka tunda ba dauka za ka yi ba". Ya sake ja
da baya ya ce, "Zuciyarki ta kamu da ciwon zina.
Ta yi duhu dumdum! har bata iya ganin
gaskiya...". "Ta daga mishi hannu, "Dakata min,
ban tambayeka labarin wa'azi ba, domin in shi
nake son ji ina da kaset-kaset kala-kala zan saka
na ji". Ta mike zuwa wata durowa ta bude, dauri
uku ta dauko ta aje gaban madubi na 'yan dari
biyar-biyar sababbi dal! Ta ce, "Wannan za ka
sha mai ne sannan kasa kati, kuma in ka kwantar
da hankalinka zan canja maka mota, zaka je
Makka. 11.... Sannan idan naga kana bin
umarnina zaka yi suna a aikin jarida fiye da duk
wani dan jarida da ka sani a kasar nan. Kai zaka
taka duk wani matsayi da dan jarida ke takawa".
ta sake nufoshi da tausasa murya. "In kabi yanda
nace ba kai ba sake kwana a talauci..." Ya
katseta da fadin, "In naki fa?" Ta hade rai tare da
zuba mishi ido, "Shima kallonta yake, sai a
lokacin ya ga tsufanta ya bayyana. Ta juya mishi
baya tana 'yar tafiya, sannan ta ce "Am sorry to
say". Ta juya ta dube shi "Za ka mutu". Gabanshi
ya fadi, amma sai ya yi karfin hali ya ce "In na
mutu sai me? Dama can mutuwa zan yi ko ba ki
kashe ni ba. Kuma ni na san ba zan wuce iyakar
ajalina ba, murnata daya zaki sauke min nauyin
zunubaina". Ta matso kusa da shi "Ka san
matasa nawa ke shiga malamai kawai don su yi
hulda da ni? In ka dade muna hulda shi ne muyi
wata biyar, sau daya na rike saurayi har tsawon
shekara daya don yana da hankali". A zuciyar
Abba ya ce "In fa na daka ta matar nan zan mutu
ban auri Ummi ba. Sannan ba Allah a ranta bare
taji nasiha, yanzu bari yabi ta hikima". Ya ce,
"Saboda me suke shiga malamai don suyi hulda
da ke? Sannan daman duniya tasan ki kina
haka?" Ta ce, "Ko kusa, sun sanni a Hajiya Nina
sai in mutum ya zo ya ganni, in ya sanni to in bai
sanni ba duk daya. Sudai burinsu kudin". 12......
Abba ya ce, "Nikam ba zan iya wannan huldar
ba". Ta ce, "Kada ka bari taurin kai yaja ka
nadama irin wadda waninka ya ta6a yi. In kana
da sha'awa in baka labarinsa don ya zamar maka
Ishara". Shirun da Abba ya yi shi yasa ta ci gaba,
domin alamar yana son ji kenan. Da a ce zan fadi
sunanshi zaka sanshi, wani malami daga cikin
Malaman garin nan, haka nan yanda na ganka a
TV kana labarai na kwadaita da kai, shima haka
na ganshi a TV yana wa'azi kuma zuciyata ta
yaba. Na neme shi ya zo kuma shi na fada masa
ni ce Zabba'u ban 6oye masa ba. Sai dai nuna
masa nai aikin rabon zakka zan ba shi, ma'ana
kudi ne masu yawa ban san yadda zan fidda
musu zakka ba. Da jin haka sai ya taho, nan
dakin na kawo shi, sannan na fito mishi da
maitata fir! ya shiga jawo min ayoyi na numa
masa cewa ba zan hakura da abinda zuciyata ke
so ba. Don ban ta6a 'kin cika mata burinta ba,
shi kuma ya fir ya ki ya nemi ya gudu na bashi
guri ya dan ci abinci na nuna masa mishi kuskure
ne ya ce zai gudu. Don gidan nan duk masu tsaro
ne har da ma layin gaba daya. Da sauri za a
kama ka a matsayin dan fashi, sannan in ka yi
kokarin shigo da jami'an tsaro lamarin to, zaka
kwana ciki. Domin duk a hannunmu suke, amma
Ustazun ya ki shan ko ruwan gidan nan, gashi ya
min shame-shame zai mutu don yunwa. Ba arziki
na saka aka fita da shi kuma aka kai shi gidan
karuwai a ka ba su na sakar musu kudi suka sa
shi a daki. Nasa Malamina ya karasa min shi,
sannan na sa karuwan suka kira 'yan sanda kan
cewa ga wani ya zo gurinsu amma kwananshi ya
kare a nan. To dama iyalanshi suna ta nemanshi
an sace shi nan fa suka dauke shi, na san yanzu
ka gane kowane Malami ne tunda labarin ya yadu
a cikin garin nan da ma wajen shi". CIKI book 3 part 3
ZURFIN CIKI book 3 part 3
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:24
Abba ya ce "Lokacin da muke cin abinci tare,
Umma ta ce, lokacin da ka ke bata dai, Abba shi
ne ya fara baki abinci a baki. 20..... Watanki
hudu, da kin hango shi za ki soma daga hannu,
Abba ya ce Umma na fa goya Ummi a bayana.
Lah, goyo? In ji Ummi. Umma ta ce, "Goyo sosai
kuwa, suka sa dariya, Umma ta ce, "Shi yasa in
naga yanda ku ke rashin shiri a tsakaninku
yanzun sai in ta mamaki. Don tun ba ki fita a
tsumma ba Abba ke rainonki, tun ba ki fi wata
hudu ba, ki ka tantance muryarshi. Haka nan
sunan shi ne ki ka fara iya fadi a duniya. Abba
yana goya ki kin sha yi masa fitsari da kashi da
tumbudi, wanka da wanki duk Abba ya miki
Ummi. In ko na aike shi ko zai tafi Makaranta to
sai da wayo da dabara. Ke har an kai lokacin da
kin yarda in tafi unguwa in bar ki gurin Abba, in
ya dawo Makaranta tun daga soro zai soma miki
wakar da yake miki. Ummin Abba da Alhaji,
Ummin Umma da Tsohuwa, da kin ji haka za ki
dibi rarrafe ki nufi gurinshi, kuma duk kudin break
dinsa zai debo miki tsaraba. Umma na bada tarihi
Ummi ta zuba ma Abba idanu cikin wani irin
yanayi da ba zata iya tantance shi ba, shi kuwa
lokacin ne ya dawo mishi, ido ya yi dan murmushi
tare da cewa "Allah sarki da na tuna ranar da aka
yaye Ummi, Umma tayi dariya ta ce, "Ranar tare
kuka kwana kuna min kuka wai in yi hakuri in
baki nono". Wata sabuwar kauna da so Ummi taji
ya rufe ta na Abba, har kwalla ta cika mata ido,
ta ce "To Ya Abba me yasa ka daina sona?" Ya
ce, "Ummi ban daina sonki ba, kanwata kiriniyarki
ce ta hada mu fada dama, yanzun kuma kin
daina ko?" Ta daga kai alamar eh, Umma ta ce
"Labarin yanda ku ka kaunaci juna mai tsawo ne,
kusan kullum sai mun yi labarin da Alhaji". Ummi
ta kalli Umma shi ne ba ku ta6a bani labari ba?
Ta ce ba gashi kin ji ba, Tsohuwa tayi sallama,
suka amsa. Ta ce, "Kai me sunan Malam me ya
faru da kai? Nan ya warware musu komai, suka
yi ta al'jabi. Umma ta ce "Ni 'yasu, yanzu haka
mata suka maida aure ba a bakin komai ba?"
Kuma ka ce matar aure ce, Abba ya ce dama z
aki san kowa ce ce za ki ji mamaki fiye da haka,
don dai kurum na rufa mata asiri ne in taci gaba
to can gabanta hadu da mai tona ta. Su Alhaji
suka shigo da sallama, nan suma aka ci gaba da
jajanta batun, Alhaji Babba ya ce, "Babana ina ga
dai rahoto za mu kai gurin 'yansanda". Abba ya
ce, "Alhaji tuni manyan shuwagabannin gurin
aikinmu suka shigo da hukuma, in Allah ya yarda
dolenta ta bar ni, Alhaji Karami ya ce, "Addu'a dai
ita ce z aka kara rikewa, Allah ya ja mana gaba".
Suka ce Amin. 21... Ranar su Alhaji a tsakar gida
suka ci abinci anata hira, Ummi dai kallonsu take
yi amma zuciyarta na can duniyar tunanin labarin
da aka bata. Ashe har yanzu Ya Abba na sonta,
Allah ya sa haka har yanzun. Sai kusan sha daya
Alhaji ya matsa wa Abba ya tafi gida. Abba ya ji
dadin hirar musamman in ya waiwaya idanunshi
suna kallon Ummi ta mai 'kuri da ido, Umma ta
ce, "Ka gaida 'yan gidan". Ya ce "Za su ji, har ya
kai soro Ummi ta ce Alhaji da an raka shi kada a
kara sace shi fa, duk suka sa dariya". Abba ya
dawo yana cewa, "Umma kun rage man fetur
kuwa? Na san yanzu na gidan ya kare tunda ba
shi da yawa, bana son kuma sai na sake daukar
galan na fita". Alhaji ya ce, "Na shigo da mai
dazu duba nan soro na aje shi, Ummi ta sake
cewa Ya Abba ka ce Alhaji su rakaka gida, yayi
'yar dariya kada ki damu Ummi, ina yin addu'a
Allah zai kare ni. Yau kam Ummi ta dade bata ga
daren da farin ciki ya hanata bacci ba irin yau.
Haka nan shima Abba zuciyarshi fes Ummi ta
fahimci dama can santa yake, da alamu ba zai
sha wuya gurin shawo kanta kuma cikin
karammin lokaci. 11 HAJIYA NINA Ta kalli
matashin, sannan ta kalli jaridar hannunshi ta ce,
"Me ya'ki kai fa ba jakadan azriki ba ne, a duk
lokacin da na ganka sai gabana ya fadi,
musamman in kazo min da jarida". Yayi 'yar
dariya "Hajjaju makatu sallah Makka Sallah
Madina, ni dai kin san ba ilimin nan gare ni ba, in
da z aki tsare ni in karanta ban iya ba, ni dan
sako ne. Muftahu ne mai siyo duk wata jarida da
ya ga ta shafe ki, ta amsa ta bude cikin azama,
hoton Abba ta gani gabanta ya fadi, ta ce dan
jarida shege ne, yaron nan tallatani zai yi? Ta
soma karanta labarin zufa tana karyo mata, har
ta gama. Kafa kurum take karkadawa tana
tunanin abin yi, murna daya tayi da bai tona ma
duniya cewa ita ce Hajiya Zabba'u ba. Amma duk
da haka ba zata bar shi ba, koda yake ta ga
manyan 'yan jarida na kokarin shigowa ciki, ta
kai hannu ta dauko daya daga cikin wayoyinta ta
danna kira. 22.... Jim kadan aka daga ta ce,
"Karamakallu barka da warhaka, ya amsa da
Ranki ya dade lafiya dai ko?" Ta ce, "Malam ba
lau ba, kana ji? Ina yaron da nake baka labari
dan jarida? Ya ce, Naji. Ta ci gaba, Yaron nan
kaga yanda ya yayata ni a duniya? Sai na koya
mishi hankali, da ni zai ja?" Malam ya ce, ya ma
ki ka ce sunanshi? Ta ce Idris, ya ce To zan kira
ki anjima, kada ki dauki wani mataki tukunna sai
na gama bincikena duka. Ta ce an gama. Sintiri
tayi ta yi tsakanin dargajejen falonta zuwa
barandar shakatawarta, lokacin da taji rurin
wayarta tayi tsammanin Malamin ne, sai data
duba taga Aminiyarta ce Haiya Attine. Ta daga da
cewa, "Hello Attinen bishasha ya aka yi ne? Ta
ce, Zabba haka kwallon dan iskan yaron nan zai
miki? Ta ce, Hum! Ke dai bari Aminiyata, yanzun
nan na gama karantawa a jarida ban ma san
hukuncin da zan yanke ma yaron nan ba. Attine
ta ce, sa su Adda su tura shi Jami'ar mi'kakku
mana. Hajiya Zabba'u ta ce, "Ai kuma na riga na
kira Teacher ya ce in saurare shi". Attine ta ce,
"Eh to kin yi dabara ma, kya iya sa Teacher din
ma ya tura ba tare da an zargi kowa ba". Hajiya
Zabba ta ce, "Kin san jami'an tsaro suna cikin
maganar tsundum! Don haka dole in yi taka tsan-
tsan, guri daya yaron ya yi min kyan kai, da bai
fada ma duniya Zabba'u ita ce Nina ba." Attine ta
ce "Eh yayi wannan adalcin, yanzun bari muji ta
bakin Teacher". 23.... Shikam Malamin duk
lamura sun kasa masa daidai, sai kusan karfe uku
saura, sannan ya kira ta da rawar jiki ta dauka.
Ya ce, Hajiya? Ta ce, Na'am ya ce ki tattara ta
batun yaron nan ki watsar domin yanda naga
al'amuran to fa in mun matsa ba zamu kai labari
ba. Haka nan allura zata tono garma game da
damuwar malamin nan, sannan asirinki zai tonu a
gurin maigidanki. Tsaki taja don maigidana
Malam nasha fada maka ban 'ki ya ji ba, tunda
shi ne sanadin komai, tafiya kullum daga waccan
kasa zuwa waccan, kullum cikin bakin yawon
neman kudi. Sam baya biya mini bukatata ba
dole in nema ba? Yarana biyu cal a duniya duk
sun yi aure su ne kawai zan ji kunyar su sani,
don haka in zai yiwu ka sa Aljanu su tsotse min
jinin matsiyaci. Malam ya ce, "Ba zai yiwu ba, ina
ce tun lokacin da ki ka zo min da batunshi kafin
ma ki sa a dauko miki shi sai d ana fada miki
yaron yana da kariyar da take kare shi daga
Ubangiji. Yaron ma'abocin kyautata Sallah ne,
tare da yin Azkar, yana da makarin da Aljanu ba
za su iya tunkararshi ba... Dakata Malam, ta
katse si duk addu'arshi ya kai Malam ne, kuma
muka ci nasara a kanshi? Ya ce kila shi Malamin
kwananshi ya kare dama ke ce sila shi ko
wannan da sauran shan ruwansa. Ta ce, "Kai ne
sila dai daina jingina min mutuwarsa, ya ce ko
kin ki dole ki dauki nauyin zunubin mutuwar
Malam". Yanzun kuma ta wannan sai ki wamu
wani don ni ba zan matsa lamba a kan al'amarin
da Aljanu suka nuna tsoronsu ba, tsaki taja
sannan ta kashe wayar. Har gari ya waye ba ta
daina tunani ba, haka nan bata yanke matsaya
ba. Gidan Aminiyarta Attine bishsha ta nufa, sun
tattauna sosai sannan suka bukaci sukai koken
ga wasu Malaman. Sai dai guri uku zancan iri
daya ne, wato ta bar shi kawai, yayin da guri
biyu suma zancan su iri daya ne, sun ce zata ci
sa'ar kashe shi amma asirinta zai tonu zata rasa
ran 'yarta daya kuma zai yiwu tayi zaman Jarun.
Ta ce, "Wannan akwai shegen yaro, shi yasa da
na ce zan sa Aljanu su dauko shi ya ce min yana
da makaminsu? Daga karshe ta ce na bar shi
mara rabo". Attine ta ce da dai yafi shi yasa tun
farko in naga wanda zai ja min aji ni ke watsi da
shi in nemi wani. Kai jama'a sai kace aikin Allah
menene amfanin zinar ma da har ake shiga
Bokaye dominta? Allah ka tsare mana Imaninmu,
amin. 12 24.... Ummi tana zaune zata wanke 'yan
kayanta na ciki, ta zubo omon cikin ruwa tana
faman karkadawa, tana 'yar wakar da ke sata
nishadi. Sam ba ta ji sallamar Abba ba, yana
jingine yana kallonta, tana fadin, Akwai wanda na
ke so, amma kunya naso, ya wanke ni da soso
dan Yayana. Ta tsoma sikyat dinta da fant da
'yan bireziyoyinta farare ne ta soma cudawa tana
maimaita wannan baitin wakar, shi kadai ta iya.
A jikinta taji cewa ana kallonta, ta waiwaya da
sauri, idanunta tsaf cikin na Abba, sai ta samu
kanta da sunne fuskarta cikin cinyoyi. Ya ce,
"Kunyata ki ke ji ne Ummi?" Ta dago da dan
murmushi, "Sannu da zuwa Yaya Abba". Ya ce,
"Yauwa dama kin iya waka?" Tsohuwa daga daki
ta cafke, tun da ta samu wannan wakar sai ka ce
me hadda, kullum Abba ya isa kofar Tsohuwa
suka gaisa. Ya dawo kofar Umma yana tabayarta.
Ummi ta ce, "Taje Hotoro sunan kanwar Umman
Bashir da ta haihu, ya manta fa matarshi ma ta
na can, Tsohuwa ta fito tana cewa, ai Ummanku
ta juri wulakanci. Waccan haihuwar da Zilai
kanwar Sahura tayi tas a ka zageta a gidan
sunan, amma yau ta koma. Abba ya ce, "Ummata
tayi nisa a zumunci, Allah zai bata lada" Tsohuwa
ta ce, "Ai sai tayi ta yi, in dai shisshigi ne ba
kwarjini". Ta dubi Ummi, wai wankin me ki ke yi
ne har yanzun ina nan ina jira ki yanke min
farce". Ta hango kayan Ummi na daura ta ce,
"Kai ni wannan zamani naku yana bani mamaki,
ace 'yammata suna saka rigar mama? Kunya ta
cika Ummi saboda Abba da ke gurin. 25.... Abba
ya ce, "Kin ji tsohuwa, lokacinku da namu daya
ne? Ku lokacinku kai bai waye ba, ta aje 'yar
kujerarta ta zauna. Tir da wannan wayewar taku
ta zamani, yarinya ta fadi a gaban iyayenta har
ta shiga sa tara mama bata kama dakin kanta
ba? Mu kuwa da wata ma ba sai tayi haihuwa
goma ba ma ta sa ran mama ba. Abba dariya ta
ishe shi yayin da Ummi kunya ta hanata shanya
kayan ta matse ta aje. Abba ya ce, "Yanzun
Ummi har wani girma tayi, shekara sha takwas
kurum ce fa, bata ma cika ba. Ta ce "Mu lokacin
sha biyu sha daya yarinya ta kama dakinta.
Ummi ta zanua ta soma yanke ma Tsohuwa
'kumba, tana cewa To dai nima na kusan tafiya in
huta gorinki. Abba ya matso, "Ummi don Allah in
tambaye ki mana? Ta tsaya da yanke 'kunbar
tana kallonshi, ya maimaita tambayar da gira ta
bashi amsa ya ce kina ko son wannan Sahabin?
Ta maida kanta ga yankan 'kunbar duk jikinta da
hannunta suna dan rawa, a zuciyarta ta ce, "Kai
ne kadai zuciyata ke so, amma a fili sai ta ce,
Um, ya ce Yaya hausar um?" Tayi kokarin
saisaita hawayenta, sannan ta ce Eh, jikinshi yayi
lakwas, Tsohuwa ta ce, "Zancan banza, in bata
sonshi zaka daga batun auren ne?" Ai ko tana so
ko bata so tunda ta kawo shi zance ya kare, ka ji
mai sunan Malam da zancen wofi. Ya ce,
"Tsohuwa ni fa ba wani abu na ce ba, kin ga ma
dai bari in tafi abina. Ummi ina Azimi yau, zan zo
in yi buda baki anjima. Ta ce, "To." Tsohuwa ta
ce, "Wai kai ba ka da gidan mata ne kullum kana
la'ke a nan? Tsoron ta ka ke ji ne da zaka kasa
lankwasata ta yi maka girki?" Ya ce, "Na nan
nake son ci Ummi kam tana can duniyar tunani
tana tambayar kanta shi kenan ta rasa Abbanta?
Son da da yayi mata da ca dama ba na aure ba
ne, na 'yan uwantaka ne? Kai ko dai ta fito ta ce
Abba take so, gaskiya ita fa Sahabi ba sonsa
take ba. Kusan wata daya kenan rabon da ya
samu biyan bukata daga matarsa, don gaskiya
baya iya zuwa dakinta saboda kazanta da kuma
datti da wari da zarni da 'karni ba za su bar shi
ya samu cikakkiyar biyan bukata ba. In ta zo
dakinshi ma jikinta tashi yake, a haka yake
maneji, amma in iskancinta ya motsa har yanga
take mishi (Mtsw! Allah rabamu da kazaman
Mata). Shi kuma yana da wani hali, duk yanda ya
matsu in har ya nuna mata bukatarshi ta 'ki sai
ya hakura ya roki Allah ya shiryeta, shi kuma ya
kare shi da fadawa sharrin zina. 26.... Bai zaginta
ko ya ce zai nuna mata karfin shi, ko ya ce zai
tsaya rokonta, shi yasa yake yawan yin Azumi.
Ummi ta ce, "Umma ki kawo kudi in siyo kwai in
soya ma Yaya Abba doya, ya ce zai zo shan
ruwa. Ta ce, "To je ki kasan filo ki dauko, amma
fa sai kin yi azama don an kusa kiran sallah. Ta
ce, "Ai na dafa ruwan shayi, sannan na masa
kunun tsamiya, doyar ce kawai, ta ce "To sai da
ta gama komai sannan tayi wanka tayi sallah.
Riga da siket na leshi tasa fari tas, bata damu da
yin fenti da dare ba amma yau tayi ta feshe
jikinta da turare wanda shi ne ya sai mata.
Sallamarshi ta jiyo suna gaisawa da su Umma, ta
fito ya bita da kallo, kin yi kyau kanwata, Umma
ta ce yau za ku hoton ne? Ta ce kila, Abba ya ce
shi yasa ki ka yi kwalliya haka? Ba ta ce komai
ba sai dai ranta bai so ma maganar da Umman
tayi ba. Suna hira da Umma ta shirya misi abinci
ta koma kan kujera ta dauki littafi lokaci-lokaci
idanunta suna kan Abba. 13 Suna hira da Umma
ta shirya mishi abinci ta koma kan kujera ta dauki
littafi, lokaci-lokaci idanunta suna kan Abba. Shi
ma haka ya ce wai ni littafin nan da ku ke nacin
karatunshi dame kuke karuwa? Umma ta ce, Ai fa
gara ka tambaye ta, don ban ga abinda ta ba
muhimmanci ba irin wannan littafin. Ummi ta cem
ina karuwa sosai Umma suna koya mana tarbiyya
yyanda zamu tafi da rayuwarmu cikin tsarin
Addini da al'adarmu. Abba ya ce amma basa
koya tsafta da biyayya, Ummi ta ce suna yi sosai
ma, ya ce Umma ni naga jarabar karatu irin na
Bishira amma kullum mugayen halayenta bayyana
suke yi. Ummi ta ce ni ko har addu'o'i zuwa girki
kala- kala ina koyo, Umma ba rannan nayi
dafadukan kwakwa ku ka ce ya yi dai ba?" Ta ce,
"To ki dai dinga daukan na kwarai kina yarda na
banza, Abba ya ce in haka ne d agaske zan samu
lokaci in zo ki karanta min in ji, ta ce "To." 27.....
Umma ta yi 'yar dariya ta ce, "Sai ka ce ba ka da
aikin yi? Ya ce, "Allah Umma da gaske nake yi
don in ji wacce irin koyarwa suke yi, marubutan
ko ko sai shirme?" Kiran sallar Isha'i ne yasa
Abba mikewa, ita kuma Umma ta tafi kicin don
shiryawa su Alhaji Abinci. Ummi kam sun bar ta
cikin takaicin tafiyar Abba don dai bata gundura
da shi. * Alhaji Ya kalli Umma, wai yau bikin
yaran nan saura wata nawa? Ta ce, "Wata ko
kwana dai?" Yau saura kwana talatin da shida,
ban ga kana motsi ba? Alhaji bikin nan zai
mamaye mu, ya ce "Yanzun ya za a yi da batun
kaya?" Ta ce, "Ni da cewa nayi ga Abba sai yaje
ko kuje ku za6a musu kaya masu kyau a siya,
kada a ba kafintoci in ba a yi sa'a ba har lokacin
yayi ba a gama ba". Ya ce, "To zan sa shi ya tafi
da su kawai su za6a". Ta ce, "Sai kayan girki na
dai sayi tukwane da risho, sai kuloli". Ya ce, "Duk
da haka uwata zan sa ta za6i wasu kayan."
Umma tayi dariya tare da cewa, "Allah ya kara
budi, nan dai suka yi ta lissafin kudi. Da safe
Alhaji ya kira Abba a waya ya sanar da shi cewa
ya dauki su Ummi suje su za6i irin kayan da suke
so, duk da cewa zancan ya doki zuciyarshi amma
ya ce "To." insha Allah zamu je, suka yi sallama.
Sam baya son ya ji batun auran su Ummi, baya
son rasata, kuma yana ji a jikinshi cewa zai same
ta. ** ** 28.....Yammacin ranar Asabar La'asar
lis garin yayi dan sanyi Abba ya nufi gidansu don
daukan su Ummi zuwa kasuwa. Jikinshi sanye da
farin yadi mai shara-shara, har ana iya hango
fara kar din singiletin da ke ciki ta manne a
jikinshi. Kamshin turarenshi ya cika dakin Umma
wanda ba shiga yayi ba daga bakin kofa suka
gaisa. Ya ce, "Ummi su fito don Ummi ce ke
shiryawa tuni Fati ta fito, ya matsa kofar
Tsohuwa suka gaisa, sannan ya ce "Umma sai
mun dawo. Ya nufi waje yana fadin su Ummi su
mishi sauri. Sun fito za su duru a baya Abba ya
ce Ummi ta dawo nan gaba, ta zauna ranta
dagule don ita bata bukatar wani za6i tunda ba
wanda take so zata aura ba. Haka nan ta
fuskanci Abba yau yana cikin wani irin yanayi,
kila daga gida aka 6ato masa rai, nata tunanin
kenan. Shi kam takaicin zuwa za6on kayan ke
damunsa, ya kalli wayarsa da ke ruri ya daga,
Salis ya ce kana ina ne? Ya ce ina nan
unguwarmu zan kai kannena ne za su za6i kayan
daki. Ya ce, "Ta ina zaku bi? Abba ya ce kai kana
ina ne? Ya ce ina nan kusa da asibitin Malam,
bari in jira ka a jikin gidan man nan, Abba ya ce
"To." Salis ya kalli yarinyar da Abba ya ce Ummi
koma baya ya ce, "'Yammata sannunku, suka
gaishe shi ya yi murmushi ke ce Ummi?" Ta ce,
"Eh, ya ce ya su Umma?" Ta ce lafiya lau, ya
maida dubansi ga Abba wanda ke tuki cikin
nutsuwa ya ce, "Idris akan batun yarinyar nan ne
don Allah ka daure muje gidansu yau". Gaban
Ummi ya fadi. Abba ya ce, "Don Allah Salis ka
bar batun yarinyar nan, kai dai kasan halin da
nake ciki game da wata". Salis ya ce, "Me yasa
ka amsa kana sonta, kuma har kana daga waya
duk lokacin da ta kira ka?" Abba ya ce, "Shike
nan za mu je da yamma tunda wancan na rasa
madafa". Salis ya ce kuma fa da hakan zai fi
maka. Ummi gashin jikinta duk ya mike, suna fitar
da zufa lumshi ido tayi luf a kan kujera ta kwantar
da kai, Salis ya waiwaya ya dubeta, yaya dai? Ta
yi dan yake, "Ba komai." . 29.... Sun je gurin
kujeru da gadaje, Fati tayi ta ruwan ido yayin da
Ummi ta koma ta jingina a kujerar da ta zauna.
Abba ya dube ta. "Ke wanne ki ka za6a? Ita ta ce
wancan farin". Ummi ta yatsina fuska, "Nifa bani
da za6i, duk wanda ku ka ga yayi". Salis ya ce, "
Idris yarinyar nan ina zaton tana sonka, naga
tunda muka yi maganar zuwa gurin wata ta
canza yanayi. Abba ya ce, "Kyaleta ba wani ya
dubeta ba, ke Ummi tashi ki za6a mu ji
farashinsu, sauri muke. Ta ce, "Ya Abba cikina ke
ciwo, ka za6ar min don Allah". Ya ce, "Salis ita
ma a bata farin kawai ko? Salis ya ce, "A daukar
mata mai ruwan madaran, mai shagon ya ce sun
fi tsada, Abba ya ce ka daukar mata su. Sun
koma gefen kujeru nan fa Abba ya ce dole sai ta
za6a, nan ma wanda ta za6a a ka ce sun fi na
Fati tsada, suka ji farashinsu su sannan ya ba da
wani abu suka tafi. Ya sauke su a gida, Fati sai
ba Umma labari take yayinda Ummi ta shiga
kuka, Umma ta ce ke kuma lafiya ki ke kuka?
Ummi ta ce "Umma ni bana son in yi auren nan,
bana son in bar gida. Fati ta ce, "Shi yasa naga
tun a gurin shagon kina ta 6acin rai? Umma ta
ce, "Shirmen banza da wofi, sai ki tayi. Ta fice,
Fati ta ce Ummi ke kin cika son damuwa. Menene
na damuwa? Kila ma kina nan unguwar.ovels / ZURFIN CIKI book 3 part 5
ZURFIN CIKI book 3 part 5
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:29
ummi sannu da zuwanku, nan sukayi masa
gaisuwa yace ummi kaisu ciki. 36.. Zainab tace a
ranta wato ma ummi yafara gani, a fallon su
umma suke don nan ta fara kai su, tace umma
wanan ce zainab, wannan kuma matar abokinshi
salis, umma tayi masu sannu da zuwa sanna tace
ummi ta kaisu dakin bishira, sun shiga sun yi
mata gaisuwa, bishira tace ke ko gaisuwa baki zo
min ba koda yake bai dame ki ba, ummi tace
nima ana ta zuwa min gaisuwan ne a gd, duk yan
dakin suka kalli ummi, sahura tace ke asuwa?
Bishira tace ita a mahaifiyar shi, ummi tace
zainab kuzo muje, tun daga lkcn zainab tasa a
ranta akwai matsala a wanan familyn din, basu
jima ba suka yi sallama, inda ummi ta rakasu
daga can itama ta wice gd, suna shiga soro
shima ya shigo yace badai tafiya zakuyi ba? Ya
kalli ummi sun sha ruwa ma kuwa?ummi wadda
dama idanunta na kanshi ta amsa mishi da
idanu. Yace yama akayi kuka gane gdn zainab
tace yaya salis ne yakawo mu, ya kalli matar
salis yace madam mun gode fa,tace bakomai
Allah ya jianshi, sam ummi batasan lokacin da
furucin ya fito mata ba, sai dai taji tace ya abba
duk ka rame baka cin abinci ko? Shi kanshi yayi
mamaki don haka ya ya tsura mata ido, sai taji
kunya ta rufee ta saita kau da kanta daga
kanshi,don kada su zargeta. Kayi hkr naji wani
malami yace duk wanda yaranshi kananan uku
suka rasu to zasu ceceshi ranar gobe. Kaga ynz
kafara da daya,matar salis tace ai koma dayane
indai kayi hkr kayi tawakkali,ummi ta kalle shi
tace to kaji ma,yace ummi nifa tuni na
dangana,ta sake tausasa murya to meyasa baka
cin abinci? Ya tausasa murya wadda dama take a
dusashe yace ummi inaci,tace ya abba baka fa
yin karya,yace to yau zanzo inci a gabanki, ya
kalli matar salis wadda ke murmushi, in naci a
gabanta saita yarda ko? Tace tabbas! 37..Zainab
wadda takaici ya cikata tace da matar salis anty
nifa natafi, abba ya dubeta zainabu nagode ki
gaida su mama sai nazo,batare da ta tsaya ba
tace to, ummi ta musu sallama itama ta tafi gd.
Zainab ta dubi matar Salis bayan tafiyar Ummi,
ta ce, "Duk da son da na ke ma Idris din nan ba
zan aure shi ba". Matar Salis ta ce dalili? Zainab
ta ce, "Bana zaton ko matarshi ta gida da ya
aura ya aje yana sonta irin yanda yake son Umiin
nan". Abin nasu yayi yawa. Dubi yanda ya manta
da ni, ta ita kawai yake yi. Matar Salis ta ce, kin
ji ki da wani shirme, ita da zata yi aure?" Zainab
ta ce, "Abinda ke tausar zuciyata ke nan in na
tuna cewa zata yi aure, amma kai naga ji ba zan
iya ba, haka suka tafi tana ta bai wa yarta
labarin yanda Abba ke ji da Ummi. Kamar yadda
Abba ya ce zai zo cin abinci da dare yazo, Ummi
ta saka shi gaba wai sai ya cinye wake da
alayyaho da kifin da ta dafa masa. Da kyar ya
cinye plate din farko ya ce "Ummi na koshi kin ji?
Ta daure fuska tana kallonshi, shi ma ita yake
kallo yana dan murmushi. Ya ce, "Ina ma a ce
tun da da haka muka yi sabo, Ummin cikin
kwanakin nan kin lura cewa muna shiri". Ta
harare shi, "Kana zaton na manta da irin dukan
da ka yi ta min ne? Shi ma ya harare ta tare da
kwaikwayon muryarta. "Kina tsammanin zan
manta da irin tsokanar fadanki ne? Ko zan manta
da Suhailar Kaduna...?" Kafin ya rufe baki tuni ta
yi uwar daka da gudu, shi kam dariya yayi ta yi
yana cewa ki zo mana Ummi, kin fitowa tayi har
sai da ya bar gidan. Duk lokacin da suka kasance
tare kowannan su yana mantawa yana da wata
matsala. Saura kwana uku daurin auransu,
lokacin dangi sun soma zuwa, musamman 'yan
Zamfara. Ummi da Abba hankalinsu ya kai
kololuwa gurin tashi. Ranar ya ziyarci Zainab wai
ko zai samu 'yar nutsuwa. Bayan sun gaisa ta
sake mishi gaisuwa, shi kuma ya mata bangajiya,
dama tun da aka yi rasuwar bai zo ba. Ya ce
"Zainab ina ganin da an gama hayaniyar bikin
Ummi zan turo". Tayi shiru bata yanke ma kanta
shawarar matsawar ya cikata da zancan Ummi
yau kam za su yi ta ta kare. Jin tayi shiru ya ce
kina jina Ummi... ta katse shi da sauri, "Ba Ummi
nake ba Sorry Zainabu. Ya ci gaba bakina ne ya
saba da kiran Ummi, da yake daga ni sai ita ne a
gidan. Yanzun haka auran nan da zata yi ina cikin
tsananin kewarta...Zainab ta ce ina Idris? Don
Allah ni na hakura ka je ka auri Ummi, Abba ya
dubeta cikin tsananin mamaki. 38.. Me ki ke
fada? Me Salis ya sanar da ke? Ta ce Idris duk
wanda ya san so, minti biyar in ya zauna da ku
zai san kuna tsananin son junanku kuma ni na
tambayi Salis cikinku daya? Ya ce min A'a tun
daga nan nasan cewa ku masoya ne, ta nufi
hanyar gida, da sauri ya sha gabanta. Zainabu
kada muyi haka da ke, wallahi auranki zan yi. Ta
ce, "Eh ai na san aurena zaka yi, amma ba sona
ka ke ba, don Allah ban hanya sonka in zai yi
ajalina ba zan aure ka ba, ya kauce ta wuce, ya
bita da kallo har ta shige. Jiki ba karfi yake tuka
motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don
haka ya nufi dakin. 21. Jiki ba karfi yake tuka
motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don
haka ya nufi dakin. Bishira na zaune ta zuba
tagumi tunanin danta take, ga Abba sam baya
sakar mata fuska, ya ce "Lafiya Mamina take
kuka?" Ya shiga ya dauketa Bishira ta ce, "Rigima
cee kawai, ya nufi kan madubi inda ya hangi
pampers ya dauki guda daya ya nufi dakinshi da
ita. Bishira ta biyo shi itama ta zauna a gefen
katifa kusa da shi, cikin sanyin murya ta ce,
"Abban Walid don Allah kayi hakuri, ya ce me a
ka yi? Ta ce, "Gani nayi kana ta fushi, ya ce ni
bana fushi wannan kadan kenan ki ka gani daga
cikin sakacinki, na tabbata kin fini jin bakin cikin
mutuwar yaron nan. Musamman da ki ka zama
sanadi, amma don batun yawo ni na daina miki
fada, kiyi tayi illa dai zan nemo wadda zata dinga
lurar min da gida. Ta ce me ka ke nufi? Ya ce
aure zan yi". Ta doki kirji tare da fadin, "Aure?" ya
ce, "Eh". Ta soma kuka haba Baban Walid, wane
laifi na maka da zaka yanke min irin wannan
mummunan hukuncin? Ya ce, "Don Allah fita, ta
ce sai ka fada min dalilin yin auranka, ba za ka
bar ni in ji da rashin dana ba ko? ta mike an
zugo ka an ce kayi aure, to bisimilla. Ta fita ta
zari mayafi tayi gidan Umman Bashir. Abba ya
rungume 'yarshi ya yi laf a kan katifa shawara ya
yanke zai tura magabanshi gidan su Zainabu ba
tare da ya sake bi ta kan Zainabun ba. * Umma
ta leko dakin Tsohuwa, Ummi kin san na ce miki
kizo ki kwashe kayanki daga dakina ki adana su
ko? Kin san dai yau duk na nesa za su iso, ki cire
wadanda za ki bada. Tsohuwa ta ce, "Suwaiba
yarinyar nan ina kallonta jiya bata runtsa ba,
sannan da Asubahi a zaune tayi sallah. Umma ta
shiga dakin warwas take a kan gado, Umma ta
tasheta zaune Ummi ciwon kai ta keya ga jiri da
ta ke gani daga zaune. 39.. Umma ta ce taso ki
dan watsa ruwa ki karya, mikewar da zata yi sai
ta sulale a kasa sumammiya, nan suka dau
salati, Toshuwa kam kuka ta saka. Alhaji ya fito
wanka kenan ya ji Umma na salati, don haka
dakki ya shiga ya dauko waya ya kira Abba
lokacin yana kokarin shiga wanka. Alhaji ya kira
shi, jin cewa Ummi ba lafiya zari mukullin mota
ya fito. Sai da suka kai asibiti sannan ya lura da
silifas ya fito da jallabiyarshi ta wanka, Lkitan ma
bai zo ba lambarshi suka amsa Abba ya kira shi.
Ya duba Ummi sosai da kyar suka samu
numfashinta ya dawo, sun daura mata ruwa
sannan aka kaita wani daki. Likitan ya ce su zo
ofishinsa, Ya kalli Alhaji ya ce, "Gaskiyar magana
yarinyar nan tana bukatar kulawarku, ciwonta
baya son sakaci. Jininta ya hau ya wuce matakin
da zata iya samun mutuwar 6arin jiki. Su Alhaji
suka dauki salati,, ya ci gaba da cewa yanzun dai
addu'a zamu ci gaba da yi. Allah yasa in ta
farfado kada wata matsala ta biyo baya. Sannan
ya basu takardar magunguna". Alhaji ne ya amsa
don Abba fita yayi ya koma dakin da Ummi ke
kwance. Idanu ya zub amata, sam bai san cewa
kuka yake ba, sai da Alhaji ya shigo ya dafa shi
tare da cewa, "Haba Abba ba girmanka ba ne
kuka. Addu'a za ka yi Allah ya bata lafiya". Ya
share hawaye. Alhaji don Allah kada ka sanar da
Umma abinda Likitan ya ce, Alhajin ya ce ai
dama ba zan fada mata ba. Bari in je sai tazo ga
takardar maganin inta zo sai ka siyo, ya ciro kudi
ya mika ma Abba, Abba ya ce a'a da kudi a
jikina. Alhaji ya ce ka amsa ka kashe kudi cikin
kwanakin nan ina sane da duk lokacin da na ce
kazo ka siyo wani abu sai kawai in gan ka da shi
ban da kayan dakin da ka siya musu, Abba ya ce
ai ina da shi ne. Bayan fitar Alhaji Abba yaja
kujera ya zauna ya zabga tagumi tare da tsura
ma Ummi ido, a zuciyarshi fadi yake ALLAH ka
tashi yarinyar nan lafiya, Allah kasa kar ko ina na
jikinta ya nakasa. Alhaji ya fada wa Umma an ba
Ummi gado, don haka ta shirya su wuce. Abba ya
tashi ya nufi ofishin Likitan, bayan ya kwankwasa
Lokitan ya ba shi izinin shiga, ya same shi yana
rubuce-rubuce. Ba tare da ya dago kai ba ya ce,
"Zauna sai da ya kai aya rubutunshi sannan ya
dago kai ya kalli Abba "Ba dai mai jikin ba ce
ko?" Abba ya ce, "a'a ina son ne nima agwada
nawa jinin, Likitan ya ce kana jin jikinka ba dadi
ne?" Abba ya ce, "Eh da har yasa a dauko fayal
din Abba kuma ya tasa ya dauki abin gwaji.
Bayan ya gama ya zaunar, ya tsare Abba da ido
wai kun yi gadon ciwon nan ne? Abba ya ce,
"A'a, Likitan ya ce, "Jininka ya hau, sai dai ba
sosai ba. Kila don kai namiji ne kana kokarin
kauce ma abubuwa. Zan rubuta maka magani na
sati daya, kuma ka dinga kokarin yin bacci a kalla
na wa shida kada ka dinga yawan tunani. Kaga
kanwar nan taka, sai sa'ar gaske zata tashi
lafiya. Ku dai cigaba da addu'a, zata yi bacci na
tsawon awa tara ko goma. Ina son daidai lokacin
da zata farka ya kasance ta soma dora ido a kan
wanda suke shiri ko wanda ta fi so a cikin
mahaifanta ko danginta, Abba ya ce "To."
Lokacin da ya koma dakin su Umma sun zo har
da tsohuwa, nan Abba yake fada musu abinda
Likitan ya ce game da farkawa in tayi. Koda bude
bakin tsohuwa sai cewa ta yi ai ko dai ba a bar
mai sunan Malam ba, tunda an ce wanda suke
shiri, don in taga mai sunan Malam karasawa
zata yi. * 22. Duk da ana cikin wani hali sai da
su Alhaji suka murmusa. Abba kam daure fuska
yayi yana kallon Tsohuwa, Umma ta ce, "Ai da ne
Tsohuwa. Yanzun shiri suke tunda ta daina rashin
jinta". Likitan ya shigo ya sake musu bayani
kamar yadda ya yi ma Abba, sannan ya ce su
bata guri kada zantukansu ya farkar da ita a
samu matsala. Suka fito, Umma ta ce da Abba ya
tafi gurin aikinsa, su Alhaji ma suka fita tare da
Abba. Fati ta je gidansu Sahabi dan uwansa yana
kankarar rake a kofar gida, inda yake saidawa ta
tambayi Sahabi. Yaron ya ce mata ya ffita, ta ce
To in yazo kaa ce masa Ummi tana asibiti ba
lafiya, an bata gado. Karfe uku ya iso asibitin
hankali a tashe, sun gaisa da Umma ta raka shi
dakin, hankalinshi ya tashi da ganin Amaryarshi
kwance a gadon. Abba kam yana gurin aikinshi
amma hankalinshi na Asibiti, su Alhaji ma duk
nan suka nufo, Abba sai da yayi magriba sannan
ya shigo asibitin. Jikinshi babu karfi, bai matsa
sai yaga farkawar Ummi ba ne saboda yasan da
gaske ba shi ne ya dace idanunta su soma arba
da shi ba, ya samu su Umma da su Alhaji.
Sahabi da abokansa duk suna gurin, ya gaida su
tare da tambayar ko ta farka? Umma ta ce har
yanzun dai shiru. Ya nufi cikin gurin Likitan suka
gaisa, ya ce Likita har yanzu ba ta farka ba. Suka
jera zuwa dakin, Likiran yana cewa cikin wannan
dan takin zata farka, In sha Allahu. Sun shiga
takin tana dan motsi suka nufi gadon Abba ya ce
Ummi. Likitan ya daga mishi hannu alamar yayi
shiru ita kam daidai lokacin mafarkin Abba take
wai suna tafiya ya rike mata hannu sai ga
Sahabi. Yana zuwa ya kama hannunta tana
tirjrewa, sai janta yake zai fita da ita, Abba yana
tsaye yana kallonsu. Ita kuma sai kiran "Ya Abba!
Ya Abba!! Take yi. Likitan ya kara kunne gurin
bakinta ya dagowa yayi ya dube shi. "Waye Yaya
Abba?" Abba ya ce ni ne. Liitan ya ce, matsa
kusa, ya kama hannunta. Ummi. A hankali ta
bude ido. Ya Abba! Ya abba, zan sha ruwa, ya ce
to ya kalli likitan za ta sha ruwa, Likitan ya ce,
"A'a bari ta dan kara warwarewa tukunna. Likitan
ya kama kafafunta ya dan matsa, sannu ko. Ta
kalle shi, kin ji zafi? Bata yi magana ba ya dauki
allira ya 6are ya dan soka mata a tafin kafa ta ja
kafafunta alamun taji zafi. Ta yunkura zata tashi,
Ya abba zan tashi, ya tayar da ita zaune. "Likitan
ya ce Alhamdulillah, Abba ya kalli likitan, ba
matsala kenan? Ya ce, Ina zaton haka insha
Allah, Abba ya ce "Alhamdulillahi, ya jinginata da
jikinshi, sannu Ummina. 41.... Alhaji ya shigo
yana cewa, "Ina Abba ne?" ya ganta zaune a'a ta
farka ne? ya kama hannunta sannu uwata. Ta
kalle shi. "Ina Ummata?" ya ce, "Bari in kira miki
ita". Yaje ya sanar da su, sun shigo da murna.
Sahabi ya iso gaban gadon. "Sannu Ummi". Ta
kalle shi sai ta kwantar da kanta a kafadar Abba,
"Ya Abba ina son in wanke bakina". Ya ce, "To
bari in siyo miki Maclean din". Ta ce, "A'a kada
kaje". Ya gyara zama "To shi kenan." Umma ta
ce, "Me ta ke so?" Abba ya ce "Baki zata wanke".
Umma ta ce "Ai nazo mata da maclean da
burushin nata, don nasan ita gwanar wanke baki
ce". Nurse ta kawo wani dan kwano na silba
Ummi ta wanke baki da taimakon Abba. Likitan
ya ce, a bata tea mara zafi sosai, sannan a bata
magani. Takaici dan'kam a zuciyar Sahabi, irin
wannan shigewa da Abba ke matar da zai aura
tayi yawa. Kai shi fa wannan Yaya Abban bai
masa ba ma, don yana daure mishi fuska ko
gaida shi yayi d kyar yake amsawa. Shi fa tun
ranar da a ka ce mishi Ummi ba cikinsu daya da
Abba ba ya ji ya tsane shi. Umma ta ce, "Abba
an kira Isha'i. Sahabi kaje kai ma ka huta yaran
nan tun tuni ya ke nan". Abba ya kalle shi, "Ya
kamata ka tafi haka ko?" ya kalli Ummi sannan
ya dan rusuna "Sannu Ummi". Ta ce, "Yauwa"
"Innata ta ce in gaida ki da jiki, ni zan tafi sai da
safe. Me zan kawo miki?" Abba ya dube shi a
kule., "Don Allah Malam kaje ba za ta iya cin
wani abu yanzun ba". Umma ta ce, "Abba". Ya
kale ta, sai ta girgiza mishi kai alamun ya bari.
Sahabi jiki a sanyaye ya fice tare da cewa "Umma
sai da safe". Ta ce, "To Sahabi, ka gaida Innar
taka". Da ya fita ta kalli Abba "Wannan ba
halinka ba ne kada in kuma gani". Ya ce "To
Umma". 23. Su Alhaji sun yanke shawarar daga
auran Ummi a darua na Fati kawai, ita sati biyu
masu zuwa sannan ta murmure sai a daura nata.
Gidan su Sahabi sun ji haushi musamman
Innarshi, sun kashe dan abinda suka tattala don
bikin amma gashi an daga, su kam da an daura
auren in ta murmure sai a yi bikin. Sahabi ya
shigo gidan ranshi a 6ace, ya kalli Mahaifiyarshi,
"Inna wai sun ki a dauram?" Ta ce, "Sun ki, dama
ai gaddamar dan yau ce. Ban da shegiyar
gaddama ga 'ya can da a ka baka a daura ka
gaddame, to yanzun ina ranar abin da aka mana?
Gida duk dangi sun cika amma wai a daga biki,
mu kuma karamin karfi ne da mu, bare mu ce nan
da sati biyu zamu sake kashe kudi". Sahabi ya
tuna abinda Abba ya masa a asibiti, shi ne dalilin
da bai sake zuwa asibitin ba, yaja tsaki. "Kin san
Allah Inna ni kaina sai yanzun nake jin haushin
kaina da na ki amincewa da Badariyya. Mu zuba
musu idanu in za su sake kawo mana cikas sai
kawai in koma gurin Badariyya." Inna ta ce, "In
da tun jiya kamin zancan nan da tuni yau ba a
fasa daura auranka ba an ma da Badariyya". Ya
ce, "Kiyi hakuri Inna mu ga nufin su". * 42... An
sha shagalin bikin Fati kuma an kaita gidanta.
Ummi jiki Alhamdulillah, Abba kullum in zai je aiki
sai ya biya. Haka nan in ya dawo gida wanka
kawai zai yi ya tafi, wataran sai goma ko sha
daya. Abokanshi suna ta zuba duba Ummi, ita
kanta da lokacin zuwanshi ya karato ta dinga
kallon agogo ke nan tana kallon kofa. A zaman
asibitin nan Umma ta gama karantar su tsaf.,
matukar son juna suke yi, sai dai taji takaicin da
sai yanzun sonsu ga juna ya bayyana. Lokacin da
ya kasance an riga an bada Ummi ga wani sai
dai ta ci gaba da addu'a Allah yayi za6i na
alkairi. Bashir yayi murna da fasa auran Ummi,
dama a fasa gaba daya. Yana fitowa dakinshi ya
ji Ummarsu tana cewa, "Kin san Allah Tasalla,
uwar yaron nan da zai auri Ummi zata ga bakin
ciki, don mallake mata da za su yi. Tana ji tana
gani sai yanda suka yi da shi. Kuma ba yanda
zata yi sai Allah ya isa". Tasalla ta ce "Ban da
halin mutanan yanzun ba da sai na fada mata ba.
Kin san makotanmu ne ta baya, gashi su ba karfi
ba. Sahabin ne fa ke rike da gidan, kin san shine
Babban a gidan". Sahura ta ce, "Don Allah Tasalla
ki taimaka ki fada musu, don ko in har aka yi
auran nan in suna cin abinci sau uku ne a rana,
to za su koma dau daya". Tasalla ta ce "Ai ko
zanje". Tana fita Bashir ya dawo kusa da
Ummarsu ya ce, "Umma dama da kanki ki ka je,
saboda za su fi yarda tunda sun ga ke kina da
danganta da gidan". Ta ce, "To in Babanku ya ji
fa?" Ya ce "Umma ai in kin fada musu ai kwa6ar
su za ki yi, sannan kada kije a kan lokaci, kije ana
gobe daurin auren". Ta ce, "Saboda me?" Ya ce,
"Saboda su Alhaji Babban suji haushin rashin
fada musu da wuri". Ta ce, "Haka za a yi, kuma
in an fasa Malamai zan shiga don a hanata auran
ma kwata-kwata". Ya ce, "Kada kije wurin
Malamai yanzun tukun". Ta ce. "Ai dama sai an
natsa". * Abba ya fito cikin suit bakake, yayi kyau
matuka hatta takalminshi sawu ciki baki ne,
tamkar wani black America. Igiyar wuyan ta
zauna tsam, sai kamshi yake. Dakin Bishira ya
nufa ya daga labule, ta dago ta kalle shi yayi
matukar birgeta. Tana alfahari da shi matsayin
mijinta, ya ce "Kin shirya?" ta ce,, "Zuwa ina?' Ya
ce, "A'a, jiya fa na sanar da ke ki shirya da wuri
zamu je asibiti ki gaida Ummi". Ta watso mishi
wani kallo uku saura kwata, tare da cewa "Ko
garin nan ba a sanyi ba zan fita gaida wata can
Ummi ba bare da sanyin nan." Ya ce, "Dalili ta
mike tsaye "Ciwo bai kai mutuwa ba, da mutuwa
ya yi tazo ta min gaisuwa?" Takaici ya turnu'ke
Abba, da yake sarkin dankara magana ne, sai ya
ce "To ita ta kashe shi da zata miki gaisuwa?"
Ta kule da bakin ciki ta zabga mishi harara "To ai
kasan ni na dora mata ciwon, don haka dole in je
gaisheta." Ya ja tsaki tare da cewa, ballahaza
wadda bata san mutuncin mijin auranta ba". Ya
yakice labulen ya wuce yana jiyo ta tana cewa,
"Ba dai za ni ba ko me za ka ce". Ranshi a 6ace
ya isa asibitin, Ummi na zaune kan gado ta kosa
Abbanta yazo, ko karyawa ta kasa yi, yana
sallama suka hada ido. Nan ta ke ya ji ya manta
da duk wani bakin ciki da ya taho da shi, ya isa
bakin gadon fuskarshi dauke da murmushi. Itama
murmushin take yi, ya ce. "Ummi ya ya jikin?" Ta
ce "da sauki". Ya Abba kayi kyau sai ka ce
Manajan Banki". Umma ta saka dariya, shi ma ya
yi 'yar dariya, "To ko bankin zan koma?" Ta ce,
"A'a kafi kyau da dan jaridanka Ya Abba, balle in
kana turancinn nan a labarai". Ya lakuci
kumatunta "Ko kwanwata?" Ya juya ya gaida
Umma, Umma ta ce "Ka zo katafi gurin aikinka
fa". Ya ce, "Umma sai sha daya yau zanje gurin
aiki". Ta ce, "Ni na ma kosa a sallame mu". Abba
ya ce "Ai kila a sallame ku yau. Likitan ya shigo
ne?" Suka ce "A'a. Suna cikin karyawa Likita ya
shigo ya same su, ya kuma kafa mata dokokin
daina tunani, daina shiga duk wani abu da zai sa
ta cikin damuwa. Rage shan gishiri tare da
samun isassen bacci, ya kuma gargadi su Umma
su dinga nisantar 6acin
Home / ZURFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 3 part 6
ZURFIN CIKI book 3 part 6
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:31
Rage shan gishiri tare da samun isassen bacci, ya
kuma gargadi su Umma su dinga nisantar 6acin
ranta. 26. 43... ABBA Ya kwaso su ya maida su
gida, cikin satin Ummi ta murmure. Sahabi na
zuwa sai dai da sun gaisa yake tafiya.
Mahaifiyyarshi ma tazo, amma Bishira da Sahura
ko le'ke, Bashir ma yana ta sintirin zuwa. Ganin
haka Alhaji ya ci gaba da shirin biki, mutan kauye
dai dama an ce kada su dawo, Ummi dai bata
maida hankali ga komai ba. Ta ce ma Umma zata
je gidan Fati, Umma ta ce To sai ki je gurin
Sahura ta kwatanta miki. Abba ya same su suna
zancen, don haka ya ce ta shirya zai kaita ya
ajiyeta in ya tashi aiki sai yaje ya daukota. Yanda
ta samu Fati da Angonta ana ta ji da juna abin
ya tsokanota, sai dai ta kasa ganin dacewar
soyayyar da Sahabi. Da mijin Fati ya fita Ummi ta
ce, "Oh, Fati cikin kwana takwas dubi yanda ki ka
yi kyau". Fati ta ce, "Amma ban rame ba?" Ummi
ta ce "Eh to, kin dan rairaye". Fati ta ce, "Kai ai
dole, gaskiya ina koduwa, wallahi ba ya barina in
huta". Ummi ta ce, "Da me?" Fati ta ce, "Dallacan
ki gane mana". Ummi ta ce, "Wai da me? Allah
ban gane ba". Fati ta ce, "Ai ke sokuwa ce, gurin
kwanciya mana. Ummarmu ta samu ta dirka min
kayan sha na mata, gashi nan nazo ina ta shan
wuya". Ummi ta zaro ido, "Da wahala ne?" Fati ta
ce, "Tab, ai kin kusa kema za ki ji". Tsoro ya cika
Ummi. Ta ce, "Zan ce ma Umma ni dai kada ta
bani wannan kayan matan". Fati ta yi ta dariya
tare da cewa, "Ke yanzun sai ki iya wa Ummanku
wannan zance?" Ummi ta ce, "Sosai ma". Fati ta
ce, "Ko ba ki sha ba yarinya sai kin sha zafi, ana
kawo ni ko dan kwana daya bai raga min ba".
Ummi dai ido ya raina fata. Koda Abba ya zo
daukarta duk ta damu. ** ** 44..... Tasalla ta
samu uwar Sahabi ta fada mata cewa, in dole ne
sai danta ya auri Ummi, to ta amso mishi karya
tambaya. Don kuwa wata rana sai ta taso ta
ganshi ko da a hanya ne ta rasa samun hakan.
Inna ta tsure ta ce, sai a fasa babu dole, ita
dama tuni abin ya sire mata. Ana gobe daurin
aure gidan su Ummi suna ta shiri Ummi na ta
kuka, wannan karon ba Umma ba har Alhaji da
Tsohuwa sun kule da wannan iskancin da Ummi
ke yi. Alhaji ya ce "Ki sani uwata, wannan karon
ko kin tsokalo ciwon nan naki auren nan dole ne
babu fashi. Idan yaso jinin naki ya tashi ya ta6o
sama ba zan kuma daga auran nan ba". Lokacin
da Alhaji ke wannan fadan Abba yana gidan yana
zaune dakin Umma yayin da Ummi ke gefanshi
tana rusa kuka. Umma ta shigo ya ce "Umma
don Allah ki lallashi Alhaji a dan daga bikin nan
mana". Abba bai ta6a ganin ranar da Umma tayi
mishi irin wannan kallon da ta masa yanzu ba
tun tasowarshi. Sannan bata ta6a daka masa irin
wannan tsawar ba ta ce "Kai! Abba shiga
taitayinka, me yasa yanzun ka canza, ko kai ba
za ka hukunta Ummi ba da irin wannan yaro da
hankalin da take mana? Don gidansu kanta a ka
soma aure? To wannan karon ba za a daga bikin
ba, in yaso ta mutu, ke ko mutuwa ki ka yi
gawarki can gidan mijinki za a je a miki sutura".
Tsohuwa ma daga can tana yo nata fadan tare da
dauko tarihe-tarihen da tana cewa, "Lokacinsu
kaza-kaza". Abba ya sake kallon Ummi,
matsanancin kukan da take yi yana daga mishi
hankali, ya mike tare da kama hannunta, "Zo
muje". Ya bude mazaunin direba ya ce ta shiga,
shi ma ya koma ya shiga motar ya tasheta, tafiya
kawai suke ba tare da ya san in da suka dosa ba.
Kukan Ummi na tsikararshi, sun yi tafiya mai nisa
sannan ya tsaya a hankali cikin wata irin murya,
ya ce "Ummi ki fada min gaskiya kina son
Sahabi?" Ta dago ta dube shi, "Ni bana son shi".
"To me yasa ki ka fito da shi?" cikin dasasshiyar
murya ta ce, "Ba ni da yanda zan yi ne, saboda in
ban za6i Sahabi ba za a bani Bashir". Ya ce, "To
ke yanzun fada min wa ki ke so?" Gabanshi ya
shiga faduwa don tsoron kada kunnenshi ya ji
mishi ta ce wani ba shi ba. Ta kuro shi da ido
tamkar ta ce kai, amma sai take ganin in ta fada
mishi haka dan shirin da suka soma yanzun zai
wargaje, kila ma sai ya hada mata da duka. Wasu
zafafan hawaye suka gangaro kan kumatunta,
daidai lokacin da yake cewa "Ko dan digo ki ka ji
son ko waye a ranki kada ki rufe min". 45... Ta
girgiza kai "Ba na son kowa Ya Abba". Cikin wani
irin yanayi ya dubeta, "Shi kenan, sai ki je ki
hakura da Sahabin a sannun kin so shi". Cikin
kuka ta ce, "Ya Abba Allah ni bana son shi, kai to
ka hada ni da ko waye mana". Ranshi 6ace ya
dubeta cikin tsawa ya ce, "Ki rufa min baki tunda
ba ki ta6a son kowa ba ki zauna da wanda ki ka
za6i zama da shi. In da kina son wani ne to da
sai in cije in tunkari su Alhaji, tunda kuwa babu
sai in ce musu me?" Ya fada mota, ya koma kofar
gidan. Koda ya tsaya tafi minti uku sannan ta
fito, yana kallonta maimakon ya wuce gida sai
kawai ya nufi gidan Maman Iman makociyarsu da
suke shiri da ita. Shima kanshi na kan sitiyarin
motar har ttsawon shudewar wasu dakiku,
sannan ya nufi gida. 27. Misalin karfe tara
Umman Bashir ta rangada sallama a tsakar gidan,
Innar su Sahabi ta amsa tare da fadin "Shigo".
Sahura ta shiga tana tambayar "Ba kowa dai ko?"
Inna ta ce "Shigo mu kadai ne". Bayan sun gaisa
ta ce "Ba ki sanni ba ko?" Inna ta ce, "Eh."
Sahura ta ce, "To ni dai tsakani ga Allah zuwa
nayi in ba ki shawara bisa ga yarinyar da danki
zai aura. Tsakani ga Allah yarinyar ba ta da
mutunci, sannan iyayenta za su mallake miki da,
don ni kaina ya faru da ni". Sahura don makirci ta
soma rishin kuka. "Dana maigidana ya ba su riko,
ina sheda miki wannan zance 'yar uwa yanzun
tsakanina da shi sai ido, sun makkale shi komai
shi yake musu, ni ko da nayi wahalar ciki da
nakuda sai na tashi a banza. To da yake an ce
ciwon 'ya mace na 'ya mace ne, shi ne nazo in
sanar da ke. Amma in kin ji haushi kiyi hakuri".
Ta yunkura zata mike. 46... Inna ta ce, "Zauna
'yar uwa, na gode. Nima fa tuni auran nan ya fice
min a rai, dama da naga shi Sahabin ya dage ne
sai kuma suka aiko gobe azo za a daura aure sai
na hakura". Kafiin Sahura tayi magana sai Sahabi
ya doka sallama, Inna ta ce "Yauwa zo nan". Ya
nufo ta "Zauna kaji ma kunnenka". Ya rage
tsawo, Inna ta ce "Baiwar Allah ya ki ka ce?" Nan
Sahura ta soma zuga sharri, ta kara da cewa
"Yaro ina ga ma za ka san dan nawa da suke riko
Abba a ke ce masa". Cikin saurin baki ya ce, "Na
san shi". Ta ce, "To dana ne da asiri suka amshe
min shi, sai dai Allah ya isa". Ya tuna irin halayen
da Abban ke nuna mishi. Yaa jinjina kai, sannan
ya dubi mahaifiyarshi "Inna to da Kawu yayo
binciken halayan iyayenta ai ana ta yabon
halinsu". Inna ta ce, "Kin ji shi ko? To bari kaji,
kwanaki ma Tasalla da ke bayan layin nan tazo
ta fadan irin wannan matsalar ban kama ba ne
don na asanta da shegiyar karya. To kuwa an yi
biyu ba zan bari ai na uku ba, don haka a daran
ta tabbatar ma da danta an fasa gobe ya wuce
gurin Badariyya a daura, su kuma in sun ji shiru
sa ba wani can". Cike da murna Sahura ta koma
gida. * Maman Iman tayi lallashin duniya amma
Ummi ta ki yin shiru, ga zazza6i tamkar wuta a
jikinta. Sai kusan sha dayan dare sannan Maman
Iman ta rako ta gida, lokacin Umma tana ta
neman layin Abba a kashe. Ta ce, "A'a sun dawo
ne yanzun ni ke neman Abba in ji suna ina ne?"
Maman Iman ta ce, "Tun dazu tana gidanmu
zazza6i da ya rufe Ummin, na bata magani ta 'ki
sha". 47... Umma ta ce "Rabu da ita kar Allah
yasa tasha, aure dai gobe babu fashim dubi irin
yanda a ka sa gidan su yaron nan wancan karon
suka kashe kudi gurin yin girki da sauransu ba a
yi bikin nan ba. Yanzun a kuma dagawa daga
lokacin da muka samu?" Maman Iman ta ce, "Ai
ba zai yiwu ba, sai dai a bi ta da lallashi". Umma
ta ce, "Mun daina lallashinta tunda ko mun
lallasheta aikin banza ne". Maman Iman ta ce,
"To Allah ya kaimu gobem bari in shiga gida sai
mun shigo aiki da safe". Umma ta ce, "To sai da
safe". Ummi tana shiga dakin Umma taga baki
kwakkwance, ta ce a ranta "Mayu, don kalata sai
da wasu suka dada zuwa". Tana fushi da
tsohuwa amma duk da haka dakin ta nufa, ta
kwanta a bayanta don ita tuni tayi bacci. Nishin
kukanta ya farkar da Tsohuwar, kala bata ce
mata ba, sai sauka tayi ta shimfida a kasa ta
kwanta, sannan ta ce "Aniyarki ta biki Takwara".
Wannan dare gurin Ummi da Abba wani dare ne
mai cike da bakin ciki da tashin hankali, ko Sarkin
sata bacci ranar bai samu galaba gare su ba.
Dukkan su a kan kunnansu aka kira sallar farko,
Abba ya mike cikin rangaji, jin jikinshi yake yi
tamkar iska ta dauke shi saboda rashin karfi.
Ruwa ya diba ya watsa, wanka sannan yayo
alwala don yin nafila, addu'a yake Allah yasa
hakan shi ne mafi alkairi a gare shi. Da ya dawo
Masallaci kwanciya yayi amma baccin ya ki bai
fita ba sai kusan takwas. Koda yaga Bishira
zaune a tsakar gida tana karatun littafin sam bai
ji haushin rashin zuwanta gidan su Umma ba.
Nashi ganin duk wanda yaje tamkar yana murna
ne da rasa Umminshi da yayi, ita kuwa da gadara
ta fito don ya ji haushi, bata je ba yana son sanin
halin da Ummi take ciki amma ba ya ra'ayin
zuwa gidan su Umma. Shagonshi ya bude ya
shiga ya dan zauna har zuwa tara, yana kallon
lokacin da Jama'a suka yi ta dafifin shiga layinsu
don halartar daurin auran. Kurum sai ya samu
kansa da tare dan Aca6a ya hau ba tare da ya
shaida masa inda za su ba. Koda dan Aca6an ya
tambaye shi ce masa ya yi mu je. 48.... Ita ko
Ummi ranar zaune tayi sallah ta koma ta kwanta,
duk kaikawon ai da 'yan shewe-shewen da jama'a
dangi da makota tana jin su. Sai dai makoshinta
ya bushe ga zufa da ta rufeta, duk da yanayin ba
na zafi ba ne. Karfe goma daidai shi ne lokacin
daurin auran, layin ya dinke da jama'a, Alhaji
ranshi a dame don bai ga Abba ba. Ya kalli Alhaji
Karami, "Ina Abba ne?" Alhaji Karami ya ce,
"Abokan aikinshi ga su can sun zo ba a ganshi ba
son daukan daurin auran". Alhaji ya ce, "Su dauka
mana nasan yana nan tafe". Har sha daya ana ta
jiran 'yan gidan Ango shiru, su Alhaji suka tashi
dan aike gidan don a ce ana jiran wakilan ango.
Amma sai a ka dawo musu da sako wai sun fasa,
kalmar da ta rikita Alhaji ta tashi hankalinsa. Ga
jama'a an tara, Alhaji Karami ya ce wadannan
akwai kananan mutane." Daidai lokacin da muryar
wani Maroki ta ratso dodon kunnuwansu da
cewa, "Alhaji ku hanzarta Jama'a sun gaji da
jira". Alhaji ya dubi Alhaji Karami, "Aminu a daura
da Bashir". Alhaji Karami yayi shiru, can ya ce "A
daura da Abba". Alhaji Babba ya ce, "Ina zuwa".
Ya fito daga dakin Abba na da inda suke yin
shawarar, ya ratsa mutane ya ce a yi masa
magana da Suwaiba. Umma ta fito daga kicin ta
same shi a dakinsa yana tsaye yana kai-kawo ta
ce lafia? Ya ce Gidan ango ne shiru, an bisu sun
ce sun fasa. To shi ne na ce me zai hana a daura
da da Bashir? 49... Umma ta ce a daura da Abba.
Ya ce, "Haka ma Aminu ya ce. To ni ban ga
Abban ba ma, amma bari muje Allah yasa hakan
shi ne mafi alkairi". Take a nan a ka daura auren,
Habiba da Idris Alhaji Babba ya kirgo sadaki ya
mika. Alhaji Karami Waliyinta ya amsa, mutane
na ta al'ajabin yanda lamarin ya sauya. Umman
Bashir kuwa Bashir din ne ya shiga gidan hankali
a tashe yana fada mata cewa da Abba a ka
daura. Nan ko ta hau bala'i da zage- zage. Ummi
ko tunda ta jiyo guda na alamta mata an daura
aure, sai ta birkice ta shiga kowa da
numfashinta. Fati da ke kusa da ita tana
lallaminta ita ce ta kwala ihu, ba shiri aka yi
asibiti da Amarya. Fati ta shiga gidansu da kuka,
nan ta taras Ummansu tana bala'i sai lokacin ta
ji da Abba a ka daura. Ta ce da Ummar su to
menen ba shi ke nan ba? Umma ta hau zaginta
tare da cewa, kar ki ga kin yi aure sai in miki
shegen duka, Fati dai ta fice ta bar gidan. Sam
Umma bata ji dar da ciwon Ummi ba, wannan
karon don haka ma bata bi su Asibiti ba, da
kanwarta Saratu a ka tafi. Likitan yayi ta fada
lokacin da yake yi mata allurai, a kuma bata gado
Umma ci gaba tayi da kula da bakinta. Yayin da
zuciyarta take fara kar, ta sani kuma tayi Imani
Allah ba ya tozarta addu'ar bawansa, matsawar
bawan yayi hakuri tare da dogewa. Haka nan in
baka samu biyan bukatarka nan duniya ba lallai
gobe kiyama zaka tarar da abinka. Ta jima tana
rokon Allah yasa 'ya'yan nata biyu su zam miji
da mata su haifa mata jikoki masu albarka. Suma
su Alhaji suna ta sallamar baki sai dai yanzun ba
wanda ya damu ya gani irin Abba. Fatanshi Allah
yasa Abban yayi farin ciki da wannan hukunci da
suka yanke. Salis kuwa burinshi ya zama shi ne
mutum na farko da zai wa Abba wannan albishir
sai dai ya kira layin Abba sama da sau hamsim
bai daga ba. Abinda bai sani ba shi Abba ma gida
ya bar wayar, haka suka gama dauke-daukensu
yayi hira da Jama'a da kuma iyayen Ango da
Amarya don jin ta bakinsu a kan yanda auren ya
juye zuwa na zumunci. Haka nan suka tafi ya
samu abin sawa a Taskar labarai, burinshi yanzu
shi ne ya je ya nemo angon. 28 50.....Abba kam
kofar dan Agundi ya yada zango gidan su Mansir
abokinsu, shi ne kurum cikin abokan Abba da bai
yi aure ba. Yana isa kofar gidan Mansur na
fitowa za shi daurin auren, wani dan layinsu a
Gwammaja suka gaisa. Abba ya ce "Bari in dan
kwanta a dakinka". Mansur cikin mamaki ya ce,
Lafiya? Abba ya ce lafiya lau. Yana kwance dakin
Mansur idanunshi suna kallon agogo, zuciyarshi
tana raya yanzun abar sonshi ta zama matar
Sahabi. Sai dai bai san dalilin da bugawar
agogon karfe sha daya daidai tazo gwame da
bugawar zuciyarshi ba. Zuciyarshi ta fada mishi
cewa wannan alamu ne na an kammala daurin
auren. Wasu hawaye ne suka biyo ta gefen
idanunshi suna sauka a kan filon. Yini zur yana
dakin in lokacin sallah yayi sai ya fito kofar dakin
yayi alwala har duhun Magriba ya gabato. Ya fito
tare da kulle dakin, don Mansur bai dawo ba,
kuma dama ya ce ba zai dawo da wuri ba. Gidan
nashi ba kowa lokacin da ya shiga, kai tsaye
dakinshi ya wuce, ban da idanunshi da suka kai
kan wayarshi ya manta ma yana mallakinta. Ya
kai hannu ya dauka, bai ji mamakin yawan
missed calls din da ya gani ba, kiran Salis ya
sake shigowa. A kasale ya daga, muryar Salis ta
ratsa dodon kunnanshi, fadi yake yana
maimaitawa Ango- Ango. Abba cikin sanyin
murya ya ce "Salis ya haramta a gare ka ka
zolaye ni a halin da nake ciki. Sanin kanka kai
kadai ne kasan yanayin da nake ciki". Salis cikin
zumudi ya ce, "Kana nufin ba ka sani ba?" Abba
ya ce, "Me?" Salis ya ce "To bani goron albishir in
sanar da kai". Abba ya ce, "Don Allah Salis kada
ka min karya". Salis ya ce, "Ina rantsuwa da
wanda ya yi mu Ummi matarka ce, da kai a ka
daura. Ina ka shige lokacin da al'amarin ya canza
salo?" Abba ya mike zumbur. "Ka fa rantse Salis!"
cikin dariya Salis ya ce, "Wai har yanzun ba ka
sani ba? To ka aje min goron albishir dina". Abba
yasa hannunshi a baki ya gatsa, zafin da ya ji ne
ya tabbatar da mishi da ba mafarki yake ba. 51...
Ai sai ya katse wayar ya zube yayi sujjada ya fita
tsakar gida yana furta "Alhamdulillah." Ruwa yaja
ya watsa ma jikinshim sannan ya yi alwala.
Sabuwar shadda ya saka kalar kunkumadi, ya
fesa turare sama da kala hudu. Hula da takalmin
bakake, ya nufi Masallaci, daga can za shi gidan
su Umma don jin karin bayani. Bayan sun idar da
Sallah, mutane suka yi ta masa murna, nan ya
hadu da su Alhaji kawai yau sai ya samu kansa
da kunyar Alhajin. Alhaji ya ce, "Ubana ina ka
shige duk yau?" Ya rasa me zai ce, sai in-ina
"Am...na kwanta ne bana jin dadi". Alhaji yayi
'yar dariya, "Kai dai ka ce kana taya kanwarka
fushi don mun ce ba zamu daga aure ba, to ba
mu daga ba amma Allah cikin ikonsa ya sauya
lamarin". Abba tamkar bai san komai ba, ya ce
"Alhaji me kuma ya faru?" Alhaji Karami ya
karaso gurin su yana cewa, "Kai Abba ina ka
shige ne?" Abba ya dube shi "Nan dan Agundi na
shiga". Alhaji ya ce, "Oho, shi yasa aka yi ta
nemanka. To ka ji kuma yadda lamari ya sauya
ko?" Alhaji Babba ya amsa tare da cewa, "Shi ne
nake massa bayani, wato Abba iyayen yaron nan
Sahabi muka yi ta jiransu su zo gurin daurin
aure, wai ashe su sun fasa. Amma ba su shaida
mana ba har bin su fa nasa aka yi, gashi mun
tara jama'a kawai sai Aminu da Ummanka suka
ce a daura da kai, da ni na ce a daura da Bashir".
Dadi ya lullu6e Abba irin wanda bai ta6a ji ba,
Alhaji ya ci gaba da cewa, kayi hakuri mun kara
maka nauyi ba tare da mun ji ra'ayinka ba". Abba
cikin matukar murna ya ce, "Haba, ai ko ba 'yar
uwata ba ku ka daura min aure da ita zan aminta
bare jinina. Nagode". Sun ji mamakin yanda Abba
yayi murna, duk da sun san biyayya irin tashi ba
zai 'ki ba, tare suka rankaya gidan su Umman, so
kurum yake yaga Ummi. Ba mutane sosai, don
haka har ciki ya kutsa, sai dai suna hada ido da
Umma sai ya ji nauyinta, ta fada da fara'a. "Ina
ka shige Abba?" Yayi dan murmushi, ta ci gaba
"Sai kuma ka ji yanda abu ya kasance?" Ya ce,
"Na ji Umma, Allah yasa haka shi ne alkairi". Ta
ce, "Amin, Insha Allahu". Tamkar ya tambayi ina
Ummin, amma ya kasa. Umma ta ce "A baka
abinci ko?" sai lokacin ya tuna da batun abinci,
amma baya gabanshi, ya ce "Na koshi Umma".
Ta ce, "To ga na 'yan asibiti can in kayi isha'i".
Da sauri ya ce "Wa ke asibiti kuma?" Ta ce,
"Ummi ce, ko 'yan daurin auran ba su watse ba
don ka ji yarintar nan ta hau farin suma don
haushi ko leka su ban yi ba. Tana can it da
Saratu sai Tsohuwa da ta matsa yanzun Alhaji
Karami ya kai ta". Jikin Abba ya yi sanyi, kenan
tsabar rashin sonshi ne ya saka Ummi suma? Ya
ce Umma bani abincin asibitin. Sai da yaje
gidanshi ya dauko dan mukullin motar, a
zuciyarshi yana tambayar kanshi ina kuma
Bishira tayi ne? Zai bude motar kenan muryar
Bashir ta dakar da shi, "Kaci nasarar samun furen
zuciyata, amma ka sani ka kulla abota da rashin
zaman lafiya a novels / ZURFIN CIKI book 3 part 7
ZURFIN CIKI book 3 part 7
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:33
kulla abota da rashin zaman lafiya a gidanka". *
52..A fusace abba ya dubeshi"xansa yan sanda
su rufe min kai inhar zaka cigaba da kiran matata
da furen zuciyarka,rashin zaman lfy kake cewa?
An dade ba'ayi yaki abgdn ba kullum,bashir yace
oho dai ni zanta zuga umma abba yaja tsaki
tareda shigewa motarshi. Bashir yashiga gdnsu
inda su ummanshi dasu bishirabke zaune jugum
jugum tamkar masu zaman makoki,bishira tabi
bashir da kallo lkcn dayace ga ya abba ya can a
waje yashiga mota ya kure wanka,kila ma asibiti
zaije ana fada maku yanaso kuna wani tilasta shi
akayi,bishira cikin dasahhshiyar murya tace aiko
da bala'i don ko bazan yarda ba,umman bashir
tace sha kutuminki bishira,barni dasu zan
maganinsu, bishira tafita fuu,amma saidai. Kafin
ta isa gurin motar tuni ya, Cilla yabar mata
hayaki. Da innna saratu kanwar umma ya soma
cin karo a asibitun suka gaisa,tace ashe kuma
haka abu ya zama? Yace eh"nima dana dawo
dazu nasamu lbrin,tace Allah yasa hakan shine
mafi alkhairi,abba yace ameen inna,ya mai jikin?
Tace dasauki,yace bacci take? Tace a'a ta farka
tun kusan karfe uku,koda fatima ta fada mata
yanda abubuwa zuka zama,tayita yan koke
kokenta,gaban abba yafadi****tabbas ummi ba
son shi take ba inba hka ba meye na kuka? Ya
kalli inna bari in karasa,tace to kaje tshuwa na
ciki,a ranshi yace jaraba road,yasan dai ko yane
sai tshuwa tayi mishi surutu,yana tura kofar
tareda salama suka hada ido da ummi,sun kure
juna da kallo,kowanne nason ya fahimci ya dan
uwansa yadauki abin"tshuwa ta katse su dacewa
to zakin fama sai ynz kaga daman zuwa? Ya
dubeta eh" ai eh ace? To me kikeso ince,tace to
madalla ai na dade da sanin halinka,kuma da ace
iyayenku sunyi shawara dani lallai da baza suyi
wanna hadin ba Domin na tabbata kai zaka
karasa takwara don baka kaunarta, haushi ya
cika abba abba yana kallon tsohuwa yana tuna
amsar data dace da ita, ummi kuwa tsura mishi
ido tayi tana son jin me zaice,yace kamar kin
sani,tace ahaf shiyasa tausan yar nan kebani
tausayi, ta soma matsar ido,yace nima yakamata.
ki tausayamin tnda cusa min ita akayi,ummi
takoma ta kwanta lakwas tareda hakikancewabl
kalaman abba sako ne zuwa gareta,matar cushe
kuma bata daraja,to inaso kasan wani abu
guda,duk randa naji wani abu daidai da
wulakanci, toba kaiba har iyayenka saisun san
naje makura. 52..Dazun nake gaya masu basun
hada kai sun kulla auren nan ba,duk randa suka
kuskura sukazo min da batun warwareshi saina
basu mamaki,abba ya tabe baki tareda kallon
ummi wadda takasa jurewa tashiga rera kuka,ya
isa gaban gadon,"jikin ne ummi? Tayi shuru,kinci
abinci? Nan ma ta share,sai kurum ya nufi wurin
likitan zuciyarshi na kuna bako shakka kukan kin
shi ummi keyi,sun zo da likita ya shiga yimata
fadan kukan da takeyi,a cewar likitan kukan illa
ne ga lafiyarta,tshuwa ta kalli likita dan nan dole
ta koka a dauke ka ahadaka da wanda baya
kaunarka"abba cikin takaici yace subhanallla! Don
Allah tshuwa kibarni inji da abinda ke
gabana,tace ina ruwana da abinda ke
gabanka,likita yayi dariya yace mama yakamata
ki koma gd haka,abba yace bari inkaita
indawo,tace ban binka da can dani kazo? Abba
yace nahuta,likita yayi dariya,da kyar suka lallaba
tshuwa ta tafi da inna saratu,abba yaja kujera ya
zauna gaban gadon,bayan fitan likita Idanu ya
zuba ma ummi,godiya yake ma Allah a zucin shi
daya amsa addu'ar shi yabashi abar sonshi,itako
kai ta dukar a ynz takasa tantance kukan farin
ciki take ko takaicin kalaman ya abbanta? Wani.
Dan zare dake jikin hijabinta take wasa dashi,a
zuciyarta kuma tambayoyi ne da fuska data jefa
masa su,ya katse ta kinci abinci? Ta daga kai
alamun eh" yace to yakamata ki dangana da
kukan haka kisani ni kaina da ina nan bazan bari
su alhji su daura maki aure da wanda bakiso ba.
53..Da sauri ta kalleshi,yace. amma inkin yi hkr
zansame su zamu san yadda zamuyi,ta lumshe
ido a zuciya tace tab! Ai rabamu sai mutuwa,zan
juri duk wani ki dazan gani daga gareka,ya
katsxeta kina zance a zuci fadi abnd kikeson
cewa,tayi tagumi tareda kallonshi,ya abba yakanfi
dacewa sa dan sanda ne ba dan jarida ba,sbd
yanada saurin nazartar mutum,to amma meyasa
yakasa gane tana son shi? Yayi murmushi,zanso
inji abnda kikeb saqawa azuciyarki ko kinn samo
mafita ne? 29. Zancan mafitar nan tana bata
haushi, don haka saita canza zancen da cewa,
tambaya zan maka guda biyu, ya dan yi shiru.
Nazari yake, wace irin tambaya zata masa? Kila
zata tambaye shi ne ko zai amince ya sahale
mata auranshi, ya dubeta amsa daya zan ba ki in
kin yarda, ta ce To dama zance ne ya ka ji
lokacin da labarin sauyawar lamari ya zo gareka?
Ya kura ta da ido, ya tambayi kansa a zuciya, me
yasa take son ji@ yayi dan yake, yi tambayarki ta
gaba, ta tsura mishi ido. Yanzun yaya za ka yi da
maganar Zainab? Ya yi 'yar dariya, wacce amsa
ki ke so a ciki? da sauri ta ce ba ni wannan
amsar. Ya ce, "Kiin manta ni mijin mace hudu ne?
Ta zaro ido kamar ya ya? Ya yi kokarin danne
dariyarsa, sakamakon yanda ya ga ta zarana. Ya
ce, "Ina nufin bayan Zainab har da wata, Ummi ta
hade rai sannan ta zame ta kwanta cike da dana
sanin tambayar. Abba ya yi mamakin kishin
Ummi gare shi, ita da ba sonshi take ba? Ko da
yake an ce mace ko bata son namiji in dai mijinta
ne ta tsani ta ganshi da wata. Duk da haka ya ji
dadin yanda ta nuna kishinta a kanshi, da ya tuna
da Bishira ya ce tab, wata fitinar tana can tana
jirana yau. Sam Ummi bata kara magana ba, shi
kam Abba waya ma yake tayi Inna Saratu ta
dawo, don haka ya mike ya kalli Ummi. Zan tafi
ba tare da ta dago ba ta ce, sai anjima. Ya tafi
yana waiwayonta bayan ya wa Inna Sallama. Kin
shiga gidanshi ya yi sai kusan sha biyu a nufinshi
lokacin Bishira tayi bacci, sannan yaje ya sai
mata wayar da layi don yasan tana son waya.
Kudinshi kenan ma ya kwashe ya sai mata, bai yi
wani motsin kirki ba don kada ta farka, ya bude
dakinshi ya shiga ya fito yana jan ruwan wanka
kenan ta fito daure da zani a kirji. Jikinta ko dan
kwali babu, gaban Abba ya fadi ta ce, "Munafukin
Allah, annamimi dama ashe abinda kuke shiryawa
kenan? To ka sani dole kasa ke ni don ba zan iya
zama da Ummi ba, Allah ya kiyaye in hada miji da
wannan 'yar yarinyar, tunda kai baka ga ai baya
ba". Ya sassauta murya, "Haba Bishira, wannan
abin fa Allah ya kaddaro za a yi haka, matar
murtum kabarinsa. Ta ce, "To wannan ajalinka ce
tunda wancan ya ki shi ne kai a ka cusa maka.
Ya bar jan ruwan ya kama hannunta suka nufi
dakinta, tana ta masifa. Ya ce, kibar maganar
yanzu dare ne duk makota suna ji za su yi, kuma
banga bain da zai sa ki daga hankalinki ba. Kin
san dai ina sonki ko? Ta yi shiru tana kallonshi,
ya ce ina zuwa. Yaje dakinshi wayar ya dauko
mata, ga wayarki. Ta ce, "Eh don ka toshe min
baki k? to bana so, ita wa ya san abinda ka sai
mata? Ya ce, ya ki ke wannan maganar? Ban sai
komai ba ko lefe ma tukunna. Ta mike tare da
jefa mishi kwalin wayar, Ga tsiyarka nan
matsiyaci, dole ka saka min da haka, tuni a ka
gaya min tsiyar talaka na tafe. Haushi ya kama
Abba ya dauki wayarshi ya tafi ya maida yazo ya
dau ruwanshi yayi wanka, yana jiyo kukanta da
duk zage-zagen da take yi. Shi kam katifarshi ya
fada tare da rungume fito yana tunanin ranar da
Ummi zata maye gurbin filon. 30. Har an tada
sallah a Masallaci lokacin da ya farka, ya jima
bai yi irin wannan baccin ba, da hanzari ya fito
ya nufi ban daki don alwala. Abin mamaki Bishira
ce zaune kan kujera a kofar dakinta, matar da sai
ta kai takwas bata farka ba, amma yau bala'in
kishi ya hanata bacci. Ta ce, "Eh na fito a ba ni
takardata na gama zama da kai, ko in da take bai
kalla ba ya ci gaba da abinda ke gabanshi, ya
nufi Masallaci yana jinta tana ina nan ina jira ba
zan zauna ba. Haba, gaskiya naji na tsani
yarinyar ashe mijina zata aura, tsaki ya yi ya
bude gidan ya fice. Har gari ya soma haske yana
cikin masallacin, tunanin zuwa gidan yake, daga
karshe dai ya fita da niyyar zuwa gidan
Ummarshi. Wata zuciyar ta tambaye shi da cewa,
tsoron ta ka ke ji ne? Kar ka zama soko dai a
gidanka. A fili ya furta cewa, tunda na bita ta
lalama ta ki, bari in koma mata ta zafin, ida din
me? Sai ya sauya hanya zuwa gida rai 6ace,
fuska daure ya shiga gidan, tana ta kai-kawo a
tsakar gida. Ta dumfaroshi sai ka ce sabon
kamun hauka, daga ganinshi ta dinfaroshi. "Ka
ban takardata ba ni ba zama da kai, tafiya zan
yi". Ya harareta "Sai da takarda za ki tafi? Lallai
ba ki ji tafiyar ba. To ba zan bada takarda ba,
don ki sani, sai dai in kotu za ki kai can Alkali ya
baki". Ta nufo shi da zummar shako masa kwala,
ya ce Kina ta6a ni sai na zane ki, in yaso ki tafi
da hujja". Ganin yanda Abba ya bude mata wuta
sai taja baya, Ka isa ka zane ni, ai da ka san ka
dake ni, don ko sai ka sha dauri. Ya nufi dakinshi,
wanka ya fito yayi sannan ya yi shirin tafiya aiki,
amma har lokacin tana nan, ga 'yarta ta tashi
daga bacci sai kuka take yi. Ta dauke ta ta goya,
ta shiga dakinta can kuma ta sauke 'yar tasa
kaya ta fito ta dauraye fuska da kafa ta goya 'yar
tasa kaya ta fito taja kofar tana fadin." "Tafiya
zan yi". Ta fito ta same shi yana goge gilashin
motarsa na gaba. Ta ce, Tafiya zan yi sai an
kar6ar min hakkina". Murmushi ya saki, sannan
ya kalleta, ta ina za ki bi in rage miki hanya? Ta
dawo ta duki motar, Ba zan shiga wannan
gwanganin motar ba, kai ne bakon mota. Kafi
kowa sanin daga gidan da na fito, ko motar zuwa
cefanen gidanmu tafi wannan tsarri. Ya ce.
"Gurinki ko? Ni ai bani da wadda ta fita tunda
bata gidan naku nike hawa ba. Sannan kuma
tunda ba za ki zo in rage miki hanya ba shi
kenan sai naga sammaci. Ya shiga motar ya
tasheta yayi gaba, ba tare da ya saurari abinda
take cewa ba. Ta isa gidansu cikin tashin hankali,
Hajiya Zainu ta saurare ta tsaf, sannan ta ce "Kin
dai ga abinda a ke fada miki, kina ganin ba zai
faru ba ke so ya rufe miki ido, to yanzu an zo
gurin. Bishira ta ce, "Ai na gane komai yanzun,
Momy nayi nadama. Ta ce, "To zan tsaya miki
matsalata Babanku, yana nan a gari na kuma san
za su zo iyayen Abba. Amma wannan karon shi
kanshi Babankun zan iya ja da shi, Bishira taji
dadi sosai, don kuwa duk son da ta ke wa Abba
yanzun kishi yasa ya koma 'ki. Gidansu Umma
yaje a gurguje suka gaisa, ya kwashe su da Alhaji
da Alhaji Karami zuwa asibiti, a motar nema ya
ke fada musu cewa Bishira ta tafi gidansu Umma
ta ce a kan me Abba, me ka mata? Ya ce, "Ban
mata komai ba, ya fada musu duk yanda aka yi.
Alhaji Karami ya ce, Sahura ke zugata, itama ai
kwana tayi bala'in. Don haka kada kaje bikonta,
Alhaji Babba ya ce, "Ba za a yi haka ba, da dare
kazo muje, Abba ya ce To. Sun isa asibitin tana
wanka, sun gaisa da Inna Saratu ta fada musu
tana wanka, sannan likitan ya sallame su amma
sai sha biyu za su tafi gida, lokacin an karasa
mata allura. Abba can baya ya tsaya kusa da
kofar shigowa ya jingina da bango idanunshi suna
fuskantar kofar bayin, matuka ya kosa yaga
Ummi. Sanye da hijabi da zani daurin kirji ta fito,
da Abba suka soma hada ido, bai ta6a kallon
Ummi da sha'awa ba sai yau. Kamshin turaren
Abba ya ratsa ko'ina a dakin, ta zare idanunta
daga nashi, ta kalli Ummanta sannunku Umma.
Suka ce Yauwa. Ta gaida su sannan ta zauna
bakin gado tare da sunkuyar da kai, Alhaji Karami
ya ce, "Uwata jiki kuma ya yi sauki ko? Kanta na
kasa ta ce, Eh, ta kasa dago kanta, gani take
Abba ya cika dakin. Abban ya ce, "To ni zan tafi
don lokacin aikina ya kusa, Alhaji zamu je ne in
sauke ku? Suka ce To, Umma ta ce In an yi mata
Allurar anjima ma nemo mai Taxi. Alhaji ya ce, To
shi ke nan. Umma ta dubi Ummi ba za ki gaida
Yayan naki ba? Ta saci kallon Abban tare da
cewa, Au, ban ganshi ba. Ina yini? Ya ce, Umma
me yasa za ki rokar min gaisuwarta? Inna Saratu
ta ce, Kai Ummi da iya shege take, ina kallonta
shi ta fara kare ma kallo sannan ta kalli kowa
amma wai bata ganshi ba. Su Alhaji dai 'yar
dariya suka yi sannan suka fita, Abba ya bi su
tare da yi wa su Umma sallama. * 31. Bayan
fitarsu, Umma ta dubi Ummi fuska daure, ina
fatan baki nuna damarar nuna kiyayya ga Abba
ba ne? Ummi ta sunkuyar da kai, a ranta ta ce,
"Kin ji Umma da wani zance, ai ina zaton nafi
Mahaifiyarshi sonshi ma bare ku. "Amma a fili sai
ta ce, To Umma shi ma fa Ya Abban bai ce yana
sona ba, Umma ta ce Saratu ji ta da wani shirme.
Ina ce ita ce zata janyo ra'ayinshi gareta? Inna
Saratu ta ce, Kwarai kuwa, ta hanyar ladabi,
biyayya da girmamashi, musamman shi da ke da
matsalar mata. Ummi ta ce, Kuma ina tsoron
masifar matarsa ba dai guri daya zamu zauna ba
ko? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?
Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai
kama? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?
Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai
kama? Kada ma in ji kin kuma zan nan, Ummi dai
tayi shiru. Da dare Alhaji ya tasa Abba zuwa
gidan su Bishira, zuwan su ne ma Alhajin yasan
'yarshi tayo yaji, cikin 6acin rai ya kira wayar
Hajiya Zainu ya ce su zo ita da Bishira. Ba tare
da ya jira amsarta ba ya aje wayar, ba tare da
yasan abinda ya faru ba ya shiga ba su hakuri.
Hajiya Zainau taje dakin su Bishira ta kira, suka
nufi sashen Alhajin tana mitar cewa munafukai
sun zo kenan, ai za'ayi ta bari muje mu ji. Suna
shiga Alhajin ya kalli Bishira, "Me ki ka zo min ki
yi a gida? Ta ce, Daddy cin amanata ya yi, aure
fa ya yi da yarinyar da suka tsane ni. Alhajin ya
daukin da ke gabanshi na plastik ya jefe ta da
shi, auren shi ne cin amana don uwaki? Hajiya
Zainu ta ce, "A'a Alhaji, zan cen gaskiya a duba
hakkinta itama, ya ya za a dau 'yar da bata
kaunarta, iyayenta basa kaunarta a ba shi.
Sannan ta yi magana ya hauta da zagin iyaye?
Ya ce, "Ke yi min shiru ban tambaye ki ba". Ya
kalli Abba, Ya abin ya faru? Ban ji ta bakinka ba?
Nan dai Abba ya fadi komai har ta taho, daidai da
cewa tazo ya rage mata haya da abin da ta ce
duka. Alhajin ya yi tsaki ya dubi Alhaji Babba, irin
wannan ai ba a biyo su, tayi ta tafiya sai dai
nima in ba zata koma gidanta ba, to ba gidana
ba. Ya zura hannu cikin aljihu ya ciro rafar 'yan
dari bibbiyu, Ga shi Abba, dama nayi maka
alkawarin baka sadaki duk lokacin da ka nemo
aure. 57..... Abba ya ce, "A'a ka bar su ai an riga
an yi. Mahaifin Bishira ya ce, "Ni nayi alkawari.
Suka yi godiya. Ya kalli Bishira, Ko ki bi mijinki,
ko ki bar gidana. Hajiya Zainu ji take tamkar ta
shake Abba. Ta ce, "Haba Alhaji, gaskiya ban
yarda da wannann hukuncin..." Ya katse ta da
cewa, Ke! Da Allah fita anan. Su Abba suna shiga
mota Bishira na fitowa da kukanta, dole ta zo ta
shiga motar. Alhaji Babba ke ta bata baki har
suka kai gida, shi kam Abba da suke sauke Alhaji
ya yi nasu gidan, suna shiga ta soma zantuka. Ba
za ka ta6a samun kwanciyar hankali ba a gidan
nan har abada, ba dai ka matsa an dawo da ni
ba? Abba ya yi murmushin mugunta, ai ni
wannan yajin naki naji dadinsa, gashi har na
samu gudunmawa, kin ga sai naje kasuwa in
soma darzo wa Amarya zannuwan lefe. Ya nufi
dakinshi ya barta nan tsaye tana zage- zage,
lefen banza, in ma uban lefe ne kai da ita sai na
koya musu hankali. Kusan goman dare Ummi
tana kan doguwar kujera, addu'a take yi Allah
yasa Abba yazo ta ganshi kafin tayi bacci. Can
kasan zuciyarta kuma kishi ne don tasan sun je
gidansu Bishira ne biko ganin Alhaji ya shigo shi
daya sai ta debe tsammani da zuwanshi. A ranta
take raya cewa yanzun haka suna can suna cin
soyayyarsu, kamshin turaren shi ne ke mata gizo
a hanci. Amma sai kunnuwanta suka tsinkayi
sallamarshi, a hankali tamkar ba ya son a san ya
shigo. Umma tana ciki? Tambayar da ya yi kenan
ba tare da ya jira ta amsa sallamar ba, ta tashi
zaune da sauri a'a tana gurin Alhaji. Ya shigo ya
zauna ta ce, "Sannu da zuwa". Ya amsa yana
kalonta, ta sunkuyar da kai, gabanta ke wata irin
faduwa. Shi kam ji yake tamkar ya manne ta a
jikinshi, sai dai yana jin nauyin hakan tunda ba
suyi wannan sabon da ba rin haka zata faru
tsakaninsu ba. Dakin yayi shiru, ita tana wasa da
yatsunta shi kuma yana kallonta, can ya ce
"Ummi". Ta dube shi "Yaushe za ki tare? Ta ce,
Nima ban sani ba, sai yanda su Umma suka ce.
Ya dauko kwalin wayar da ya sai ma Bishira ta
jefe shi da shi ya ciro wayar ya hadata da batir
din bayan ya 6are sim din ya saka. Ummi dai
tana ta kallonshi, ya manna chajar a jiki, ya mika
ma Ummi jona min can, ya nuna mata soke din
da ke bayanta. Ta amsa cike da sha'awar wayar
duk da bata nuna hakan ba sannan ba ta ce kala
ba. Ya ci gaba da cewa, "Karfe nawa a ke kashe
inji? Ta ce, har yanzu ba a canza daga yanda ka
ke kashewa ba. Ya ce, "Sha daya zuwa sha biyu?
Ta ce, "Eh, ya ce in har zuwa wannan lokacin ba
kiyi bacci ba to ki cire in an kashe, ki kunna ko da
yake in dai ke ce ba sai na ce ki kunna ba. Ta
dago ido ta kalle shi, ya ce, Eh kunnawa za ki yi
ko za ki musa ne? Don kin fi ni ma sanin kan
waya. Ta ce, Wayar Umma kadai na iya kunnawa,
sai taka. Ya ce, Oho, cikin dan murmushi, na za
ci ba za ki fadi tawa ba in tuna miki lokacin da
kika kunna tawa. Haka nan don tsabar iya sarrafa
wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin
Kaduna. * 58....Haka nan don tsabar iya sarrafa
wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin
Kaduna. Ta zuba fuskarta cikin tafukan
hannayenta, sam bata son Ya Abba yana tada
wannan zancen, Umma ta shigo da sallama tana
cewa, Yuwa Ummi, ina ki ka sa min 'yar kwalbar
turaren nan? Ummi ta dago fuska, "Cikin jakarki
ta rataye. Umma ta dubi Abba, "A'a ha, yaushe
ka shigo? Ya ce Ban jima sosai ba. Ta zauna ya
gaisheta, sannan ta ce masa dama Alhaji yanzu
yake ce min zaman me Ummi ke yi a gidan nan?
Ya zaci tun daga asibitin zata wuce dakinta,
Ummi ta turo baki. Umma Alhaji ya gaji da ni
sosai, suka kalle ta, Umma ta ce, Ji wani shirme,
me ya yi na gajiya? Ta ce To dubi fa daga cewa
an fasa aurena sai da ya matsa ya daura min
aure. Sannann kuma yanzun wai ya zaci daga
asibiti zan tare? Abba ya ce, Ai yana daki yi
hanzari ki same shi don shi ya san amsarki ba
Ummata ba. Umma ta ce, "Wallahi daga nan suka
share Ummi. Ta kalli Abba ta ce, "To kawai
yanda za a yi gobe ka kwashe kayanka daga
dakinka sai a kai na Ummi din kawai. In yaso
zuwa yamma ko Saratu da sauran makota sai su
rakota. Abba ya kalli Umma, ni da so nayi a dan
yi kwaskwarima a gidan kafin sannan na dan
samu na sai ma Ummin Zannuwa. Umma ta ce,
"Zancen wofi, yanzun tsirara take yawo? Kawai in
kana da fenti a hannu a goga a kawo ta haka, in
babu ma dai goben nan zata tare don ba zan
amince ran mijina ya 6aci ba. Abba ya yi
murmushi, to shi kenan Umma da safe kafin na
fita zan nemo masu aiki ina da fenti da siminti
sai ayi 'yar kwaskwarima shi ke nan. Dama ga
kudi nan da Mahaifin Bishira ya bani, wai dama
ya yi min alkawarin biya min sadaki. . 59...
Umma ta ce, "Yanzun Alhaji ya gama bani labari,
Mahaifin yarinyar nan mutumin kwarai ne, don
Allah Abba ka rike yarinyar nan ko don darajar
mahaifinta. Ummi ta ta6a baki, kishi ya motsa.
Abba ya ce "In sha Allahu Umma nima abinda
nike dubawa kenan, ni ke hakuri da ita. Ta ci
gaba da cewa, Sannan kada kaga Ummi yar
uwarka ce ka ce zaka fifitata, sam ba zan yarda
da haka ba. Kayi adalci a tsakaninsu ka dinga
addu'a Allah ya hada maka kansu. Ya ce, "In
Allah ya yarda Umma zan kula. Ta ce, "To maza
ka tashi ka tafi gurin iyalinka. Sam bai ma dace
ka fito ba, kamata ya yi a ce ka zauna gida ka
kara ba matarka baki, ya cee To Umma. Ta mike
tana cewa, tashi maza. Ya mike yana kallon
Ummi, yayin da ita kuma ta juya fuskarta cike da
6acin rai. Ya ce, Ummi ki fa kunna in an kashe
injin? Sam ba ta tanka ba don haushi, sai da ya
tafi sannan Umma ta dubi Ummi. Ki tashi ki
kwanta don gobe ki tashi da wuri, kiyi duk shirin
da ya dace saboda babu daga kafa a tarewarki
gobe. Ki ta fasha-fishenki ba zamu kuma yarda
da kalace-kalacen ciwonki ba, ta tafi abinta. A
zaton Umma, Ummi tana fushin ba zata tare ba
ne, ita ko haushinta korar mata miji da Umma
tayi ya tafi gurin kishiyarta. Koda ta kulle kofar
ba ta shiga uwar dakin ba, nan kan doguwar
kujeta ta mike abinta. Jira ta ke a kashe Injin ta
kunna waya. Abba ko kafin ya isa gida sai da ya
fita titi ya fanshi kaji guda biyu da madara mai
tsafta.I novels / ZURFIN CIKI book 3 part 8
ZURFIN CIKI book 3 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:37
Jira ta ke a kashe Injin ta kunna waya. Abba ko
kafin ya isa gida sai da ya fita titi ya fanshi kaji
guda biyu da madara mai tsafta. 60...Sai dai
yana shiga gidan ya iske mahaifiyarshi da matar
tashi suna ta zage- zage. Ya nufi gurinsu, Sahura
ta ce, Sai yanzun suka barka ka taho? Ya ce,
"Umma dama ban dade da zuwa ba". Ta ce, "Ina
ta aiken kazo ina nemanka shi ne ka 'ki zuwa
saboda ka maida ni 'yar iska ko? Ya ce, A'a
Umma ba a fada min ba. Sannan aiki ne yasha
kaina... Ta ce, "Rufe min baki, ai baka daga kafa
da zuwa gun Suwaiba. To saurare ni da kyau ka
ji, nazo ne in fada maka cewa ka rubuta saki ka
ba wannan 'yar iskar yarinyar. Ya ce, Kiyi hakuri
Umma, ki bari sai a hankali. Bishira ta ce, Umma
yana sonta fa, jin ku kawai nake. Maganar Bashir
gaskiya ce da ya ce da shi a ka shirya hakan.
Umman Bashir ta ce, "Dama Abba kaima son
Ummi ka ke yi? Ya ce, Umma ba zan ki Ummi ba,
in kun yi la'akari da kaunar da iyayenta suke
nuna min. Amman wallahi ban san komai game
da auranmu ba, ta ce kana nufin kan dole a ka
daura muku aure ba don kana sonta ba? Abba ya
yi dan jim, ta ce kai nake sauraro, don ta tafi sai
ya ce kusan haka dinne, itama kuma ba sona take
ba. Umma ta ce, Ina ruwana da bata sonka, in
bata so iyayenta ai suna so. Ni dai bukatata
yanzun kada ka bari ta tare, sannan ko kusa kada
taga fuska a gurinka. 33. 61... Umma ta ce, "Ina
ruwana da bata sonka, in bata so iyayenta ai
suna so. Ni dai bukatata yanzu kada ka bari ta
tare, sannan ko kusa kada taga fuska a gurinka".
Ya dan yi shiru yana tunanin wannan irin lamari a
zuciyarshi ya ce, bari kawai in lalla6ata, zan yi
yanda ki ka ce sai dai kuma in su Alhaji suka sa
kawo ta ni ba zan iya ja da su ba. Sannann ke
kanki bana so a ce ke ki ka sa ni in ma Ummi
rashin mutunci, amma ki bar ni da ita in har ta
yarda ta tare a nan gidan. Bishira ta ce, "Tab, ba
ko zata tare a nan gidan ba". Umma ta ce "A'a ki
bari in sun matsa ta tare a nan din ta tare, gara
suna kusa muna kallon irin zaman da za su yi.
Can gefe ba sai su rinjaye shi ba". Bishira ta ce,
"Umma na tsani shegiyar yarinyar nan ne, bana
son in ganta ko cikin mafarkina, bare a zahiri".
Sahura ta ce, "Bishira na ce ki nutsu ki bar komai
a hannuna, in ma zan hada da Bokaye ne ba
Malamai ba in sha Allahu sai kin dara a gidan
nan. Ta ce, "To Umma, Sahura ta ce, Yauwa ke
dai ki zuba ido, Abba dai yana tsaye yana
kallonsu. Sai lokacin yayi magana, Umma dare fa
yayi, ta ce to muga ledar hannunka, ya mika
mata. Ta buda ta gani, "A'a kaza? To ku zuba
min nawa". Ya mika wa Bishira, Ki dibarwa
Umma. Ya nufi dakinsa yana jin sallamarta tana
fadin ta wuce, ya fito ya ce "To Umma sai da
safe, ya rufe gidan ya koma dakinsa. Da ya shigo
gidan ne da niyyar lallashin Bishira, amma yanda
abubuwan suka zama sai ya ji ba ma ya son
ganin Bishiran. Zantukan Bishiran da na
Mahaifiyarshi sun saka shi cikin tunani, lamo ya
kwanta a kan katifa yana ta harsaso irin zaman
da za a yi a gidan. Anya kuwa ba zai kama wa
Ummi haya ba? Cak! Hasken wutar dakin ya
dauke tare da tsayawar Injin. A fili ya futa, Mai
ya kare kenan, sai da ya yi shirin bacci ya
kwanta tare da manne filo a kirjinshi, sannan ya
dauko wayarshi ya kira layin da ya hada cikin
sabuwar wayar da ya ba Ummi. 62.. Gabanta ne
ya fadi, lokacin da taga lambar Ya Abba suna
rawa a fuskar wayar, ta haddace lambobinshi tun
shekarun baya. A fili ta ce, kenan ma ya hada
wayar ba yau ya soma hada ta ba, ta sake yin
lamo a kan gado tare da janyo filo ta manna a
kirjinta. Ta daga wayar lokacin tana daf da
tsinkikewa, can cikin makoshinta tayi sallama. Ya
amsa, tsigar jikinsa a tashe sakamon jin muryarta
tana ratsa jikinshi, ya ce "Ummi, ta ce Na'am Ya
Abba. Ya ce, "Kina son ki tare goben? Ta lumshe
ido, ba ni da za6i Ya Abba, duk yanda ku ka ce.
Dadi ya cika zuciyarshi. To shi kenan ki tare
goben, zan yi parking tun Asubahi sai in sa mai
fenti yayi kafin in tafi aiki. Ta ce, "Ba an ce in
mutum ya yi aure ana ba shi hutu ba? Ya yi 'yar
dariya, "To ni ba ki ga yanda auren nawwa yazo
daga sama ba? Amma duk da haka in na nemi
hutun za a bani, ta ce kayi aikin kama kawai ba
sai ka nemi hutu ba.. Ya katseta, "Don ba a sona
shi yasa ba a damu na amshi hutu ba? Ta ce,
"Ba nufina kenan ba, naga kana matukar son
aikinka ne". Ya yi dan murmushi "Kin dai
wayance kawai, to yanzun haka zaki tare babu ko
dan kunshi bare gyaran kai irin na Amare? Koda
yake ba aure so ba ne. Cikin muryar shagwa6a ta
ce, "Ya Abba ka daina, ya ce me zan daina? Kana
cewa bana sona, ai kai ma ba ka sona... Ya dan
yi shiru, yanda ta ke shagwa6ar ne ta tsuma shi.
Ya ce, ok, to goben sai kije ki gyaranki ko? ta ce,
"Umma ba za ta bari in fita ba, amma me yin
fulawa za ta iya ta mini". Ya ce, "To ina ne a ke
gyaran gashin? Ta ce, "Cikin gari ne, ya ce kin
san gurin? Ta ce, "Eh, amma ban ta6a yi ba, ya
ce to ki bari zan shigo gidan kafin na tafi aiki zan
ce Umma ta bar ki, ta ce "To." Suka dan yi shiru.
Can ya katse shirun da cewa, "Me ki ke tunani?"
"Yaushe?" "Yanzun." Ta dan musukuta, "Ina
tunanin yanda abubuwan za su kasance gobe.
Yanda har za'a yi fenti, sannan a jire kuma in tare
duk a gobe". Ya ce "Duk mai sauki ne, ni kuma
kin san tunanin da nake yi yanzun? Ta ce, "A'a,
ya ce gobe kamar yanzun muna tare... da sauri ta
katse wayar, me Ya Abba ke son fada? Ta kashe
wayar sannan ta kudundune. Ita ma yanzun ya
jona mata wannan tunanin, a fili ta furta gobe
kamar yanzun me ya ke faruwa? Shi kuwa sai ya
ji haushin kansa sakamakon furucin da ya yi har
ta yanke wayar, wani gefen kuma sai ya ga kila
don bata sonshi ne shi yasa har ta ji haushin
furucin nashi. Kila ma yanzun tana can tana kuka
in ta tuna gobe tana gidansa, dare ya tsala amma
ya kasa bacci, don haka sai ya mike yayo alwala.
Sallah ya shiga don kara nuna godiyarsa ga Allah
da ya bashi Ummi tare da rokon Allah ya kimsa
mata sonshi, daga karshe ya roki hadin kan
matansa. 34 63..Yana wanka da safe ya jiyo
muryar mum dinsa harta zo gdn, a zuciyarshi
yace innalillahi wa inna ilaihir raji'un, yana fitowa
tace wurinka nazo, Bashir yazo ya fada min cewa
yau za'a kawo fitsararriyar yarinyar nan ko? Abba
cikin damuwa yace umma nima bansani ba, tace
munafiki kasani, bari kaji ko an kawota ko
magana bance ta hadaku da ita ba, kai in ma
kaje girin munafukan iyayen nan nata su ka ce
yau zata tare kace saika shirya. Bishira tace
umma bazan yarda ta tare ba, bai sai min komai
ba, ya kalli Bishira to itama na sai mata wani
abun ne? Sahura tace to ina ruwan wani da baka
sai mata ba? Abba yace toni bani da kudi ma,
Bishira tace to kudin jiya da babana ya baka fa?
Umma tace fito dasu, yace umma dama fa kudin
sadaki ne ya biya min, kuma naba alhji karami
waliyyinta sai dai ki je gun shi ki amsa, tace don
kasan bazan tunkareshi bane shi yasa to tana
binka bashi, zaka chanza mata kayan daki, ka sai
mata zannuwa sannan ka bata jari, yace umma
banyi alkawari ba, in dai na samu kudi kuma ta
kwantar da hankalinta to xan mata, ya nufi daki
yabar su nan sunata zantukan su. Lkcn daya
shiga gdn su umman shi, ummi tana linke kaya
tana sakawa cikin jaka, yana daga bakin kofa ta
dago ta amsa sallamar shi ta kalle shi, ya kalli
kayan sam zuciyarshi bata mishi dadi, ya nufi
wurin umma don yana son neman alfarma abar
ummi zuwa dan wasu kwanaki don yana so ya
dan gyara gidan, rashin galihun zai yi yawa, ba
lefe kuma gida ba gyara? Yayi sallama suka
amsa, bayan ya gaishe su, ya dukar da kai yace
alhji dama nazo ne neman alfarma, suka ce
alfarman me? Yace inaso ne kudan bar ummi
zuwa nan da sati daya, sannan na gyara gdn,
kuma nayi mata sabbin dinki, alhji yace ba kana
da fentin ba? Kaje kasa a goga, sai ka biyo ta
kasuwarmu ka amshi zannuwa, abba yayi shuru
umma tace koda wani abu bayan nan? Yace a'a,
umma tace to an daga maka zuwa gobe, yace to
umma da alhji nagode, ya mike ya zai fita, yace
am umma ummi tace zata je gyaran gashi, suka
yi dariya su kace ai wannan ikon kane, yace to na
tafi alhji sainazo kasuwar, ummi ta jera masa
kayan karin kumallo koda ya leka dakin sai tace
ya abba ka shigo ga break, yace ummi zanyi latti,
tace to da yunwa zaka tafi? Yace akwai shayi a
can, tace come on ya abba zoka karya, ya kalli
agogo minti biyar gareni, ta dau copi ta tsiyayo
kunu ta mika masa, ya fara kurbar kunun, ta zubo
kosai a plate tarike a hannunta dauka kaci, ji take
tamkar ta bashi a baki, tsohuwa ta dago labulen
dakin, tace zura masa a baki za kiyi? Ummi tace
kada ya kware tsohuwa, an hana yin magana in
ana cin abinci, toshuwa tace tafi can da cusa kai
ba kwarjini, abba ya dire kofi tareda mikewa yace
ummi saina dawo, ki bari da dare zan kai ki
gyaran gashi, yasa hannu a aljihu ya zaro yan
dari binbiyu guda biyar ya bata, tayi godiya ya
ciro dari yaba tshuwa yace yar sa ido kema kiyi
kotso da wannan, ta rike baki tana fadin wannan
yara da munafunci suke, ya fita yana murmushi
ummi tace a dawo lfy, ya sake waiwayo wa ya
kalli ummi, suka saki murmushi, 35. 64....
Tsohuwa da ke bin su da ido ta ce, "Kai ban
yarda da ku ba Takwara, dama can ke da me
sunan Malam soyayya ku ke? ---- Umma da ta
tsinci zancen bayan fitowarta daga dakin Alhaji,
ta ce "Ya a ka yi?" Ta ce, "Suwaiba ina ga
yarannan tuni kallonmu kawai suke. Sai wannan
salo suke wa juna, sannan ga Takwara ciwon
barin gida shiru, ina ga dama ciwon nan na mai
sunan Malam ne." Umma ta saki dariya tare da
cewa "Allah yasa haka ne. Ummi kam cikin daki
ta kule zuciyarta zallah dadi. Misalin karfe biyu
Umma ta dan kishingide baya, ta idar da sallah,
tsuwar wayar da da Abba ya ba Ummi ajiya ce ta
farkar da ita. Ta ce, Ummi me ke tsuwa a dakin
nan? Wannan dai ba wayata ba ce. Ummi da ke
tsakar gida ana mata zanan fulawa ta ce, Lah,
Umma Ya Abba ne ya bani ajiya. Kila ma shi ne
ya kirata, ta dubi wadda ta yi mata zanen fulawar
ta ce Sabira don Allah shiga ki dauko min a kan
gado. 2missed call ta gani, ta ce kash! Sai gashi
ya sake kira, kafin ta daga sai da ta leka dakin
tsohuwa ta hango ta kwance a gadonta. Dama a
kofar dakin Tsohuwar take ta biyo inuwa ta daga
wayar tare da sallama, ya amsa cikin dokin jin
muryarta. Ina ki ka shiga ne? Ta amsa a can
cikin makoshinta, ana min fulawa a tsakar gida
wayar kuma tana daki. Ya ce, Ok ana miki zanen
fulawar ne? Ta ce an ma ganin har ya fara
bushewa ya saki murmushi tamkar yana gabanta.
Ana yi miki me kyau? Ta ce, Eh yayi kyau sosai,
ya ce Good, zan dawo kamar karfe uku saboda
zan kwashe kaya za a yi fenti a daki, so kin ga
ba zan samu kai ki gurin gyaran gashin da wuri
ba. 65... Don haka sai mu bar shi zuwa dare ko?
Ta ce, "To Ya Abba, ehm za a dafa maka wani
abu ne? Dadi ya lullu6e shi amma saboda
burinshi na kimanta Bishira a idonta sai ya a'ah.
Na hutar da ke zan ci na Antynki Bishira,
maganar ta soki ran Ummi har ta kasa magana,
ya fahimci hakan don haka sai ya kawo zancen
da cewa sai nazo. Ta tura baki tare da cewa
uhm, tana kashe wayar ta shiga kunkunan cewa
in yaso kaci abinci gidansu bana ta ba. Tsohuwa
da ke sauraronta ta sheka dariya tare da cewa,
ba dai ke kin ce me sunan Malam ba? Sai ma kin
je gidanshi yarinya ban miki baki ba amma za ki
raina kanki. Ummi ta cafke cikin jin haushi ta ce,
wai to Tsohuwa da za ki ce na ce Ya Abba cewa
nayi ina sonshi? Kuma da su Alhaji suka jona ni
da shi da naki har da ke za a dinga cewa ban yi
biyayya ba. Tsohuwa ta ce, Raba ni da gulmarki,
kina sonshi ai ni ba yarinyar goye ba ce, kina
waya kina kashe murya, san nan ciwoce-
ciwancanki duk sun lafa. Sai wannnan rawar kai
ki ke, to ki sani me sunan Malam dai ya aure ki
ne don dole, matar cushe kuwa ba daraja take
ba. Ummi ta ce, "To nima dai ai ba sonshi ni ke
ba, ni dai tsohuwa don Allah ki daina samin ido.
Ta mike, Na ma bar miki kofarki. Ta nufi kofar
dakin Alhaji tana kunkunai. 36. 66... Sai dai duk
da haka kalaman tsohuwa sun tsaya a ranta,
matar cushe bata daraja, Ya Abba kan dole ya
aureta, lallai zancen tsohuwa abin dubawa ne.
Abba ya shigo gidan uku da doriya, tare yake da
yara guda biyu, dayan zai mishi dan face-face,
dayan kuma zai masa fenti. Sune suka taya shi
kwasar kaya, bai samu Bishira a gidan ba, kila
tana gidan Ummanshi, ko makota. Sun kama
aikinsu shi kuma ya shiga kicin don ya dan dafa
abinda zai ci. Bishira gidan Anty ta tafi kuka take
wiwi wai ita fa ba za ta iya zaman gidan nan ba,
ta ce "Aunty Farida tunda kuna shiri da Baban
Walid ki ce masaya sawake min". Anty Farida ta
tsura ma kanwarta ido, tausayin Bishiran ya
cikata. Tabbas kishiya bata da dadi koda
mahaukaciya ce bare mai hankali. Sai dai ita bata
da ikon da zata hana ayi kishiyar koda kuwa
mijinta ne ke son yi, don sunna ce ta mai tsira da
Aminci. Bishira ta katse mata tunani da cewa,
dubi fa Anty hatta Dady yanzu yafi son Baban
Walid fiye da ni. A gabana ya dauki kudi yaba
baban Walid, a halinni kara na kai a kar6ar min
'yancina, kuma Momy zata yi magana ya hanata
cikin tozartawa. Hakan da Daddy yayi ba zubar
min da kima yayi ba, har da ita Momy? Yaushe
Baban Walid zai sake ganin darajarta? Anty
Farida ta sauke ajiyar zuciya, ta ce "Bishira Dady
bai zubar miki da mutunci ba, illa kara tarairayo
miki mutunci da yayi daga ke har Momy. Kuma ni
ba zan ce mijinki ya sake ki ba, haka nan ba zan
ga laifinshi ba, domin aure sunna ce ta Manzon
Allah (S.A.W), sam ba zan yi fushi da wanda ya
raya Sunna ba, koda mijina ne. Kiyi hakuri
kanwata koda bani da kishiya nasan akwai zafi,
amma kema kina da laifi, dube ki fa. Yanzu
Bishira wa zai gan ki ya amince ke kanwata ce ta
hudu? Zato za a yi ke yayata ce, kin saki kin yi
ragwaf, nonuwa har ciki haihuwa biyu jal, dubi
yanda tsabar datti yasa fuskarki da dokin wuyanki
zuwa bayanki duk kyasbi ya miki riga. Da kin
zauna kusa da mutum wari ki ke tashi, hakora
sun miki yalo, kai mijinki fa ya yi kokarin ba
kowane zai dauki hakan ba. Duk ba ki kalli laifinki
ba sai don ya kara aure yanzun? Ina ce kwanaki
garin shegen gantalinki ne ki ka bar danki a gida
ya fada rijiya ya mutu? To hatta Abban Nasir ce
min ya yi da shi ne ba zai yarda ba, saboda haka
ki dawo hankalinki ki zubar da kazantar nan ki
kama Ibadarki. Bishira ba kya jin kunya a ce ba
kya sallah? Kuma a tare da haka kina da wannan
kazantar ki ke kaurace ma shimfidar mijinki.
Kwanan baya ya kira ni a waya ya sanar da
nicewa kin ce min ina wari, don haka ni kuma na
ceya tafi gurin mai tsafta mai kamshi. Shima fa
Anty magana yake dankara min don ba kisan
halinshi ba ne. Anty ta ce, "Bishira kina cikin
hadari, ga kin sallah sannan ga kauracewa miji ki
kwana Mala'iku suna tsine miki. To daidaita
sahunki, ga mijinki dan kwallisan dan Jarida mai
farin jini, ki kalli yanda in yana gabatar da
shirinsa yanda 'yammata kan kira su ce suna son
lambarsa. Amma ke kina sakaci da shi, ki dubi
yanda wata mata ta kawo masa hari kwanaki da
a ce ya yarda ke ba za ki san kina da kishiyar
waje ba. Ki shiga taitayinki zan dai miki taimako
daya in kinamince za ki natsu. 67.... Bishira ta
ce, Anty taimakon me? Ta ce, "Zan samu Momy
su taimaka su canza miki kayan daki, sannan
Dady ya ba mu kujerar Makka ni da ke da Aisha.
To sai ya ce tunda ke kin ki kwantar da
hankalinki ki kwantar da na mijinki to ya fasa
naki, mu harmun yi passport. Bishira ta zaro ido,
da gaske Anty? Anty ta ce, Allah da gaske. To
yanzun shi ne ni ke son in ce muje mu ba shi
hakuri kila ya amince. Bishira ta ce, Tashi muje
Anty don Allah, Anty ta ce kin tambayo zuwa can
ne? Bishira ta ta6a baki, nifa ko nan din ban
wani tambaya ba, wallahi gidan ne bakikkirin
nake ganinshi. Anty ta ce, "Ki dinga addu'a, kishi
yayi miki yawa. Sannan ki daina fita ba tare da
izinin mijinki ba, duk in da ki ka je har ki dawo
Mala'iku suna tsine miki. Don haka yanzun tashi
ki tafi gidanki, ni zan samu Hajiya da Dady yau
din nan kuma in sha Allah za amiki gyaran dakin,
sannan tafiyar za ta kasance tare da ke. Bishira
ta ce, Na gode Anty, amma don Allah ki barni na
dan huta a nan gidan duhunsa nake gani, don ba
ki ji yanda ni ke ji ba ne Anty ko da dana Walid
ya rasu ban ji kunci irin wannan ba. Ta sake
rushewa da sabon kuka wiwi, Anty kallonta kawai
take ta ma rasa me zata ce. Wayarta ta ciro
daga chaji ta shiga kiran layin Abba, lokacin ya
kira kananan kannanshi su Kamal suna ta fito da
kayan dakin Bishira saboda ayi fenti har an gama
nashi dakin. Wayarshi da ya ajiye a kan windown
dakinshi ta shiga ruri, ya duba, Anty ce. Ya daga
tare da sallama, ta amsa ya gaida ta cikin
girmamawa da mutuntuwa, ta amsa da fara'a
sannan ta ce, "Abba ga Bishira nan tazo tana
kuka, kuma ta ce min ba ka san ta fito ba". Ya
ce, "Eh haka ne, ta ce don Allah in baka wani abu
ina son ganinka. Ya ce To zan zo Anty, amma
yanzu ina aiki ne kayan dakin ta muke fita da shi
za a yi mata fenti ne, ta ce To ko da dare ne
haka, ya ce to zan zo. * 68.... Ummi tana ta zuba
ido ganin Abba amma shiru har a ka yi Magriba
tayi wanka tayi sallah. Tana zaune har Isha'i tayi
daga Masallaci shima ya nufo gidan su Ummi,
lokacin Ummi tana bakin gado tana 'yan shafe-
shafenta.Ta juyo Abba suna gaisawa da su
Umma, ta shirya cikin leshi mai ruwan lemun
tsami, da dan mayafinta fari haka takalminta. Ta
fito tana zaune kan kujera, ta ce "Sannu da zuwa.
Za ka ci abinci?" ya ce, "Da sauri haka ba muko
gaisa ba?" Ta zauna ina yini? Ya ce, lafiya lau. To
na kawo abinci? Ya ce, daga gida fa nake, ina da
kuma mata. Ummi ta ta6a baki, oh, haka ne ashe
kana da mata, gani nayi da matar taka ka ke
zuwa cin abincin daga nan ta lafe a kujera tare da
hada rai. Ya mike muje ko? itama ta mike, ya
kalle ta da wannan mayafin za ki? Ta ce, eh, ya
ce a'a dauko hijabi ba zan lamunci yafa wannan
dan mayafin ba. Ta kalle shi kamar ta ce ai
matarka tana yafa irin shi sai kuma tayi shiru ta
nufi uwar daki don dauko hijabi. Shi kuma ya nufi
waje, ta yi wa su Umma sallama sannan ta fito.
Yana tsaye jikin mota ya ce, ina wayar nan? Ta
ce, "Gata nan a hannuna ya yi dan murmushi
yace mayyar waya dama nasan sai kin dauko har
yanzun cikin haushin maganar shi ta dazun take
yi. Don haka bata kula shi ba, ya shiga motar ya
bude mata gefen kusa da direba ta zauna cikin
fushi. Lura ya yi da hakan, don haka sai ya ce ba
ni tamata ta ce so nake in loda mata kudi. Ya
guntse baki don kada yayi dariya, ganin yanda
tamiko mishi wayar cikin hanzari gata Allah yasa
bacewa nayi a bani ba. Ta juyar da kai tana
kallon titi, shima bai sake cewa kala ba har suka
shiga cikin gari. Ya dube ta, wane shagon zamu?
Ta ce, duk wanda kaje, ni sanin wani saloon nayi?
Shagon wata mata ya kaita kusa da inda yake
aski, sun samu shagon Musulma ce 'yar
Maiduguri.Shamsy belloRFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 3 part 9
ZURFIN CIKI book 3 part 9
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:40
nayi? Shagon wata mata ya kaita kusa da inda
yake aski, sun samu shagon Musulma ce 'yar
Maiduguri. 69.... Abba ya ce mata ga Amaryata a
gyara mata kai duk da ba wai gashi ne da ita ba
ya yi kyau sosai ko nawa ne zan biya. Mai
shagon tayi 'yar dariya, zan mata yanda ka keso
ya dubi Ummi wadda ta samu kujera ta zauna
fuska daure. Ya ce, "Kanwata zan tafi nayi aski
nima, daga nan sai na dauki matata daga unguwa
na kaita gida, sannan ta san in har ta bude baki
to kuka ne zai kwace mata, don haka sai ta yi
shiru. Ya fita yana 'yar dariya, mai shagon
Yagana saloon ta ce, "Kai kanwata kun dace fa,
kuma da alamayana sonki sosai.Ta kalli mai
shagon hawayen da take makalewasuka zubo, ta
ce "Anty ina so a nan, dubi fa abinda yake
min.Komai sai ya ce min matarsa, matarsa, ko
inaruwana da matarsa? Yagana ta ce, "Yana da
matane? Sam bai yi kama da mai mata ba.Ummi
ta ta6a baki ta ce, "Yana da mata da yakeso ni
bana sonshi, baya sona, iyayenmu ne sukahada
mu.Yagana ta ce, in ma ke ba kya sonshi shi kam
yanadauke da tsantsar sonki a idanunshi n
fuskancihakan. Ummi ta ce, "Anya kuwa? Bana
zaton yanasona ne, in kin ce yabi iyayenmu ne
zan fi yardadon shi din mai biyayya ne.Yagana ta
tura mata kujera, zauna in soma miki,sai da ta
fara gyara mata kai sannan ta ce, "In mamijinki
ba ya sonki to kuwa ba za a yi wuyarshawo kai
ba.Ummi tayi murmushi tare da kallon fuskarta
tamadubin da suke fuskanta, ki ke gani Anty? Ta
cesosai kuwa, ki tarairaye shi da kyau, kin san
shinamiji dai dan shauki ne da son nishadi.
(((KWARAI KUWWA!!!)))Ga kuma son tarairaya
kamar jaririn yaro, ummi tace, "To zan yi hakan in
har yin hakan zai sa ya soni.Yagana ta ce, "Zai
so ki, zan so kiyi gyaran jiki dafata, Umi ta ce,
kamar ya ya? Yagana ta ce, kayanmata zuwa
gyaran fata, wanda za ki sha don 'karinni'ima.
Ummi tayi shiru, don bata son irin
wannanzantukan.Ta ce, "Kin yi shiru, Ummi ta ce
Ummana ta ce bata son in sha komai, tunda ni
budurwa ce, in je wamijina da ainihin halittata.In
yaso daga baya sanin saboda 'yan garinmu sunzo
da shi daga Zamfara. Yagana ta ce, Hakan
mayana da kyau, domin Amare da yawa suna
shanwahala sosai kasancewar ba su saba
ba.Sannan mazajen ba su bambance ainihin
yandamatan suke. Ummi cikin gundira ta ce, Gara
ma nagyara fatar.Yagana ta ce, "Wancan ma za
ki neme shi, ko nangaba Ummi ta ta6a baki, ni
dai fada min na gayarnfatar.Ta ce, "Ina sai dawa
in kina so zan baki kije gida kihada kiyi zan hada
ma angon lissafi da shi Ummita ce, ba ni sai da
suka gama a ka gyara matagashi fes, sannan ta
dauko kayan ta shiga lissafamata kamar haka:-1.
Man Zaitun2. Lalle3. Kurkur4. Madara ta ruwaZa
ki hada su guri daya ki kwa6a, sannan ki
shafejikinki da su kafin shiga wanka, in ya bushe
idan zaki shiga wankan sai ki murje shi tas,
dukwadannan 'yan kurajen na fuskarki za su
mutu,jikinki ya yi laushi da sheki.Ga kuma wani.1.
Sabulun Ghana2. Dettol3. Zogale4. Farar
AlbasaZa ki hada Sabulun Ghanada da Dettol da
garinzogale, da farar albasa, ki hada su ki kir6a
kimurmule shima a jikin za ki ringa shafawa.Da
fuska kafin ki shiga wanka, zan bar ki da biyunin
sun amshe ki ma sun ishe ki. Yanzun ko inwanke
miki kafa? 39. 70.... Ummita ce, "Ina tsoron kada
yazo kuma kudin shi ba su kai ba, Yagana tayi
'yar dariya, kina tausayinsa ne? Ki daina tausayin
mijinki shi ne zai amfana da gyaran da duk za ki
yi. Ummi ta ce, "To wanke mini".Ta hada kayan
wankin kafa ta ce yarana ke yi amma zan miki da
kaina. Sai kuma taga zanen fulawa. Ta ce, "Au,
an riga an yi zanen fulawa ma ba dama ayi,
Ummi ta ce, Ohi ni na manta ma, to ki fada min
yanda zan dinga gyara kafar, ta ce To bari in ba
ki mai sauki ma. 1. Man kwaka 2. Man shanu 3.
Man Zaitun Ki samu man kwakwa da man shanu
da man zaitun ki hada man kwakwa da man
shanu guri daya, ki shafa da dare da safe. Ki dan
gasa kafar sannan ki wanke ki shafa man zaitun,
za ki ga yanda kafafunki za su yi tamkar ta jariri.
Ko ki yi na ruwan ko kumba, lalle ki hada su guri
daya ki shafa a kafafunki da dare. Da safe ki
wanke ki shafa man ridi, wadan nan kurum in kin
rike su za ki ba wani labari, Ummi tace zan
kiyaye in sha Allah. Shi kuma Abba yana fitowa
daga shagon aski kai tsaye gidan Anty ya nufa,
ya samu Bishira Anty ta matsa mata tayi wanka
ta bata kaya ta saka. Ta kira mai kitso tazo tayi
mata ta sata ta shafa turaruka. Tunda Abba ya
shigo yake kallon Bishira, sun gaisa da Anty,
sannan ta ce dama dai na ce kazo ne don Bishira
ta baka hakuri. Sannan in maka tuni da yin adalci
a tsakanin matanka, kuma na yi wa Bishira fada
sosai. Ta dubi Bishira, ki ba shi hakuri, Bishira ta
hada rai tare da turo baki, ta kalle shi cike da
tsananin jin haushin shi. Kayi hakuri ya ce ba
komai dama ni ban yi fushi dake ba, a zuciyarta
ta ce, ba ka isa in baka hakuriba, albarkacin ina
son zuwa Makka ne da kuma canjin kayan dakin.
Ya yi wa Anty godiya ta ce ma Bishira gobe da
wuri kiyi parking din duk kayan ki a waje da mun
zo sai mu shirya miki. Bishira ta ce, Allah dai
yasa su yarda, Anty ta ce,"Za mu su yarda in
Allah ya yarda. Ta dauko wasu kayan sawa da
sabbin kuloli ta ce ma Bishiran je kisa a motarku.
Abba ya ce, "Kawo in kai, Anty na gode sai
anjima, ta ce To Abba ayi ta hakuri". Ya ce, Ba
komai, Insha Allahu. Suka biyo shi a baya tana
kara jawa Bishira kunne kan cewa in har ta
kuskura ta ji wata magana ta 6ullo ta rashin
mutunci sai ta fasa tsaya mata a kan maganar
aikin Hajji ko Dady ya amince sai tasa ya janye.
71.... Sun shigo mata Muhibba tana baya tana
'yanwutsil-wutsil dinta tamkar kurame, haka suke
tafiyar. Ta zaci su nufi gida sai taga sun nufi
cikin gari. Bata tambaye shi ina za su ba, har
suka isa inda yayi parking ya dubeta, Madam ina
zuwa, hum kawai ta ce. Ya bude baya ya dauko
Muhibba ya sa6a a kafada ya nufi shagon saloon
din. Daidai lokacin sun kammala komai, Ummi ta
zari hijabinta da niyyar rufe kanta, Yagana ta ce
a'a kanwata bari ya gani don ya biya ni 'yan
kudina. Abba bai zaci Ummi tana da gashi ba,
domin dai acikin Hausawa 'yan Arewa za a iya
saka Ummi acikin ma su gashi. Yayi laya-laya a
dokin wuyanta baki sidik. Yayi murmushi, lallai
kin gyara da kyau. Nawa ne kudinki? Ta fada ya
ciro ya bata, sannan Ummi tazari hijabinta.
Mamaki take, Gida ya koma ya dauko Muhibba?
Yamiko mata ita, Ga 'yarki. Ta amsheta. Yagana
tace, yarinyar tana kama da ku. Abba ya ce, "Ai
'yarmu ce, suka yi mata sallama suka fito. Ummi
da Bishira a tare gabansu ya fadi lokacin da suka
ga juna. Bishira ta kauda kai yayin da Ummi taja
baya daga mazaunin kusa da direban da ta nufa,
ya bude mata baya ta zauna tana rike da
yarinyar. Ya tada motar suka dauki hanyar tafiya
kowanne zuciyarshi da abinda take karantowa.
Ummi tunaninta Abba ya je ya zo da matarshi ne
don yanuna mata shi fa matarshi yake so. Ita ko
Bishira nata ganin wulakanci ne na karshe da ya
dauko ta yazo da ita gurin wannan karamar
yarinyar. Shi ko Abba addu'a ce a zuciyarshi
Allah ya hada masa kan matansa, sai kuma ya
soma tunanin ina zai soma zuwa? Nashi ganin in
ya kai Bishira gida ya sauke ya tafi kai Ummi bai
mata adalci ba. Amma ya kula Ummi tana fushi
kuma yaso ya lallasheta, yana cikin wannan
tunanin ya tuna dawayar nan. Ya kalli wayar a
gefanshi. Dan murmushi yayi da ya tuna lokacin
da ta dangwarar masa da wayar don ya ce ta
matarsa ce. Yanayin yanda Ummin ke nuna
kishinta yana birge shi, koda bata sonshi tana
kishinshi sannan bata masa raini ko rashin
kunya. Kofar wani gidan saida gasassun kaji da
ire-iren kayan kwalam ya tsaya. Ya kalli Bishira
Madam mu shiga ko? Ta ce, "A'a ni fa ba zan fita
ba, ya ce To bari in dawo, ya nufi ciki. 72.. Ta
waiwayo ta dubi Ummi, ta ce "Ba ni 'yata
fitsararriya. Ummi ta mika mata tare da cewa
nima ai ba cewa nayi a bani ba, ta ce "Kar dai ki
min rashin kunyaki bar ganin an jona ki da mijina
ki zata za ki hada sahu da ni. Ummi ta ce, "Sai
dai kada a kuma in dai batun hada sahu ne, kuma
ban damu don mijinki ba bai sona ba, tunda ni ina
sonshi. Bishira cikin daga murya ta ce, oho?
Dama sonshiki ke yi? Yanzun na gane da nufi aka
yi. To ki sani kin sai ma kanki masifa da bala'i.
Ummita ce, "Kin ga bala'inki can, daga nan
batakara magana ba ta bar Bishira na ta masifa.
Tundaki ka za6i ki auri mijina zan shayar da ke
ruwan dana sani. Sai kin gwammace zama a
kurkuku fiye da gidan mijina, daidai lokacin Abba
ya dawo da ledoji guda biyu. Bishira bata yi shiru
ba sai zagin Ummi take yi,"'Yar iska, 'yar daba...
tsawa Abba ya daka ma Bishira, tare da cewa ba
ki ji kunya ba da ki ke zaginta amma bata kula ki
ba? "Ta ce, "To ka ji abin da ta ce min ne? Tsaki
yaja tare da daukar wayar da ta aje yasa a ledar
Ummi, sannan ya tada motar. Kofar gidan su
Umma ya tsaya, Ummi wadda dama ta kosa tazo
gida, ta bude motar ta fada gida cike da takaici.
Ya kashe motar sannan ya dauki ledarta ya kalli
Bishira, Ina zuwa. Kala bata ce ba. Illa baki da ta
cije, kirjinta na yin wata irin suya. Ban da tana
tsoron Anty kada ta fasa zuwa gurin Dadynsu da
tuni ta shago Ummi ta nadi 'yan kayanta. Dakin
Umma ta shige, Ummar tana shirin fitowa Ummi
na shiga, ta ce kun dawo? Ummin ta hadiye 6acin
ranta."Eh, mun dawo Abba a ya shiga gaida
Umma sannan ya mika ma Ummi ledar, gashi kin
manta Ummi ta amsa tare da cewa, an gode.
Umma ta ce, "Me ku ka siyo in ce dai ka sai ma
Bishira? Ya ce, "Eh na sai mata, kaza ce fa
Umma ba wani abu ba". Ta ce, "To shi ke nan
maza ka koma gurin su, yace "To. Tana fita ya
kalli Ummi akwai waya a cikin zan kira ki, kuma
bana bukatar ki kashe min waya. Ummi ta ciro
wayar da sauri, ta dibe shi ba wayar matarka ba
ce? Ya ce, "Eh tata ce, ta mika mishi cike da
kunan rai, ga abinku ka kira ni da layin Umma. Ya
ce, "Ke ce za ki cigaba da rike ma mata
tawayarta, ba tare da ya jira jin me za ta ce ba
yana murmushi, Ummi ta kasa gane cewa ita ce
matarta shi. Ko kallon kazar bata yi ba illa dai
tayi duk wasu abubuwan da ta saba yi kafin ta
kwanta, sannan ta kunna wayar tana tsammanin
kira. 73..... Shi ko Abba koda yazo Bishira tana
ta mitar don tsohon wulakanci an zo da ita an
shanya ta, bai ce mata kala ba illa dai motar da
ya tada suka nufi gida. Gidan duk kaya saboda
bai maida ba da a ka gama fentin, ya dauki
tsintsiya ya share dakin, sannan ya shimfida
katifa ya fito inda take zaune bakin Rijiya.
Muhibba tayi bacci tana rungume a jikinta, ya ce
kawo ta, ta mike a fusace ta nufi dakin ba tare
data bashi 'yar ba. Ya bi bayanta, so kurum yake
ya lallasheta ba wai don tsoronta ba sai don
tausayinta, yasan mata kan kishi za su iya yin
'yar karamar hauka. Wasu ma sai sun yi babbar
kuma bai dace ana nuna kishinsa ba, shi kuma
yana nuna ko 'in kula a gare ta, gefen katifar ya
zauna ya lalubo hannunta ya rike cikin
nashi."Bishira!" ya ambaci sunanta cikin sanyin
murya, bata amsa ba kuma bata dube shi ba, ya
ci gabada cewa, "Bishira ban ga abin damuwa ba.
Ko damata uku a ka daura min aure da su bare
daya, inkin yi la'akari da irin son da nake miki ke
kin san Bishira ba kiyayya ta hada mu ba. Kina
manta wannan ne? Ta dago ta dube shi ta dan
soma saukowa, yayi murmushi har yau ban daina
sonki ba, ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta turo
baki sai kace 'yar yarinya. To ai na sha jin a ana
cewa so daya ne tak, ya cehaka ne, ta ce "To
tsakanin ni da Ummi wa ke keyi wa? Da sauri ya
ce ke, ta ce Allah?Ya sake tausasa murya, haba
Bishira ya ki ke wannan zancen kema kin sani,
kuma don Allah na roki ki in muna tare ki daina
min zancen Ummi, ke kadai ce za6i na. Bishira
taji dadin wannan kalamai, don haka sukaci
namansu suka kwanta, ya bukace ta a nan masai
da ta ce kaje gurin Ummin mana. Ya ce, "Na ce
in muna tare bana son kina min zancenta. Sai dai
in kina son ci gaba da horon daki ke min ne.
Haba Bishira, ko tausayina bakya yi?An fi wata
uku kina haramta min halas dina. Kullum sai dai
ina azumi sai ka ce gwauro? Yajawota jikinshi, ya
rungume da kyar dai ya samu yadan rage
matsala, sai dai ita ma ya lura tayi missing
dinsa. Suna kwance har kusan sha daya saura
tuni ita tayi bacci, shi kam daman so yake tayi
bacci yakira Ummi. Ya mike yaje yayo wanka
sannan ya nufi dakinshi. Yaja katifarshi ya kai
dakin, sannan ya kwanta akai, ya kira Ummi
lokacin bacci ya soma figarta. Ringing din ne ya
farkar da ita, sai da ta kusa tsinkewa sannan ta
daga, kafin ta amsa sallamarshi sai da tayi wata
doguwar hamma.Ya ce, "Ke baccin ki ma ki ke
alhalin na ce zan kira ko? Ta ce, "Amma ka san
bacci ba ya jira in ya zo,ni kuma ba zan iya yiwa
bacci gardama ba". Ya ceto sarkin iya zance, yayi
nufin zolayar ta. Yanzun dai na soma tunanin kin
soma sona, gabanta ya fafi, sam bata son ya
gano hakan yanzu. Tafi son sai lokacin da shima
ya soma sonta. Ya katse mata tunani, hasashe
na haka ne? Ta ce, ko kusa, mene hujjarka da
fadin haka? Ya gyara kwanciya. Na farko naga
ana ta kishina, sannan tun da a kadaura aure da
ni sai ciwo ya kame kansa, kuma nalura kina ta
zumdin tarewa a gidana.Ya saki 'yar dariya,
yasan ya cika mata ciki da takaici, shiru tayi
nazari take wacce amsa zata bashi, ko dai wayar
zata kashe? Tamkar ya shiga zuciyarta, sai ya
ce.... 41 Tamkar ya shiga zuciyarta sai ya ce,
"Koda wasakada a kashe waya. Ranta ya sake
6aci, ta ce Ya Abba ka tafka kuskure da kayi
zaton ina sonka,sam ni bana wani kishinka. In
don ka ce wayar matarka ce na ce ka rike abinka,
sanin kanka ne ba ma shiri da matarka, kuma duk
abinda ka ce nata ne dole na guje shidon ba zan
dauki wulakanci ba. Batun ciwo kuma daka ce
tunda aka daura mana aure ka neme shi ka rasa
dama bani na dora makaina ba, kaima ina naka
hawan jinin ya tafi? Sannann kuma wane zumudi
na nuna na tarewa a gidanka, Ya Abba ka sani
yanda a ka tilasta maka aurena, to ni ma fa dole
tasa na hakura. Amma ka rike a ranka bana wani
sonka bani kamarina ina sonka, kalaman nata na
karshe sun burgeshi har sun sa shi yin da ya
sanin tsokale zancen. Sai kuma ya canza salo da
cewa, haka dai ki ka ce amma ina da ja mu dai
bar zancen, shin dazun kafin ki soma wannan
tunanin me ki ke yi? Ta danyi shiru tana
tambayar kanta. Dama mutumin nan haka ya ke?
Oh yanzun dabara zai min sai ya gano ko ina
sonshi dole, to kuwa bazai ji ba, ya katse ta da
cewa ban san ki da karya ba. Ta ce, ina tunanin
irin ukubar da zan sha a gidanka ne ta
wulakancin da zaka min, ya yi shiru zuciyarshi
tana cewa yarinyar nan ba ta san irinson da ka ke
mata ba ai ta ma dauke ka mugu kenan. A fili sai
ya ce, "Kuma fa kin yi tunani, Allah yabaki ikon
daukar ukubar da zaki sha tare kuma dajure
wulakancin da na tanadar miki goben Ummi. "Ya
fadi, wai dama da gaske wulakancin zai mata.
Gyara kwanciya kawai tayi bata kara cewa komai
ba, kuma bata da nufin cewa wani abu, yasa taji
haushi sosai, don haka sai ya tausasa muryarshi.
"Ummi kina ji na?" Uhm" Kurum ta ce, don ya
gane tana jin shi. Alkawari ta dauka ba zata sake
cewakala ba, tunda ya hanata kashe wayar. "Ba
ni da nufin miki..." Sai layin ya yanke daga
gefanshi, ta ce, "Gara ma haka". Tana kokarin
kashe wayar gaba daya kiranshi ya sake shigowa.
Tsaki taja kafin ta daga, kuma a ciki ta amsa
sallamarshi, sannan cikin murya mai kamar zata
rushe da kuka ta ce "Ya Abba ni fa bacci nake
son in yi". Ya ce, "Sam ba wani bacci da za ki iya
yoa sai tunani". Ta ce "To na ji, ina son yin
tunanin please".Ya ce, "Tunanin me za ki yi".
Cikin gundira ta ce,"Dole in yi tunanin yanda zan
kare kaina daga wulakancinka, don bana
tsammanin zan dauka" .Ya ce, "Wasa nake miki
fa." Ta ce, "Uhum, ban amince da cewa wasa ka
ke min ba, don na tabbata mu ba abokan wasa
ba ne".Ya ce, "To shi ke nan bari in bar ki kiyi
tunanin, amma tunanin yanda za ki faranta min
za ki yi". Muryar Bishira ce ta katse shi. "Oho! Ai
tun da na farka ban ganka ba na san ana nan
ana cin amanata". Ya kashe wayar da sauri, duk
da dai Ummi ta riga ta jiyo muryar Bishiran. Sai
dai bata fahimci me Bishirar take cewa ba,
ringingine tayi tare da dora filo a kirjinta, tunani
take yi wane irin zama za su yi? Koda bata da
amsa ta kudurce har abada ba za ta dauki
wulakanci ba, a shi ko a matar shi. Sai dai
alkawari ta dauka ba za ta musu raini ba,
matsawar ba su suka 6ullo da hakan ba. *
************************************** Shi ko
Abba rigima suka dinga yi da Bishira cikin tsohon
daren wai ya cuce ta ya kwanta da ita yazo yana
hira da wata banza. Kila ma ya saba kwanciya da
Ummin ne yau bai samu dama ba, Abba ya ce kin
so kanki in ki ka yimin wannan zaton, don ban
ta6a nemanki ba, kafinki shigo gidana, ko na
ta6a?"Ta ce, "Don ka san dai ni ba fuska". Da ya
gaji da iya korata ya rufe kofar ya koma can
dakin. 40. 74... Washegarin ranar, ga mamakin
Ummi tun misalin karfe goma jama'asuka cika
gidansu, a ka dora abinci. Can kuma saiga yaran
shagon Abba da dinkunan zannuwan daAlhaji
Babba ya sai mata.Ranar Abba bai shigo gidan
ba a waya ya kiraUmma suka yi magana, zuwa
karfe uku angama yiwa Ummi jeren dakin da yake
yana da girma yacinye komai tsaf.Fitar 'yan jere
babu jimawa sai ga Anty Farida dakannasu motar
tana da kaya tana biye da su, gadoda kujeru a ka
canzo mata.Suka jera mata sannan suka lodawa
motar na dasuka dauki hanya suka koma, Abba
kam yana gurinaiki amma zuciyarshi tana
gida.Fatanshi Allah yasa yana zuwa ya tarar an
kaimishi Umminshi, kawayen Bishira da
makotansu'yan jam'iyyarta duk sun shigo gidan
sun hadu saizugata suke yi tare da nuna mata
koda wasa kadata sakar ma Ummi fuska, kuma in
ta mata takamata ta duki 'yan kayanta.Suna
gidan a ka kawo Ummi, 'yan kawo Amaeyakam
suna jiyo habaici da zagin da su Bishira ke yi,don
haka suka ce kada a kai musu yarinyar.Inna
Saratu da Inna Harira suka ce ai kuwa sai
ankaita.Ba ko kunya Bishira ta zabga musu
harara lokacinda suka fada mata cewa ga
kanwarta sun kawomata, don Allah su zauna
lafiya tare da Aminci.In yarinyar tayi ba daidai ba
ta sata a hanya... takatse su cikin tsawa da
mikewa tsaye. "Don Allahku fice min daga daki
amanar kishiya? Har wai muzauna da aminci ku
ke cewa?Tayi 'yar dariyar yake "Kun yi kuskure,
ai batacanza daga sunan ta na kishiya ba, kuma
kowa yasan kishiya abokiyar gaba ce."Inna
Saratu ta ce, "Baiwar Allah jahilan mata sunesuke
yin irin wannan tunanin, amma ga masu ilimisuna
koyi da gidan mai tsira da Aminci
(S.A.W)ne".Bishira ta ce, "To kawai dai ki ce min
jahila ki huta,bari ku ji ba za n ba ku a 6oye ba,
zama ne za muyi shi na rashin mutunci, na kowa
ya iya allonshi. Don ina kishin mijina, kuma zan
nuna". Tirkashi! Lallai akwai daru kenan. To
masu karatu ku biyo ni cikin littafi na 4, kumana
karshe domin jin yadda za ta kasance atsakanin
Bishira da Ummi da kuma Oga kwata-kwata wato
@BABA MONO HAXOR
:-2**** ta dafa kafadata tana cewa kayi haquri mubarak na sani kana son nabeelah sannan itama tana sonka,sai dai kuma kayi kuskuren rashin bayyana soyayyarka gareta a sanda ta bukaci hakan,nayi kokarin dai- daita tsakaninku amma naji tsoron kada mutane suyi tunanin na aurar da nabeelah ga d'ana ba bisa son ranta ba sai dai bisa dole kasancewar ta girma a hannuna.......haka kuma yanzu bazan saka kaina cikin wannan matsalar taku ba amma zan goya muku baya bisa dukkan shawarar da kuka yanke,idan kuna nemana ku sameni a fallow*** na kalli nabeelah idona cike da hawaye na fara magana kamar haka'nabeelah ina sonki,kuma ina kaunarki, sai dai na kasance cikin irin mutane da sukan boye sirrin zuciyarsu,kiyi haquri ki gafarceni,nasan nayi miki laifi...nagode ki tashi ki tafi allah ya bada zaman lafia sannan allah yasa shine mafi alkhairi gareki........na miqe zan fita daga motar,ta kamo hannuna ta zaunar dani tana magana hade da wani kuka mai tsuma zuciya gami da sa tausayi kamar haka'yamubarak da farko na yarda kana sona amma yanzu na gane cewar soyayyar batayi tasiri a zuciyarka ba tunda har ka yarda zaka haqura dani kan wani ya aura,lallai na yarda baka kishina baka tausayina irin zaman da zanyi tare da wani namiji wanda ba kaiba,ka sani cewar zuciya ba zata aminci rabuwa da kaiba,jikina na haramtashi ga dukkan wani d'a namiji idan ba kaiba dan haka na qudiri niyyar mallakarka ka ta wane hali,yamubarak kayi kokari ka soni kamar yanda nake sonka,yamubarak kada ka bani kunya'*** na share hawayen dake zuba kan kuncinta,na kama hannayenta na kwantar da ita bisa kirjina,nabeela h ki amince da soyayyata gareki kada ki zargeni da komi sai alkhairi,nabeelah ina sonki kuma nine mijinki da yardar allah,da sauri ta tashi daga kan kirjina ta dafa kafaduna tana kallon fuskata,ta sumbaci goshina sannan ta rungumeni kan kirjinta tana cewa hakika farincikina ya karu,burina ya cika sannan alheri ya tabbata gareni.....amma *menene mafita? *da wane zance zamu tunkari abba? *sannan kuma lokaci yana da karanci garemu.... Na kalli nabeelah dake kan kirjina nace zaifi sauki muje wurin kawu aminu mu shaida masa halinda muke ciki...ni nasan me zan fada masa kuma zai yarda. *kai tsaye na tuka motar zuwa gidan kawu na tarar ya gama cin abinci yana gindin bishiya yana hutawa..bayan mun gaisa ya cigaba da magana kamar haka'lallai daga ganinku akwai matsala dan naga alamun damuwa gareku, shin ko baki son auren ne? Ya tambaya' na fara da cewa gaskiya kawu ita nabeelah ba wanda take son za'a bata ba,kawu yace wannan zancen banza ne dama shi yasa suke boye min to wallahi wannan maganar babu ita,ku tashi mu tafi gidan.... Na tuka mota har kofar gidan muka shiga shi kuwa kawu tun daga kofar gida yake ta fada..yana shiga su mama suka fito suna gaisuwa amma ko amsawa bayyiba ya cigaba da cewar'maganar auren nabeelah babu na soketa yanzu zata fada mana wanda take so kuma goben zan daura mata aure dashi...nabeelah ta kada baki tace'ya mubarak nake so' kawu yayi dariya yace au to ai shikenan ta kwana gidan sauki kuda dan iskanci abin na gidane ma kuke bata lokaci,to ai ni yanxu xan daura auren idan yaso kuje chan kuyi ta bikinku,sannan baba ya shigo yaji meke faruwa amma ba yanda zaiyi da kawu dan yasan halins doe qura ya zama waliyina shi kuma waliyin yamubarak aka daura auren*** take yamubarak ya daukeni muka tafi gidan kunshi daga nan ya kaini nayi kitso muka wuce gidan aunty nafeesat nayi wanka na saka rigar atamfa kaina ba dankwali na fito gareshi,wow nabeelah amma kinyi kyau,ya kamo hannu daga inda yake zaune gefen gadon,ya sumbaceni har saida numfashina ya dauke,ya kwantar dani kan gadon ya fara cire kayan dake.......hakika ban taba sanin haka yamubarak ya iya soyayyaba sai yau,lallai da tuni nayi asar miji,haka muka kasance cikin nuna kaunar juna har zuwaN CIKI book 2 part 1
ZURFIN CIKI book 2 part 1
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:05
Abba kwance kan gado,dare yayi nisa amma shi
ya kasa bacci sam.saboda matsalar da yake ciki
yanzun. domin kuwa matar shi in yaga bazai iya
ba sai ya sawwake mata,amma maganar auran
ummi koda Alhaji bai goya mishi ba bazai iya guje
mata ba. "yanzun menene mafita?"ya tambayi
kansa,wata zuciyar ta ce, "kayi shiru tamkar baka
ga wannan takarda ba,tunda ba wanda yasan ka
gani." a fili ya ce,"haka ne." ya ci gaba da
tunanin kila ma yanxun ya janye kudirinshi,tunda
yaga ummin bata da kan gado. don yaga rubutun
yayi shi ne tun ranar da aka haifi ummi,ko kuma
ranar sunanta. tunda gashi har da sunan ummi a
jiki.mafita kenan yayi shiru.wata zuciyar ta ce,"in
ko kayi haka kayiwa Alhaji da ummanka adalci?
koda yar su ba yar adam ba ce bai kamata ka
gujeta ba.ko don albarkacin son da suka nuna
maka. shin da ummi ta kasance mai jin magana
da nutsuwa,kuma mai tsananin kyau zaka
gujeta? Kada kayi zaton Alhaji yayi kudurin aura
maka yarsa ne don yasan zata zama mara ji,kayi
nazari. haka Abba yayi ta tunani har asubah
tayi,amma hukuncin da ya yanke shine yayi shiru.
sai dai ya janye batun rabuwa da matar shi,don
yasan yana sakinta zai zama mijin ummi,kai
batun nan hadiye ma cikinshi shine mafi dacewa.
dunkuna masu kyau yayi wa matarshi saboda cin
suna.haka yayi wa dan siyayya daidai karfinshi,ya
kawo ma umma. Taji dadi sosai nan ahj ya iske
su, shima ya shiga dakin umman ya xauna ya ce
a dauko masa abinci nan xai ci yau.ya dubi abba,
babana nayi sautun raguna xuwa qauye nace xa
a siyo nmanya.abba ya ce biyu?umma tace
hakan yayi.abba ai tuwan girma miyarsa nama,
aja rago daya xiqal a shiga wannan gida da shi?
abba yace,me xai hana tunda ban musu qaryar
arxiki ba sun san mu talakawa ne.ahj yace
xancanka dutse bacna,amma maganar ummanka
ita xa a bi, sannan xa a sai buhun shinkafa da
cefane a kai musu.ana gobe suna abba da
abokansa suka dira gidan da ragunan da kayan
mai jego da na yaro sannan ga kayan abinci. sun
samu anty a gidan,ta musu tarbar mutunci.da
yake abba xana waya da ita,ya fada mata komai
ta sani.hjy zainu da taji kukan raguna ta fito,anty
tace dan Allah momy kada ki musu magana,kin
ga shi da abokansa ne.da qar ta samu ta turata
sashin ahj,shi kuma murna yayi yace aje a daure
su.zainu tace ahj menene na numa farin ciki sai
kace ba ma cin nama?can ba xa a ka kada ba
dan kawai shagalin sunan, sannan tace harda
shinkafa suka kawo sai kace muna yunwa? nana
take ya hade rai tare da cewa,zainu kada dai ki ce
min kin sa an dawo da yarinyar nan gidan ne dan
ki kashe mata aure?tace haba dai. ya ce to hir
dinki dan bansan in kuma jin irin xantukan nan
yayi ma matarsa daidai arxikinsa. mu kuma mu
ma yarmu da jikanmu gwargwadan arxikinmu,in
ya fito daga gun mai jegon ki turo min shi,sbd mu
ji in da xa a yi sa sunan.tace ina xa ayi in ba nan
ba?ya dube ta an taba haka?ki dai turo minshi.ta
taba baki sannan ta wuce.lkcn da ta leqa dakin
abba da abokansa suna xaune,abba yana ta fama
da danne dannen waya,domin tun da suka shiga
ya qi ko kallan inda bishira take bare danta.tace
bishira ki eada musu in sun fito ahj na san
magana da su.ta wuce ba tare da jiran jin amsa
ba,ko amsa gaisuwan da abokan abba suke mata
bata yiba.bishira ta kalli abba wanda tana
hankalce da shariyan da yayi mata,tace kaji abin
da momy tace?sai lkcn ya dubeta me tace? yayi
maganar ne cikin tsare gida.dadynmu yana san
ganin ku. bai amsa ba,sai kurun ya tura mata
jakar kayanta,ki duba,ta xaxxage dinkuna ne na
gani na fada masu kyau,duk da xannuwan ba
masu tsada ba ne kala uku atamfa daya shaea
daya sai kuma leshi.sai ko kayan yaron.ta dube
shh an riga an sai mana kayan fitar
sunanmu.ahmad ya dube ta wannan din baki so?
tace ni bance ba.abba yace ku tashi muje.tace
ina san magana da kai.ya ce kiyi
maganarki.muktar yace kuxo mu fita ta dauki
yaran tare da miqa mashi ta ce ina lura da kai
rabon da ka dauke shi tun randa aka
haifeshi,alhalin mu kuma yana nan yana hana mu
baccin dare.kai kana can kana baccin ka.ta fadi
haka ne cikin sanyin murya.ya amshi dan tare da
cewa ai gara ya hanaku bacci tunda kunqi ku
kaishi gurin babanshi.ya tsura ma yaran ido,wata
qaunan dan ce take shigarsa.ta matso
jikinshi.abba ya kalli furkarta,ita ma kallansa
take,ta ce yanxu ko dan murmushin ka bana
gani.yace,in da kina san gani da baki dawo ghda
ba.yaci gaba da cewa na sha mamakinki
bishira,da har xa ki yarda ki dawo gidanku ba da
ixinina ba. kuma tun kafin ki haihu sai da na fada
miki ba za ki zo gida ba.Ta ce To Abba mony ce
ta ce sai an zo. Ya ce shi kenan ku zauna. ya
mike mata yaron ta amshe shi ta kwantar ta
kama mishi hannu. Abba wane suna ka sa masa?
ya ce Sunan Alhj babba. Da sauri ta saki
Hannushi . Sunan 'yan da? ya kalle ta Na zaci
zaki ce suna mara ma'ana,tund da ne da sauki.
ya fice. Haushin hali irin na Bishira ya ke ji.dn
son shi yasan tana matukar sonshi,amma bata
son yin biyayya ga abn d yake so. Ya samu su
Mktr sannan suka shiga gurin Alhj ya tambaye su
in d za a sa sunan,Abba ya ce a masallaci kusa d
gidn babnshi ne za a yi addu a. Amma tuni an sa
wa yaro suna Sulaiman.sunan babana. Alhj ya ce
Madalla Allah ya raya mana shi, ba sai mun zo
ba dn yanayin sanyi ne. Nan dai Abba d
abokansa suka tafi suna yabn Alhjn. An ci sunan
shima Abba shi d abokansa sun yi walima da
Azahar. matar abokinshi Bala ita ce suka bai wa
girkin ta yi masu. Mai jego taci gaba d wnk. Abba
kan leka su lkc zuwa lkc,kusan dk lkcn d yaje ba
su cika rabuwa d dadi ba sbd mgnr d hjy zainu kn
datsa mishi. Umma shi ma bata yi fushi ba tana
leka su dk d rashin sakar mata fuska d mai jegon
tare d mahaifiyar keyi. Ummi tana tafe tana 'yan
tsince-tsincenta,kmr yadda ta saba,sai ko taga
sim,take ta yarda dk wani abu d t samu t dauki
Sim din. Gefen zaninta t samu ta kulle,sannan ta
tafi,cikin jakr mkrntrta t saka.wata rana ta dauki
wayar umma ta shige daki,ta bude wayar ta cire
sim din ta saka wanda ta tsinto a cikin zani ta
soke wayar ta fito soro.Jikin dakin yaya Abba a
bakin kofar ta dauki lamar Abba da ya rbt sbd
masu zuwa nemanshi tana kira taji wayr tana
ringing. Ta kashe tana ta dry,hk tayi ta yi wa
Abba Flashing dg nan tayi gidn du Amina
kawarta,tana ba wa Amina lbrn abn d ta ke wa
Abba. Ta ce Amina nsn yanzun hk yana cn yana
jin haushi,shi yasa ki ka ga ina murna.Ta ce in ya
gane fa?Ummi ta ce Ai tsintar sim din nayi,Umma
kuwa ba za ta san na dauki wayarta ba,domin
yaya Abba da Alhjnmu kawai suke kiranta. Amina
ta ce Yadda za a yi ki kira shi ne in ya dauka sai
ki make murya ki canza suna. Ummi ta ce Tab,dn
in ci duka. Amina ta ce Dalla cn gane ki zai yi?
suka kira ya daga ummi ta sirantr d muryarta
tana fadin "Hello! Abba ya ce Ke wace ce ki ke
kiran layina? Ta ce Sunana '"Suhaila. ya ce
Menene ki ke kirana?Ina ma ki ka samu lambata?
Ta ce Gani nayi ni ma a cikin wayr. Tsaki yaja
Sannan ya kashe.Suka dinga tsuntsira dry. Amina
ta ce Sake kiranshi ki ce ma ke a kaduna ki ke.
Ummi ta ce Kai yin waya akwai dadi ni ina son
buga waya. Ta sake kira cikin Zafin rai ya ce Ke
lfy??kin dame ni fa!Ummi ta ce To tsaya mana
kaji ina son mu gaisa ne ni ina kaduna ne. Ya ce
To na gode. Sai ma ya kashe wayar gaba daya
suka yi ta kira a kashe. Tun daga ranar Ummi ta
samu in umma tana aiki ko tana bacci sai ta sace
wayar ta cire sim tasa nata ta kira Abba. Tun
yana kyararta hr ya daina ya koma rokon ta
daina kiranshi,dk a banza. Daga baya sai Abba ya
soma sauraronta, ranar kuma ta kira shi ne
misalin dayan dare,ranar taki zuwa dakin
Tsohuwa ta kwanta a dakin umma. umma kuma
dama dakin Alhj take kwana. A dai-dai lkcn ya
kwanta kadaici ya dame shi,ga garin yanayin
sanyi. wayar ta katse tunaninshi d yake yi na
matarshi zuwa yanzu ya haddace lambar Suhaila.
Ya daga ya ce "Hello ya ce Ke wai me ya hana ki
bacci?Ta ce Ni ba sunana ke ba,Ni sunana
Suhaila,kai fada min sunanka. Ya ce Abba Ta
danne dryr d taso kwace mata ta ce Abba ba
suna bane,Fada mn sunanka n gsky. Ya ce "Idris
Yadda ya fadi sunan sai da ta dage kwarai
sannan ta maida dryrta. Ya katseta d cewa Ina
ku ke a kaduna?tayi dim,dn dai bata san ko ina
ba a garin kaduna ba,ba ta ma ta6a zuwa ba.
Take ta tuno Amina sun ta6a zuwa unguwar
Sarki,dn hk ta ce "Unguwar Sarki. Ya ce, wai
shekaranki nawa? Ta ce Sha takwas. Ta sheka
masa karya.Ya ce Amma shi ne a ka ba kiwaya?
ta ce ta ka san wanene Babana? Ya ce A"a ta ce,
To shi ne mai bawa Gwamna shawara a jihar
kaduna. Abba ya ce Lallai, ki ce in nazo kawo
miki ziyara ba zan samun ganinki ba? Ta ce za
ka ganni mana. Ya ce To zan zo. Ta ce To, Ya
ce,Amma fa ina d mata ta haihu ne ta tafi
wankan gida. . Ummi ta ce Lallai to sai da safe.
Ya ce, Wa ke zuba miki kudi ne cikin waya?Ta ce
Babana mana. ita sai lkcn ne ma ta tuna cewa
ana saka kudi tunda ta ke kira bai taba kin zuwa
ba,aranta ta ce kila wannan ba a sa kudi. Sunyi
Sallama babu dadewa,wayar ta sake daukar
tsuwwa. Ga zaton Ummi Abba ne sai da ta daga
sannan taji muryar wani. Ya ce Da wa nake
waya? ta ce wa ka ke nema?Ya ce Me wayr. ta
ce Ummata ce kuma tayi bacci. Ya ce Yallabai
nake nema. Ta ce Ban san wani yallabai ba,kada
ka dame ni Ta kashe wayar tare da jan tsaki.
Sannan ta cire layin ta maida na umma Wasa-
wasa cikin kwanakin Abba ya soma damuwa da
lamarin Suhaila kaduna, lokuta da dama ya kan
kira layinta amma sai ya ji shi a kashe. Sam ba
ya samunta sai lkcn d ta kira shi,ko da ya yi
mata korafin hk,sai ta ce "Eh ita ce ke kashe
layin sbd ana damunta. Sun yi jarabawar (J. S.
C.E.)sakamako suke jira. dn hk yanzu tana gida
ko yaushe tsokana kuwa bata fasa ba. Kullum ita
d Amina cikin shirya yadda za su yi wa Abba
waya suke, kudin cikin layin ya kare,Abba shi ke
tura kati yanzun. Duk lkcn d Abba yazo gidansu d
ya ga ummi ya hade rannan yana muzurai,ita km
sai ta yi ta sheka dry,dmn tana tuno yadda yake
kwantat d murya a waya. Wata rana hr duka ya yi
mata sbd dryr d ta dinga yi daga sallamrshi a
gdn. Tsohuwa kam ranar yini tayi fada,wai ita za
ta bar gidan.Cin kashin d ake yi wa ummi ya yi
yawa. A ce rashin 'yancin yakai ko dry ba a son
tayi. Da kyar umma ta sha kanta t hkr. Wannan
ta kaicin dukn yasa ummi tace ita kam sa tasa
shi wahala. dn hk ranar gdn su Amina taje. suka
shirya yadda in ta kira shi zata ce yaxo Kd ta
ganshi, ummi ta ce mugu dama in yaje ya 6ace in
huta. Hakn kuwa ta fada mishi, a ranar d suna
waya. Ta ce '"Idris.dn Allah yaushe za ka zo ne?
Ya ce Tun yaushe Suhaila nake cewa zan zo
amma kin ki,to yanzun yaushe zanzo? ta ce kazo
Juma'a ya ce A"a zan dai zo Asabar,Juma'a
rabin rana ce. Ta ce,To sai kazo.Nan d kwana 4
kenan?ya ce Insha Allah,sannan ina son ki toro
min da adireshin dn gdnk,sannan ranar d zan zo
ki bar wayarki a kunne. Ta ce To." Ranar Asabar
misalin goma na safe Abba ya shigo cikin sabbin
kaya,ya yi matukar kyau tamkar sabon Ango.
Umma ta ce za ka je gurin su Maigida ne?Ya ce
A"a umma koda yake zan bi ta can.Kd zan je.
Umma ta rike baki "Kd,? Me a ke yi?ya ce sai na
dawo za ki ji.Ummi d ke wanke-wanke ta kwashe
da dry. Umma ta dirma mata dundu tare d
cewa,Ke wai ciwon dry ne y kama ki?Abba ya
dubeta cike da tsana. Ummi ba za ki shiga
hnklnki da ni ba?ta sunkuyar da kai tare d maida
dryrta ciki. Sannan ta ce Yaya Abba dn Allah ka
siyo min biredi,wlh biredin Kd dadi ne da shi.
Lkcn d Amina suka dawo ta sammin. Ya galla
mata harara,tare d fadin an ce miki nima bakauye
ne irinki?In ma ki ka sake min mgn sai na gabje
ki. . Ya kalli Umma Kada ki ce ma Alhj nayi tafiya
amma in na dawo zan fada masa. ta ce ,To" Allah
ya tsare. Abba ya fita. Ummi tana gama wanke-
wanke ta shige daki dn yin gyaran gado. Umma
na shiga kicin itama ta fito falo ta ciri wayr a caji
taje ta saka sim. Take kuwa kiranshi ya shigo, ta
daga ta matse murya kamar yadda ta saba, ka
taso ne? ya ce Ina mota mun kusa tasowa. Ki
turo mn adireshin. Ta ce Ba fa wahala,d kun
sauka tasha sai ka ce a kawo ka unguwar sarki
gidn mai ba Gwamna shawara. Ya ce Suhaila ma
su ba Gwamna shawara d yawa Ta ce Um to ai a
nan unguwar Sarki shi daya ne. Ya ce Ya sunan
layin?ta ra sa me zata ce,gabnta y shiga
faduwa.Ta samu kanta da cewa, Abuja Ya ce
Abuja kuma Suhaila?ko dai Abuja road? Ta ce Eh
gida mai lamba 6. ya ce To zan ci gaba da kiran
layin. ummi ta ce To," Ta zauna tana sauke
numfashi. Tab da ya dogata d ta bani,Sannan ta
saka dry murna take yau yaya Abba zai sha
wahala. Jefi-jefi ya kan kira ya ce sun zo gari,dk
lkcn d ya kira in ta ji ringing sai tayi bayi da
gudu, har Tsohuwa da suke zaune tare ta ce, ke
takwara gudawa ki ke ko atini ne? Ta yamutsa
fuska, sannan ta ce Bacin ciki ne. Tsohuwa ta ce,
To taso uwarki ta baki magani. Ummi ta ce ya yi
min sauki ma. Can kuma masu kiran layin suka
kara kira. Ummi tayi kofar gida ta daga wayar a
ka ce ke ina ki ka samu wannan wayar? Ta ce
Oho 'yan rainin wayau kada ku sake kirana. Ta
kashe wayar ta koma gida. Lokacin da Abba ya
ce sun shiga KD har ma sun kusa sauka, sai ta
cire layin ta ci gaba da harkokin gabanta ta
manta ma da labarin wani yaya Abba. KADUNA
Abba suna sauka a tashar kawo, ya sauka ya
shiga raba ido yana kallon garin kaduna. Yau ce
rana ta 2 d ya ta6a zuwa KD, daman sun zo
daurin auran wani abokin su bara waccan. Ya
kalli wani dan aca6a sannan ya yafito shi da
hannu. Ya iso yana cewa Ina za ka? ya ce
Unguwar Sarki. Dan aca6a ya ce Wane layi? Abba
ya ce Abuja Road. Ya dubi Abba Rigasa kenan,
unguwar Sarki babu layi mai wannan sunan.
Abba ya ce, Ina zuwa, bari dai in kirata. Koda ya
kira layin Ummi sai ya ji shi a kashe, yana ta kira
a kashe. Ya dubi dan aca6a ya ce, Kasan gidn
Mai ba Gwamna shawara? Dan aca6a ya ce, Hau
dai muje sai mu tambaya. Abba ya hau mashin
yana mai ci gaba da nemn layin Suhaila. Sun
zagaye unguwar Sarki layi-layi suna tambayar
masu gadi da 'yan dai-daikun mutanen da ke
giftawa kasancewar unguwa ce ta manyan
mutane, daga karshe dan aca6a yaba Abba
shawar ya tafi gida kawai. Don haka sun gama
zagayen unguwar Sarki har da makotanta, amma
ba su samu ba. Gida daya ne aka ce musu da
akwai Suhaila, amma yarinya ce ta goye. Kusan
karfe 3 sannan suka koma tasha,ya biya dan
aca6a, sannan yaje ya yi sallah. Zuciyarsa cike
da takaici sai yanzu yake Sallah. gashi ya kasa
samun layin Suhaila. kila ma tana sane ta kashe
wayr dn kawai ta tazarta shi. Ya tuna d zagin d
wani mu2m ya masa lkcn d suka tambaye shi ko
ya san ina ne gidan mai ba wa Gwamna
shawara? Mutuminya ce,mai ba Gwamna
shawara a kan me? Ma su ba da shawara suna
da yawa, ya sunan layin da ka zo? ya sunan mai
gidan? kama ina lambarsu? Abba ya ce, Lambr
kadai gare ni,km taki shiga.Mutumn ya ce,"Amma
kai soko ne,gashi kmar wayayye.Ya ja tsaki ya
wuce. Shi kanshi sai yanzu yaga wautarshi. ko
me ya kawo shi gurin yarniyar?Shida dai ba za
ya ce sonta ya keba,km ba ya ce ba sonta yake
ba. Wani ma ya zaci dn kudi ubanta yazo,shi kam
in ya koma shiru zai yi ko abokanshi zai ce musu
bai gane ba kawai,dn yabi ya fada musu lbrn
Suhaila,sun km san d batun zuwanshi gurinta
sarai,km yasan hlinsu za su maida abn na
tsokanarshi. Cikin matukar takaici suke tafe cikin
motar kaduna zuwa kani,sun zo kwanar Dangora
tsautsayi ya akfa musu. in da tayar motarsu guda
ta fashe. . Nan take motar ta bar hannunta ta
mulmula da su suna ta salati,nan aka kwashe su
xuwa asibiti.wasu sun mutu take,wasu sun yi
dogon suma.masu waya ta cikin wayarsu aka yi
ta kiran yan uwansu,shi ma abba a cikin wayarsa
aka kira lambar ummanshi da alhj da sauran su
aka shaida musu cewa mai wannan layin sun
samu hadari,kuma an kawo su asibitin mlm
aminu kano yanxu.iyakan rudewa su umma sun
rude,tsohuwa kam take cikinta ya kada ta soma
xagawa bandaki tana kuka tana face
majina.ummi bata gidan tana can gidan su amina
suna ta hira suna cin dariya ,tace bari in je in
qara sa layin in ya kira sai ince wayata chaji ne
sai yanxu nayi.sadaf sadaf ta shige daki,kan
kujera taga wayar,ta dauka ta saka sim din ta
cire wancan. tana kunnawa sakuna suka soma
shigowa. kafin ta bude ta duba sai ta jiyo muryar
tsohuwa cikin kuka tana cewa wannan yaro ashe
ajalh ne ya kira shi,ko me xashi yi kaduna?ni ban
sani ba.ummi ta fito da sauri tana cewa,tsohuwa
me ya faru?tace ba kina can gun yawanki na
tsiya ba.Mai sunan mlm da ya tafi kd sun tafka
hadari, yanxun haka suna asibitin mlm. ana xatan
shi ma ya mutu.ummi ta saki ihu,sam bata san
ta damu da dan uwan ta abba ba sai yau,ko tana
kukan ita ce sila?oho.kafin kice haka,lbr ya watsu
a unguwa abba ya mutu.cikin kuka ummi ta
tambayi tsohuwa ina ummata? tace tare suka
nufi asibitin da ummarku.taqi yarda ta jira
su.ummi tana jiyo ihun kukan umman bashir ta
xaga gidan.gidan ya rincabe da kuka,ummi fa
hankalinta ya qara tashi.matarsa ta iso da kuka
da yan uwanta a motoci.yayyantamaza suka nufa
asibitin.can kusan qarfe takwas su alhj suka
shigo.alhj ya ba mutane haquri,ya ce bai mutu ba
dogm suma yayi.kuma Allah yayi taimako ba
karaya.likitocin sunce xast duba shi xuwa gobe
su gani.nan ko jama'a suka dinga fadin
alhamdulillah.ummi ma tadan ji dadi a
ranta,sanna fa kowa ya tafi dama wasu sunce xa
stje yin sallah su dawo.saida suka koma sannan
suka taho da umma,ummi cikin kuka tace umma
da gaske bai mutu ba, umma tace eh bai mutu
ba,muyi magana dashi. . Umma tace in sha Allah
gobennan xai dawo gida. ummi tace to,umma
tace kinga wayata? gaban ummi ya fadi ta tashi
da sauri ta shiga neman waya,taci sa'ar ganin
wayar,sai dai bata san inda ta saka sim din ba
sai wanda ta tsinto ne a ciki.ummi dai tayi shiru
ta miqa ma umma waya. kusan qarfe goma sha
daya wayar abba da umma ta taho da ita ta
soma qara,umma ta dauka.alhj ne ya ce ina
wayarki ina ta kira ana cemin a kashe?una tace,
a ku6e take gata ma a hannuna.yace to inata
kira.tace qila faduwan da tayi daxu ne ta samu
matsala.yace to dama zance ne ki dafa masa
ruwan xafi a xuba a flask dan uwan matansa xai
kawo mu yanxun a mota xai amsa ya kai.ta ce to
alhj wayn xai kwana gunsa?yace bashir na nan
kuma matarsa anyi anyi ta qi tafiya shi yasa na
haqura xan dawo dan ba na xauna gun su ba ko?
umma tace amma yaya jikin nashi?ya ce da sauqi
yanxu ma yana son shan tea ne.tace to xan hada
harda wayar tasa inya so ma dunga kiran shi
kafin gari ya waye.ya ce yauwa ki
bada.Alhamdulillah abba jiki ba matsala. Don hk a
ka sallamo shi zuwa gd.kai tsaye gdn su umma a
ka wuce d shi. A salin dakinsa a ka gyara a cikin
kwana nan 3 ya yi ras sannan ya koma shago.
Bishira kuwa lkcn mahaifinta ya ce maza ta koma
dakinta,tunda ga abn d ya samu mijinta.Sun
dawo hr da tafkeken injin Janareto wai yaron ba
ya son duhu. Sannan ga kayan kallo d
saraunsu.TabbasAbba ya ji dadin dawowar
iyalanshi,dn dama yana cike d bukatarsu. Ranar
yini suka yi gyaran gd ita da 'yan uwanta,sai byn
magrib sannan ya shigo d tsarabobi.madara
tatacciya da kaji. Ya dauki dansa cikin jin dadi
yana kallonta cike da so da kauna,Nayi missing
din ku da yawa.URFIN CIKI book 2 part 3
ZURFIN CIKI book 2 part 3
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:08
Ai bama shiri. shi ne fa ya kawo ni mkrntr kwana
dn kawai baya son ganina. Suka yi ta mamaki.
Can jimawa ya dawo, sun fito rakiyar 'yan
uwansu Safiyya da na Khadija, suka ganshi tsaye
yana danne- dannen waya. Ya taho ya gaida
iyayensu duka,sannan suka koma gefe d ummi,
ya ce Ni ma zan tafi. Ta ce, Ya Abba ko fa
gaisawa ba mu yi ba. Ta karkatar da kai,Cikin
raunin murya tamkar mai shawagaba,ta ci ga ba
da cewa Ya Abba su Umma ba wanda ya ce a
gaishe ni? Sai hawaye suka soma zuba.
Hankicinshi da ke hannunta tasa tana sharar
kwalla.Abba yana da matukar tausayin mace. Don
haka duk da tsanar da ya yi wa Ummi sai da ya
tausaya mata.Ya tausasa Murya. Sun ce in
gaishe ki sosai, za ki ga gyada mai gishiri,
Tsohuwa ta ce a ba ki.Umma ta miki miya, ta
kuma daka miki yaji. Ta ce Na gode, Alhj me
yasai min?ya ce kayan tea ne da lemun kwali. Ta
ce Na gode. Tana ci gaba da share hawaye. Ya
mike Zan tafi. yasa hannu cikin aljihu ya ciro kudi
ya mika mata, ta ce A'a ya Abba ka bar kudinka.
Ya ce Ba ni ne na baki ba,Alhj Karami ne ya ce in
ba ki. Ta sa hannu 2 ta amsa tare d godiya.Sun
raka shi kusa da Gate ita da su khadija,sai kuka
Ummi ke yi. Bayan sun dawo dakinsu ne ta zauna
tana duba kayan da ya lissafo mata,duk ta gani.
Sai kuma saitin sabulun wanka da manshi da
turaransa da hodarsa duk na (Aloe vera.) Shi
kuma bai fada mata ko daga wa ba,ko ba komai
ta dai yi murna sobada tana da 'yan kuraje a
fuska,tasan kuma za su mutu. Sai kuma audagar
mata,tayi dan murmushi. . Tunda Umma taji
sallamar Abba ya shigo dakin ta bar komai tazo
ta zauna tana son jin lbrn Ummi. Abba ya fahimci
Haka,dn haka sai ya boye mata cewa, Ummi na
kuka hr yanzun. Ya nuna mata ai Ummi ta
kwantar da Hankalinta,km tayi hnkl dn ya bincika
ya ji ana ta yabonta. Umma taji dadi Sosai,Sai da
ya fara zuwa gurin Ummu,sannan ya je gida.Ya
samu Bishira tana zaune tana aikin nata,wato
Kallo. Tun da ta dawo daga wankan gida tazo da
janareto da kayan kallo,shi kenan ta sanu abn
yi.Kullum tana gabn (TV)da ta shi da safe in ta
kokarta shi ne ta dafa ruwan tea ko wanka ba za
ta yi wa dan ba,sai lkcn d man injin ya kare. Ya
nufi gurin injin ya kashe,dif din da ta ji komai ya
tsaya shi ne yasa ta zabura ta mike tana fadin
Ba dai har man nan ya kare ba? Ta fito da niyar
dubawa.Abba ta gani tsaye gabn injin yana bn
tsakar gidan da kallo cikin takaici. Ta ce Baban
Walid kashe min injin kayi??Ya ce Eh na kashe dn
Allah dubi gidanki?kalli wanke-wanke kuda na bi
dubi tulin wankin kayan Fitsarin yaronki. Dubi
kicin dinki,kuma ko da bn shiga dakinki da
wannan falon da ki ke kallo ba.na tabbata da
wanda ki ka dauke ko tsinkw a cikin sa.Kila ma
ba ki yi Sallah ba. Ta ce Dan karashe ne fa ya
rage min in gama kallon in zo in yi aikin.Haushi
ya sake kana shi,Sai kurum ya shige daki.
Tsakuwar da ya dora kafa a kai tasa tsigar
jikinshi tashi,sam ya tsani ya shiga daki ya dora
kafa kan datti. Ya dawo yasa takalmanshi ya
shiga da su,Walid yana kwance tun kayan da ya
bar shi da su da safe sune a jikinshi yana ta
bacci cikin fitsarin da ya shafka wanda ba wata
leda da zata hana katifar ta jike. Ko wankan safe
ma ba a mishi ba kenan.A fili ya ce,",Inna lillahi
wa'inna ilaihinr raji'un. ya juya ya nufi shagi. Ita
kam sai ta kunna injinta ta karasa kallonta,
sannanta tashi ta dora girki.sai lkcn ta ma Walid
wanka. Ta dan dauraye kwanukan da za su ci
abnci,wai ta gaji sauran wanke-wanken sai gobe.
Fati ta shigo,Bishira ta ce Yauwa Fatima naji
dadin zuwanki.shuga dakina ki gyara min gado,ki
dan yo min shara. Fati ta ce To. Ta shiga ita ma
duk shegiyar darin ce gurin kuiyar aikin,dn haka
ta dan birbira ta fito ta ce ta gama. Bishira ta ce
Yauwa dan dauraye min kaya can na Walid. Nan
ma tasan sama ta shanya. Bishira ta ce Yauwa
ta ga abnci nan kici.sai ki dauki na Ummarku ki
kai mata. Har Fati ta kai waje,Bishira ta kwala
mata kira. ta ce,Zo ki tafi da wannan galan din
na man fetir kije shagon Babn Walid kice ya taho
mana da shi,dn man ya kare. Koda Fati ta same
shi da galan ta fada mishi sako ya ce Ba zan siya
ba,Maida mata galan din. Ta tafi,Shi kuma ya ci
gaba da mita a zcyrshi. Yana fadin Na daina
sayan man tunda ba za a bari sai dare a kunnan
ba.Gidan Ummanshi yaje,ba ta nan ma taje
barkar Haihuwa. Ko dakin Tsohuwa bai shiga
ba,ya zauna nan falonta.Ya za kula ya zuba
abncinshi ya ci.sannan ya dan huta sai ya fita
zuwa gidan su Ahmad. Cam ya samu wasu daga
cikin abokanshi suka shiga hira. Ranar dai Abba
bai je gida ba sai misalin sha daya ko daya shiga
bai nemi matar gidan ba,ya dibi ruwa ya yi wanka
sannan ya shiga dakin. Ya lalibo makunnan wuta
ya kunna,dn Nefa sun kawo wuta. Tana kwance
irn banzan kwanciyarta da ta iya,dakin sai tashin
wani irin wari yake kamar na ruma,kamar na
fitsari ko na datti.Ya kalli ko'ina kullin kaya ne na
wanki ne,na gaga ne ciki da guri.Ranshi ya
baci,Ya kuma dubanta ga wata kiba da ta tafka.
Tun da ta haihu ta zama rusheshiya,gashi bata
son kama jikinta.Tsaki yaja,sannan ya dauki fiko
ya fita. kan doguwar kujera ya jefa filo,ya kwanta
a gajiye.Amma me?sai ya ji dora gadon bayansa
acikin lema.Da sauri ya mike ya kunna wuta.Duk
fitsarin yaron ne a kan kujerun dakin,dn haka sai
ya nufi dakin da takw aje tarkace ya kunna
wuta,shi ma dai duk shirgi. . Ya share Ya
shimfida ta barma ya kwanta,a ranar ya dauri
aniyar maida dakin ya zama nashi din-din-dn.
Don haka washegari yasa a ka zo a kayi masa
fenti,ya siyo kati fa ya yar da zanin gado,dk wani
abu nashi sai da ya kwashe su. Kafin wata guda
ya maida dakinshi cikakken daki,ya zuba dk wani
abu da yake bukata. kafin ya fita kullum sai ya
gyara dakinsa fes. ita kuma sam bata zuwa
dakin,sai dai in yana da lalura yaje can ya sauke
ya dawo. kazantarta kam ta kai in da ta kai,tunda
hr kayan kashi tana zube su a cikin daki. Ya gaji
yaje ya samu Anty ya fada mata,hr gidan Anty
tazo ta zazzageta,ta tasata suka gyara gidan,
amma ko a jikinta.Washegari ta ci gaba da in da
ta tsaya. Sam babu wanda zai ganta ya ce
haihuwarta daya. ¤¤¤¤¤¤ ¤¤¤¤¤¤ UMMI yau
ba wanda ya kaita murna,domin yau dai an basu
hutu..Sai dai tunaninta zata ko iya kai kanta
gida? Sunyi ban kwana bata da kudin mota, dan
duk tayi taba su safiya kudin gurinta, amma ta ce
yau ko da qafa ne xata gida.sun fito wajan mkrt
wata maryam tana cema,ki tsaya mota xato da
xata kaimu cikin kn.ummi tace baxan jira ba.sai
ga abba kamar daga sama,tsoro ya kamata karya
ce ta xauna gidan abokin sa da yace.hanka linta
ya tashi cikin in ina ta gaida shi ya amsa.ya
shiga mkrtn jim kadan ya dawo.hakan ta sha
alwashin yau ko da shiya saita je gida.shi kam
ma ya manta yai mata wannan maganan ma.ya
sabi akwatinta suka je suka shiga mota. abba
mamakin natsuwan ummi yake yi, ko da yake
baxai ce ta natsu ba, qila lafawa tayi.tundaga
soro ta saki jakanta da bokin tayi ciki da
gudu,cikin kuka tana kiran ummanta.umma ta
share do min tsohuwa tana cikin gida,kada tace
tayi rashin kara,sai tsohuwa ne ta tashi da sauri
tana fadin oyoyo takwara.suka qungume juna
tace to menene kuma na kuka?umma ta fito nan
fa ummi taje ta rungume ta.sai umma ta doje
tace bubi shirme,sakar ni ni.tsohuwa tace haba
suwaiba yarinya tana dokin, . Tsohuwa tace haba
suwaiba yarinya tana dokin ganinki amma ki
gwasale ta? abba ya ce daman nasan ba
natsuwan da yarinyan nan tayi,har ina
yabonta.dubi yanda ta xubarda kayan a soro.to
xaki debo su.tsohuwa tace bari ni in debo mata
tunda kai baka da tausayi.laile umma taga
canji,do min ummi dai tunda ta dawo ko qofar
gida bata fita ba,sai ko in an aike ta.sannan
yanxu ba gudu da tsalle tsalle bare tsokana.ga
aiki har girki ita kema umma komai.alhj yana
shan shayi da safe,ummi ta yi sallama ta shiga.
can gefen su umma ta xauna,sannan ta gaida alhj
ta gaida umma wanda ta saka alhj agaba tana
masa fira.wannan qa'idan umma ne bata barin
mijinta shi kadai,in har yana gida.alhj yace
suwaiba kinga ummina ko?laile abba yayi namijin
qoqari. yarinya ta natsu.umma tace Allah ya
amsa addu'an mu ka duba tsayuwan daran da
muka dunga yi bayan tafiyan ta kan cewa Allah
ya kintsa mana ita.alhj yace hakane,ummi dai na
jinsu tana murmushi.can tace alhj anjima xanje
gidan inna saratu in gaishe ta. qanwan sahura ce
da ke aure a kabuga.ya ce to ummi, xanba
umman ki kudin mota ko? ummi ta ce,to na
gode.ta miqe ta fita ta bar mahaifanta cikin farin
ciki jin dadin natsuwarta, suna godiya ga Allah
mai shirya bayinsa.lkcn da ta shirya dan xuwa
kabuga.sai umma tace ki kwana dan bana san ta
fiyan yamma,kabuga da nisa.tace to sannan ta
dauki kayanta kala guda, sannan ta fito.har xata
wuce sai ta shiga gidan alhj qarami,sahura na
ganinta ta hade rai,daman daqar take amsa
gaisuwan ummi tunda ta dawo.ummi ta gaisheta
a ciki ta amsa,sam ummi bata damu ba,tace
umma ina fati?ta yatsine baki tace tana gidan
abba,tace to inta xo ki ce mata naje kabuga sai
gobe xan dawo.umman bashir tayi tsaki,tare da
cewa ni yar aiken ki ne?ita dai ta wuce.tun
dawowan ummi suke shiri da fati kamar me,ko
yaushe suna tare suna fira.ummi tana mata
labarin mkrtn su.ita kuma fati tana bata lbrn
saurayin da tayi fahad,da irin son da take
masa.ummi tace tab,ni ko xanyi saurayi nafi san
irin ya abba...... . fati ta dubeta da al'ajabi kina
nufin ya abba kike so?ummi ta xabura tana fadin
tir, ko a mafarki Allah ya kyauta.ina nufin mai irin
hirarsa da tsafta.fati ta qyalqyale da dariya tare
da cewa ai na xaci shi kike cewa,inko ya ji kici
duka ummi ta ce,ai ni ba ma da shi nake ba
tab,shi da yayi auran so?kusan ko yaushe
yanayin hiran tasu kenan.ummi tana tafe
wadansu samari suka yi ta binta, sun shawo
kanta ta tsaya da kyar,kuma har ta masu
kwatancen gidansu. kwanaki uku bayan haka tana
ki shingide kan kujeran dakin umma,misalin
takwas saura ma dare.krtn wani littafi take yi na
hausa da fati ta ara mata,sam ita bata taba krnt
irin littafin ba,amma fati ta ce mata ta karanta da
dadi sunan littafin NAGA TA KAINA na
(sodangi).kasance wan wannan ne karo na farko
da ta taba krnt lbrn soyayya,sai abin ya
birgeta.amma nata ganin gwarxon sojan nan xai fi
dacewa a ce abba ne, jefi jefi takan kalli abba da
ke xaune kan kujera kusa da umma suna wani
xance da bata jiyo su. 'Amma tasan ko me suke
tattaunawa mai mahimmanci ne a gare
su.sallamar wani yaro ne ya katse su,umma da
abba suka amsa mishi a lkc gudu.yace wai ana
kiran ummi a waje inji wadansu.da sauri abba ya
kalla yaron,sam ba xai ce me yasa xance yaran
ya fadar masa da gaba ba.sai ya lumshe ido
sannan ya kalli ummi wadda kunya ta rufe
kasancewar yau ce rana ta farko da aka soma yin
sallama da ita.umma wadda kullum fatanta ummi
ta samu miji,sai tayi murmushi,sannanta ce da
yaron kace tana xuwa.abba ya dube ta da sauri,
umma kin san ko su waye?ta ce, a'a.yace ya
kamata a san ko su wanene dan kin san bata da
kan gado,kowa ma sai ta jajibo kuma ma duk
nawa ummin take da har xata soma tsayawa da
samari?umma tace,to abba ai gara ta kama
dahir, tana qare sakan dire ba sai ayi mata aure
ba?yace gaskiya umma gara ta dan taba krt,dan
yanxu xamani ne na krt.umma tace,tayi acan a
dakinta.ta dubi ummi tasgi kije.ummi ta miqe ta
fita.abba ya miqe shi ma,umma bari dai in gani
ma su kamun kai ne? umma tace to.., . Sun
gama gaisawa kenan sai ga abba ya fito.ganinsu
tsaye da ummi sai ya tsinci kanshi cikin wani
bacin rai.ya isa gun ya musu sallama, suka
amsa, sannan suka gaisa.yace daga ina kuke?
suka dube shi dayan ya ce lfy dai ko? ummi tayi
karaf ta ce yayana ne.anan suka sake gaida
abba.bai amsa ba, sai ma cewa yayi na tambeye
ku kai ma kana tambayana,wai lfy? suka ce,kayi
haquri,nan suka gabatar da sunansu.mai san
ummi shine nazir, abokinsa kuma sagir. sun 3a
masa cewa dukkansu daga kabuga suke.yace krt
kuke ko kasuwanci? sagir yace,eh krt muke,amma
muna taba kasuwanci a shagon mahaifinsa da ke
kwari.abba ya dan yi jim,sannan yace to kai ka
shirya aure ne?nazir yace eh to, nasan dai kafin a
tashi yi mata aure na shirya.abba ya ce, to ita
kam krt xata yi, kuma c ma buqatan ta hada krt
da soyayya. ya dubi ummi da fatan xaki sallame
su.ya juya gida.sagir ya ce, wannan wanki ne da
gaske? ummi tace qwarai kuwa. nazir ya ce to
yanxu ya kenan? kin ji abin da ya ce.ummi yayi
shiru tana tunani, ita fa basu kwanta mata rai,
tun randa ta hadu dasu,sam basu iya saka kaya
kalar yadda ya abba ke sawa ba.dan haka sai
tace, ina ganin xai fi mu haqura kada yaxo ni yayi
ta mun fada.nazir ya ce yanxun haka xaki ce?
ummi tace, um,sai da safenku.kada ku ja min
duka.sagir cikin jin haushi ya ce,ki xama
mangofak qarewan krt.sannan in kin gama wan
naki ya aure ki. ita dai ta shige gida.kusa da soro
ta iske umma da ya abba ta yo masa rakiya, tana
kuma ba shi aaki kan cewa yayi ta haquri,tace ina
fada maka ko yaushe ba fa fushi ko fada ne xai
saka matarka a hanya ba.lallashi da nashiha,ka
dunga koya mata giqki daka nutsu ka koya mata
ba gashi ka ce ta iya daidai gwargwado ba?abba
yace,hum lamarin yarinyan nan yayi nisa fa
umma,wankan jikinta ni xan koya mata? sallah fa
daga nake da ita.amma abin yaci tura.antynta
sau nawa tana xuwa tai mata fada duk a
cnxa,mkrtn ma ta qi xuwa.ni kuma da ce
ruwanta.umma cikin al'ajabi tace, sallah! sallai
ma bata san yi abba?abba yace umma baxan
mata sharri ba... Ta ce Tabdi,to kuwa ba kuwa
kazantarta ta wuce jiki hr d zcy. wannan ita ce
kazanta mafi muni. Don haka dole ne ka zage
damtse don ganin ta kama sallah,to menene
marabar arne d Muslmi in ba Sallah ba?Abba ya
ce Umma na mata nasiha na gaji. Ta ce To kasa
ta a mkrntr Islamiyya,kila ta ji tsoran Allah in
tana jin Wa'azi. Sannan ka dainga siyo mata
kasasuwan wa'azi.Abba ya ce Umma kaset nawa
na kawo mata bata sakawa,Kullum sai indiya da
Hausa fim,in naki sayan man fetur in tana da kudi
ta saya. In kuma ba a ta da shi sai ta dauki
ittafin Hausa ta dukufa.umma ta ce Allah ya
kyauta,kaje kayi ta hkr tare da addu'a. Ya kalli
Ummi,sannan ya ce ma umma,kada ta sake fita
gurin wadanan kananan yaran,sannan ya fita. A
daki umma take tambayar Ummi daga ina suke?
Ta ce um,Umma kyale su ni sam ma ba su min
ba. Umma ta ce to Allah dai ya miki za6i nagari.
Abba yana kwance a dakinsa ya yi lamo cikin
bargo,ya kasa amsa ma kanshi tarin tambayoyin
da ke yawo cikin kanshi. Haka tambayoyi suke
zuwa masa daya-bayan-daya ,me yasa ya damu
da lamarin Ummi??me yasa da a ka yi sallama da
ita ya samu kanshi cikin wani tashin Hankali? Me
ya sa ranar da zai je mata ziyara ya za6i ya sai
mata kayan kwalliya? A fili ya ce,don tana
kanwata.Zuciyarshi ta ki amincewa da haka. Me
yake shirin faruwa da ni ne? ya fada a fili. Ya yi
juyi zuwa rigingine,sannan ya dauki filo ya manna
a kirjinshi, ya ci gaba da magana shi daya. Bana
zaton cewa Son Ummi nake yi.don lkcn da na yi
tsananin Son Bishira bn ta6a samun kaina cikin
wannan yanayin ba. Kai Allah ya tsare ni da Son
ummi,wannan mahaukaciyar
yarinyar..........bugun kofarshi da a ke yi ne ya
katse shi. Murayar Bishira ce ta na cewa Babn
Walid!Babn Walid!! Ya bude kofar da sauri,ta ce
Walid ne ke ta amai. Ya fita ya dauki yaron daga
hannunta yana fadin Me zai hana shi amai,in ba a
ci sa'a ba har zawo sai ya yi,Saboda
kazantarki.Sam ba ki lura da me zai wawuro ya
tura bakinsa. Ta ce Yau fa bai ci komai ba,tun da
safe yake wannan aman.Ya ce shi ne ba ki sanar
da ni ba?Ya cire masa kayan jikinsa wadanda ya
ji suna ta doka karni.. . Ya isa igiyar shanya ya
ciri wasu yasa masa,sannan ya fita dashi.Wani
babban kyamis ya tafi da shi,mai kyamis din
likita ne,sai dai ba na yara ba ne,amma kowa
yazo sai ya duba shi.Nan dai ya masa bayani ya
ba su magunguna. Sha biyu dai dai ya dawo,tana
zaune tana kallo ya ce "A'uzubillahi,wai ke kallon
nan masifa ya zamarmiki ne?to ki sani na kusan
fita da kayan kallon nan. Ta ce,Tab,ka kaisu ina?
dadinta dai dafa gidan ubana a ka kawo su. Ya
ce ta za su koma gidan uban naki. Ta dafe kirji
"Zagina ka ke yi?ya dora mata dan a jiki "An
zage ki,ke din banza,kazama!yazube mata
maganguna ya fita. Ya jima zaune a kofar
gidanshi dafe da kai,yana tunanin shin wai shi
kadai ne bai yi sa'ar mata ba,ko kuwa duk maza
ne.Ya tuna abokanshi 2 da suka yi aure. Muktar d
Jamilu,sam ba su da wannan matsalar,duk lkcn
da yaje gidansu tsaf matansu,ga mutunci da
mutanta mutane. Shi kuma a cikin abokanshi
babu mai zuwa gidan sbd bata gainin kowa da
gashi. 'Yan uwanshi sai wanda ta za6a sannan
zata yi hulda da su. 'Yan garinsu kuwa can
¤ZAMFARA¤In suka zo kiri- kiri take nuna musu
kyama ga rowa,sam bata hulda da matan
abokanshi. Ya numfasa zai bi shawarar Umma ya
gani, amma gaskiya Bishira ba matar zama ba
ce. Tun da ya dawo sallarAsubahi dakinta ya
shiga tana ta shirga bacci. Walid kuma ya yi
faca-faca cikin kashi ya tausasa zuciyarshi ya ce
"Bishira! . Bishira!!Ya dan duki kafarta,sannan ta
tashi. Ya ce Ki tashi ki gyara masa jiki kiyi
sallah.Ta ce,Tab, me ya yi?ya ce, "kashi ya
yi.kurum sai ya ji ta ce Tab,wannan akwai dan
iskan yaro.Yanzun dan ubanka kashi ka min?
Sam bai san lkcn da ya watsa mata mari a baki
ba,cikin murya mai karfi ya ce "kada ki kuskura ki
sake ce ma dana dan iska!kar ki sake zagar min
yaro kada ki yi wa dana baki.Ba zan dauki
wannan ba. . Ta mike daga kan gadon tana kuka
Ni ka daka? wlh sai na rama. Kasancewar lebe
baya raina duka,sai jini.Nan da nan sai kumburi.
Ta cakumo shi,wlh sai na rama.Ya hankadata kan
gado ya bar gidan.cikin zcyrshi yana fadin
,"Wannan fitina da me tayi kama? Ita kam ruwa
ta dafa sannan ta wa yaron wanka, cukuikuiye
zanin gadon ta saka shi cikin baho,sannan tayi
kwaskwarima ta sabi danta baki suntum ta nufi
gida tana kuka. Mahaifinta bai nan yana
Abuja,Hjy Zainu ta kalle ta bayan ta gama kero
karyarta. Wai don yaro ya yi kashi ta ce yaron
bai kyauta ba shine ya hau ta da duka da zagi.
Hjy Zainu ta ce Amma wannan da muciya ya
dake ki ko?ta ce, Da hannu ne,nushina fa ya
dinga yi. Hjy Zainu ta ce Ai kin gani ba yadda ba
a yi ba ki tsaya kiyi karatunki kin ki,kin kafe sai
kin aure shi,wannan matsiyacin? Dama talaka
yana da wannan tsiyar.Yanzun za ki zauna mu
jiraZuwan Alhj,ba za ki koma ba.Ya dai baki
takardarki in yaso ki koma mkrnt.Su kuma su
dauki dan nasu. Bishira dai tayi shiru,zcyrta tana
jinjina rabuwa da Abba d kuma danata. Abba kam
gidansu ya nufa.Ummi ya soma cin karo da ita
tana sanye da doguwar rigar bacci,ta dora rigar
sanyu ta sakar ulu, a kai tana wanke baki da
busushi. Ta dube shi,mmkn ganinshi tayi a
wannan lkcn.Sai da ta dauraye baki sannan ta ce
masa sannu da zuwa,ya amsa a hnkl bai san mai
yasa ya kasa dauke idanunshi daga kanta ba,hr
ta gama alwala tayi addu a ta mike. Ta dube shi
da niyar yin magana,amma sai ta fasa don tana
tsoron kada ya daka mata tsawa. Ta daga
labulan dakin Umma zata shiga. Ya ce, "Ke!' ta
waiwayo cikin hada rai,domin ta tsani kiranta da
yake da ke!Ya ce Ummana fa?ta kalli dakin Alhj
Ba ta fito ba,,Ta shige ta zura hijabi ta tada
Sallah. Ya shiga dakin ya zauna,yana kallonta
tana Sallah zcyrshi tana nazarin Rayuwar
Ummarshi. Tun tasowarshi ya ke ganin kulawa da
kyautatawa da take yiwa Alhj Babba ga biyya,
sam bata wasa da dk wani abu nashi daga lkcn
da ya shigo gida ta gama sauraron kowa sai lkcn
da ya fita. Bai ta6a jin sunyi sa'in-sa ba bare ta
daga murya sama da tasa.Shin sauran matan ba
su fahimci irin wannan ladabi ba ne?Ummi tana
addu'a zcyrta cike da tunanin shi kuma ya Abba
me ya kawo shi da wannan sassafen? Muryar
Umma suka ji daga waje tana cewa,"Ummi in kin
idae ki fito ki share gidannan,ki wanke bayi,Ummi
ta ce To''. Sam Umma ba ta san Abba ya shigo
ba,dmn da ta ba Ummi umurni sai ta sake
komawa dakin mijinta, Ummi ta wanke bayi
kansu,sannan ta share ko ina na gidan, ta kunna
risho ta dora ruwan karyawa, sannan ta shiga
firar doya. Gyangyadi yake daga zaunw, Muryar
Ummanshi ce ta farkar da shi tana cewa, "A'aha!
ya bude ido cike da bacci.ZURFIN CIKI book 2 part 4
ZURFIN CIKI book 2 part 4
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:10
"A'aha! ya bude ido cike da bacci. Ya kalle ta tare
da yin mika,ta ce "Lafiya"? Ya ce,Umma lfyr
kenan.Ta zauna da sauri Me ya faru Kuma? Yayi
dan tsaki,umma na gaji da auran nan ina ga
wannan karan xan yar da qwallon mangwaro in
huta ta quda. umma ta ce abba! abba!! me yasa
baka da haquri? ban xace ka haka ba abba,ina ce
jiyannan ka min alqawarin kawo qarshen duk
wata matsala tsakaninka da matanka?shin ban
fada maka hanyoyin da xaka bi ka xauna da
matarka lfy ba?ya kamo hannun ta,umma ba na
san bata ranki, ban san yadda xanyi da halin
yarinyan nan ba ne. jiya fa ina kwance taxo tace
min yarona amai naje kai shi kyamis,ina dawowa
na samu ta xauna tana kallon,ina mata magana
ta hayayyaqo min da asuba na tashe ta
sallah,wai dan yayi kashi shine ta hau xagin
yaron nan,wai dan iska. ni ko na bige mata baki
har da cukume ni da dambe fa.umma tace kaine
harda duka abba? dukan mace?ta xuba tagumi
tana kallon shi,ya ce umma xaginshi fa tayi,kuma
kin san dai ba kyau uwa ta dinga xagin danta.dan
ba haka kikai min tarbiyya ba.kalli rashin ji irin na
ummi, amma ban taba jin kin ce mata yar iska
ba.tace to ba sai ka xaunar da ita cikin tsanaki
ba?? . Yayi shiru a xuciyarshi fadi yake umma ba
xata fahinta ba.tace, tashi kaje ka bata haquri, ka
lallasheta.matafa sai haquri,kasan da qashin
haqarqari aka yi su,dole ka ganta a karka
ce.saidai nasiha da lallashi,da xaran ka ce kan
dole xaka miqar da ita,sai ta karye.nan dai ta yi
ta ma abba fada, har sai da shi kanshi yaga
cewa eh,yayi saurin fushi.dan haka ya miqe ya
nufi gida da nufin bata baki.sai dai kuma kash!
lkcn da yaxo tuni tana gidansu.ya dawo ya sanar
da umma, tace to dole sai alhj yaji kenan.ta shiga
gun alhj yana shirin fita. yace yau dai suwaiba
akwai abin da ya dauke miki hankali daga kaina
ko? tace, me kagani? yace tunda kika fita ban
kuma jin duriyarki ba, hatta karin kumallo yau
uwata ce ta kawo min.ko taya ni shafa mai yau
ban samu ba, tace uhum, abba ne in gaya maka
na gani hankalinshi a duk tashe, matsala ce suka
samu da matarshi,wai ta yi yaji.alhj yace,yaji?
umma tace eh wai a ce kamar abba bai san
yadda xai yi haquri da mace ba, alhj yace ina
abban?ta ce yana daki yana karya wa. Ya ce kira
min shi.abba ya xauna ya xayyane ma alhj komai
duk abubuwan da ke faruwa wanda take
masa,hatta batun sallah da bata san yi duk ya
fadia.alhj yayi shiru,can ya ce in ko haka ne ba
qaramin haquri kake yi ba, amma kaje xamu je
gidan.abba ya ce, ni dama xa a baita can dana
huta.alhj yace ba xa ayi haka ba haquri dai xa ka
ci gaba da yi.xuwan su alhj biyu gidan amma ba
suyi dace ba ance musu mahaifinta baya nan.
antynta kuwa ta kira shi a waya ya ce yana nan
xuwa gidanta.da dare suka je da ahmad sun
same ta ita da mijnta,anty ta tare su cikin fara'a
aka kawo musu kayan shaye shaye.nan dai abba
ya fada mata komai.ya qara da cewa ban sani ba
ko dan ni talaka ne shi yasa bishira bata ji
maganata? anty tace dame ka gaxa mata?
iskancintane kawai, wai bishira har da rashin
sallah,xa ko taci qaniyarta gun alhj.mijin anty
yace,tabdi lalle kana haquri nan dai suka ci gaba
da hira har mijin antyn yayi mishi alqawarin cewa
ya kawo takardunshi.MD din gidan rediyon
tarayya na jihar kd, amininshi ne. Amininshi ne
tun da abn da ya karanta kenan za a sama mishi
aiki.Abba ya yi ta godiya. Bai san da wane baki
zai gode ma mijin anty ba,tun daga nemna auran
Bishira yake taimakoshi, darajar su shi da Anty
da Alhjn su Bishiran yake hkr da halayanta. Ya zo
ya sanar da su Umman,Sun yi murna hr Alhj ya
ce dole ne in in masa godiya. Umma ta ce To
Abba ka gani fa,ta dailin matarka gashi zaka
samu aiki,ka yi ta hkr fa. Abba ya ce Umma ba fa
ta dalilinta ba,in Allah ya rubuto zan samu ta
hanyarshi sai ki gani,ko ban santa ba Allah ya
kawo sila.Ta ce To yanzun dai ita ce Silar,Allah
yasa albarka.Sai dai ba zan ji dadin tafiyarka
garin Kd ka barni nan ba. Ya ce Umma ko ni
tunda ya ce kd ke kurum ni ke tunan.Umma tayi
Murmushi,Allah ya maka za6i na alkairi,dk in da
za ka je.Amin Ummata. Mahaifin Bishira ya dawo
kuma Alhj ya tasa Abba sun je in da aka kirata
gata ga shi ga kuma iyayensu. Abba ya jero duk
laifunkanta bai rage ko daya ba. Sannan ya ce,shi
ma yana son ta fadi tsakani ga Allah me yake
mata wanda ba ta So?Nan fa a ka ce ta fadan,
sai ta shiga Kame-kame, Wai in ya shigo gida sai
ya yi ta fadace-fadace sannan ba ya zama a gida
sai tayi bacci,km ga abnci ta dafa amma sai ya
amso na Ummarshi ya c. Alhjnta ya daka mata
tsawa."Yi min shiru,yaushe ki ka bar musulunci?
Ba kya sallah ko?sannan ki bude baki kina zagar
masa da a gabansa?Ya bige miki baki kin kwaso
kin taho gida,to a miki uban me?ya dubi Abba
"Idiris me yasa ma ka mata duka ba?Ai ke babu
abn da ya dace da ke irin duka. Maza ki kakkabe
mayafinki ki koma gidanki,bana son in sake
ganinki da sunan yaji a gidana, . Zan wulakanta
ki. Kuma game da batun sallah dk lkcn da bata yi
ba ka dakar min ita ni na saka,batun tsafta kuwa
kada tayi,ka nemi mata ka aura ka barta da
tsiyarta. kai dk lkcn da ka samu matar ma zan
biya maka sadakinta ko 'yar wanene.Sai a lkcn
Alhjn Su Abba ya yi magana. Hakuri za ka yi
ranka ya dade,Allah ya saka da Alkairi bisa
karamcin da a ka yi mana,kuma insha Allah ba za
su sake ba. Abba ma ya yi godiya,sannan suka
masa sallama.Ita ko Bishira mayafi ta dauko tana
kuka suka tafi. Hjy Zainu ranta ya 6aci,taso a
kashe auran don dama bata son Abba sam,kafin
zuwan iyayen Abba da shi kansa Abban ta
fadawa mijinta karairayi,kamu ransa ya 6aci. Ya
kuma daukar wa kansa alkawari in ya bincika ya
tarar haka ne dukanta da zaginta yake ba tare da
ta masa laifin komai ba?sai yasa an raba auran.
Amma da yaji batun Abba gata a gurin bata musu
ba,sai ranshi ya baci da ita, har dai batun sallar
nan.dn haka ya bincike yana da kyau ayi shi,kada
ka yanke hukunci da maganar gefe daya,wannan
shi ne adalci. Bayan sun dawo Abba ya rakata
gida ya zo gurin Alhj da ya ce ya dawo yana
jiranshi. Alhaji ya masa fada cewa dk in da tara
tayi to ya kansace a gida. Sannan fadan da ta ce
yana yi in ya shiga shi ma ya daina,haka ya
dinga zama yana cin abncin.Abba ya ce to.Umma
ma da ya shiga suyi Sallama nan dai ta kara
masa fada tare da nuna mishi hanyoyin da zai bi
ta ce kuma cikin satin nan yayo mata rijistar
Islamiya tunda da ita a kusa. Ya shiga ya same
ta zaune bakin gado tana ta fushi,ya zo ya zauna
kusa da ita.Yasa hannunshi ya kamo nata,sannan
ya kira sunanta bata amsa ba bata kalle shi ba
ya ci gaba da mgn. Kin san dai ina sonki ko??ta
dube shi Da ba kafin a zuga ka.Ya ce wa zai zuga
ni? ta ce Wa kuwa in ba Ummar taka ba. Ya yi
tsam ya ji haushin maganarta sosai,amma sai ya
danne kada ki zargi Ummata tana sonki kin ki
fahimta ne kawai.amma mu bar zancan kiyi hkr
akan abubuwa da nike miki. ki yafe min nima na
yafe miki. . Ya jawota zuwa jikinshi,hr gobe ina
sonki sosai.Ranta ya yi sanyi don mata na son
wannan kalma daga mazajensu. Ya kira sunanta
ta dube shi cikin ido suke kallon juna,ya ce kin ya
fe min?ta daga gira,kina sona hr yanzun?Ta kara
mannewa a jikinshi "Ina sonka sosai ma.Ranar
dakin shi suka kwana,kuma ranar ce rana ta
farko da suka soma kwana a dakin nasa. Washe
gari tunda ya dawo Masallaci ya soma akin share
gida,lungu-lungu ya gama ya wanke bayi kan su
sannan ya yako ta da kyar ta tashi ya ce tayi
sallah ta yiwa yaro wanka. Tayi Sallar,wankan ta
kuke wai akwai sanyu,sai ranar ta daga. Ya ce,To
t dafa musu ruwan zafi su karya.Shi kuma ya
fitar da wankinshi yana yi ya gama ya ce ta fito
da duk wankinsu ita da yaron.Tsawaya ya yi yana
kallon tilin kayan,amma gudun kada suyi rigima
sai ya yi shiru ya ci gaba da wanki. . Ya cire
kayan yaron da zannuwanta hr ma zanin gado
wadanda yaron ya yi kashi ta aje su suka
bushe,,wasu kayan hr da tsutsotsi. Ya kira ta ya
ce "To kalli kayanki hr da tsutsotsi,wanna n ya
dac fisabilillah?samo leda ki kwashe su,ba zan
iya wanke su ba,in kuma za ki wanke to. Nan ta
samo bako ta kwashe takai gurin bola,ya ce
Bishira tsafta cikin addini ce,Annabi (S.A.W)ya ce
Babu mai shiga Aljanna sai mai tsafta. Don Allah
ki dinga kula,ke kanki za ki ji dadi in har ki ka
tsaftace ko'ina na gidanki.Ta tura baki ta wuce.
Ranar haka ya yini wanki kayan yaron dk sun
dafe kaya masu tsada da kyau irin wadanda a ka
sai masa daga gidan iyayenta,ranar dai ko shago
bai je ba. Cikin satin dai babu laifi suna ta
shiri,kuma tana daurewa tana yin tsaftar
jikinta,haka nan yasa ta wanke kai tayo kitso. sai
dai ita gani take dk an takura mata,amma tana
jin dadin yadda ya sakar mata fuska kamar
farkonauresu. Mitar da take masa kullum ya
daina dadewa a waje,ita don Allah ya zauna a
gida suyi hira. Ranar dai saiya gwada zama tun
da ya dawo sallar Isha'i ya shigo gida. Tana
zaune ba riga ya ce,Wai Bishira kayan kwalliyarki
sun kara ne? ta ce,Me ka gani?ya ce,Rabon da in
ga kwalli a idonki tun kina amarya bare dan jan
baki. . Taja dan tsaki "kwalliyar me zan yi sai
kace wata budurwa?Da dai nayi.Ya ce kin ji wani
shirme kuma,ban da ke ai matar aure me miji a
hannu ita ce da yin kwalliya. Ta ce, To ko ma
nayi ba zama ka ke ba.Ya ce "To yau dai gani na
zauna,kuma ina son a sheka min kwalliya. Ta
dube shi Gsky sanyi ba zan iya yin wanka yanzun
ba.Shiru ya yi yana kallonta,can sai ta zame ta
kwanta,sai kuma bacci. Ya yi murmushi.Dubi
matar da ta ce wai ba na zama a gida. to yau na
zauna amma kalli yadda ta bingire tana shirgar
bacci. Ya mike ya fice.cikin takaici korafin banza
kenan take yi tunda ba ta san yadda za ta yi fira
da mijin ta ba. haka dai abba yayi ta hakuri don
baxai yiwu ya ce shi kadai zai dauke mata duk
aikin gidanta ba. sai dai yayi wanda zai iya,amma
duk wanda ya shigo gidan shi ko ba a fada ba
yasan matar gidan kazama ce ta bugawa a
jarida. ummi tana zaune gaban umma,fuska
shabe- shabe da hawaye.ta rikewa ummar
hannu."kinji don Allah umma kice wa ya Abba ya
dawo dani garin nan.wallahi bana son makarantar
kwana,ni dai bazan koma ba."umma ta ce "haba
ummi xuwa yanzu ya ci ace kin saba da
makarantar" ta ce,"umma bazan saba da rashinku
ba....."karaf a kunnen Abba. ya ce,"to sai ko ki
shirya sabawa,don wata rana ma aure zaki yi."
umma ta ce sosai kuwa. tsohuwa dake zaune a
kofarta,tana jinsu ta sako baki da cewa,"ku dai
lallasheta,karatun nan fa da ake ta matsanta
mata bana ganin manzo bane." Abba ya ce
mata,"in ji wa? kin ji ki,to ana neman aljanna da
karatun boko kuma ana neman wuta." ta ce,"kai
ni raba ni da shegiyar karya tunda bata so a
barta." Abba ya dubi ummi,"kada ma kiyi za ton
maganar tsohuwa za tayi wani tasiri,gara ma ki
shirya komai gobe da wuri zamu wuce." ta dube
shi,"don Allah ya abba." ya mike ki shirya da
yamma zanzo muje (sahad store). ya dubi umma
na tafi. . Ta ce,"abba bamu ko gaisa ba,ya mutan
gidan?" ya ce,"suna lafiya,sauri nake in karasa
wasu dinkuna,saboda gobe bana nan jibi litinin
zanje interview da gidan radiyo da talabijin na
(c.t.v) ta ce,"a'a ka samu anan din ne?" ya
ce,"eh bana fada miki ba da aka tura takarduna
can sai suka ce gurin da zasu saka ni akwai wani
wanda suke jin dadin aikinshi a gurin? don haka
zasu turo ni kano,suna ganin ana bukatar irina.to
shine mijin anty ya fada min to yanzu sun kirani
ranar litinin zasu min (interview).ummi dai na
jinsu bata ba kukanta ba.abba na ficewa umma
ta ce tashi kije kiyo kitso ummina,kin ji? dakyar
taje ta dawo.umma tana yankan kubewa wayarta
ta shiga ruri,ta dauka Abba ne.ya gaisheta ta
amsa,ya ce ummana ummi fa ta shirya? umma
takai duba cikin daki inda ta hango unmi nade
kan kujera tunda ta fito wanka. Tace can cikin
kujera,wai sanyi take ji.yace sanyin lfy kuma? ta
shirya ta sameshi gida,umma tace to gatanan
xuwa sukayi sallama.umma tace ke ummi fito
man in kin gama shirin.ummi tace umma nifa
sanyi nake ji,ina ganin xaxxabi ne xai
kamani.tace to ku biya ta kyamis kusai
magani.tsohuwa tace ke yi kwanci yanki, dole ne
fitan? umma ta miqe tana cewa, yanxu in ban je
ba da yaxo xai fara min masifan shi ne. ta shirya
ta fuce rai a bace.a nutse ta ke tafiya har daf da
qofan gidan ya abba. sallama taji anyi mata.wani
matashi ne suka gaisa, ya tambaye ta nanne
gidansu? tace a,a lafiya?ba tare da bata lkc ba ya
fara xayyane mata manu fanta,santa yake kuma
da aure,tace kaga mlm sai anjima.ta shige gidan
abba shiko ya kafe yaqi tafiya.da sallama ta
shiga gidan,qaran inji baisa aji sallaman ba,dan
haka ta jingina da rijiya tana kallan tsakar
gidan.mamakin daya yadda mace daya a gidan ta
kasa gyara gidan.sai kace gidan namiji, namijin
ma qaxami. . abba ne ya fita wanka sanye da
jallabiya fara.ya aje bokitin ya dube ta. yace ki
siga ciki mana, ai tana falo.tayi
sallama,bishiratana xaune da baso tana kalan tv,
ganin umma ta daga labule sai ta hada rai tare
da cewa lfy? ummi tace ina wuni. bishira tace
lau, nace lfy? ta fada hadi da xare ido. ummi tace
ya abba ne ya ce na xauna anan na jira shi. tace
baxa a xo nan adame ni ba, ehe dan kallo nakeyi.
ummi ta ja tsaki tare da sakin labulan, ta koma
ta jin gina da rijiya.bishira ta fito.ke sarkin rashin
kunya wa kike ma tsaki? ummi ko kallanta batayi
ba.sannan tace baki isa kixo min har gidana
ba,kice xakimin rashin kunyan da kika saba.abba
ya jiyo hargowanta ya fito, yana qoqarin saka t-
shirt baqa akan faran singiletin shi,wandan jeans
ne mai laushi blue.yace,menene? tace, wannan
mara kunyan yarinyan nanne xata sameni har
dakina tamin tsaki.oa dubi ummi dake kallan
qasa tamkar bata san me akeyi ba. yace ke
ummi, ta dube shi da sauri,xan bata maki rai
kinsan bana san raini ko? tace nifa ya abba
banfa yi mata komai ba kawai fa.ya daga mata
hannu,yace banasan ji. yace na fada maki dai
bana san raini. takaicin duniya ya isheta,ta
sunkuyad da kai cikin qunan rai.wanna shine
gaba kura baya damisa.bishiqa kam sai ci gaba
da mita take, shiko abba tuni ya koma dakinsa da
qarasa shiri. ya fito fes, sam baxaka ce mijin
bishira bane.qamshin turaransa ya karade gidan
ya daga labule.ni na fita. tace sai ina? xan kai
ummi ta sai duk abinda xata nema dan gobe xata
koma mkrt. ta tabe baki. ya dubi ummi wadda ke
cika tana batsewa,sannan ga sanyi alamun
xaxxabi yana damunta.yace muje ko? ta dube shi
sannan ta bishi.a qofar gida ya iske wannan
saurayin,yace lfy, ko kana jiran wanine? saurayin
ya ce wata yarin....sai ya hango ummi,dan haka
ya katse batun da cewa yauwa gatanan. . abba
ya kalleta ke uwar rore rore wannan ke yake jira
ko? ummi tace oho mashi, bina yake tayi.abba ya
ce, kayi haquri dan samari,ba aure xa a mata ba,
krt takeyi. yace nima din bawai ina nufin yanxu
bane.ya ce na fahince ka.to ka bari sai nan
gaba,ina nufin in auran yayi sai kaxo ko???? Ya
dubeta ranshi bace,ke kuma wuce muje.suka bar
shi nan tsaye yana kallansu.yaga kishi qarara a
idon abba.yace wannan ba wanta bane shima
santa yake.ya raya aransa shima yayi gaba abin
shi.shi kam abba suna tafe yana yi mata fada,wai
tabi ta sakar ma maxa fuska kowane gaja sai ya
xo yace yana santa.maimakon ta tsaya tayi
krtnt,xamani na ilimi,ita dai ta qi kula shi,har
yanxu takaicinta abin da matarshi ta mata,kuma
ya nuna ya goyi bayanta.wayarshi tayi ringing,ya
kalli ummi muje shago na mashin din
nacan.sannan ya daga wayar,ita tana tafe ne
amma sam bata jin dadi.da yake tafiyanta yanxu
tamkar tana jin tausayin qasa take yinta,sabanin
da da sai dai tayi gudu,shi da ke tafe yana waya
ya riga ta isa.gefe ta tsaya ya shiga shago bayan
ya gama amsa wayar.ahmad abokinsa yaxo xai
shiga shagon ya ganta tsaye.tace ina yini ya
ahmad? yace lfy lau yar daru.daman haka ya kan
ce mata.ya shiga shagon yana
waiwayanta,abbana barma yan shagon sallahu
wasu kayan da xa a xo dauka,ahmad ya shigo.
suka tafa,sannan suka gaisa.ahmad yace naxo ne
in fada maka anjima xamu shiga gidan su hafsa
dan gaida iyayenta,sai dai kuma ganin ummi ya
sani jin wani abu.anya ba xan dawo gida da
neman aurena ba?a rude abba ya ce wace ummi
kenan? ahmad ya ce qawarka mana.abba ya ce
dan Allah saki xancen nan kada ma ta jiyo ta
raina mu,me ka gani naso a gun ummi? dan Allah
kada ka cta min rai. . ahmad yace, allah in xai
yiwu, nutsuwan ta birge ni .abba ya ce to ba da
ni xa aci amanar hafsa ba.ummi kuwa dan Allah
ka bar xancenta.yaea ahmad yaga abba ya sha
mur ya tsare gida,dole ya saki batun.suka yi
sallama ya tafi,abba na cewa sai yaxo da
dare.yasa yaron shagon ya goge mashi mashin
din sannan ya tada,ya kalli ummi fuskarshi daure
xo ki hau.itama tata fuskar a daure take.tahau
suka tafi,iskar dake kadata tasa xaxxabin dake
san kamata ta qaru.ya kafe mashin dhn ya
kalleta,muje mana.ta bishi suka shiga cikin sahad
store din.tsaye tayi tana kallanshi yana diba
kaya.da alama na iyalanshi yake diba,dan taga ya
soma da pampas. Hannuwanta harde a qirjinta
tana kallan shi,kome nashi yana birgeta.ya
waiwayo ya dubeta, tsayuwarme kike yi a nan da
ba xaki dauki abinda ya kawo kiba? ta rasa me
xata dauka,sai kurun ta dauki makilin ta riqe a
hannu,ya gama diban abin da yake so,sannan ya
aje gaban masu amsar kudi.ya dubeta,bakya
buqatar komai kenan? ta nuna mishi makilin din
hannunta,tana murxa shi.ya harareta baxa ki
dauki komai ba,kina da kayan tea dasu complex?
tace a,a.y2e to ki tsaya kada ki dauka.ya soma
dibo mata saitin sabulan nan daya taba sai mata
na aloe vera,dan yaga duk kananan qurajen sun
mutu.sannan ya hada mata da audugar mata
guda biyu.ya kai table.lkcn ta dauki madara da
milo ta kawo.yace wawiya,dalla matsa ki bani
gu.yaje ya qara tsinto mata ,sanna akayi musu
total ya biya.suka fita.kafin sukai gida haqoranta
sun s6a haduwa,gashi tana ta takurewa,yace
lfy,wani irim xama kika yi haka?tace,sanyinake
ji.tana magana muryarta na makyarkyata.wani
dan asibiti ya nufa da ita nan kusa da unguwansu
aka dubata. Wurin allura,nan fa a ka soma
daga.Ta ce,ita kam bata san allura.Abba ya daka
mata tsawa da cewa,Allurar ce abn tsoro?Na
gane sam ba ki son ki koma mkrnt,a gobe ne
kuma sai kin koma duk abnki. Ta ce, Naji zan
koma amma yanzun kam dn Allah Ya Abba kada
amin allura.Nurse dai sai kallonsu take yi tana
dariya. kwai Ummi sai ta soma hawaye ita fa har
ga Allah bata son allura.Nurse ta ce,To ka rike ta
mana ko ba Amarya ba ce?Naga shagwabar tayi
yawa. Abba ya ce,Me? cikin tsawa ya yi
maganar,hr sai da Nurse din ta tsorata,ya ce
kanwata ce fa,kin ga wannan kucakar tayi kama
tayi kama da Amare? Nan take Ummi taji ta
muzanta,sannan km ta tsorata da irin tsawar da
ya yi,ba ta san lkcn da ta shige a ka yi mata
allurar ba. Ta fito tana sharar kwalla suka koma
gida. Sai dai tana hada kayanta a Jaka,Sannan ta
ga wadannan sabulun da kuma audugar,kenan shi
ne dama ya sai mata wancan?ko me yasa ya sai
mata kuma hr da augugar mata? . wata zuciyar
ta ce,kila dn yaga Umma bata san kan abubuwan
zamani ba sosai.A fili ta ce,kai umma tasan
audugar mana. Haka dai ta ci gaba da tufka tana
warwarewa,hr ta gama shirya kayanta. Yau kuma
a bayan Tsohuwa ta za6i kwanciya,da dn komai
ba sai dn suyi hirar yaushe gamo. Sai dai
Maimakon hira sai ta tsunduma a tunani,ta bar
Tsohuwa tana ta zance ita daya. Fitarsu da Ya
Abba ta tsaya mata a rai,ita tayi ta tunowa tana
murmushi.Sai dai bata Son tuna lkcn da ya yi wa
Nurse din nan tsawa dn ta ce ko ba amarya ba ce
kom me yasa zai mata Tsawa? ita kam kalamn
Nurse din nan sun birgeta,shi kuma daga ganin
yadda ya yi tsawar nan kalamn ba su masa dadi
ba.......... wai takwara bacci ki ka yi ne?Muryar
Tsohuwa ta katseta,ta ce,Idona biyu Tsohuwa.Ta
ce, Tunanin me ki ke yi ne haka?Ummi ta ce
"Um" ina tuna gobe yanzun ina can.Tsohuwa taja
tsaki,Ai mai sunan Malam ya san takan mugunta.
UMMI dai ta ce "Um.Tsohuwa kuwa sai yi take
da mai sunan Malam.Tun Ummi naji tana "Um",
hr zcyrta ta soma tsanar kalaman Tsohuwa. Sai
dai bata da damar ta katse Tsohuwa tunda dn ita
take yi,bata da mafita da ta wuce ta bar
dakin,don haka ta suri butar Tsohuwa,wai zata je
kewaye(bandaki). Shi ma Abban da ke kwance a
tsakar dakinshi kan kafet ya tada kai da
katifarshi,ban da tunanin fitarsu ta dazun ba abn
da ya keyi. Sai dai damuwarshi daya,me yasa
samari da dama suke kawowa Ummi hari?Me
yasa ya ke jin zafin haka?Zuciyarshita amsa da
cewa,ka so ko ka ki kana Son UMMI."a fili ya
furta "Haba dai so,Allah ya tsare ni." Tun misalin
tara Ummi ta gama shirinta tsaf,cikin kayan
mkrnt mai ruwan hoda,mai gida-gida.Da kuka ta
bar gidan yau ma. Haka nan kuka take hr suka
isa mkrnt,ta samu Khadija hr tazo,dn haka tare
suka kwashe kaya.Kafin Abba ya tafi sai da ya yi
mata fada kwantankwacn wnda Umma tayi
mata.Waton ta kula d kanta,kuma tayi abn da ya
kawo ta,waton krt.Sannan ba ya son tayi
kawance d yaketa shari'a.irin wanda wasu
watsatstsun yaran ke yi.(Allah ya shiryesu).
Sannan ya jadadda mata batun ibada,sannan ya
kawo kudi ya bata,ta ce Umma fa ta riga ta bani.
Ya ce,"Ki kara."ZURFIN CIKI book 2 part 5
ZURFIN CIKI book 2 part 5
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:12
Umma fa ta riga ta bani. Ya ce,"Ki kara."
Rayuwarta a mkrnta wannan karon ba laifi,sai dai
fa hr yanzun ta tunu da gida sai tayi kuka. Su
Safiyya suna mmkn yadda Habiba take da
matsanancin nacin gida. ******** Abba ya shigo
gidanshi dauke da ledajin kayan miya,da sauri ya
dire su kofar kicin ya nufi Bishira da ke kofar
bandaki tana shara amai. Ya kama ta,"lafiya?Me
ki ka ce? Sai da ta gama aman sannan ya karasa
da ita ta wanke baki da fuska a cikin bayin. Ya
ce,Ba ki d lfy ne?Ta soma Hawaye, Ka gani ko
Babn Walid,kila fa ciki ne da ni.Tun wancan Satin
ya kamata in ga al'aldata amma shiru. Ya ce, To
menene na kuka? Yi shiru,Allah ya inganta.Ta
harare shi Dana fa bai shekara ba.Ya ce,To dole
ne sai danki ya shekara sannan Allah zai baki
wata kyautar? Ta soma kuka,Ni dai zan je a
ciremin ne. ya hade fuska,Ban yarda da haka ba.
Ganin ta tada hnklnta tana cewa "Dama Hjyrsu ta
ce mata tabi a hankalu ta ki ji gashi nan yanzun
tana da wani ciki. Ya ce To kada ki damu kin ji?
Zamu je asibtin dn a tabbatar da cikin kafin a san
abnyi. Da za suje asibiti shi ne ya dage sai da
tayi wanka,dn d farko kaca-kaca ta dauko
mayafi, ya ce sai tayi wanka ta canza tufafi.
Gwajin farko ya tabbata tana da ciki,nan ta shiga
kuka. shi kanshi ya damu domin bai so ciki
yanzun ba.A son ranahi sai an yaye yaron kafin
wani cikin. Amma ba shi da ra'ayin
zubarwa,nashi ganin kyautar Allah ce,dn haka ya
amsa ya kuma gode. Ya lallashe ta da cewa,ta yi
hkr su amshi kyautar Allah dn haka wani na nema
da kudi bai samu ba. likita ya ce,Kada ta
damu,taci gaba da bai wa danta abnci tana hada
mishi da nonon,a hnkli zata yaye shi bana farat
daya ba. Bayan ya kaita gida ya kuma
lallashenta,saiya nufi gurin Umma. Bayan sun
gaisa,ta tambayi iyalanshi ya ce "Daga asibiti ma
muke da Bishira." Umma ta dube shi da
sauri,Waye ba lfy? ya ce, Ita ce.Sai kuka ma take
yi wai dn an ce tana da ciki. Umma ta ce, Ikon
Allah, to Allah ya inganta.Sai dai kuma kada
Walid ya sha ciki. Abba ya ce,likiya ma ya yi
mata bayanin yadda za ta yi masa,hr ta janye shi
daga nono cikin hikima.Umma ta ce, Da za ta
yarda ma an kawo mana shi nan. ya ce,Ai dama
nan zan kawo shi da zarar an yaye shi Umma.
Sam bai fada ma Bishira nufinshi na baiwa Umma
Walid ba,dn yasan ba zata ta6a laminta ba.Sai
dai itama tasan dole hakan zai yi. Don haka ta
garzaya gurin Umman Bashir ta shaida mata
cewa sunje asibiti,dk ta fada mata komai,sannan
ta ce ita danta take tunani kada ya dauka ya
kawo wa Ummarshi ita ma a mallake mata yaro.
Umman Bashir Ta ce Wannan a zaune take,sai
dai in ko ba a kai shi ba.Amma ki bari daga kin
kula ya daina damuwa da nonon ki janye shi,zan
zo in taho da shi wurina. Bishira taji dadi tare da
cewa, Hakan dai yafi. Sabuwar kazanta ta
samu,Bishira dk abn bi bangon daki an tofe da
yawu.Rashin wanka sabo,kai abn nata sai
addu'a. Ibada kuwa ba a mgn,domin dai tuni ta
aje Sallah a gefe,Azumi dai tana yi amma in ta
sha bata ramawa.Allah ya shirye wanda ya 6ata.
Abba ya dai yanzun tuni ya yafe abincin
gidansa,matsawar ba shi da kanshi ya girka
ba,don kuwa dama can shi mutum ne mai
kyankyani. In zata fita takan wanke kafafunta ta
dauki kaya ta saka,sai ka rantse tayi
wanka.Amma da zata matso kusa da kai,nan za
ka ji kauri na tashu da karni da kuma wari. Dole
ya hkr da laluranshi ta aure a gurinta,domin in
yaje shimfidarta ba zata ki ba,amma wari da
zarni suna hana shi yin komai cikin nutsuwa. In
kuma dakinshi ya kirata ko bata kwana ciki ba
har gari ya waye yana jin warin jikinta a
shimfidarshi don haka lokuta da yawa yake
hakura da ita. *********** . Ummi tana kwance
kan gadonta,yayin da Khadija da Safiyya suke
zaune bakin gadon Safiyyan wadda ke kallon
Ummi. Hirar masoyinta take basu,Safiyya bata ko
gajiya da zancensshi. Khadija ta ce,ita ma da
zata taho har kuka nata Saurayin ya yi. Sai lkcn
Ummi ta dube su,"kuka Khadija?Khadijata
ce,"Riris Kuwa. Ummi ta ce, Hu'um ba namijin shi
yasa nike da za6i a kan irin mijin da zan aura.
Safiyya ta ce,"ke banza,dk cikin so ne. Ummi ta
ce Ban damu da sai namiji yaso ni ba,in dai ya
tara abubuwan da nake so ga namiji to zan yi
amfani da kasantuwata 'ya mace in koya mishi
Sona. Khadija ta tashi ta dawo kusa da Ummi,Kin
san me ki ke fada?Koda yake sanar damu yadda
ki ke son mijinki ya kasance? Ummi ta ce "Na
farko mai son Addini,Mai Ilimi duka 2,mai hakuru
,sannan yana da saurin fushi,mai kuzari da
kwarjini. Ma"abocin tsafta da tsantseni,wandadk
tufafin da yasa sai sun kar6e shi,mai biyayya ga
iyayensa,sannanmai kula da gidansa,baki mai
tsare gida,ga yawan Ibada, Safiyya da khadija
suka kwashe d dry,Khadija ta ce, Ina za ki samu
dk mai wadannan lissafin da ki ka yi??? Safiyya
ta ce, Kuma fa bata gama lissafin ba ke ba ki ji
ana cewa dan Adam tara yake bai cika goma ba?
Ummi ta ce,Akwai shi,Ya Abbanmu haka
Halayansa suke. Yanzu ma da ni ke lissafin shi
na ke kallo a idona.Khadija ta ce,To ba dan
uwanki ba ne da shi kenan kin samu a gida.Ummi
ta ce,Wuu fitina Road,wannan ya mugun tsanata,
ina son dai me irin halayarshi ds
dabi'unsa.Khadija ta ce,Har da kamaninsa? Ummi
ta ce,sosai ma. Saitaga sun sa dry.Safiyya ta ce,
Malma shi ki ke so,kuma dk yanda a ka yi ba
shakikin ki ba ne,da aure a tsananinku. Umma
tayi Shiru tana kallonsu,Khadija ta ce,Habiba
kenan,wai har saurin fushinshi tana so. Ummi ta
6ata rai tare da cewa,Tunda kun kasa fahimtata
shi kenan.Ya zan yi in ce ina son Ya Abba yana
da matarsa? SAfiyya ta ce,ke dai in da aure
Tsakaninku kada ki tsaya "ZURFIN CIKI, kizo a
karshe kina da kin sani. Ummi ta ce,A bar
zancen. 32... Sai dai kuma a daran ranar ta
tsinduma duniyar tunani.Tabbas zuciyarta da
shisshiga take,tunda ta rasa wanda zata so sai
Ya Abba. Wanda ya yi mata muguwar tsana.Afili
ta ce,Duk kauce-kauce da kewaye-kewaye ba za
su kai ni ba,Ya Abba nake so. Hawaye Suka
soma sintiri daga idanunta. Wannan lkcn ziyarar
da yazo Abba da Umma d Tsohuwa da Alhj
Karami dk suka zo. Dadi ya kashe Ummi,ta rasa
jikin wanda zata fara fadawa don dadi. Alhj
karami ta soma kamkamewa sannan
Umma,Tsohuwa kam ai tana manne jikinta hr
suka zo tafiya.Shi ko Ya Abba yanzun kunyarshi
take ji,dn haka tunda suka gaisa mgn bata kara
hada su ba. Sai dai jife-jife suna satar kallon
juna,in sun hada ido sai ya dan daure
fuska.Safiyya da khadija sun gaisa da su sannan
sun yaba da yadda a ke ji da Ummi. Da za su tafi
kuwa Ummi kuka Tsohuwa kuka,sai da Abba ya
ce ba za a sake zuwa da su ba,Sannan Ummi tayi
shiru.Sun tafi sun barta d kewarsu,Kamar yadda
suma suka tafi suna kewarta. ********** . Bishira
da kanta ta dauki Walid ta kai ma Umman
Bashir,domin ta san zai kai ma Ummanshi ne.
Abba ya rufe ta da fada lkcn d y tambayi dan ta
ce ta yaye shi ta kai ma Umman Bashir. Ya ce To
je ki dauko mn yarona,dn ba can nayi niyyar kai
shi ba,Ta rike kugu,kaje mana da kanka,tunda ba
ka son zamn danka hannun mahaifiyarka to ni ba
zan yi saken da Mahaifiyarka tayi ba a ka raba ta
da danta ina fata ka fahimci karatuna? Kallo
kurum ya bita da shi,sannan yaja tsaki tare da
cewa,Dube ki kmr wata Bauna,jiki sai tsami yake.
Ta ce,Eh dk abn da zaka ce kace. Ya juya ya fita
rai 6ace. Umma ya Samu ya fada mata, ta ce, To
menene na bata rai Abba? Can din da nan ba dk
daya ba ne? ai ba za su cutar da shi ba. Ya ce, ki
fahimce ni Umma,ba ina nufin zai cutu ba
ne,amma can da yara kanana,nan kuma babu.
Sannan......... ...... Sai kuma ya yi shiru tare d
cewa,Shi kenan. Umma ta ce,Yauwa bana son
kana daga murya kan abn da bai kai ya kawo ba.
Allah ya raya mana shi ya kuma sauketa lfy.
Abba Ya ce Ameen. Gidan (T.V)sun kira Abba sun
masa (intervier)da kusan wata 2,dmn ya cire ran
samun akin, ko da yaje suka ce sun dauke shi
aiki. Abn d yasa suka yi jinkiri daukarshi,suna
canza tsarukan aikin ne sannan sun sake
tantance ma'aikatansu. Litinin Abba ya soma
zuwa aiki kmr yadda a ka bukata,dakin watsa
labarai a ka kai Abba. Sam bai samu matsala
ba,dk d shi na mai yawan surutu ba ne,amma a
cikin sati 1 ya goge da aikin,km an yaba da yadda
yake watso labarai. Yana yi da Hausa minti sha
biyar da turanci minti sha biyar,ana sakawa karfe
7 na yamma. Abba ya kama aiki cikin sa'a nan
da nam sai farin jini cikin abn d bai fi wata ba ya
nemi izinin a bashi fili koda mint 15 ne don
gabatar da wani fili da ya yi masu don matasa.
filin yana kiran shugabannin matasa na
unguwanni suna hira da su akan halin da matasa
suke ciki na shaye- shaye da sace-sace da kuma
rashin sana'a. Da turanci a ke shirin,sannan a kan
baiwa sauran matasa na gida su bugo waya su
fadi nasu ra'ayin,game da abin da ya kawo
hakan,da kuma hanyoyin da za a bi don magance
su. Haka nan ya kan samu lkc ya shiga cikin
matasan musamman ma su shaye-shayen da
marasa sana'a dn jin ra"ayoyinsu,da dalilan
fadawarsu cikin harkar. Kafin wani lkc filin ya yi
suna kuma kullum yakan tallata filin kan cewa ya
kamata Gwamnati ta dauki nauyi filin don yana
taimakawa mata wurin inganta rayuwar matasa.
Cikin ikon Allah sai gashi Gwamnati ta yaba da
filin,ta dauki nauyin shirin kuma an sa shi hr
fannin Radiyo. Lallai Abba ya shigo da kafar
dama,Sannan hukumar gidan Radiyo tayi Matukar
farin ciki da zuwan Idris Aminu Idris,wannan
Ma'aikata. Sannan sai Abba ya zama wani sabon
tauraro wurin Al'umma,dk in da a ka ganshi ya
zama abn kallo. Matsalar shi daya gidanshi,in ka
ganshi a waje Sam ba za a kayi tsammanin haka
zaka samu gidanshi ba,Dattin ya karu,musamman
da ya kasance yanzun ba shi da lkcn kanshi
ballatana ya yi sammakon share gidan. Wankinshi
mai kaiwa yake yi,haka nan nasu ya ce ta dinga
kaiwa makota gidan wanki. Amma kafin ta hada
ta kai aiki ne ita dai tayi kallo ko a shiga makota
hira. Sam Abba ko adreshin Zai bada ya
gwammace ya bada na gidansu Ummanshi dn ba
ya so aje gidanshi ************* . Kwanci tashi
Ummi suna ta fana da jarabawa zuwa (SS2) cikin
ikon Allah suka gama. ranar da aka yi musu hutu
kamar ta sani bata tsaya jiran Abba ba,Ta nufo
gida. Shi kuwa lkcn suna kici-kicin kai Bishira
asibiti zata haihu,amma yana sane da cewa yay
Ummi zata dawo kuma hnklinshi na can. Motar
wani Salis Abokin aikinsa ya aro ya kai su
asibitin ita d Ummanashi. Bayan ya ba d dk wani
abu da suke bukata ya ce Umma za shi dauko
ummi. Umma ta ce,Ka barta tukunna in matarka
ta sauka lfy gobe sai kaje tunda tana mkrnt ne.
Ya yi-ya yi Umma ta ki,dole ya hkr. sai bayan
la'asar sannan ta haihu,Nurse ce ta zo tayi musu
albishiri an samu 'ya mace. Bayan an kintsa
uwar,sannan a ka kaita dakin hutu,su kuma a ka
kawo musu 'yar.Nurse din da ta kawo 'yar ta ce
d Umma ke ce Mamanta? Umma ta ce,'Eh."Nursr
din ta ce "kazantar yarinyar tayi yawa,kafin ta
haihu sai da likita ya korata ta yi wanka,muka yi
mata aski ko'ina jinkinta datti. Gsky Mama
mijinta yana kokari,yanzun kuje ku dafa ruwan
dumi ku kawo mata tayi wanka. Abba ya yi tsaki
ya ce, kin ji ko Umma,Allah ya kara.Umma ta
ce,Yanzun kaje gida ka dauki babban filas dina ka
shiga wurin Umman Bashir ka ce Mata ta dafo
ruwan Zafi,daga nan ma sa ji haihuwar. Yana
shiga gidan tun daga zaure ya jiyo Muryar
Tsohuwa tana cewa,Naji shiru-shiru kin ga dai hr
yanzu. Yana saka kafa a tsakar gidan muryar
Ummi ta daki dodon kunnanshi.in da ta ce,Kila
kuma ta haihu yanzun. jinin jikinshi ya tsinke dn
jin Muryae. Ya nufi dakin.Tana zaune tana shan
rake. Ya dubeta, ita ma shi take kallo dn tunda ta
diro ba wanda take muradin Gani irin shi,cikin
sanyi murya ya ce,Ummi ke da wa ki ka taho? Ta
sunkuyar da kai,Ni da wasu 'yan mkrntrmu ne
muka dawo. Ya ce '"Good,tashi ki dafa ruwan zafi
ki zuba a babban flask. ya dubi Tsohuwa da take
ta tambayarshi ko mai dakin nashi ta sauka? Ya
ce, Eh ta haifi 'ya mace. Tsohuwa cikin takaici ta
ce,Sai yanzu kaga damar bani amsa?Dan
walakanci kawai? Kai mai sunan Malam ka gyara
halinka. Abba ya ce,Yi hkr Tsohuwa dk na gaji
ne,Nan kuma ina yi wa Ummi mgn. Ta ce kana
mata fadan ka dai. Ya ce,Tsohuwa wai ni hr
yanzun ba zan wanku a wurink ba game da
Ummi? ta ce, Ina fa zaka wanku?Har abada mai
sunan Malam kai ba me kaunar takwara bane. .
Yace to naji a bar maganar yanzu dai kishiyarki
ta haihu.an samu ya mace.tace Allah ya raya
mana. Yana jingine da bango yana kallon ummi
tana ta shige da ficen daura ruwan zafi.komai
cikin tsafta da natsuwa take yi. Sai da tasa
ruwan zafi ta wanke flask din kasancewar anjima
ba'ayi amfani dashi ba.ta tafasa ruwan tazo ta
bashi,ya ciro wayarshi ya mika mata. "sa min a
caji naga nepa sun kawo wuta" ummi ta jona
waya sannan ta ci gaba da girkin dare don tasan
Alhaji bai cika son wani abu da dare ba sabanin
tuwo. Ta gama wanka sannan tayi sallar
magariba tana kwance gadon tsohuwa tana
tunanin abba. Tsohuwa nata lazimi in tayi
magariba bata tashi sai tayi isha sannan taci
abinci.ummi ta tuna wayar da yaya abba ya bata
ajiya. Da sauri ta tashi tare da cewa "ke tsohuwar
nan anzo tayaki hira kin share mutane" ta mike
ta nufi daki ta dauko wayar ta kunna HEHE KIN
MANTA YAYA ABBA KENAN?" Sakwanni ne sukai
ta go slown shigowa sannan sai kira tashin farko
data daga wayar muryar mace taji, ta ce "dawa
nake magana" wadda ta kira ta ce "ina mai
wayar?" ummi tace "dq matarshi kike magana,ke
din wacece?" waccac n ta ce "in yazo ki
tambayeshi? yasan me lambar." nan da nan sai
ummi ta samu kanta yana juyawa,tayi tsakita
kashe.ta shiga duba sakonnin da yawansu na
mata ne masu sonshi,daidaikune na maza masu
nuna yabawar aikinsa.hankalin ummi ya tashi
ganin yadda mata suke farautar abinda take
tsananin so.ta kashe wayar cike da nadamar
kunnata Hankalin Ummi ta samu kanta yana
juyawa,tayi tsaki ta kashe.Ta shiga duba
sakonnin da yawansu na mata ne ma su
sonshi,dai-daiku ne na maza ma su nuna
yabawar aikinsu. Hankalin Ummi ya tashi,ganin
yadda mata suke farauta abnda take tsananin So.
Ta kashe wayar cike fa nadamar kunnata. Sintiri
ta dinga yi a tsakar dakin,Sallamarshi ce ta, katse
ta.Ta amsa ciki,sannan ta zauna ba tare da ta
kalle shi ba. Ya ce,Bani wayata da abinci 'yan
asibiti. Ta mike ta dauko masa abncin,sannan ta
bashi wayar.sai dai tana yin komai ne fuskarta
daure. Ya ce,Lafiya na ganki wani iri?ta dago ido
ta kalle shi,ta sake tsuke fuska. lfy lau.Ya ce,shi
kenan na tafi Sam bata tanka ba. Yana fita ta
mike a kujera,so takeyi a lkcn ta samu makanta
mafita,shin ko dai ta tare shi ne ta fada masa?
wata zuciyar ta ce,In ko ya dinga kwallo da ke
sai kin rasa mai cetonki. Ta tashi tare da
cewa,Bari kawai in fada ma Tsohuwa.Zuciyarta ta
sake rayawa.Tsohuwa fa ba zata yarda ba, domin
kullum tana bada shaidar tsanar da Ya Abba ya
mata,ta koma ta zauna. Sai ta samu kanta da
fashewa d kuka,tana fadin wannan wace irin fitina
ce ta same ni?me yasa zcyt ke son tozarta ni?
Me yasa zata so wanda ya tsane ta?Ta mike ta
shige uwar daka. Gado ta hau tana son ta lallashi
zcyrta,dn ta daina son Ya Abba. Shi kuma yana
tafe a mashin zcyrshi na mitar bata gaji da ganin
Ummi ba,yadda take ta kai kawo ya ke gani a
idonshi. Lkcn da ya kai musu abnci me jego ta
gyare,dama ta zubar d jini ne shi yasa suka ki
sallamarta,sukace sai da Safe. Ya samu kannanta
sun zo da wata 'yar Babnsu.Sun gaisa an yi 'yar
hira sannan suka ta fi lkcn ya dauki 'yar ya yi
mata kallon sosai. Ya dubi Umma kin san
yarinyar nan da wa take min kama?Ta ce,A'a.
Bishira ta tsare shi da ido,ya ce lkcn d Ummi na
karamarta sak wannan. Umma ta ce,Kana nufun
d Ummi take kama?ya ce,"Eh,Bishira ba kunya ta
ce,Allah ya kyauta ni 'yata bata kama da wata
can wai ummi. Umma tayi saurin cewa,Dama
zolayarki yake ba suyi kama ba.Shi kuma ya
kalleta.Ko ki so ko kada ki so yarinyar nan sak
take kama d Ummi. Ya mika ma Umma ita,yana
ci gaba da fadin Maman Walid kina bani
mmki,kina zaton zan ki raba 'ya'yanku d Ummi?
Ya girgiza kai"Sun hadu hr abada ,domin in kin
tsaga jikin 'ya'yanki dole za ki ga jinin Ummi. to
ya ya ma ki ke tsammanin zan so wanda ba ya
son Ummi? Ta ce, "Oho! Ni ba ka sona kenan?To
in da na gode ma Allah dk dyniya ta san cewa
Ummi bata kaunarka.dk da kana wanta.Ba ita ba
ce silar kariyarka?ko an kashe ka ma bata da
asara. Umma ta ce,'Abba jeka ban son in kuma
jin bakinka in na isa. / ZURFIN CIKI book 2 part 7
ZURFIN CIKI book 2 part 7
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:16
Ta samu an saka ranar auren fati da saurayinta
Fahat,nan fa Alhj ya ce dama ke ni ke jira uwata
ki dawo. A masu sonki ki fito da daya a hada
auranku da 'yar uwarki Fati. Hankalin Ummi ya yi
matukar tashi,ranar kasacin abnci tayi. Da suka
zauna da Umma a daran ta ce Umma baki fada
ma Alhj bani da tsayayyen saurayi ba?Umma ta
kalleta,ba shi yasa na ce Kitsada ba,amma ba kya
son fita. Duk kin bi kin kori masu sonki Abba na
daure miki gindi,kin san dai Alhj ba yarda zai yi ki
wani ci gaba ba,gara ma kin yi kokarin fidda miji
kafin lkcn da ya dibar miki,in ki ba haka ba ya
daki da mai rabo. Ummi tasa kuka ranar,kwana
tayi tunani hr ta yanke shawarar zata fada ma
Alhj Ya Abba take so. Da safen taje hr dakin Alhjn
ta gaishe shi,ya ce uwata naga kamar bakinki da
magana ko?Ta dube shi "Eh,a'a ba komai.Ta
mike,dakin Tsohuwa ta shiga ta haye gado ta
soma kuka. Tsohuwa ta dubeta a rude,Takwara
ke da waye,? Nasan ba zai wuce me sunan
Malam ba,dn shi ne kadai ke hana ki sukuni. A
ran Ummi ta ce,shi ne kam,amma ba irin wanda
ki ka sani ba. Amma a fili sai ta ce,Tsohuwa Alhj
ne wai in fito da miji,kuma abn da ke damuna ni
ba wanda na ke so. Tsohuwa ta ce, "Au, shi ne
abn kuka?To bari kiji bana ba zan goyi bayabki
ba,dn da ubanki ya ji ta tawa da yanzyn kina da
diya 2 in da rabo. Amma mai sunan Malam ya ce
za ki ci gaba da krt,yamzun ko tun da Allah ya
kawu mu angama wannan kaddararriyar mkrnt ba
sai aure ba? Ga Bunta nan hr an yi baiko, to rana
guda za a yi shi in muna cikin masu rai. FUU
Ummi ta fice,ta shiga dakin Umma tana tunanin
wa zata fada ma matsalarta?kamar an tsikareta
ta dauki mayafi zata fice. Umma ta ce, "Zo nan,
ina za ki? ta ce "Wurin Fati. Tana shiga Bashir
zai fito . Ya ce Yauwa Ummi ina son magana da
ke. Ta dawo baya ya fita kofar gida ita ma ta
fito,suka tsaya ya ce "Ummi gaskiya dama ba
wani abu ba ne, ni dai na tsinci kaina da sonki.
Ummi ta dafe kirji da sauri."Sona?" ya ce kwarai
kuwa, dn haka za ya ki ka gani?ta dube shi,sam
babu wata alama da ke nuna cewa dan uwan Ya
Abba ne. Ta girgiza kai "kayi hakuri kawai Ya
Bashir,wlhy zuciyata ta jima da kamuwa da son
waninka." ya ce, Me ki ke nufi?Kin fi son bare da
ni jininku? Ummi ta ce,"Ni dai na fada maka." Ya
ce, "To kin fada min,ni kuma zan fada wa su
Alhj." Gabanta ya fadi. Shi kuma ya yi tafiyarsa, .
Sabon tashin hankali kenan. Sai damuwa ta
lunku,bata ta6a marmarin zamn mkrntr kwana ba
sai ranar. Ta rasa me zata yi taji dadi,gida ta
koma cike da nadamar fitowa,ta zauna a falon
Umma ta soma kuka. Umman tana dakin mijinta
ya yi karin kummali. Sai da ya fita sannan Umma
ta maido hankalnta ga lamuran gidan, kan kujera
ta samu Ummi ta nata rera kuka. Umma ta ce
"Ke Ummi lafiyanki? Abun ya soma zama iya
shege,daga cewa ki fito da miji sai ki tsira kuka?
To ina ganin kwadantaki zamu yi muci. Ummi ta
ce, "Ni fa ba kukan da nike yi ba kenan,ni fa Ya
Bashir ne fa. Umma ta ce Bashir me,? kiranki aka
yi? Gara daya da ke ki. ta ce ba fa dukana ya yi
ba wai cewa yai wai fa yana sona. Tab,Allah ya
tsare ni. Umma dn Allah bana sonshi,gaban
Umma jikinta a mace ta ce "Tabdi,ai ko in Alhj ya
ji wannan zancan ta zauna. Ummi ta sake
firgicewa, cikin kuka ta ce Da na shiga 3 Umma,
ya ya zan yi ne don Allah?Umma ta ce,"Mafita
daya ce ki fidda wani kafin zancan yaje wurin
Alhj. Yinin ranar Ummi ta rasa mafita Addu'arta
daya,Allah ya turo mata ko ma waye a daran yau
ta ce ya turo iyayenshi. Wayar Umma tana
hannunta,ta rubuta text ta goge yafi sau 20 da
niyyar ta tura ma Ya Abba cewa tana
sonshi,amma da ta tuno da irin dukan da zai zo
gidan ya yi mata in ya karanta sai ta share. Ita
dai ta san shi kadai take so. Tayi Sallar Istihara
kusan sau 3,amma hr yau zcyrta na nan makale
da son Ya Abba. Don bayan Isha'i kuwa a ka aiki
kiranta, ai tare da dan aike suka fita. Wani
saurayi ne wai shi Sahabi,dan unguwar ne Kuma
sana'ar aca6a yake yi. Na dai manta. Suka gaisa
ya gabatar da kanshi sannan ya fada mata dalilin
zuwanshi ba tare da wani nazari ba,ta ce ta
amnice. suka yi sallama ta dawo gida,umma ta
tambaye ta wanene?Ta fada mata,sai dai Umma
bata gane shi ba. Can jimawa Bashir ya aiko
Kamal kaninsa wai Ummi tazo,ta ce kaje ka ce
masa ba zan zo ba,ya sake aiko shi cewa in bata
zo ba shi zai shigo. Umma ta ce mata tashi kije.
Ummi hr d kuka ta fita,dn a rayuwarta ta tsani
Bashir,sbd yanda ya raina Umma. Kuma ba ya
ganin kowa da gashi sannan tana ganin in hr ta
auri Bashir zai mata tsakani da auren Abba. Tana
zuwa ta same shi zaune a dakalin kaofar gida,ta
isa gurishin. Ya Bashir kiran me ka ke min? Ya
ce,kin sani kema. Ta ce Ya Bashir dn girmn Allah
ka bar ni ba,Usaina gidan kurma ce buduwarka
ba? Ya ce Da ba, ya ci gaba da cewa,Ummi ina
sonki so na hakika nayi mamakin yadda lkc daya
zcyta ta kamu da sonki,to wai dn Allah ni me
yasa ba ki sona? ta ce Ya Bashir ina da wanda
nake so tun farko..........kamar daga sama suka ji
muryar Abba yana cewa,Kai Bashir me ka ke
fada? ya ce sonta nake. Abba sai da wayarshi da
ke hannunshi ta kwace ta fadi don figici,bai bi
takan wayar ba ya isa gabn Bashir ya ce, In ka
kuma furta kalmar so ga Ummi sai na maka
matsiyacin duka,ke kuma hr da fitowa kin zo tadi
ko? kafin tayi magana ya ce,Bace min daga nan.
Bashir ya ce,Amma ai ba laifi ba ne don nace ina
sonta? Abba ya bige mishi baki tare da cewa In ji
wa ya ce maka ba laifi ba ne?Bashir ya ce,An
haramta aure tsakaninmu ne? Abba ya cakumo
wuyan rigarsa Ni ne nan na haramta haka,kuma
kar in kara jin wannan mgnr. Bashir ya fige ya
nufi gida yana fadin cewa Yau zan samu Alhj da
mgnr. Ina ruwanaka da zaka ce ka haramta min
sonta? . Abba jikinshi hr 6ari yake dn tashin
hankali, yasan in mgnr taje teburin Alhj to ta kullu
yanda yake mishi mgnr hada auran Ummi da Fat.
Har ya saka kafa a zauran gidan su Umma,sai
kuma ya fasa ya dawo ya nufi gidan su Bashir
din,yana saka kafa a zauren gidn Alhj Krm na
fitowa. Don haka sai yaja baya,Alhj ya fito ya
ce,A'a Abba ne? Abba ya ce "Eh ni ne. Ya gaida
Mahaifin nasa,sannan Alhj ya tambaye shi cewa
Babn naka yana gida? Gaban Abba ya yi
mummunan faduwa,ko dai Bashir ya fada wa
mahaifinsu ne? Alhjn ya ce ko ba ka ji ba?Abba
ya ce "Eh a'a ban riga na shiga gidan ba. Alhjn
ya ce To bari in ganshi. Nan jikin Abba ya jike da
zufa. Da azama ya shiga gidan. Mahaifiyarsu tana
alwala ya ce Umma ina Bashir? ta dube shi
Lafiya ba ko sallama? ya ce Nayi ba ki ji ba ne?
ta amsa sannan ta ce lfy ka ke nemanshi? ya ce
lfy lau. ta ce Yana daki,shima na ganshi ya shigo
a fusace. Abba ya nufi dakin. Bashir na zaune kan
katifar idonshi na kasa yana girgiza kafarshi ta
dama,Abba ya shiga ya ce,Bashir nazo ne in sake
gargadinka a kan Ummi,sai dai naga hr kayi
kuskuren fada ma Alhj krm ko,? Bashir ya mike
ya daga sauti Ban fada mishi ba,amma ina da
niyya. Ina sonta babu wanda kuma ya isa ya
hana ni sonta. Abba ya kashe masa fuska da
mari. Sai suka ji muryar Mahaifiyar tana cewa,
Kara mishi Abba,ka cika dana. Ta shigo dakin hr
gabn Bashir ta ce, Ni za ka tozarta? kayi kuskure.
Ai da in ga ranar aurenka da Ummi gara naga
gawarka kwance yafi min sauki. Abba da Bashir
suka dubeta a rude. Ta ci gaba da cewa Bashir
kai ma kasan ba zai ta6a sa6uwa ba ne in hada
jini da Suwaiba,kafi kowa sanin kin da nike
mata,zan iya daukar ranta ba don tsoron hukuma
ba. Kuma hr dny ta nade ba zan ta6a kaunarta
ba,kai ko fatan alheri ba zan ta6a mata ba. Ta
kalli Abba, Baka ta6a faranta min rai ba irin
yau,dama nasan cewa dole wata rana ka bayyana
dana in dai kai jinina ne,na gode Allah da yasa ka
zama mai kishina Kuma ka wanke dukkan
laifukan da ka min a baya da ka nusar da ni
Bashir na shirin jefa rayuwata a cikin garari,da ba
ka mishi mgn ba yaushe zan san yana shirin jefa
ni cikin bala'i. . Abn da Umma bata sani ba shi
ne,tuni Abba ya yi mutuwar tsaye,hnklshi ya
ninka na Bashir tashi,dn haka Bashir ya riga shi
fita daga dakin. Da kyar Abba ya dago ido ya kalli
Umma,ta ce Daina damun kanka shi ma din ko
ba don Allah ba zai dawo hanya,duku-dukayau
sati guda fa kenan da naje kauye na saida 'yar
Akuyata guda daya sannan na bada kaji 2 ga
Bokan kuka sbd a min akin da Ummi ba zata
samu miji ba. Sai kuma a ce ko satin bai rufe ba
dana na cikina ya zo ya ce yana sonta? Da sauri
Abba ya dafa kirji Umma Boka! Boka ki ka ce
Umma? Inna lillahi wa'inna ilaihin raji'un,Umma
kin san cewa zuwa gurin Boka shirka ne ga
Allah? kin san duk wanda ya mutu a shirka Allah
ya yi alkawarin kona shi a wuta?Umma kina cikin
hadari............ta kaste shi. Kai Abba!Ni ce nake
cikin hadari?Ni ce Allah zai kona a wuta? ya ce,
umma bana nufin haka, ina fada miki ne ki kiyaye
da zuwa gurin Bokaye makaryata,macuta 6arayin
Imanin Jama'a. Na ranste miki da girmn Allah
umma Bokaye 'yan wuta ne,matsawar ba su tuba
ba. Ta ce, Kai ni rufe min baki,da za ka ce karya
ne sau nawa suna min asirn kuma yana ci. Ba
gashi nan da ya min na kada Ummi ta riga Fati
samun miji baga Fatin ta riga samun ba? ummi
kuma ba ta d masoya. Abba ya ce, Umma kin ga
karya ko? wa ya fada miki Ummi bata d masoya?
ta ce, To me yasa ba wanda ya tsaya? Ya ce, Ni
dai Umma ki bar zancan nan a wurina, Bashie zai
bar Ummi ko yana so ko baya so,dn haka na
hada ki d girmn Allah kada ki koma gidan
mishieikin Bokan nan. Ta ce, Ba zan koma ba in
hr zaka raba Bashir da alakakai din yarnyar nan.
Ya ce Na miki Alkawari. ta ce, Shikenan. Ya fice
jiki babu karfi.URFIN CIKI book 2 part 8
ZURFIN CIKI book 2 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:18
Kasa shiga gidan su Umma ya yi,haka nan ya
manta sam da batun motar da yazo da ita a
kofar gidan Umma. Ko Bishira bata san cewa ya
shigo gidan ba,tana can jarabar kallonta na
tsiya,ya rufe gidan ya nufi dakinshi. Ranar mu2m
5 bacci sai dai 6arawo,Umman Bashir kwana tayi
saka da mugun zare. Umman Abban ma juyi
kurum take yi hr Alhj ya gaji ya ce,Yau dai sai
juyi ki ke yi. ta ce Na kasa bacci Alhj. Ya ce,
Tashi to kiyo alwala kizo ki kama sallah,in kina
da damuwa ne sai ki fada ma Allah. Umma bata
tsaya ba,ta tashi. shi ko Abba wani matsanancin
ciwon kai ne ya hana shi sallah. Ya dai yi
nasarar yin alwala da ya shiga daki sai jiri. Dole
ya kwanta rigingine tare da dafe kanshi da
hannuwa guda 2,sunan Allah yake ta kira dan
neman dauki. Ita ko Ummi dirshan ta zauna tana
kuka,hr sai da hawayenta suka kafe,idanunta
suka shiga zafi,kanta ya soma sarawa gefe daya.
Ita ma ringingine ta kwanta tare da lumshe
ido,Istigfari kurum take yi tare da hailala,shi ko
Bashir mafarkai ne suka hana shi bacci,dk
mafarkan na Ummi ne. Da safe da matsannancin
zazzabi ya farka,dn haka bai iya zuwa Masallaci
ba,da kyar ya yi alwala.yana idar da sallah ya
kundundune cikin bargo. Matsanancin ciwon kan
da Ummi ta tashi dashi ya firgita 'yan
gidan,Musamman Umma wadda ta same ta
kwance a tsakar daki da safe. Ganin fuskarta a
kumbure ya tsorata Umma,hr sai da ta kira
Alhj.Nan fa Alhj ya dauko wayarshi ya shiga kiran
Abba,kan cewa yazo ya kaita asibiti. Sai dai tayi
ringing ya kai sau 10 amma ba a daga ba. Alhj ya
ce Ina yaron nan ya shiga ne?kuma ga motarshu
a kofar gidan nan,na ganta da asubahi da na fita
Masallaci. Umma ta ce,Tao Allah yasa dai lfy.
Har karfe 8 Alhj na neman layin Abba shiru ba a
dauka ba,ga Ummi rike da kai tana ta salati
Umma ta ce,Alhj ko Bashir za ka sa ya duba shi?
Alhj ya koma daki ya dauki hula ya nufi gidan
Abba. Gidan a kulle ya same shi,dn haka ya dinga
bugawa.Abba na jiyowa amma ba zai iya tashi
ba,haka dk ringing din da wayarshi ke yi yana ji
ya kasa tashi ne. cikin bacci Bishira taji bugun
gida ya yi yawa,ta tashi ta bude. Da Alhj suka yi
ido 2,ya ce lfy ba ku tashi ba? Ta ce Mun tashi.
ya ce Ina maigidan naki? ta ce Ina ga ya fita,bari
in duba. Ta juya ta nufi ciki. Alhj ya cika da
mmk,ya za a ce wai mace bata san fitar mijinta
ba? Anya wannan matar tasan darajan mijin?
Tunaninshi ya katse lkcn da ta dawo tana cewa
Alhj yana kwance ba shi da lfy. Alhj ya bita yana
cewa Ba shi da lfy,amma ke ba ki sani ba?Wanna
wane irin zama ku ke yi ace kina matarsa amma
ba ki san cewa ya tashi ba lfy ba? Bishira ta ce
To ai shi ne bai kira ni ya fada min ba. Alhj ya ce,
Allah ya kyauta. ya nufi dakin. Abba na kwance
ya kundundune cikin bargo sai rawar sanyi yake
yi. Alhj ya yi Sallama ya shiga dakin ya rusuna ya
daga daidai fuskarshi ya janye bargon ya ce,
Abbana ba ka ji dadi ba? Abba ya bude
ido,idanunshi jajir,ya ce Abba kaina ne tamkar zai
6alle. Sai zazza6i tun daren jiya. Alhj ya ce,Ikon
Allah Yau kuma abn da na wayi gari da shi
kenan? Ummi ma na can kwance da ciwon kan,to
tashi. Shi yasa nake ta kiranka don ka kaita
asibiti amma da ka daga ba. Yanzu tashi in za ka
iya ka kira Ahmada abokinka sai ya kai ku
asibitin. Abba ya ce To Wayar Ahmada din a
kashe don haka sai Alhj ya ce "Af, na tuno da
Bashir,kintsa bari in je muzo naga mator can
kofar gidanmu ko?Abba ya lulubo makullin motar
yaba Alhj., Zani kawai Umma ta daura ma
Ummi,sai ta zura mata hijabi,suka shiga bayan
mota su 3 da Umma da Alhj,sukaje gidan Abba
suka dauko shi. Bishira taso zuwa amma suka ce
ba wuri ta bar shi kawai. Asibitin kudi ne kuma
likita guda ne ya duba su. Ummi dai hawan jini
ne don ita a ka fara dubawa. Gado likitan ya
bata,sannan Abba ya shiga shima likitan ya ce
jininsa ya hau,amma ba kamar nata ba. Nan ya
roki likitan cewa kada ya fada ma iyayensu abnda
ke damunsa,ya rubuta mishi magunguna kawai.
Likitan ya ce Ba komai. Amma me ya ke
damunku kai da sister dinka ciwonku iri daya
kuma ya kama ku a lkc daya? Abba ya ce Ba
komai lalura ce kawai a ka kaddara ta same su
lkc daya.Da Abba ya fito sai ya ce ma su Alhj
Zazza6i ne. sai dai shi kanshi ya ji mmkn
ciwonsu iri daya. Yana jingine da bango a dakin
da a ka ba Ummi gado,yayin da Bashir ya tsaya a
gabn gadon Umma tana zaune a kan kujera. Alhj
krm d Bbba suka shigo tare da Likitan ya kalli
Abba Yarona kana bukatar bacci ga. Abba ya ce
To yanzun zan tafi gida. Ya iso kan Ummi wadda
a ka daura ma ruwa,ya ce ku barta ta huta bata
bukatar hayaniya,don haka ku rage daga cikin
dakin. Alhji ya ce, To mun gode. Suka tafi suka
bar Umma. A mota Alhj ya ce da Abba,ka fada a
wurin ainkan? ya ce, Eh abokin aikina ya kira ni
kuma na fada masa. Alhj ya ce,To shi
kenan,yanzun sai muje can gidanmu zaka fi
hutawa... .Yanayin aikinku ne ba ka samun bacci
ko? eh kurum Abba ya ce,amma shi yasan
tunanin Ummi ne ya ke hana shi bacci da
matsalolin da yake hangowa. Yinin ranar yasha
bacci,sai kusan 4 ya tashi ya yi Sallah,ya ji dadin
jikinshi. Bishira tana gidan Umman Bashir wai ita
da tazo jinyar miji,tana bata lbrn wai Abba bai
fada mata ba shi da lfy ba,ya kira Alhj yazo yana
ta min surutai wai mijina ya fita ban sani
ba,meye- meye? Umman Bashir ta ce, Da Allah
kyale su,don wani sabon iskanci ma wai Bashi ne
ke son Ummi. Bishira ta mike zumbur tare da
cewa, Bashir fa ki ka ce Umma? Hu'um,lallai da
wani abu. Bashi da ya tsani Ummi shi ne zai ce
yana sonta? Umma ta ce, Sannu 'yar albarja,ashe
kin fahimta,? Tabbas nasan ke za ki fahimta,to in
gaya miki Bashir ko yau da safe fa sai da muka yi
ta dashi. Dubi yadda Bashir ke min biyayya amma
yau ina fada yana fada. wai hr da ce min shi bai
ga wani mugun halin Suwaiba da nike fada
ba,tana min alkairi amma ni kullum ina binta da
sharri. Kai dai jin wannan zancan ka san ba yin
Bashir ba ne,don haka na ce masa ba komai
nasan ba yin ka ba ne. Bishira ta ce,Tabdi,Umma
sai kin tashi tsaye. Ta ce ke dai bari ai ina cikin
wani hali shi kanshi miji naki sai na nema masa
taimako. Don wannan ciwon nashi ban yarda shi
ba, kuma lkcn daya. Fati ta shigo gidan da
sallama,ta shiga dakinsu ta canza kaya. Umma
ta ce,sai ina? ta ce Ya Abba ne ya ce in zo in
canza kaya zamu je asibiti wurin Ummi. Bishira
ta mike ya farka ne? Ta ce Eh hr ya yi wanka da
sallah Umma ta ce Bari in same shi bai gama jin
sauki ba zai tafi wurin wata can kema banza
mara kishi kin taho jiki Na 6ari,Fati ta ce,Umma
don Allah ki daina irin wannan abubuwan,wlh
Umman su Ummi bata yin haka Bishira ta fita
tana fadin Ai Ummi yanzun ita ce uwar Fati, don
bata jin mgnr kowa sai ta Ummi,tunda ta dawo
mkrnt. Sun samu Tsohuwa ma hr ta shiga
mota,shi kuma Abba yana jingine a jikin Motar
yana sanye da shadda (Sky blue) Rigar 'yar 3
Quarter kanshi da hula. Bishira ta ce,Babn Walid
hr ka tashi? ya dube ta,sannan ya kai idanunshi
kan fati Shiga muje. Bishira taja baya Ina ba in
da za ni. Ya kalleta ke Kuma ke da wa? Wa ya
fada miki da ke nake? yaja tsaki. Ta iso Ummar
tasu Abba ka hakura mana da wannan tafiyar. Ta
ce Naji sauki Umma. Tsohuwa ta ce, Mai sunan
Malam ka shiga don Allah mu tafi. cikin sauri ya
fada mota suka wuce. Yana yi wa Umman nuni
da Hannu wai yana zuwa. Tsohuwa ta
ce,Kinibibin banza ne da wannan matar taka mai
sunan Malam kana bukata kara aure,me a ke da
kazamar mace? Abba ya ce, Tsohuwa sha
kuruminki zan sake aure,ke ce ma za ki bani, Ta
ce, Ni a wa zan shiga maka ga . Bishira ta fita
tana fadin Ai Ummi yanzun ita ce uwar Fati, don
bata jin mgnr kowa sai ta Ummi,tunda ta dawo
mkrnt. Sun samu Tsohuwa ma hr ta shiga
mota,shi kuma Abba yana jingine a jikin Motar
yana sanye da shadda (Sky blue) Rigar 'yar 3
Quarter kanshi da hula. Bishira ta ce,Babn Walid
hr ka tashi? ya dube ta,sannan ya kai idanunshi
kan fati Shiga muje. Bishira taja baya Ina ba in
da za ni. Ya kalleta ke Kuma ke da wa? Wa ya
fada miki da ke nake? yaja tsaki. Ta iso Ummar
tasu Abba ka hakura mana da wannan tafiyar. Ta
ce Naji sauki Umma. Tsohuwa ta ce, Mai sunan
Malam ka shiga don Allah mu tafi. cikin sauri ya
fada mota suka wuce. Yana yi wa Umman nuni
da Hannu wai yana zuwa. Tsohuwa ta
ce,Kinibibin banza ne da wannan matar taka mai
sunan Malam kana bukata kara aure,me a ke da
kazamar mace? Abba ya ce, Tsohuwa sha
kuruminki zan sake aure,ke ce ma za ki bani, Ta
ce, Ni a wa zan shiga maka gaba a baka ku taru
kai da matarka ku halakata?Duk da Abba yana
jin jikinshi gim, sai da ya dar dara,sannan ya ce,
Sai ka ce ma su yankan kai? Tsohuwa kuma da
za ki ce na cika zcy yanzun ba ga mata nan ina
da ita ba tana kawo miki karan ina dukanta ne?
Tsohuwa ta ce Tabdi,ni yaushe ma wannan
guzumar matar taka zata zo guna da sunan kawo
min kara? Ban da ma haka ni bani shi da mara
kunya. Ya ce, sai Ummi ko? koda yake ita ai
takwararki ce shi yasa lkcn da tayi tata rashin
kunya ta zama 'yar lelanki. Tsohuwa ta ce ai
wannan ba kuciya ba ce? Yanzun ko kai ba ka fi
ta hankali ba.Abba da fati suka sa dry. suna isa
dakin suka samu Umma suna waya da Alhj,Ummi
kowa hr lkcn bacci take yi. Abba ya jingina da
bango yayin da Tsohuwa da Fati suka je suka
tsaya a gabn gadon. Sunyi Sallama da Alhj shi
ma ya kira ne ya ji ko Ummi ta farka. Ta ce
masa ba ta farka ba,kuma Likitan ya ce an fi son
tayi baccin. Nan suka gaisa tare da tambayar mai
jiki,Abba kallon Ummi yake,yau daya duk ta fyade
kmr ta yi sati,sonta da tsananin kaunarta ne
suka sake mamaye ko'ina na jikinshi. Ya kalli
Umma wadda ke tambayar nashi jikin, ya ce da
sauki. Sannan ya kalli Ummi tare da cewa Umma
wai dame Ummi ta fara? Umma ta ce kamar ya
ya? Ya ce mmkn ciwon Ummi nake,wai hawan
jini?Dama can bata da lfy ne? Tsohuwa ta amshe
da cewa, ko kai ai kasa mata hawan jini,irin
tsanar da ka mata Mai sunan Malam ai ta isa.
Abba ya ce Don Allah Tsohuwa ki daina mgnr
nan. Ya dubi Umma yana me kara maimaita
tambayarshi. Ta ce ko kusa ai kasan Ummi bata
cika laulayi ba ma,lalura ce dai yanzun bata ga
babba ba ta ga yaro,amma mafari daga yi mata
zancen aure shi kenan take ta kuka. Abba ya ce
to don Allah Umma ku barta da zancen nan,ina
krtn take so tayi kayanta,don gudun hawan jinin
nan kada yakw tashi akai-akai. Tsohuwa ta ce
Don kawai kada jinita ya hau sai a zura mata ido
kada tayi aure?ai ko lallai sai dai kada jininta ya
sauka. in ya hau,aure ya haifeta dole tayi shi,in a
kasarmu ce ta Zamfara wane ita. . Abba ya ce
Muje in kai ki gidan Tsohuwa. Ta ce ban tafiya,
sai naga dama Umma da fati suna ta musu dry.
Nan dai Abba ya fita yaje wurin likitan ya amshi
takardn maganin,dn da farko bai rubuta ba
magaungunan ba. Kwanan Ummi 3 a asibiti a ka
sallem ta. Abba ya kwashe su zuwa gida.
Saurayinta Sahabi zuwanshi 2, kuma sun je da
mahaifiyarshi. sai lkcn ne ma ta mishi kallon
tsaff,sam ita ba sonshi take yi ba,sai dai gara shi
da Bashir. Kuma ta lura Bashir din da gaske yake
yi. Domin kullum zai zo safe da yamma,haka nan
yakan dan tsaya hr yafi Abba wanda ke zuwa sau
daya hr tana cewa ina ma yadda Bashir ke nuna
tausayinshi a gare ta Abba ne. An shuri sati 2 da
sallamo ta kuma ta warke sarai,sai dai fa hr
yanzun Alhj yana nan kan bakanshi,ganin Bashir
na son takura mata sai ta daina fita. Abba ya
kira Basshir shagonshi wani yammaci,ya sake
fada masa ya rabu da Ummi sai dai yau da
lallashi yazo masa,. Ya ce Bashir ka ga
mahaifiyarmu bata sonka da ummi,dn haka ka
hkr ka nemi wata,na maka alwashin kashe ko
nawa ne dn yin hakan zai faranta ran Umma.
Bashir ya yi 'yar dry,sannan ya mike tsaye Ya
Abba kenan! kana tsammanin ni wawa ne?nasan
ba don Umma ka ke fafutukar in bar Ummi ba
kana yi ne don kana sonta. Gaban Abba ya
fadi,cikin saurin baki Abba ya ce,In ji wa ya fada
maka? Allah ya kiyaye. kai ka san Ummi kanwa
na dauke ta. Bashir ya kakki cikin idon
Abba,sannan ya ce,"Haba Malam,fadan da ka ke
da kalaman da ka ke furtawa suna nuna kishinka
ne karara. Dubi cikin idanunka,kishinUmmi ka ke
yi. don haka sai ka hkr ka bar min ita,domin ka
san ba wanda zai fi girgiza Umma tsakanina da
kai irin ka. Ya nuna Abba da yatsa, Za tafi bakin
ciki ka zama mijin Ummi fiye da ni. Abba ya daga
hannu ya falla mishi mari Bashir ya dafe wurin
sannan ya kalli sau 'yan shagon wadanda marin
ya janyo hankalinsu. Don farko ba su san abn da
a ke tattaunawa ba.Bashir ya ce, ka mare ni?
Abba ya ce, Zan kara maka,ko za ka rama ne?
Bashir ya ce, Ba zan rama ba,amma zan fada ma
su Alhj yau dinnan ina son Ummi. ya fita fuu.
Abba ya zauna ya rike kai yana huci. shi kam
Bashir ya kudurci niyyar fada wa iyayensu yau
dinnan. Abba ya kira wayar Umma ta daga suka
gaisa lkcn karfe 6 na yamma ya ce, Ummi fa? ta
ce Gata can kwance. Ya ce Ba dai jikin ba? ta ce
A" aikin karance-karancenta take. Ya ce, Ba ni ita
Umma. Umma ta kwala ma Ummi kira,ta mika
mata wayar tare da cewa "Yanyanki ne ke son
magana da ke. Yau ce rana ta farko da suka yi
waya a matsayin shi na Abba,ita kuma Ummi, in
an debe lkcn da suka yi waya a matsayin shi na
Abba ita kuma Suhailat. Tayi sallama cikin sanyi
murya can kasan makoshinta ya amsa tare da
runtse ido sakamakon tsigar jikinshi da ta tashi.
Ya ce "Ummi ta ce Na'am yaya. Ya ce "Kina son
Bashir? ta raunana murya. Yaya am sorry to say
bana son shin gsky. Ya ce To yau kam zai sanar
da su Alhj cewa yana sonki,in kina san kida
wanda ki ke so to ki gabatar da shi kafin shi ya
rigaki. Takaici ya kama ta, kamar ta ce, Ni kai na
ke so.......ya ce kina jina? ta ce,To Ya ce, kin san
in su Alhj suka ji ba ki da mafita,Ummi ta ce To
ni fa bani da wanda nake so shi ne ban san
yadda zan yi ba. Ya ce, shi kenan matsalarki ce.,
ya kashe wayar. Ummi tayi shiru tana tunanin
mafita,ko dai ta hkr ne ta aure Bashir din? kai a'a
to kuma gashi wanda take so ya ce matsalarta
ce. Can dai ta yanke yadda zata yi,don haka ta
kosa Alhj ya dawo. Tun kafin suje wurin cin abnci
ta same su a dakinshi su da Umma,ya yii wanka
yana kokarin fita sallar magriba. Ta ce Alhj dama
wanda ya ke zuwa gurina ne ya ce in fada muku
iyayenshi za su zo. Dadi ya kashe Alhj ya ce To
to dan nan unguwar ne? ta ce Eh ya ce To
madallah dama wannan yaron na sabon titi din
nan Suwaiba wanda kwanaki nake fada miki
nasan ubansa a kasuwarmu ya ke? Ta ce Naji
wanda ya soma zuwa wurin Ummi? ya ce Shifa,
Uban danai masa zancen naga dansa wurin 'yata
sai cewa ya yi auran gida za su yi masa,ko ni na
so hadin nan sai dai Allah bai so ba. Ya kalli
Ummi Yaushe za su zo? ta ce Ya dai ce in
tambaya ne. Alhj ya ce To Allah ya kawo su. Da
dare Sahabi yazo ta ce Sahabi an ce in maka
mgn ka turo ya ce Alhamdulillah, dama ina son in
miki mgn sai ina tsoron kada ki ce ya yi wuri don
haka gabe zan turo. Bashir yazo ya zauna gabn
Alhj suna cin abnci ya gaishe su. Suka amsa ya
yi shiru yana tunanin ta ina zai fara? Alhj Babba
ya ce ya ya Bashir akwai wata matsala ne?Ya ce
Am dama ina son in ce ni dai ina son Ummi ne.
Ummi kuma?Alhj karami?Ya ce Eh Alhj Babba ya
ce Ta amma ya aka yi kayi nauyin baki hr a ka
ba wani dama? Bashir ya ce Alhj Wanene? Alhj
karami ya ce Sai ka san shi? koda ba a tambaya
ba, ba zan ba da goyon baya a baka Ummii ba,
tashi ka bamu wuri. Abba ya ce, Bashir je ka ci
gaba da addu'a Allah yasa Ummi ta zam
rabinka,zan so haka dn na jima ina son zumuncin
nan. Iyayen Sahabi sun zo kuma an basu hr ma
an tsaida ranar daya fa ta Fati. Tun daga ranar
Ummi kullum cikin kuka take wanda iyayenta
suka kasa gane nufinta. Bashir bai daina cin
alwashin sai ya auri Ummi ba, dn haka kullum
cikin aiken kiranta yake. Ban da haka ma ya
maida hnkl kan sana'arshi tunda ubansa ya mishi
gorin wa zai ba shi mata ya ki tsayawa sana'a
nashi ganin in ya rike sana'a r za a ba shi. Abba
kuwa ya ji ya yi ma gidan wai don ya goge Ummi
a ranshi. Anya "ZURFIN CIKIN nan zai kai su? .
Sai mu hadu a littafi na Uku don jin yadda za a
kare. ZURFIN CIKI book 3 part 1
ZURFIN CIKI book 3 part 1
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:21
Na Halima Abdullahi K/Mashi 1... Abba ya fito
cikin suit bakake, yayi kyau matuka hatta
takalminshi sawu ciki baki ne, tamkar wani black
America. Igiyar wuyan ta zauna tsam, sai kamshi
yake. Dakin Bishira ya nufa ya daga labule, ta
dago ta kalle shi yayi matukar birgeta. Tana
alfahari da shi matsayin mijinta, ya ce "Kin
shirya?" ta ce,, "Zuwa ina?' Ya ce, "A'a, jiya fa na
sanar da ke ki shirya da wuri zamu je asibiti ki
gaida Ummi". Ta watso mishi wani kallo uku
saura kwata, tare da cewa "Ko garin nan ba a
sanyi ba zan fita gaida wata can Ummi ba bare
da sanyin nan." Ya ce, "Dalili ta mike tsaye "Ciwo
bai kai mutuwa ba, da mutuwa ya yi tazo ta min
gaisuwa?" Takaici ya turnu'ke Abba, da yake
sarkin dankara magana ne, sai ya ce "To ita ta
kashe shi da zata miki gaisuwa?" Ta kule da
bakin ciki ta zabga mishi harara "To ai kasan ni
na dora mata ciwon, don haka dole in je
gaisheta." Ahankali yake tukin, kira'ar Ahmed
Suleiman ce ke tashi wadda ya yi murya biyu
cikin sanyin murya. Wayarshi d ake gefe ta soma
ruri. Ya kali fuskar wayar, Hajiya Nina ce, don
haka ya ci gaba da tukinshi, kusan kira na bakwai
sannan ya daga. Ta ce, "Lokacinka ne za ka iya
yin duk yanda kaso, amma kafin kazo hannuna
wacce shawara ka yanke?" ya ce, "Ta me?" Ta
ce, "Au, ka manta kenan? To ba damuwa za ka
zo yau ne ko sai an dauko ka?" 2.... 'Yar dariya
ta kufce masa, "Ki sa a dauko ni sai ka ce wani
karamin yaro? In kin ci gaba da bibiyata za kiyi
nadamar hakan." Ta ce, "Ko kuma kai kayi ba, na
baka awa goma ka kawo kanka in ko ka 'ki, hum!
Za a kawo ka." Abba yaja tsaki "Yanda ki ke
zatona na wuce haka". Ta ce, "Idris Aminu Idris
raina ya biya da kai, kuma dole sai na cimma
hakan, jarumtarka din nan ta sake bige ni, kasan
dalilin da yasa na ce nan da awa goma? In ka
lissafa zai baka bakwai na yamma. Daidai lokacin
da ake watso mana labarai ina kwadayin ina tare
da kai, lokaci guda kuma ina kallonka cikin TV
kana feso turanci, kasan ina son muryarka ga shi
ka gwanance da iya tsara turanci, sai ka ce
yarenka. Kada in cika ka da surutu sai mun hadu
anjiman". Ta kashe wayarta. Abba yayi kokari ya
tsaida motar shi a gefen titi a hankali ya furta
"Allahumma ajir ni fi musibati..." ya kifa kansa a
jikin sitiyarin motar, yana tunanin wai shin ba za
ta sauya masa a halin da yake ciki ba? Wata
zuciyar ta ce in tasan kana cikin wani halin ko? A
haka ya isa gurin aikinsa, tunda suka shiga dakin
daukar labarai, abokanshi suka gane yana cikin
wani hali duk da bai kasance mai yawan magana
ba, amma yau ba kamar kullum ba. Salis ne ya
kasa hakuri, don haka bayan an gama daukar
labarai da kyar sun je su yi sallar Azahar suna
zaune wata Bafulatana da ke kawo musu fura ta
kawo. 3..... Dama shi Abba bai cika shan fura da
rana ba, yafi shanta da dare, don haka siyan
kurum yake yi. Bayan yaje gida sai yasha, amma
ranar ya ce mata ta bar shi kawai, ta jiya ma
tana nan bai sha ba. Da ta tafi Salis ya dube shi,
"Idris ba ka da lafiya ne?" Ya ce, "A'a me ka
gani?" Ya ce "Ba yanda ka saba ba, duk kwanakin
nan na lura kana cikin damuwa". Abba ya dube
shi amma ai kasan nayi rashin lafiya ko? Salis ya
ce dakata Idris kada kaga kamar na matsa maka
sai na ji cikinka, ko kusa ba haka ba ne. Ni
mutum ne mai saurin karantar duk dan Adam din
dana zauna kusa da shi na awa daya bare kai da
na zauna da kai tsawon lokaci, muna kuma ci
gaba da zama. Idris na fahimci kana da matukar
'ZURFIN CIKI' dalili kenan da yasa ban ta6a
damuwa da in tambaye ka matsalarka ba.
Sannan dalilin 'ZURFIN CIKIN' da naga kana da
shi ne yasa har kwanakin baya na kawo maka
matsalata da iyalina. Alhamdulillahi ka bani
shawara kuma nayi amfani da ita, kuma naga ci
gaba, matsalolina sun ragu". Abba yayi dan
murmushi. "Wai kana nufin saboda ina da
'ZURFIN CIKI' ne kaga ya dace ka sanar da ni
sirrinka?" Salis ya ce "Kusan haka ne, don me
Zurfin Ciki ya iya hadiye magana, sai dai a ganina
zurfin ciki wataran zai iya fadawa halaka, ko
wata gagarumar matsala". Abba ya dube shi,
"Wace irin halaka? Salis ya ce, "Me zurfin ciki sai
ciwon zuciya ya kama shi yana muku-muku da
matsalarshi, wani ma har ya mutu da ita ba
wanda ya sani. Amma in abu na cinka ka samu
wanda ka yarda da shi mai amana ka fada masa
zaka ji dan dadi". Abba ya ce, "To kai tunda baka
da zurfin ciki, kenan bai dace ka ji matsalar ba?"
4....Salis ya tuntsire da dariya, "Ta nan ka 6ullo?
Ai dama ka sani ba ina son yabon kaina ba ne,
a'a duk surutuna nasan abinda nake fadi". Abba
ya ce, "Salis na gode da kulawarka, matsalata ko
ka ji ta nasan shawarar da za ka bani bata wuce
ka ce in yi hakuri ba, ni kuma ba wannan ni ke
son ji ba. Salis ba komai nake yiwa 'ZURFIN CIKI'
ba, yawanci in ina da matsala nakan tunkari
Ummata ne kuma ta warware min komai. Saboda
na taso da wannan koyin da ta min, yanda na
shaku da ita ko su Alhajina ba mu shaku haka
ba". Salis ya ce, "To me ya hana ka fada mata
wannan karon?" Abba ya ce, "Ba zan iya ba, sai
dai in za ka samo min mafita ban da hakuri, to in
fada maka". Salis ya ce "In sha Allah ba za arasa
mafita ba". Nan Abba ya bai wa Salis labarinshi
da Ummi tun farko har zuwa yau. Salis ya
numfasa, sannan ya ce "Kaga illar 'ZURFIN CIKI'
ko? Ummin ma taka ce amma kana nema ka
rasata, ai ba mafitar da ta wuce ka samu
Ummarka ko Alhajinka ka fada musu muradinka".
Abba ya ce, "Tabbas haka ce mafita, sai dai idan
na aikata haka abu biyu za su faru, na farko na
zubar da mutuncin Alhajina, domin babu girma,
sun ba da 'ya ba tare da wani dalili ba ya ce ya
fasa. Sannan haramun ne neman aure cikin aure".
Salis ya ce, "Haka ne, to hakurin kawai zaka yi".
Abba ya ce "Ai mun yi ban da bada hakuri ko?"
Salis ya saki dariya, sannan ya ce "To kayi
addu'a". Abba ya mike tare da fadin "Ka tayani
da addu'a". Daga nan ya shiga dakin, Filin Don
Matasa na Hausa, don likkafar shirin tayi gaba
yanzu har na Hausa yana gabatarwa. Kullum
sake kar6uwa shirin yake a gurin Jama'a.
5......UMMI Tana kwance kan doguwar kujera,
yau kwana hudu kenan bata saka Abba a idonta
ba. Tamkar Umma ta san abinda ke ranta, sai ta
tsinkayi Umma na cewa "Yau kwana uku ne ko
hudu rabon Abba da gidan nan, sai dai ya kira mu
a waya. Alhaji dai ya ce, yana zuwa gunsa
kasuwa". Ummi ta ce, "Nima yanzun nake tunanin
haka". Ta miko ma Ummi wayarta da ke gefenta.
"Lalubo min shi in ji". Da ta soma /ringing/ sai ta
mika mata. Ya dauka suka gaisa ta ce "Abba ko
dai na maka laifi ne?" Ya ce, "Umma me a ka yi?"
Ta ce, "Tsaf, ka dauke min kafa, wanda kullum
komai saurinka sai ka biyo". Ya ce, "Ina nan
zuwa Ummata, kina raina duk inda nabi, harkoki
ne suka taru suka sa ni gaba". Ta ce, "Ni kuma
sai na ke ganin kamar don ba mu dauki
shawararka ba ne ta game da karatun Ummi shi
yasa ka". Ya ce, "Umma ba haka ba ne, zan shigo
da zarar na dawo". Ta ce. "To". Sam shi batun
shi yayi ba, sai dai baya son yazo ya ga Ummi
domin da ya ganta yake neman kwanciyar
hankalinsa ya rasa na tsawon lokaci. Amma
yanzun kalmar Salis ta karshe daya fafa masa da
za su rabu a gurin aiki ita yake tunawa. Dafa shi
ya yi tare da cewa "Miste Man shawara ta
karshe, ka nunawa kanwarka kana sonta a fili".
Ya ce "Tab, wannan shi ne me wahalar ai,
furtawa Ummi kalmar so. Zubar da kai kenan".
Ga shi ba sonsa take ba, duk yanda mace ke
girmamaka da zaran ka ce kana sonta shi kenan
ka zube a idonta. Musamman in kai ke sonta ita
ba ta sonka, wata ma har da rashin kunya zata
tsula maka, a fili ya ce, "Ina, ai ba zan ta6a gigin
bari ta san ina sonta ba". Daga kasan zuciyarshi
yaji an ce za ko ka sarata. Sai da ya yi sallar
Isha'i sannan ya yi wanka ya saka kananan kaya,
ya fito da nufin gidan su Ummarshi. Bishira ta
bishi da kallo, daga ganin fita zai yi ta fito da
saurinta tana cewa "Baban Walid! Baban Walid!!."
Ya tsaya, ta dube shi "Ina za ka?" Ya ce "Gidan
su Umma". Ta ce, "Ba wani gidansu Umma, kai
dai kurum tadi za ka je". 6.... Dariya ta su6uce
masa, sai da ya dara sannan ya ce "To in ma
tadin zan je ya za ki yi dani?". Ta ce, "Tab!, ai na
rantse maka kayi kadan. Kullum kuma ina 'kara
fada maka kai mijin mace daya ne rak!" Ya ce, "In
ji ki ko?" ta ce, "Eh." Ya ture ta gefe tare da cewa
"Da sauki tunda ba fadin Allah ba ne". Yayi
ficewarsa ya barta nan tana ta masifarta. Kan
dakalin kofar gidan, Ummi ce zaune da Sahabi
suna hira, duk da cewa Sahabin shi kadai ke ta
surutanshi Ummi na can duniyar tunanin abinda
zuciyarta ke so. Tun daga nesa ta shaki kamshin
turaransa, zaraf ta mike tsaye. So take ta kalli
fuskarshi amma ya dauke kanshi daga gare su.
Haka nan ya share sannun da zuwan da ta ke
mishi tare da shigewa cikin gida abinsa. Sahabi
ya ce, "Ya Abba na nan kuwa kwana biyu na rabu
da ganinshi?" Ta dauke kai sannan ta ce "Zan
tafi gida". Ya ce, "Haba Ummi, zuwana fa
kenan?" Ta dube shi. Ji take tamkar ta sheka
mishi mari, ta ce "To kaina ciwo yake yi, sannan
kuma ga Ya Abba yazo baya son ina dadewa a
waje". Ya ce, "To shi kenan sai gobe?" Ta ce,
"Don Allah kada kazo gobe, ka bari sai jibi". Ya
ce "Za ki azabtar da ni, ba zan iya kwana biyu
ban gan ki ba." Maimaikon taji dadin kalmar, sai
taji takaici ya mamayeta. A ranta ta ce,, "Tunda
ga gyatumarka ba". Ya ce, "In zo goben don
Allah?" Cikin muryar tausayi yake maganar, ta ce
"To shi kenan". Ta soma tafiya, ya dan tako ya
biyo ta tare da cewa "Sahibata mu kwana lafiya"
A kagare ta ce "Uhum". Ta samu Abba suna hira
da Umma, ta tura mishi kular birabisko tana
lallashinshi ya ci, tayi sallama Umma ce ta amsa.
Ta shiga idanunta kan Abba, ta zauna a kujerar
da ke fuskantarshi. Umma ta ce "Har Sahabin ya
tafi?" Ummi ta ce "Eh". Ta tsura ma Abba ido
tare da cewa, "Ina kwana Ya Abba?" Umma ta ce
"Wane irin kwana kuma Ummi da wannan daren?"
Ta ce, "Au, zan ce ina yini?" Ya amsa tare da
kallonta, "Lafiya". Ya mayar da dubanshi ga
Umma. "Umma Matar Ahmad fa ta haihu". Ta ce,
"Eh, ba jiya ka fada min ba a waya? Me ta samu
ne?" Ya ce, "Mace ta haifa, gashi ta sha wuya".
Umma ta ce, "Allah Sarki, to Allah ya raya mata,
zan je in dubota in mata barka gobe". Ya ce,
"Allah ya kai mu, ai Ahmad yayi dacen mata ba
kamar ni ba. A da Umma bana tunanin sake aure,
amma yanzun ina ganin dole sai nayi mata biyu".
Umma ta ce, "To ba dai yanzun ba duk nawa ka
ke kuma yaushe kayi wancan?" Ya ce, "Umma ke
dai ki min addu'a, ban samu irin macen data dace
da ni ba". Ta ce, "Ina maka addu'a, Allah ya
shirya maka matarka." Abba ya ce, "Ko ta shiryu
sai nayi aure insha Allahu". Ta ce, "Abba ni ko
gani nake ba ka san wadda za ka aure din ba
itama da nata kalar halin zata zo, sai su taru su
ruda ka". Ya kalli Ummi wadda ya lura da kallon
da ta tsare shi da shi kamar tana son jin abin da
yake fada ne. Ya maida idanunshi kan Umma.
"Na yarda da tarbiyar wannan yarinyar da nake
son aure yanzun, duk da yarinyar bata sona tana
girmamani". Umma ta ce, "Har ka samu kenan,
'yar gidan waye? Ummi kuwa tuni makoshinta ya
bushe, ta zaro idanu tana son ji wa kuma Abba
ke so? 7:....Ya kalli Ummi ganin yadda ta zaro
ido ya ce "Ke ni ke fadama wa ki ka zaro ido ki
ka tsare ni da su?" A hankali ta lumshe idanu
sannan ta maida kanta kan hannun kujera, ya
fuskanci Umma "Ba 'yar unguwar nan ba ce",
matsalar da yarinyar bata sona". Umma ta ce,
"To ka bar ta mana ka samu mai sonka? Yo in
haka ne ma ka ce gara matar taka ta gida, don
ita tana sonka". Yayi shiru zuwa can ya ce
"Umma in dai zan sameta zan aureta a haka".
Umma ta ce, "Kayi addu'a, ina ko mamakin mene
ne ta gani na 'ki a tare dakai Abba?" Ya ce cikin
'yar dariya "Umma ai ba dole ba ne sai ka birgke
kowa". Ummi ta mike jiri na dan dibanta ta shige
ciki. Zance ya dada watsewa, ta furta bayan ta
fada kan gado, ni ina son shi shi kuma ashe yana
can ya zarme da son wata. Ranar ta raba dare
tana kuka daga karshe ta soma ba kanta
shawarar ta samu Abba ta ce a fili dama
shisshigi ne irin na zuciyata Ya Abba ba irina
yake so ba. Shi kuwa zuciyarshi ta soma zargin
wani abu a kan Ummi, irin yanda ya ga tayi
kamar hankalinta ya tashi da batunsa. In ko haka
ne zai fi kowa murna, wata zuciyar ta ce ka sani
ko tsabar jin gulma ne yasa ta kafa maka ido duk
da haka yasha alwashin bibiyarta. Sun taso daga
sallar Juma'a shi da su Ahmad gidan budurwar
Tukur suka dosa, wayar Salis ta katse shi. Wani
aiki ne ya taso dole ya koma gurin aiki. Ya sauke
su a unguwar shi kuma ya nufi gurin aikinshi.
Karfe biyar ya baro gurin aikin da nufin yada
zango gidan Ummanshi. 8.... Yasan yau juma'a
duk yanda aka yi zai samu abinci na musamman,
don al'adarta ce girkinta na juma'a daban ne,
tana girmama ranar da abincin da ta san mijinta
zai yi farin ciki da shi. Haka nan ta kan yi
kwaliyyar musamman, shi yasa yake kara
kwadayin aura Ummi, ya san zata dauki wannan
tarbiyyar. Matasa guda uku a tsaye gefen titi cikin
fara'a da murna suka tsaida shi, ya saba kusan
kullum sai irin haka ta faru. Matasa kan tsaida
shi suna ma su nuna jin dadi da ganinshi, a gaisa
su wuce. Wasu kuma su amshi lambarshi har da
ma su son adireshinsa, yanzun ma sai ya tsaya
zai fito, tsum! Yaga sun bude motar sun shigo.
Biyu baya daya gaba, ya ba su hannu suka gaisa
su duka. Na gaban ya ce. "Mai matasa ai muna
jin dadin taimakon da ka ke mana. Ya kamata a
baka Sardaunan Matasa". Daya daga baya ya ce
"Sarkin Matasa gaba daya zamu ba shi, don yana
kokarin gurin binciko matsalolin matasa". Abba
ya yi murmushi tare da cewa, "Na Gode". Dayan
da bai yi magana ba sai ya ce "Amma mai
Matasa ka san da wannan matsalar?" Abba ya
waiwaya da nufin jin karin bayani, sai ko ya fesa
mishi wata farar hoda a fuska. Take nan atishawa
da tari suka tirnike shi. Ya soma mutsuka
idanunshi bakinshi na furta "Inna lillahi wa'inna
ilaihir raji'un". Kafin 'yar sakwanni kanshi yayi
din, kuma ya fita daga hayyacinsa. Suka tuka
motar suka tashi dashi. * Farkawa ya yi tamkar
wanda ya tashi daga bacci, a hankali ya bude ido
tangaran a kan silin, irin na masu hali. Kwan
lantarki irin na kasaitattun gidaje ya daki
hancinshi. Nan take ya shiga tunanin me ya kawo
shi nan? ba 6ata lokaci ya tuna duk abinda ya
faru, da sauri ya tashi zaune yana fadin "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raji'un". Ya ci gaba da kallon
dakin, cikin tangameme ne yana dauke da
tafkeken gado da sauran saitin shi. Sai kafet din
tsakar daki da kayan kallo, ga kuma kofofi guda
biyu. Ya tambayi kanshi da cewa me ya kawo ni
nan? me matasan suke nema a gurina?" Take
muryar Hajiya Nina ta fado masa, inda take cewa
"Za ka zo yau din ne ko sai an dauko ka?" ya
girgiza kai tare da cewa, Lallai wannan makirar
matar ce tasa aka mi shi haka". 9... Nan take ya
soma karanta addu'ar neman tsari. Daya daga
cikin kofofin ta bude, ya kure idonsa gurin da
kallo, matar ta shigo sanye cikin doguwar riga
baka mai ma6allai a gaba. Fara ce kyakkyawa,
shekarunta suna tsakanin Talatin da takwas zuwa
arba'in da biyar, domin kyawun nata sun 6oye
shekarunta, ta baza gashi a kafada. Tsura mata
ido yayi yana son tuna inda ya ta6a ganinta,
domin tabbas yasan fuskar. Muryarta ce ta katse
shi,"Dama nasan zuwa yanzun ka farko, kuma ka
gama nazarin yanda aka yi kazo nan. Kila ma
tunda kana da kamannin ma su basira ka hararo
wadda tasa a ka dauko ka". Ya ce, "Kwarai
kuwa". Lokacin ne ya tuno inda ya santa, wato
Hajiya Zabba'u ce matar shaharraran Attajirin nan
Alhaji Uzairu wadda a ke nuno ta a TV da Jaridu
tana taimakon talakawa da Marayu. Wadda ake
labarin tsoron Allahnta da gudun duniyarta,
wadda ta gina Masallatai da Makarantun Addini
ma su dama. Ya girgiza kai cikin matukar
mamaki, ta ce "Ka gane ni kenan?" Ya ce (Cikin
karfin hali) "Lallai mutum mugun ice. Wannan shi
ne Allah a baki shaidan a zuci". Ta ce "Kai ne na
biyu da ka furta wannan kalmar, sai dai bana fata
ka zama na biyu da ya bakunci inda na farkon ya
tafi. 10.... Ta tako a hankali ta dunfaro shi, ya
matsa baya cikin zuciyarshi yana korar shaidan,
'yar dariya tayi. "Nutsu Idris ko ince Abba. Ba
fyade zan maka ba". Ya dubeta da sauri, "Eh haka
nace, in na son hakan zan maka, amma ba
hakanne burina ba". Ta zauna bakin gadon, "Ka
zo mu daidaita, in kana tsoron ciwo zan baka
makari, sai dai ina so ka sani bana dauke da
wata cuta". Ya ce, "Karya ki ke, kina dauke da
mummunar cuta". Ta ce "In ka tashi daga dan
jarida ne, ka koma Likita zan baka dama ka
gwada ni". "Ya ce ba ki bukatar gwaji don ga
ciwonki nan a fili ciwon zuciya". Ta ce, "Sam ba
ni da ciwon a zuciyata, to in ma ina da shi me zai
dameka tunda ba dauka za ka yi ba". Ya sake ja
da baya ya ce, "Zuciyarki ta kamu da ciwon zina.
Ta yi duhu dumdum! har bata iya ganin
gaskiya...". "Ta daga mishi hannu, "Dakata min,
ban tambayeka labarin wa'azi ba, domin in shi
nake son ji ina da kaset-kaset kala-kala zan saka
na ji". Ta mike zuwa wata durowa ta bude, dauri
uku ta dauko ta aje gaban madubi na 'yan dari
biyar-biyar sababbi dal! Ta ce, "Wannan za ka
sha mai ne sannan kasa kati, kuma in ka kwantar
da hankalinka zan canja maka mota, zaka je
Makka. 11.... Sannan idan naga kana bin
umarnina zaka yi suna a aikin jarida fiye da duk
wani dan jarida da ka sani a kasar nan. Kai zaka
taka duk wani matsayi da dan jarida ke takawa".
ta sake nufoshi da tausasa murya. "In kabi yanda
nace ba kai ba sake kwana a talauci..." Ya
katseta da fadin, "In naki fa?" Ta hade rai tare da
zuba mishi ido, "Shima kallonta yake, sai a
lokacin ya ga tsufanta ya bayyana. Ta juya mishi
baya tana 'yar tafiya, sannan ta ce "Am sorry to
say". Ta juya ta dube shi "Za ka mutu". Gabanshi
ya fadi, amma sai ya yi karfin hali ya ce "In na
mutu sai me? Dama can mutuwa zan yi ko ba ki
kashe ni ba. Kuma ni na san ba zan wuce iyakar
ajalina ba, murnata daya zaki sauke min nauyin
zunubaina". Ta matso kusa da shi "Ka san
matasa nawa ke shiga malamai kawai don su yi
hulda da ni? In ka dade muna hulda shi ne muyi
wata biyar, sau daya na rike saurayi har tsawon
shekara daya don yana da hankali". A zuciyar
Abba ya ce "In fa na daka ta matar nan zan mutu
ban auri Ummi ba. Sannan ba Allah a ranta bare
taji nasiha, yanzu bari yabi ta hikima". Ya ce,
"Saboda me suke shiga malamai don suyi hulda
da ke? Sannan daman duniya tasan ki kina
haka?" Ta ce, "Ko kusa, sun sanni a Hajiya Nina
sai in mutum ya zo ya ganni, in ya sanni to in bai
sanni ba duk daya. Sudai burinsu kudin". 12......
Abba ya ce, "Nikam ba zan iya wannan huldar
ba". Ta ce, "Kada ka bari taurin kai yaja ka
nadama irin wadda waninka ya ta6a yi. In kana
da sha'awa in baka labarinsa don ya zamar maka
Ishara". Shirun da Abba ya yi shi yasa ta ci gaba,
domin alamar yana son ji kenan. Da a ce zan fadi
sunanshi zaka sanshi, wani malami daga cikin
Malaman garin nan, haka nan yanda na ganka a
TV kana labarai na kwadaita da kai, shima haka
na ganshi a TV yana wa'azi kuma zuciyata ta
yaba. Na neme shi ya zo kuma shi na fada masa
ni ce Zabba'u ban 6oye masa ba. Sai dai nuna
masa nai aikin rabon zakka zan ba shi, ma'ana
kudi ne masu yawa ban san yadda zan fidda
musu zakka ba. Da jin haka sai ya taho, nan
dakin na kawo shi, sannan na fito mishi da
maitata fir! ya shiga jawo min ayoyi na numa
masa cewa ba zan hakura da abinda zuciyata ke
so ba. Don ban ta6a 'kin cika mata burinta ba,
shi kuma ya fir ya ki ya nemi ya gudu na bashi
guri ya dan ci abinci na nuna masa mishi kuskure
ne ya ce zai gudu. Don gidan nan duk masu tsaro
ne har da ma layin gaba daya. Da sauri za a
kama ka a matsayin dan fashi, sannan in ka yi
kokarin shigo da jami'an tsaro lamarin to, zaka
kwana ciki. Domin duk a hannunmu suke, amma
Ustazun ya ki shan ko ruwan gidan nan, gashi ya
min shame-shame zai mutu don yunwa. Ba arziki
na saka aka fita da shi kuma aka kai shi gidan
karuwai a ka ba su na sakar musu kudi suka sa
shi a daki. Nasa Malamina ya karasa min shi,
sannan na sa karuwan suka kira 'yan sanda kan
cewa ga wani ya zo gurinsu amma kwananshi ya
kare a nan. To dama iyalanshi suna ta nemanshi
an sace shi nan fa suka dauke shi, na san yanzu
ka gane kowane Malami ne tunda labarin ya yadu
a cikin garin nan da ma wajen shi". CIKI book 3 part 3
ZURFIN CIKI book 3 part 3
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:24
Abba ya ce "Lokacin da muke cin abinci tare,
Umma ta ce, lokacin da ka ke bata dai, Abba shi
ne ya fara baki abinci a baki. 20..... Watanki
hudu, da kin hango shi za ki soma daga hannu,
Abba ya ce Umma na fa goya Ummi a bayana.
Lah, goyo? In ji Ummi. Umma ta ce, "Goyo sosai
kuwa, suka sa dariya, Umma ta ce, "Shi yasa in
naga yanda ku ke rashin shiri a tsakaninku
yanzun sai in ta mamaki. Don tun ba ki fita a
tsumma ba Abba ke rainonki, tun ba ki fi wata
hudu ba, ki ka tantance muryarshi. Haka nan
sunan shi ne ki ka fara iya fadi a duniya. Abba
yana goya ki kin sha yi masa fitsari da kashi da
tumbudi, wanka da wanki duk Abba ya miki
Ummi. In ko na aike shi ko zai tafi Makaranta to
sai da wayo da dabara. Ke har an kai lokacin da
kin yarda in tafi unguwa in bar ki gurin Abba, in
ya dawo Makaranta tun daga soro zai soma miki
wakar da yake miki. Ummin Abba da Alhaji,
Ummin Umma da Tsohuwa, da kin ji haka za ki
dibi rarrafe ki nufi gurinshi, kuma duk kudin break
dinsa zai debo miki tsaraba. Umma na bada tarihi
Ummi ta zuba ma Abba idanu cikin wani irin
yanayi da ba zata iya tantance shi ba, shi kuwa
lokacin ne ya dawo mishi, ido ya yi dan murmushi
tare da cewa "Allah sarki da na tuna ranar da aka
yaye Ummi, Umma tayi dariya ta ce, "Ranar tare
kuka kwana kuna min kuka wai in yi hakuri in
baki nono". Wata sabuwar kauna da so Ummi taji
ya rufe ta na Abba, har kwalla ta cika mata ido,
ta ce "To Ya Abba me yasa ka daina sona?" Ya
ce, "Ummi ban daina sonki ba, kanwata kiriniyarki
ce ta hada mu fada dama, yanzun kuma kin
daina ko?" Ta daga kai alamar eh, Umma ta ce
"Labarin yanda ku ka kaunaci juna mai tsawo ne,
kusan kullum sai mun yi labarin da Alhaji". Ummi
ta kalli Umma shi ne ba ku ta6a bani labari ba?
Ta ce ba gashi kin ji ba, Tsohuwa tayi sallama,
suka amsa. Ta ce, "Kai me sunan Malam me ya
faru da kai? Nan ya warware musu komai, suka
yi ta al'jabi. Umma ta ce "Ni 'yasu, yanzu haka
mata suka maida aure ba a bakin komai ba?"
Kuma ka ce matar aure ce, Abba ya ce dama z
aki san kowa ce ce za ki ji mamaki fiye da haka,
don dai kurum na rufa mata asiri ne in taci gaba
to can gabanta hadu da mai tona ta. Su Alhaji
suka shigo da sallama, nan suma aka ci gaba da
jajanta batun, Alhaji Babba ya ce, "Babana ina ga
dai rahoto za mu kai gurin 'yansanda". Abba ya
ce, "Alhaji tuni manyan shuwagabannin gurin
aikinmu suka shigo da hukuma, in Allah ya yarda
dolenta ta bar ni, Alhaji Karami ya ce, "Addu'a dai
ita ce z aka kara rikewa, Allah ya ja mana gaba".
Suka ce Amin. 21... Ranar su Alhaji a tsakar gida
suka ci abinci anata hira, Ummi dai kallonsu take
yi amma zuciyarta na can duniyar tunanin labarin
da aka bata. Ashe har yanzu Ya Abba na sonta,
Allah ya sa haka har yanzun. Sai kusan sha daya
Alhaji ya matsa wa Abba ya tafi gida. Abba ya ji
dadin hirar musamman in ya waiwaya idanunshi
suna kallon Ummi ta mai 'kuri da ido, Umma ta
ce, "Ka gaida 'yan gidan". Ya ce "Za su ji, har ya
kai soro Ummi ta ce Alhaji da an raka shi kada a
kara sace shi fa, duk suka sa dariya". Abba ya
dawo yana cewa, "Umma kun rage man fetur
kuwa? Na san yanzu na gidan ya kare tunda ba
shi da yawa, bana son kuma sai na sake daukar
galan na fita". Alhaji ya ce, "Na shigo da mai
dazu duba nan soro na aje shi, Ummi ta sake
cewa Ya Abba ka ce Alhaji su rakaka gida, yayi
'yar dariya kada ki damu Ummi, ina yin addu'a
Allah zai kare ni. Yau kam Ummi ta dade bata ga
daren da farin ciki ya hanata bacci ba irin yau.
Haka nan shima Abba zuciyarshi fes Ummi ta
fahimci dama can santa yake, da alamu ba zai
sha wuya gurin shawo kanta kuma cikin
karammin lokaci. 11 HAJIYA NINA Ta kalli
matashin, sannan ta kalli jaridar hannunshi ta ce,
"Me ya'ki kai fa ba jakadan azriki ba ne, a duk
lokacin da na ganka sai gabana ya fadi,
musamman in kazo min da jarida". Yayi 'yar
dariya "Hajjaju makatu sallah Makka Sallah
Madina, ni dai kin san ba ilimin nan gare ni ba, in
da z aki tsare ni in karanta ban iya ba, ni dan
sako ne. Muftahu ne mai siyo duk wata jarida da
ya ga ta shafe ki, ta amsa ta bude cikin azama,
hoton Abba ta gani gabanta ya fadi, ta ce dan
jarida shege ne, yaron nan tallatani zai yi? Ta
soma karanta labarin zufa tana karyo mata, har
ta gama. Kafa kurum take karkadawa tana
tunanin abin yi, murna daya tayi da bai tona ma
duniya cewa ita ce Hajiya Zabba'u ba. Amma duk
da haka ba zata bar shi ba, koda yake ta ga
manyan 'yan jarida na kokarin shigowa ciki, ta
kai hannu ta dauko daya daga cikin wayoyinta ta
danna kira. 22.... Jim kadan aka daga ta ce,
"Karamakallu barka da warhaka, ya amsa da
Ranki ya dade lafiya dai ko?" Ta ce, "Malam ba
lau ba, kana ji? Ina yaron da nake baka labari
dan jarida? Ya ce, Naji. Ta ci gaba, Yaron nan
kaga yanda ya yayata ni a duniya? Sai na koya
mishi hankali, da ni zai ja?" Malam ya ce, ya ma
ki ka ce sunanshi? Ta ce Idris, ya ce To zan kira
ki anjima, kada ki dauki wani mataki tukunna sai
na gama bincikena duka. Ta ce an gama. Sintiri
tayi ta yi tsakanin dargajejen falonta zuwa
barandar shakatawarta, lokacin da taji rurin
wayarta tayi tsammanin Malamin ne, sai data
duba taga Aminiyarta ce Haiya Attine. Ta daga da
cewa, "Hello Attinen bishasha ya aka yi ne? Ta
ce, Zabba haka kwallon dan iskan yaron nan zai
miki? Ta ce, Hum! Ke dai bari Aminiyata, yanzun
nan na gama karantawa a jarida ban ma san
hukuncin da zan yanke ma yaron nan ba. Attine
ta ce, sa su Adda su tura shi Jami'ar mi'kakku
mana. Hajiya Zabba'u ta ce, "Ai kuma na riga na
kira Teacher ya ce in saurare shi". Attine ta ce,
"Eh to kin yi dabara ma, kya iya sa Teacher din
ma ya tura ba tare da an zargi kowa ba". Hajiya
Zabba ta ce, "Kin san jami'an tsaro suna cikin
maganar tsundum! Don haka dole in yi taka tsan-
tsan, guri daya yaron ya yi min kyan kai, da bai
fada ma duniya Zabba'u ita ce Nina ba." Attine ta
ce "Eh yayi wannan adalcin, yanzun bari muji ta
bakin Teacher". 23.... Shikam Malamin duk
lamura sun kasa masa daidai, sai kusan karfe uku
saura, sannan ya kira ta da rawar jiki ta dauka.
Ya ce, Hajiya? Ta ce, Na'am ya ce ki tattara ta
batun yaron nan ki watsar domin yanda naga
al'amuran to fa in mun matsa ba zamu kai labari
ba. Haka nan allura zata tono garma game da
damuwar malamin nan, sannan asirinki zai tonu a
gurin maigidanki. Tsaki taja don maigidana
Malam nasha fada maka ban 'ki ya ji ba, tunda
shi ne sanadin komai, tafiya kullum daga waccan
kasa zuwa waccan, kullum cikin bakin yawon
neman kudi. Sam baya biya mini bukatata ba
dole in nema ba? Yarana biyu cal a duniya duk
sun yi aure su ne kawai zan ji kunyar su sani,
don haka in zai yiwu ka sa Aljanu su tsotse min
jinin matsiyaci. Malam ya ce, "Ba zai yiwu ba, ina
ce tun lokacin da ki ka zo min da batunshi kafin
ma ki sa a dauko miki shi sai d ana fada miki
yaron yana da kariyar da take kare shi daga
Ubangiji. Yaron ma'abocin kyautata Sallah ne,
tare da yin Azkar, yana da makarin da Aljanu ba
za su iya tunkararshi ba... Dakata Malam, ta
katse si duk addu'arshi ya kai Malam ne, kuma
muka ci nasara a kanshi? Ya ce kila shi Malamin
kwananshi ya kare dama ke ce sila shi ko
wannan da sauran shan ruwansa. Ta ce, "Kai ne
sila dai daina jingina min mutuwarsa, ya ce ko
kin ki dole ki dauki nauyin zunubin mutuwar
Malam". Yanzun kuma ta wannan sai ki wamu
wani don ni ba zan matsa lamba a kan al'amarin
da Aljanu suka nuna tsoronsu ba, tsaki taja
sannan ta kashe wayar. Har gari ya waye ba ta
daina tunani ba, haka nan bata yanke matsaya
ba. Gidan Aminiyarta Attine bishsha ta nufa, sun
tattauna sosai sannan suka bukaci sukai koken
ga wasu Malaman. Sai dai guri uku zancan iri
daya ne, wato ta bar shi kawai, yayin da guri
biyu suma zancan su iri daya ne, sun ce zata ci
sa'ar kashe shi amma asirinta zai tonu zata rasa
ran 'yarta daya kuma zai yiwu tayi zaman Jarun.
Ta ce, "Wannan akwai shegen yaro, shi yasa da
na ce zan sa Aljanu su dauko shi ya ce min yana
da makaminsu? Daga karshe ta ce na bar shi
mara rabo". Attine ta ce da dai yafi shi yasa tun
farko in naga wanda zai ja min aji ni ke watsi da
shi in nemi wani. Kai jama'a sai kace aikin Allah
menene amfanin zinar ma da har ake shiga
Bokaye dominta? Allah ka tsare mana Imaninmu,
amin. 12 24.... Ummi tana zaune zata wanke 'yan
kayanta na ciki, ta zubo omon cikin ruwa tana
faman karkadawa, tana 'yar wakar da ke sata
nishadi. Sam ba ta ji sallamar Abba ba, yana
jingine yana kallonta, tana fadin, Akwai wanda na
ke so, amma kunya naso, ya wanke ni da soso
dan Yayana. Ta tsoma sikyat dinta da fant da
'yan bireziyoyinta farare ne ta soma cudawa tana
maimaita wannan baitin wakar, shi kadai ta iya.
A jikinta taji cewa ana kallonta, ta waiwaya da
sauri, idanunta tsaf cikin na Abba, sai ta samu
kanta da sunne fuskarta cikin cinyoyi. Ya ce,
"Kunyata ki ke ji ne Ummi?" Ta dago da dan
murmushi, "Sannu da zuwa Yaya Abba". Ya ce,
"Yauwa dama kin iya waka?" Tsohuwa daga daki
ta cafke, tun da ta samu wannan wakar sai ka ce
me hadda, kullum Abba ya isa kofar Tsohuwa
suka gaisa. Ya dawo kofar Umma yana tabayarta.
Ummi ta ce, "Taje Hotoro sunan kanwar Umman
Bashir da ta haihu, ya manta fa matarshi ma ta
na can, Tsohuwa ta fito tana cewa, ai Ummanku
ta juri wulakanci. Waccan haihuwar da Zilai
kanwar Sahura tayi tas a ka zageta a gidan
sunan, amma yau ta koma. Abba ya ce, "Ummata
tayi nisa a zumunci, Allah zai bata lada" Tsohuwa
ta ce, "Ai sai tayi ta yi, in dai shisshigi ne ba
kwarjini". Ta dubi Ummi, wai wankin me ki ke yi
ne har yanzun ina nan ina jira ki yanke min
farce". Ta hango kayan Ummi na daura ta ce,
"Kai ni wannan zamani naku yana bani mamaki,
ace 'yammata suna saka rigar mama? Kunya ta
cika Ummi saboda Abba da ke gurin. 25.... Abba
ya ce, "Kin ji tsohuwa, lokacinku da namu daya
ne? Ku lokacinku kai bai waye ba, ta aje 'yar
kujerarta ta zauna. Tir da wannan wayewar taku
ta zamani, yarinya ta fadi a gaban iyayenta har
ta shiga sa tara mama bata kama dakin kanta
ba? Mu kuwa da wata ma ba sai tayi haihuwa
goma ba ma ta sa ran mama ba. Abba dariya ta
ishe shi yayin da Ummi kunya ta hanata shanya
kayan ta matse ta aje. Abba ya ce, "Yanzun
Ummi har wani girma tayi, shekara sha takwas
kurum ce fa, bata ma cika ba. Ta ce "Mu lokacin
sha biyu sha daya yarinya ta kama dakinta.
Ummi ta zanua ta soma yanke ma Tsohuwa
'kumba, tana cewa To dai nima na kusan tafiya in
huta gorinki. Abba ya matso, "Ummi don Allah in
tambaye ki mana? Ta tsaya da yanke 'kunbar
tana kallonshi, ya maimaita tambayar da gira ta
bashi amsa ya ce kina ko son wannan Sahabin?
Ta maida kanta ga yankan 'kunbar duk jikinta da
hannunta suna dan rawa, a zuciyarta ta ce, "Kai
ne kadai zuciyata ke so, amma a fili sai ta ce,
Um, ya ce Yaya hausar um?" Tayi kokarin
saisaita hawayenta, sannan ta ce Eh, jikinshi yayi
lakwas, Tsohuwa ta ce, "Zancan banza, in bata
sonshi zaka daga batun auren ne?" Ai ko tana so
ko bata so tunda ta kawo shi zance ya kare, ka ji
mai sunan Malam da zancen wofi. Ya ce,
"Tsohuwa ni fa ba wani abu na ce ba, kin ga ma
dai bari in tafi abina. Ummi ina Azimi yau, zan zo
in yi buda baki anjima. Ta ce, "To." Tsohuwa ta
ce, "Wai kai ba ka da gidan mata ne kullum kana
la'ke a nan? Tsoron ta ka ke ji ne da zaka kasa
lankwasata ta yi maka girki?" Ya ce, "Na nan
nake son ci Ummi kam tana can duniyar tunani
tana tambayar kanta shi kenan ta rasa Abbanta?
Son da da yayi mata da ca dama ba na aure ba
ne, na 'yan uwantaka ne? Kai ko dai ta fito ta ce
Abba take so, gaskiya ita fa Sahabi ba sonsa
take ba. Kusan wata daya kenan rabon da ya
samu biyan bukata daga matarsa, don gaskiya
baya iya zuwa dakinta saboda kazanta da kuma
datti da wari da zarni da 'karni ba za su bar shi
ya samu cikakkiyar biyan bukata ba. In ta zo
dakinshi ma jikinta tashi yake, a haka yake
maneji, amma in iskancinta ya motsa har yanga
take mishi (Mtsw! Allah rabamu da kazaman
Mata). Shi kuma yana da wani hali, duk yanda ya
matsu in har ya nuna mata bukatarshi ta 'ki sai
ya hakura ya roki Allah ya shiryeta, shi kuma ya
kare shi da fadawa sharrin zina. 26.... Bai zaginta
ko ya ce zai nuna mata karfin shi, ko ya ce zai
tsaya rokonta, shi yasa yake yawan yin Azumi.
Ummi ta ce, "Umma ki kawo kudi in siyo kwai in
soya ma Yaya Abba doya, ya ce zai zo shan
ruwa. Ta ce, "To je ki kasan filo ki dauko, amma
fa sai kin yi azama don an kusa kiran sallah. Ta
ce, "Ai na dafa ruwan shayi, sannan na masa
kunun tsamiya, doyar ce kawai, ta ce "To sai da
ta gama komai sannan tayi wanka tayi sallah.
Riga da siket na leshi tasa fari tas, bata damu da
yin fenti da dare ba amma yau tayi ta feshe
jikinta da turare wanda shi ne ya sai mata.
Sallamarshi ta jiyo suna gaisawa da su Umma, ta
fito ya bita da kallo, kin yi kyau kanwata, Umma
ta ce yau za ku hoton ne? Ta ce kila, Abba ya ce
shi yasa ki ka yi kwalliya haka? Ba ta ce komai
ba sai dai ranta bai so ma maganar da Umman
tayi ba. Suna hira da Umma ta shirya misi abinci
ta koma kan kujera ta dauki littafi lokaci-lokaci
idanunta suna kan Abba. 13 Suna hira da Umma
ta shirya mishi abinci ta koma kan kujera ta dauki
littafi, lokaci-lokaci idanunta suna kan Abba. Shi
ma haka ya ce wai ni littafin nan da ku ke nacin
karatunshi dame kuke karuwa? Umma ta ce, Ai fa
gara ka tambaye ta, don ban ga abinda ta ba
muhimmanci ba irin wannan littafin. Ummi ta cem
ina karuwa sosai Umma suna koya mana tarbiyya
yyanda zamu tafi da rayuwarmu cikin tsarin
Addini da al'adarmu. Abba ya ce amma basa
koya tsafta da biyayya, Ummi ta ce suna yi sosai
ma, ya ce Umma ni naga jarabar karatu irin na
Bishira amma kullum mugayen halayenta bayyana
suke yi. Ummi ta ce ni ko har addu'o'i zuwa girki
kala- kala ina koyo, Umma ba rannan nayi
dafadukan kwakwa ku ka ce ya yi dai ba?" Ta ce,
"To ki dai dinga daukan na kwarai kina yarda na
banza, Abba ya ce in haka ne d agaske zan samu
lokaci in zo ki karanta min in ji, ta ce "To." 27.....
Umma ta yi 'yar dariya ta ce, "Sai ka ce ba ka da
aikin yi? Ya ce, "Allah Umma da gaske nake yi
don in ji wacce irin koyarwa suke yi, marubutan
ko ko sai shirme?" Kiran sallar Isha'i ne yasa
Abba mikewa, ita kuma Umma ta tafi kicin don
shiryawa su Alhaji Abinci. Ummi kam sun bar ta
cikin takaicin tafiyar Abba don dai bata gundura
da shi. * Alhaji Ya kalli Umma, wai yau bikin
yaran nan saura wata nawa? Ta ce, "Wata ko
kwana dai?" Yau saura kwana talatin da shida,
ban ga kana motsi ba? Alhaji bikin nan zai
mamaye mu, ya ce "Yanzun ya za a yi da batun
kaya?" Ta ce, "Ni da cewa nayi ga Abba sai yaje
ko kuje ku za6a musu kaya masu kyau a siya,
kada a ba kafintoci in ba a yi sa'a ba har lokacin
yayi ba a gama ba". Ya ce, "To zan sa shi ya tafi
da su kawai su za6a". Ta ce, "Sai kayan girki na
dai sayi tukwane da risho, sai kuloli". Ya ce, "Duk
da haka uwata zan sa ta za6i wasu kayan."
Umma tayi dariya tare da cewa, "Allah ya kara
budi, nan dai suka yi ta lissafin kudi. Da safe
Alhaji ya kira Abba a waya ya sanar da shi cewa
ya dauki su Ummi suje su za6i irin kayan da suke
so, duk da cewa zancan ya doki zuciyarshi amma
ya ce "To." insha Allah zamu je, suka yi sallama.
Sam baya son ya ji batun auran su Ummi, baya
son rasata, kuma yana ji a jikinshi cewa zai same
ta. ** ** 28.....Yammacin ranar Asabar La'asar
lis garin yayi dan sanyi Abba ya nufi gidansu don
daukan su Ummi zuwa kasuwa. Jikinshi sanye da
farin yadi mai shara-shara, har ana iya hango
fara kar din singiletin da ke ciki ta manne a
jikinshi. Kamshin turarenshi ya cika dakin Umma
wanda ba shiga yayi ba daga bakin kofa suka
gaisa. Ya ce, "Ummi su fito don Ummi ce ke
shiryawa tuni Fati ta fito, ya matsa kofar
Tsohuwa suka gaisa, sannan ya ce "Umma sai
mun dawo. Ya nufi waje yana fadin su Ummi su
mishi sauri. Sun fito za su duru a baya Abba ya
ce Ummi ta dawo nan gaba, ta zauna ranta
dagule don ita bata bukatar wani za6i tunda ba
wanda take so zata aura ba. Haka nan ta
fuskanci Abba yau yana cikin wani irin yanayi,
kila daga gida aka 6ato masa rai, nata tunanin
kenan. Shi kam takaicin zuwa za6on kayan ke
damunsa, ya kalli wayarsa da ke ruri ya daga,
Salis ya ce kana ina ne? Ya ce ina nan
unguwarmu zan kai kannena ne za su za6i kayan
daki. Ya ce, "Ta ina zaku bi? Abba ya ce kai kana
ina ne? Ya ce ina nan kusa da asibitin Malam,
bari in jira ka a jikin gidan man nan, Abba ya ce
"To." Salis ya kalli yarinyar da Abba ya ce Ummi
koma baya ya ce, "'Yammata sannunku, suka
gaishe shi ya yi murmushi ke ce Ummi?" Ta ce,
"Eh, ya ce ya su Umma?" Ta ce lafiya lau, ya
maida dubansi ga Abba wanda ke tuki cikin
nutsuwa ya ce, "Idris akan batun yarinyar nan ne
don Allah ka daure muje gidansu yau". Gaban
Ummi ya fadi. Abba ya ce, "Don Allah Salis ka
bar batun yarinyar nan, kai dai kasan halin da
nake ciki game da wata". Salis ya ce, "Me yasa
ka amsa kana sonta, kuma har kana daga waya
duk lokacin da ta kira ka?" Abba ya ce, "Shike
nan za mu je da yamma tunda wancan na rasa
madafa". Salis ya ce kuma fa da hakan zai fi
maka. Ummi gashin jikinta duk ya mike, suna fitar
da zufa lumshi ido tayi luf a kan kujera ta kwantar
da kai, Salis ya waiwaya ya dubeta, yaya dai? Ta
yi dan yake, "Ba komai." . 29.... Sun je gurin
kujeru da gadaje, Fati tayi ta ruwan ido yayin da
Ummi ta koma ta jingina a kujerar da ta zauna.
Abba ya dube ta. "Ke wanne ki ka za6a? Ita ta ce
wancan farin". Ummi ta yatsina fuska, "Nifa bani
da za6i, duk wanda ku ka ga yayi". Salis ya ce, "
Idris yarinyar nan ina zaton tana sonka, naga
tunda muka yi maganar zuwa gurin wata ta
canza yanayi. Abba ya ce, "Kyaleta ba wani ya
dubeta ba, ke Ummi tashi ki za6a mu ji
farashinsu, sauri muke. Ta ce, "Ya Abba cikina ke
ciwo, ka za6ar min don Allah". Ya ce, "Salis ita
ma a bata farin kawai ko? Salis ya ce, "A daukar
mata mai ruwan madaran, mai shagon ya ce sun
fi tsada, Abba ya ce ka daukar mata su. Sun
koma gefen kujeru nan fa Abba ya ce dole sai ta
za6a, nan ma wanda ta za6a a ka ce sun fi na
Fati tsada, suka ji farashinsu su sannan ya ba da
wani abu suka tafi. Ya sauke su a gida, Fati sai
ba Umma labari take yayinda Ummi ta shiga
kuka, Umma ta ce ke kuma lafiya ki ke kuka?
Ummi ta ce "Umma ni bana son in yi auren nan,
bana son in bar gida. Fati ta ce, "Shi yasa naga
tun a gurin shagon kina ta 6acin rai? Umma ta
ce, "Shirmen banza da wofi, sai ki tayi. Ta fice,
Fati ta ce Ummi ke kin cika son damuwa. Menene
na damuwa? Kila ma kina nan unguwar.ovels / ZURFIN CIKI book 3 part 5
ZURFIN CIKI book 3 part 5
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:29
ummi sannu da zuwanku, nan sukayi masa
gaisuwa yace ummi kaisu ciki. 36.. Zainab tace a
ranta wato ma ummi yafara gani, a fallon su
umma suke don nan ta fara kai su, tace umma
wanan ce zainab, wannan kuma matar abokinshi
salis, umma tayi masu sannu da zuwa sanna tace
ummi ta kaisu dakin bishira, sun shiga sun yi
mata gaisuwa, bishira tace ke ko gaisuwa baki zo
min ba koda yake bai dame ki ba, ummi tace
nima ana ta zuwa min gaisuwan ne a gd, duk yan
dakin suka kalli ummi, sahura tace ke asuwa?
Bishira tace ita a mahaifiyar shi, ummi tace
zainab kuzo muje, tun daga lkcn zainab tasa a
ranta akwai matsala a wanan familyn din, basu
jima ba suka yi sallama, inda ummi ta rakasu
daga can itama ta wice gd, suna shiga soro
shima ya shigo yace badai tafiya zakuyi ba? Ya
kalli ummi sun sha ruwa ma kuwa?ummi wadda
dama idanunta na kanshi ta amsa mishi da
idanu. Yace yama akayi kuka gane gdn zainab
tace yaya salis ne yakawo mu, ya kalli matar
salis yace madam mun gode fa,tace bakomai
Allah ya jianshi, sam ummi batasan lokacin da
furucin ya fito mata ba, sai dai taji tace ya abba
duk ka rame baka cin abinci ko? Shi kanshi yayi
mamaki don haka ya ya tsura mata ido, sai taji
kunya ta rufee ta saita kau da kanta daga
kanshi,don kada su zargeta. Kayi hkr naji wani
malami yace duk wanda yaranshi kananan uku
suka rasu to zasu ceceshi ranar gobe. Kaga ynz
kafara da daya,matar salis tace ai koma dayane
indai kayi hkr kayi tawakkali,ummi ta kalle shi
tace to kaji ma,yace ummi nifa tuni na
dangana,ta sake tausasa murya to meyasa baka
cin abinci? Ya tausasa murya wadda dama take a
dusashe yace ummi inaci,tace ya abba baka fa
yin karya,yace to yau zanzo inci a gabanki, ya
kalli matar salis wadda ke murmushi, in naci a
gabanta saita yarda ko? Tace tabbas! 37..Zainab
wadda takaici ya cikata tace da matar salis anty
nifa natafi, abba ya dubeta zainabu nagode ki
gaida su mama sai nazo,batare da ta tsaya ba
tace to, ummi ta musu sallama itama ta tafi gd.
Zainab ta dubi matar Salis bayan tafiyar Ummi,
ta ce, "Duk da son da na ke ma Idris din nan ba
zan aure shi ba". Matar Salis ta ce dalili? Zainab
ta ce, "Bana zaton ko matarshi ta gida da ya
aura ya aje yana sonta irin yanda yake son Umiin
nan". Abin nasu yayi yawa. Dubi yanda ya manta
da ni, ta ita kawai yake yi. Matar Salis ta ce, kin
ji ki da wani shirme, ita da zata yi aure?" Zainab
ta ce, "Abinda ke tausar zuciyata ke nan in na
tuna cewa zata yi aure, amma kai naga ji ba zan
iya ba, haka suka tafi tana ta bai wa yarta
labarin yanda Abba ke ji da Ummi. Kamar yadda
Abba ya ce zai zo cin abinci da dare yazo, Ummi
ta saka shi gaba wai sai ya cinye wake da
alayyaho da kifin da ta dafa masa. Da kyar ya
cinye plate din farko ya ce "Ummi na koshi kin ji?
Ta daure fuska tana kallonshi, shi ma ita yake
kallo yana dan murmushi. Ya ce, "Ina ma a ce
tun da da haka muka yi sabo, Ummin cikin
kwanakin nan kin lura cewa muna shiri". Ta
harare shi, "Kana zaton na manta da irin dukan
da ka yi ta min ne? Shi ma ya harare ta tare da
kwaikwayon muryarta. "Kina tsammanin zan
manta da irin tsokanar fadanki ne? Ko zan manta
da Suhailar Kaduna...?" Kafin ya rufe baki tuni ta
yi uwar daka da gudu, shi kam dariya yayi ta yi
yana cewa ki zo mana Ummi, kin fitowa tayi har
sai da ya bar gidan. Duk lokacin da suka kasance
tare kowannan su yana mantawa yana da wata
matsala. Saura kwana uku daurin auransu,
lokacin dangi sun soma zuwa, musamman 'yan
Zamfara. Ummi da Abba hankalinsu ya kai
kololuwa gurin tashi. Ranar ya ziyarci Zainab wai
ko zai samu 'yar nutsuwa. Bayan sun gaisa ta
sake mishi gaisuwa, shi kuma ya mata bangajiya,
dama tun da aka yi rasuwar bai zo ba. Ya ce
"Zainab ina ganin da an gama hayaniyar bikin
Ummi zan turo". Tayi shiru bata yanke ma kanta
shawarar matsawar ya cikata da zancan Ummi
yau kam za su yi ta ta kare. Jin tayi shiru ya ce
kina jina Ummi... ta katse shi da sauri, "Ba Ummi
nake ba Sorry Zainabu. Ya ci gaba bakina ne ya
saba da kiran Ummi, da yake daga ni sai ita ne a
gidan. Yanzun haka auran nan da zata yi ina cikin
tsananin kewarta...Zainab ta ce ina Idris? Don
Allah ni na hakura ka je ka auri Ummi, Abba ya
dubeta cikin tsananin mamaki. 38.. Me ki ke
fada? Me Salis ya sanar da ke? Ta ce Idris duk
wanda ya san so, minti biyar in ya zauna da ku
zai san kuna tsananin son junanku kuma ni na
tambayi Salis cikinku daya? Ya ce min A'a tun
daga nan nasan cewa ku masoya ne, ta nufi
hanyar gida, da sauri ya sha gabanta. Zainabu
kada muyi haka da ke, wallahi auranki zan yi. Ta
ce, "Eh ai na san aurena zaka yi, amma ba sona
ka ke ba, don Allah ban hanya sonka in zai yi
ajalina ba zan aure ka ba, ya kauce ta wuce, ya
bita da kallo har ta shige. Jiki ba karfi yake tuka
motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don
haka ya nufi dakin. 21. Jiki ba karfi yake tuka
motar har ya iso gida, kukan Muhibba ya jiyo don
haka ya nufi dakin. Bishira na zaune ta zuba
tagumi tunanin danta take, ga Abba sam baya
sakar mata fuska, ya ce "Lafiya Mamina take
kuka?" Ya shiga ya dauketa Bishira ta ce, "Rigima
cee kawai, ya nufi kan madubi inda ya hangi
pampers ya dauki guda daya ya nufi dakinshi da
ita. Bishira ta biyo shi itama ta zauna a gefen
katifa kusa da shi, cikin sanyin murya ta ce,
"Abban Walid don Allah kayi hakuri, ya ce me a
ka yi? Ta ce, "Gani nayi kana ta fushi, ya ce ni
bana fushi wannan kadan kenan ki ka gani daga
cikin sakacinki, na tabbata kin fini jin bakin cikin
mutuwar yaron nan. Musamman da ki ka zama
sanadi, amma don batun yawo ni na daina miki
fada, kiyi tayi illa dai zan nemo wadda zata dinga
lurar min da gida. Ta ce me ka ke nufi? Ya ce
aure zan yi". Ta doki kirji tare da fadin, "Aure?" ya
ce, "Eh". Ta soma kuka haba Baban Walid, wane
laifi na maka da zaka yanke min irin wannan
mummunan hukuncin? Ya ce, "Don Allah fita, ta
ce sai ka fada min dalilin yin auranka, ba za ka
bar ni in ji da rashin dana ba ko? ta mike an
zugo ka an ce kayi aure, to bisimilla. Ta fita ta
zari mayafi tayi gidan Umman Bashir. Abba ya
rungume 'yarshi ya yi laf a kan katifa shawara ya
yanke zai tura magabanshi gidan su Zainabu ba
tare da ya sake bi ta kan Zainabun ba. * Umma
ta leko dakin Tsohuwa, Ummi kin san na ce miki
kizo ki kwashe kayanki daga dakina ki adana su
ko? Kin san dai yau duk na nesa za su iso, ki cire
wadanda za ki bada. Tsohuwa ta ce, "Suwaiba
yarinyar nan ina kallonta jiya bata runtsa ba,
sannan da Asubahi a zaune tayi sallah. Umma ta
shiga dakin warwas take a kan gado, Umma ta
tasheta zaune Ummi ciwon kai ta keya ga jiri da
ta ke gani daga zaune. 39.. Umma ta ce taso ki
dan watsa ruwa ki karya, mikewar da zata yi sai
ta sulale a kasa sumammiya, nan suka dau
salati, Toshuwa kam kuka ta saka. Alhaji ya fito
wanka kenan ya ji Umma na salati, don haka
dakki ya shiga ya dauko waya ya kira Abba
lokacin yana kokarin shiga wanka. Alhaji ya kira
shi, jin cewa Ummi ba lafiya zari mukullin mota
ya fito. Sai da suka kai asibiti sannan ya lura da
silifas ya fito da jallabiyarshi ta wanka, Lkitan ma
bai zo ba lambarshi suka amsa Abba ya kira shi.
Ya duba Ummi sosai da kyar suka samu
numfashinta ya dawo, sun daura mata ruwa
sannan aka kaita wani daki. Likitan ya ce su zo
ofishinsa, Ya kalli Alhaji ya ce, "Gaskiyar magana
yarinyar nan tana bukatar kulawarku, ciwonta
baya son sakaci. Jininta ya hau ya wuce matakin
da zata iya samun mutuwar 6arin jiki. Su Alhaji
suka dauki salati,, ya ci gaba da cewa yanzun dai
addu'a zamu ci gaba da yi. Allah yasa in ta
farfado kada wata matsala ta biyo baya. Sannan
ya basu takardar magunguna". Alhaji ne ya amsa
don Abba fita yayi ya koma dakin da Ummi ke
kwance. Idanu ya zub amata, sam bai san cewa
kuka yake ba, sai da Alhaji ya shigo ya dafa shi
tare da cewa, "Haba Abba ba girmanka ba ne
kuka. Addu'a za ka yi Allah ya bata lafiya". Ya
share hawaye. Alhaji don Allah kada ka sanar da
Umma abinda Likitan ya ce, Alhajin ya ce ai
dama ba zan fada mata ba. Bari in je sai tazo ga
takardar maganin inta zo sai ka siyo, ya ciro kudi
ya mika ma Abba, Abba ya ce a'a da kudi a
jikina. Alhaji ya ce ka amsa ka kashe kudi cikin
kwanakin nan ina sane da duk lokacin da na ce
kazo ka siyo wani abu sai kawai in gan ka da shi
ban da kayan dakin da ka siya musu, Abba ya ce
ai ina da shi ne. Bayan fitar Alhaji Abba yaja
kujera ya zauna ya zabga tagumi tare da tsura
ma Ummi ido, a zuciyarshi fadi yake ALLAH ka
tashi yarinyar nan lafiya, Allah kasa kar ko ina na
jikinta ya nakasa. Alhaji ya fada wa Umma an ba
Ummi gado, don haka ta shirya su wuce. Abba ya
tashi ya nufi ofishin Likitan, bayan ya kwankwasa
Lokitan ya ba shi izinin shiga, ya same shi yana
rubuce-rubuce. Ba tare da ya dago kai ba ya ce,
"Zauna sai da ya kai aya rubutunshi sannan ya
dago kai ya kalli Abba "Ba dai mai jikin ba ce
ko?" Abba ya ce, "a'a ina son ne nima agwada
nawa jinin, Likitan ya ce kana jin jikinka ba dadi
ne?" Abba ya ce, "Eh da har yasa a dauko fayal
din Abba kuma ya tasa ya dauki abin gwaji.
Bayan ya gama ya zaunar, ya tsare Abba da ido
wai kun yi gadon ciwon nan ne? Abba ya ce,
"A'a, Likitan ya ce, "Jininka ya hau, sai dai ba
sosai ba. Kila don kai namiji ne kana kokarin
kauce ma abubuwa. Zan rubuta maka magani na
sati daya, kuma ka dinga kokarin yin bacci a kalla
na wa shida kada ka dinga yawan tunani. Kaga
kanwar nan taka, sai sa'ar gaske zata tashi
lafiya. Ku dai cigaba da addu'a, zata yi bacci na
tsawon awa tara ko goma. Ina son daidai lokacin
da zata farka ya kasance ta soma dora ido a kan
wanda suke shiri ko wanda ta fi so a cikin
mahaifanta ko danginta, Abba ya ce "To."
Lokacin da ya koma dakin su Umma sun zo har
da tsohuwa, nan Abba yake fada musu abinda
Likitan ya ce game da farkawa in tayi. Koda bude
bakin tsohuwa sai cewa ta yi ai ko dai ba a bar
mai sunan Malam ba, tunda an ce wanda suke
shiri, don in taga mai sunan Malam karasawa
zata yi. * 22. Duk da ana cikin wani hali sai da
su Alhaji suka murmusa. Abba kam daure fuska
yayi yana kallon Tsohuwa, Umma ta ce, "Ai da ne
Tsohuwa. Yanzun shiri suke tunda ta daina rashin
jinta". Likitan ya shigo ya sake musu bayani
kamar yadda ya yi ma Abba, sannan ya ce su
bata guri kada zantukansu ya farkar da ita a
samu matsala. Suka fito, Umma ta ce da Abba ya
tafi gurin aikinsa, su Alhaji ma suka fita tare da
Abba. Fati ta je gidansu Sahabi dan uwansa yana
kankarar rake a kofar gida, inda yake saidawa ta
tambayi Sahabi. Yaron ya ce mata ya ffita, ta ce
To in yazo kaa ce masa Ummi tana asibiti ba
lafiya, an bata gado. Karfe uku ya iso asibitin
hankali a tashe, sun gaisa da Umma ta raka shi
dakin, hankalinshi ya tashi da ganin Amaryarshi
kwance a gadon. Abba kam yana gurin aikinshi
amma hankalinshi na Asibiti, su Alhaji ma duk
nan suka nufo, Abba sai da yayi magriba sannan
ya shigo asibitin. Jikinshi babu karfi, bai matsa
sai yaga farkawar Ummi ba ne saboda yasan da
gaske ba shi ne ya dace idanunta su soma arba
da shi ba, ya samu su Umma da su Alhaji.
Sahabi da abokansa duk suna gurin, ya gaida su
tare da tambayar ko ta farka? Umma ta ce har
yanzun dai shiru. Ya nufi cikin gurin Likitan suka
gaisa, ya ce Likita har yanzu ba ta farka ba. Suka
jera zuwa dakin, Likiran yana cewa cikin wannan
dan takin zata farka, In sha Allahu. Sun shiga
takin tana dan motsi suka nufi gadon Abba ya ce
Ummi. Likitan ya daga mishi hannu alamar yayi
shiru ita kam daidai lokacin mafarkin Abba take
wai suna tafiya ya rike mata hannu sai ga
Sahabi. Yana zuwa ya kama hannunta tana
tirjrewa, sai janta yake zai fita da ita, Abba yana
tsaye yana kallonsu. Ita kuma sai kiran "Ya Abba!
Ya Abba!! Take yi. Likitan ya kara kunne gurin
bakinta ya dagowa yayi ya dube shi. "Waye Yaya
Abba?" Abba ya ce ni ne. Liitan ya ce, matsa
kusa, ya kama hannunta. Ummi. A hankali ta
bude ido. Ya Abba! Ya abba, zan sha ruwa, ya ce
to ya kalli likitan za ta sha ruwa, Likitan ya ce,
"A'a bari ta dan kara warwarewa tukunna. Likitan
ya kama kafafunta ya dan matsa, sannu ko. Ta
kalle shi, kin ji zafi? Bata yi magana ba ya dauki
allira ya 6are ya dan soka mata a tafin kafa ta ja
kafafunta alamun taji zafi. Ta yunkura zata tashi,
Ya abba zan tashi, ya tayar da ita zaune. "Likitan
ya ce Alhamdulillah, Abba ya kalli likitan, ba
matsala kenan? Ya ce, Ina zaton haka insha
Allah, Abba ya ce "Alhamdulillahi, ya jinginata da
jikinshi, sannu Ummina. 41.... Alhaji ya shigo
yana cewa, "Ina Abba ne?" ya ganta zaune a'a ta
farka ne? ya kama hannunta sannu uwata. Ta
kalle shi. "Ina Ummata?" ya ce, "Bari in kira miki
ita". Yaje ya sanar da su, sun shigo da murna.
Sahabi ya iso gaban gadon. "Sannu Ummi". Ta
kalle shi sai ta kwantar da kanta a kafadar Abba,
"Ya Abba ina son in wanke bakina". Ya ce, "To
bari in siyo miki Maclean din". Ta ce, "A'a kada
kaje". Ya gyara zama "To shi kenan." Umma ta
ce, "Me ta ke so?" Abba ya ce "Baki zata wanke".
Umma ta ce "Ai nazo mata da maclean da
burushin nata, don nasan ita gwanar wanke baki
ce". Nurse ta kawo wani dan kwano na silba
Ummi ta wanke baki da taimakon Abba. Likitan
ya ce, a bata tea mara zafi sosai, sannan a bata
magani. Takaici dan'kam a zuciyar Sahabi, irin
wannan shigewa da Abba ke matar da zai aura
tayi yawa. Kai shi fa wannan Yaya Abban bai
masa ba ma, don yana daure mishi fuska ko
gaida shi yayi d kyar yake amsawa. Shi fa tun
ranar da a ka ce mishi Ummi ba cikinsu daya da
Abba ba ya ji ya tsane shi. Umma ta ce, "Abba
an kira Isha'i. Sahabi kaje kai ma ka huta yaran
nan tun tuni ya ke nan". Abba ya kalle shi, "Ya
kamata ka tafi haka ko?" ya kalli Ummi sannan
ya dan rusuna "Sannu Ummi". Ta ce, "Yauwa"
"Innata ta ce in gaida ki da jiki, ni zan tafi sai da
safe. Me zan kawo miki?" Abba ya dube shi a
kule., "Don Allah Malam kaje ba za ta iya cin
wani abu yanzun ba". Umma ta ce, "Abba". Ya
kale ta, sai ta girgiza mishi kai alamun ya bari.
Sahabi jiki a sanyaye ya fice tare da cewa "Umma
sai da safe". Ta ce, "To Sahabi, ka gaida Innar
taka". Da ya fita ta kalli Abba "Wannan ba
halinka ba ne kada in kuma gani". Ya ce "To
Umma". 23. Su Alhaji sun yanke shawarar daga
auran Ummi a darua na Fati kawai, ita sati biyu
masu zuwa sannan ta murmure sai a daura nata.
Gidan su Sahabi sun ji haushi musamman
Innarshi, sun kashe dan abinda suka tattala don
bikin amma gashi an daga, su kam da an daura
auren in ta murmure sai a yi bikin. Sahabi ya
shigo gidan ranshi a 6ace, ya kalli Mahaifiyarshi,
"Inna wai sun ki a dauram?" Ta ce, "Sun ki, dama
ai gaddamar dan yau ce. Ban da shegiyar
gaddama ga 'ya can da a ka baka a daura ka
gaddame, to yanzun ina ranar abin da aka mana?
Gida duk dangi sun cika amma wai a daga biki,
mu kuma karamin karfi ne da mu, bare mu ce nan
da sati biyu zamu sake kashe kudi". Sahabi ya
tuna abinda Abba ya masa a asibiti, shi ne dalilin
da bai sake zuwa asibitin ba, yaja tsaki. "Kin san
Allah Inna ni kaina sai yanzun nake jin haushin
kaina da na ki amincewa da Badariyya. Mu zuba
musu idanu in za su sake kawo mana cikas sai
kawai in koma gurin Badariyya." Inna ta ce, "In
da tun jiya kamin zancan nan da tuni yau ba a
fasa daura auranka ba an ma da Badariyya". Ya
ce, "Kiyi hakuri Inna mu ga nufin su". * 42... An
sha shagalin bikin Fati kuma an kaita gidanta.
Ummi jiki Alhamdulillah, Abba kullum in zai je aiki
sai ya biya. Haka nan in ya dawo gida wanka
kawai zai yi ya tafi, wataran sai goma ko sha
daya. Abokanshi suna ta zuba duba Ummi, ita
kanta da lokacin zuwanshi ya karato ta dinga
kallon agogo ke nan tana kallon kofa. A zaman
asibitin nan Umma ta gama karantar su tsaf.,
matukar son juna suke yi, sai dai taji takaicin da
sai yanzun sonsu ga juna ya bayyana. Lokacin da
ya kasance an riga an bada Ummi ga wani sai
dai ta ci gaba da addu'a Allah yayi za6i na
alkairi. Bashir yayi murna da fasa auran Ummi,
dama a fasa gaba daya. Yana fitowa dakinshi ya
ji Ummarsu tana cewa, "Kin san Allah Tasalla,
uwar yaron nan da zai auri Ummi zata ga bakin
ciki, don mallake mata da za su yi. Tana ji tana
gani sai yanda suka yi da shi. Kuma ba yanda
zata yi sai Allah ya isa". Tasalla ta ce "Ban da
halin mutanan yanzun ba da sai na fada mata ba.
Kin san makotanmu ne ta baya, gashi su ba karfi
ba. Sahabin ne fa ke rike da gidan, kin san shine
Babban a gidan". Sahura ta ce, "Don Allah Tasalla
ki taimaka ki fada musu, don ko in har aka yi
auran nan in suna cin abinci sau uku ne a rana,
to za su koma dau daya". Tasalla ta ce "Ai ko
zanje". Tana fita Bashir ya dawo kusa da
Ummarsu ya ce, "Umma dama da kanki ki ka je,
saboda za su fi yarda tunda sun ga ke kina da
danganta da gidan". Ta ce, "To in Babanku ya ji
fa?" Ya ce "Umma ai in kin fada musu ai kwa6ar
su za ki yi, sannan kada kije a kan lokaci, kije ana
gobe daurin auren". Ta ce, "Saboda me?" Ya ce,
"Saboda su Alhaji Babban suji haushin rashin
fada musu da wuri". Ta ce, "Haka za a yi, kuma
in an fasa Malamai zan shiga don a hanata auran
ma kwata-kwata". Ya ce, "Kada kije wurin
Malamai yanzun tukun". Ta ce. "Ai dama sai an
natsa". * Abba ya fito cikin suit bakake, yayi kyau
matuka hatta takalminshi sawu ciki baki ne,
tamkar wani black America. Igiyar wuyan ta
zauna tsam, sai kamshi yake. Dakin Bishira ya
nufa ya daga labule, ta dago ta kalle shi yayi
matukar birgeta. Tana alfahari da shi matsayin
mijinta, ya ce "Kin shirya?" ta ce,, "Zuwa ina?' Ya
ce, "A'a, jiya fa na sanar da ke ki shirya da wuri
zamu je asibiti ki gaida Ummi". Ta watso mishi
wani kallo uku saura kwata, tare da cewa "Ko
garin nan ba a sanyi ba zan fita gaida wata can
Ummi ba bare da sanyin nan." Ya ce, "Dalili ta
mike tsaye "Ciwo bai kai mutuwa ba, da mutuwa
ya yi tazo ta min gaisuwa?" Takaici ya turnu'ke
Abba, da yake sarkin dankara magana ne, sai ya
ce "To ita ta kashe shi da zata miki gaisuwa?"
Ta kule da bakin ciki ta zabga mishi harara "To ai
kasan ni na dora mata ciwon, don haka dole in je
gaisheta." Ya ja tsaki tare da cewa, ballahaza
wadda bata san mutuncin mijin auranta ba". Ya
yakice labulen ya wuce yana jiyo ta tana cewa,
"Ba dai za ni ba ko me za ka ce". Ranshi a 6ace
ya isa asibitin, Ummi na zaune kan gado ta kosa
Abbanta yazo, ko karyawa ta kasa yi, yana
sallama suka hada ido. Nan ta ke ya ji ya manta
da duk wani bakin ciki da ya taho da shi, ya isa
bakin gadon fuskarshi dauke da murmushi. Itama
murmushin take yi, ya ce. "Ummi ya ya jikin?" Ta
ce "da sauki". Ya Abba kayi kyau sai ka ce
Manajan Banki". Umma ta saka dariya, shi ma ya
yi 'yar dariya, "To ko bankin zan koma?" Ta ce,
"A'a kafi kyau da dan jaridanka Ya Abba, balle in
kana turancinn nan a labarai". Ya lakuci
kumatunta "Ko kwanwata?" Ya juya ya gaida
Umma, Umma ta ce "Ka zo katafi gurin aikinka
fa". Ya ce, "Umma sai sha daya yau zanje gurin
aiki". Ta ce, "Ni na ma kosa a sallame mu". Abba
ya ce "Ai kila a sallame ku yau. Likitan ya shigo
ne?" Suka ce "A'a. Suna cikin karyawa Likita ya
shigo ya same su, ya kuma kafa mata dokokin
daina tunani, daina shiga duk wani abu da zai sa
ta cikin damuwa. Rage shan gishiri tare da
samun isassen bacci, ya kuma gargadi su Umma
su dinga nisantar 6acin
Home / ZURFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 3 part 6
ZURFIN CIKI book 3 part 6
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:31
Rage shan gishiri tare da samun isassen bacci, ya
kuma gargadi su Umma su dinga nisantar 6acin
ranta. 26. 43... ABBA Ya kwaso su ya maida su
gida, cikin satin Ummi ta murmure. Sahabi na
zuwa sai dai da sun gaisa yake tafiya.
Mahaifiyyarshi ma tazo, amma Bishira da Sahura
ko le'ke, Bashir ma yana ta sintirin zuwa. Ganin
haka Alhaji ya ci gaba da shirin biki, mutan kauye
dai dama an ce kada su dawo, Ummi dai bata
maida hankali ga komai ba. Ta ce ma Umma zata
je gidan Fati, Umma ta ce To sai ki je gurin
Sahura ta kwatanta miki. Abba ya same su suna
zancen, don haka ya ce ta shirya zai kaita ya
ajiyeta in ya tashi aiki sai yaje ya daukota. Yanda
ta samu Fati da Angonta ana ta ji da juna abin
ya tsokanota, sai dai ta kasa ganin dacewar
soyayyar da Sahabi. Da mijin Fati ya fita Ummi ta
ce, "Oh, Fati cikin kwana takwas dubi yanda ki ka
yi kyau". Fati ta ce, "Amma ban rame ba?" Ummi
ta ce "Eh to, kin dan rairaye". Fati ta ce, "Kai ai
dole, gaskiya ina koduwa, wallahi ba ya barina in
huta". Ummi ta ce, "Da me?" Fati ta ce, "Dallacan
ki gane mana". Ummi ta ce, "Wai da me? Allah
ban gane ba". Fati ta ce, "Ai ke sokuwa ce, gurin
kwanciya mana. Ummarmu ta samu ta dirka min
kayan sha na mata, gashi nan nazo ina ta shan
wuya". Ummi ta zaro ido, "Da wahala ne?" Fati ta
ce, "Tab, ai kin kusa kema za ki ji". Tsoro ya cika
Ummi. Ta ce, "Zan ce ma Umma ni dai kada ta
bani wannan kayan matan". Fati ta yi ta dariya
tare da cewa, "Ke yanzun sai ki iya wa Ummanku
wannan zance?" Ummi ta ce, "Sosai ma". Fati ta
ce, "Ko ba ki sha ba yarinya sai kin sha zafi, ana
kawo ni ko dan kwana daya bai raga min ba".
Ummi dai ido ya raina fata. Koda Abba ya zo
daukarta duk ta damu. ** ** 44..... Tasalla ta
samu uwar Sahabi ta fada mata cewa, in dole ne
sai danta ya auri Ummi, to ta amso mishi karya
tambaya. Don kuwa wata rana sai ta taso ta
ganshi ko da a hanya ne ta rasa samun hakan.
Inna ta tsure ta ce, sai a fasa babu dole, ita
dama tuni abin ya sire mata. Ana gobe daurin
aure gidan su Ummi suna ta shiri Ummi na ta
kuka, wannan karon ba Umma ba har Alhaji da
Tsohuwa sun kule da wannan iskancin da Ummi
ke yi. Alhaji ya ce "Ki sani uwata, wannan karon
ko kin tsokalo ciwon nan naki auren nan dole ne
babu fashi. Idan yaso jinin naki ya tashi ya ta6o
sama ba zan kuma daga auran nan ba". Lokacin
da Alhaji ke wannan fadan Abba yana gidan yana
zaune dakin Umma yayin da Ummi ke gefanshi
tana rusa kuka. Umma ta shigo ya ce "Umma
don Allah ki lallashi Alhaji a dan daga bikin nan
mana". Abba bai ta6a ganin ranar da Umma tayi
mishi irin wannan kallon da ta masa yanzu ba
tun tasowarshi. Sannan bata ta6a daka masa irin
wannan tsawar ba ta ce "Kai! Abba shiga
taitayinka, me yasa yanzun ka canza, ko kai ba
za ka hukunta Ummi ba da irin wannan yaro da
hankalin da take mana? Don gidansu kanta a ka
soma aure? To wannan karon ba za a daga bikin
ba, in yaso ta mutu, ke ko mutuwa ki ka yi
gawarki can gidan mijinki za a je a miki sutura".
Tsohuwa ma daga can tana yo nata fadan tare da
dauko tarihe-tarihen da tana cewa, "Lokacinsu
kaza-kaza". Abba ya sake kallon Ummi,
matsanancin kukan da take yi yana daga mishi
hankali, ya mike tare da kama hannunta, "Zo
muje". Ya bude mazaunin direba ya ce ta shiga,
shi ma ya koma ya shiga motar ya tasheta, tafiya
kawai suke ba tare da ya san in da suka dosa ba.
Kukan Ummi na tsikararshi, sun yi tafiya mai nisa
sannan ya tsaya a hankali cikin wata irin murya,
ya ce "Ummi ki fada min gaskiya kina son
Sahabi?" Ta dago ta dube shi, "Ni bana son shi".
"To me yasa ki ka fito da shi?" cikin dasasshiyar
murya ta ce, "Ba ni da yanda zan yi ne, saboda in
ban za6i Sahabi ba za a bani Bashir". Ya ce, "To
ke yanzun fada min wa ki ke so?" Gabanshi ya
shiga faduwa don tsoron kada kunnenshi ya ji
mishi ta ce wani ba shi ba. Ta kuro shi da ido
tamkar ta ce kai, amma sai take ganin in ta fada
mishi haka dan shirin da suka soma yanzun zai
wargaje, kila ma sai ya hada mata da duka. Wasu
zafafan hawaye suka gangaro kan kumatunta,
daidai lokacin da yake cewa "Ko dan digo ki ka ji
son ko waye a ranki kada ki rufe min". 45... Ta
girgiza kai "Ba na son kowa Ya Abba". Cikin wani
irin yanayi ya dubeta, "Shi kenan, sai ki je ki
hakura da Sahabin a sannun kin so shi". Cikin
kuka ta ce, "Ya Abba Allah ni bana son shi, kai to
ka hada ni da ko waye mana". Ranshi 6ace ya
dubeta cikin tsawa ya ce, "Ki rufa min baki tunda
ba ki ta6a son kowa ba ki zauna da wanda ki ka
za6i zama da shi. In da kina son wani ne to da
sai in cije in tunkari su Alhaji, tunda kuwa babu
sai in ce musu me?" Ya fada mota, ya koma kofar
gidan. Koda ya tsaya tafi minti uku sannan ta
fito, yana kallonta maimakon ya wuce gida sai
kawai ya nufi gidan Maman Iman makociyarsu da
suke shiri da ita. Shima kanshi na kan sitiyarin
motar har ttsawon shudewar wasu dakiku,
sannan ya nufi gida. 27. Misalin karfe tara
Umman Bashir ta rangada sallama a tsakar gidan,
Innar su Sahabi ta amsa tare da fadin "Shigo".
Sahura ta shiga tana tambayar "Ba kowa dai ko?"
Inna ta ce "Shigo mu kadai ne". Bayan sun gaisa
ta ce "Ba ki sanni ba ko?" Inna ta ce, "Eh."
Sahura ta ce, "To ni dai tsakani ga Allah zuwa
nayi in ba ki shawara bisa ga yarinyar da danki
zai aura. Tsakani ga Allah yarinyar ba ta da
mutunci, sannan iyayenta za su mallake miki da,
don ni kaina ya faru da ni". Sahura don makirci ta
soma rishin kuka. "Dana maigidana ya ba su riko,
ina sheda miki wannan zance 'yar uwa yanzun
tsakanina da shi sai ido, sun makkale shi komai
shi yake musu, ni ko da nayi wahalar ciki da
nakuda sai na tashi a banza. To da yake an ce
ciwon 'ya mace na 'ya mace ne, shi ne nazo in
sanar da ke. Amma in kin ji haushi kiyi hakuri".
Ta yunkura zata mike. 46... Inna ta ce, "Zauna
'yar uwa, na gode. Nima fa tuni auran nan ya fice
min a rai, dama da naga shi Sahabin ya dage ne
sai kuma suka aiko gobe azo za a daura aure sai
na hakura". Kafiin Sahura tayi magana sai Sahabi
ya doka sallama, Inna ta ce "Yauwa zo nan". Ya
nufo ta "Zauna kaji ma kunnenka". Ya rage
tsawo, Inna ta ce "Baiwar Allah ya ki ka ce?" Nan
Sahura ta soma zuga sharri, ta kara da cewa
"Yaro ina ga ma za ka san dan nawa da suke riko
Abba a ke ce masa". Cikin saurin baki ya ce, "Na
san shi". Ta ce, "To dana ne da asiri suka amshe
min shi, sai dai Allah ya isa". Ya tuna irin halayen
da Abban ke nuna mishi. Yaa jinjina kai, sannan
ya dubi mahaifiyarshi "Inna to da Kawu yayo
binciken halayan iyayenta ai ana ta yabon
halinsu". Inna ta ce, "Kin ji shi ko? To bari kaji,
kwanaki ma Tasalla da ke bayan layin nan tazo
ta fadan irin wannan matsalar ban kama ba ne
don na asanta da shegiyar karya. To kuwa an yi
biyu ba zan bari ai na uku ba, don haka a daran
ta tabbatar ma da danta an fasa gobe ya wuce
gurin Badariyya a daura, su kuma in sun ji shiru
sa ba wani can". Cike da murna Sahura ta koma
gida. * Maman Iman tayi lallashin duniya amma
Ummi ta ki yin shiru, ga zazza6i tamkar wuta a
jikinta. Sai kusan sha dayan dare sannan Maman
Iman ta rako ta gida, lokacin Umma tana ta
neman layin Abba a kashe. Ta ce, "A'a sun dawo
ne yanzun ni ke neman Abba in ji suna ina ne?"
Maman Iman ta ce, "Tun dazu tana gidanmu
zazza6i da ya rufe Ummin, na bata magani ta 'ki
sha". 47... Umma ta ce "Rabu da ita kar Allah
yasa tasha, aure dai gobe babu fashim dubi irin
yanda a ka sa gidan su yaron nan wancan karon
suka kashe kudi gurin yin girki da sauransu ba a
yi bikin nan ba. Yanzun a kuma dagawa daga
lokacin da muka samu?" Maman Iman ta ce, "Ai
ba zai yiwu ba, sai dai a bi ta da lallashi". Umma
ta ce, "Mun daina lallashinta tunda ko mun
lallasheta aikin banza ne". Maman Iman ta ce,
"To Allah ya kaimu gobem bari in shiga gida sai
mun shigo aiki da safe". Umma ta ce, "To sai da
safe". Ummi tana shiga dakin Umma taga baki
kwakkwance, ta ce a ranta "Mayu, don kalata sai
da wasu suka dada zuwa". Tana fushi da
tsohuwa amma duk da haka dakin ta nufa, ta
kwanta a bayanta don ita tuni tayi bacci. Nishin
kukanta ya farkar da Tsohuwar, kala bata ce
mata ba, sai sauka tayi ta shimfida a kasa ta
kwanta, sannan ta ce "Aniyarki ta biki Takwara".
Wannan dare gurin Ummi da Abba wani dare ne
mai cike da bakin ciki da tashin hankali, ko Sarkin
sata bacci ranar bai samu galaba gare su ba.
Dukkan su a kan kunnansu aka kira sallar farko,
Abba ya mike cikin rangaji, jin jikinshi yake yi
tamkar iska ta dauke shi saboda rashin karfi.
Ruwa ya diba ya watsa, wanka sannan yayo
alwala don yin nafila, addu'a yake Allah yasa
hakan shi ne mafi alkairi a gare shi. Da ya dawo
Masallaci kwanciya yayi amma baccin ya ki bai
fita ba sai kusan takwas. Koda yaga Bishira
zaune a tsakar gida tana karatun littafin sam bai
ji haushin rashin zuwanta gidan su Umma ba.
Nashi ganin duk wanda yaje tamkar yana murna
ne da rasa Umminshi da yayi, ita kuwa da gadara
ta fito don ya ji haushi, bata je ba yana son sanin
halin da Ummi take ciki amma ba ya ra'ayin
zuwa gidan su Umma. Shagonshi ya bude ya
shiga ya dan zauna har zuwa tara, yana kallon
lokacin da Jama'a suka yi ta dafifin shiga layinsu
don halartar daurin auran. Kurum sai ya samu
kansa da tare dan Aca6a ya hau ba tare da ya
shaida masa inda za su ba. Koda dan Aca6an ya
tambaye shi ce masa ya yi mu je. 48.... Ita ko
Ummi ranar zaune tayi sallah ta koma ta kwanta,
duk kaikawon ai da 'yan shewe-shewen da jama'a
dangi da makota tana jin su. Sai dai makoshinta
ya bushe ga zufa da ta rufeta, duk da yanayin ba
na zafi ba ne. Karfe goma daidai shi ne lokacin
daurin auran, layin ya dinke da jama'a, Alhaji
ranshi a dame don bai ga Abba ba. Ya kalli Alhaji
Karami, "Ina Abba ne?" Alhaji Karami ya ce,
"Abokan aikinshi ga su can sun zo ba a ganshi ba
son daukan daurin auran". Alhaji ya ce, "Su dauka
mana nasan yana nan tafe". Har sha daya ana ta
jiran 'yan gidan Ango shiru, su Alhaji suka tashi
dan aike gidan don a ce ana jiran wakilan ango.
Amma sai a ka dawo musu da sako wai sun fasa,
kalmar da ta rikita Alhaji ta tashi hankalinsa. Ga
jama'a an tara, Alhaji Karami ya ce wadannan
akwai kananan mutane." Daidai lokacin da muryar
wani Maroki ta ratso dodon kunnuwansu da
cewa, "Alhaji ku hanzarta Jama'a sun gaji da
jira". Alhaji ya dubi Alhaji Karami, "Aminu a daura
da Bashir". Alhaji Karami yayi shiru, can ya ce "A
daura da Abba". Alhaji Babba ya ce, "Ina zuwa".
Ya fito daga dakin Abba na da inda suke yin
shawarar, ya ratsa mutane ya ce a yi masa
magana da Suwaiba. Umma ta fito daga kicin ta
same shi a dakinsa yana tsaye yana kai-kawo ta
ce lafia? Ya ce Gidan ango ne shiru, an bisu sun
ce sun fasa. To shi ne na ce me zai hana a daura
da da Bashir? 49... Umma ta ce a daura da Abba.
Ya ce, "Haka ma Aminu ya ce. To ni ban ga
Abban ba ma, amma bari muje Allah yasa hakan
shi ne mafi alkairi". Take a nan a ka daura auren,
Habiba da Idris Alhaji Babba ya kirgo sadaki ya
mika. Alhaji Karami Waliyinta ya amsa, mutane
na ta al'ajabin yanda lamarin ya sauya. Umman
Bashir kuwa Bashir din ne ya shiga gidan hankali
a tashe yana fada mata cewa da Abba a ka
daura. Nan ko ta hau bala'i da zage- zage. Ummi
ko tunda ta jiyo guda na alamta mata an daura
aure, sai ta birkice ta shiga kowa da
numfashinta. Fati da ke kusa da ita tana
lallaminta ita ce ta kwala ihu, ba shiri aka yi
asibiti da Amarya. Fati ta shiga gidansu da kuka,
nan ta taras Ummansu tana bala'i sai lokacin ta
ji da Abba a ka daura. Ta ce da Ummar su to
menen ba shi ke nan ba? Umma ta hau zaginta
tare da cewa, kar ki ga kin yi aure sai in miki
shegen duka, Fati dai ta fice ta bar gidan. Sam
Umma bata ji dar da ciwon Ummi ba, wannan
karon don haka ma bata bi su Asibiti ba, da
kanwarta Saratu a ka tafi. Likitan yayi ta fada
lokacin da yake yi mata allurai, a kuma bata gado
Umma ci gaba tayi da kula da bakinta. Yayin da
zuciyarta take fara kar, ta sani kuma tayi Imani
Allah ba ya tozarta addu'ar bawansa, matsawar
bawan yayi hakuri tare da dogewa. Haka nan in
baka samu biyan bukatarka nan duniya ba lallai
gobe kiyama zaka tarar da abinka. Ta jima tana
rokon Allah yasa 'ya'yan nata biyu su zam miji
da mata su haifa mata jikoki masu albarka. Suma
su Alhaji suna ta sallamar baki sai dai yanzun ba
wanda ya damu ya gani irin Abba. Fatanshi Allah
yasa Abban yayi farin ciki da wannan hukunci da
suka yanke. Salis kuwa burinshi ya zama shi ne
mutum na farko da zai wa Abba wannan albishir
sai dai ya kira layin Abba sama da sau hamsim
bai daga ba. Abinda bai sani ba shi Abba ma gida
ya bar wayar, haka suka gama dauke-daukensu
yayi hira da Jama'a da kuma iyayen Ango da
Amarya don jin ta bakinsu a kan yanda auren ya
juye zuwa na zumunci. Haka nan suka tafi ya
samu abin sawa a Taskar labarai, burinshi yanzu
shi ne ya je ya nemo angon. 28 50.....Abba kam
kofar dan Agundi ya yada zango gidan su Mansir
abokinsu, shi ne kurum cikin abokan Abba da bai
yi aure ba. Yana isa kofar gidan Mansur na
fitowa za shi daurin auren, wani dan layinsu a
Gwammaja suka gaisa. Abba ya ce "Bari in dan
kwanta a dakinka". Mansur cikin mamaki ya ce,
Lafiya? Abba ya ce lafiya lau. Yana kwance dakin
Mansur idanunshi suna kallon agogo, zuciyarshi
tana raya yanzun abar sonshi ta zama matar
Sahabi. Sai dai bai san dalilin da bugawar
agogon karfe sha daya daidai tazo gwame da
bugawar zuciyarshi ba. Zuciyarshi ta fada mishi
cewa wannan alamu ne na an kammala daurin
auren. Wasu hawaye ne suka biyo ta gefen
idanunshi suna sauka a kan filon. Yini zur yana
dakin in lokacin sallah yayi sai ya fito kofar dakin
yayi alwala har duhun Magriba ya gabato. Ya fito
tare da kulle dakin, don Mansur bai dawo ba,
kuma dama ya ce ba zai dawo da wuri ba. Gidan
nashi ba kowa lokacin da ya shiga, kai tsaye
dakinshi ya wuce, ban da idanunshi da suka kai
kan wayarshi ya manta ma yana mallakinta. Ya
kai hannu ya dauka, bai ji mamakin yawan
missed calls din da ya gani ba, kiran Salis ya
sake shigowa. A kasale ya daga, muryar Salis ta
ratsa dodon kunnanshi, fadi yake yana
maimaitawa Ango- Ango. Abba cikin sanyin
murya ya ce "Salis ya haramta a gare ka ka
zolaye ni a halin da nake ciki. Sanin kanka kai
kadai ne kasan yanayin da nake ciki". Salis cikin
zumudi ya ce, "Kana nufin ba ka sani ba?" Abba
ya ce, "Me?" Salis ya ce "To bani goron albishir in
sanar da kai". Abba ya ce, "Don Allah Salis kada
ka min karya". Salis ya ce, "Ina rantsuwa da
wanda ya yi mu Ummi matarka ce, da kai a ka
daura. Ina ka shige lokacin da al'amarin ya canza
salo?" Abba ya mike zumbur. "Ka fa rantse Salis!"
cikin dariya Salis ya ce, "Wai har yanzun ba ka
sani ba? To ka aje min goron albishir dina". Abba
yasa hannunshi a baki ya gatsa, zafin da ya ji ne
ya tabbatar da mishi da ba mafarki yake ba. 51...
Ai sai ya katse wayar ya zube yayi sujjada ya fita
tsakar gida yana furta "Alhamdulillah." Ruwa yaja
ya watsa ma jikinshim sannan ya yi alwala.
Sabuwar shadda ya saka kalar kunkumadi, ya
fesa turare sama da kala hudu. Hula da takalmin
bakake, ya nufi Masallaci, daga can za shi gidan
su Umma don jin karin bayani. Bayan sun idar da
Sallah, mutane suka yi ta masa murna, nan ya
hadu da su Alhaji kawai yau sai ya samu kansa
da kunyar Alhajin. Alhaji ya ce, "Ubana ina ka
shige duk yau?" Ya rasa me zai ce, sai in-ina
"Am...na kwanta ne bana jin dadi". Alhaji yayi
'yar dariya, "Kai dai ka ce kana taya kanwarka
fushi don mun ce ba zamu daga aure ba, to ba
mu daga ba amma Allah cikin ikonsa ya sauya
lamarin". Abba tamkar bai san komai ba, ya ce
"Alhaji me kuma ya faru?" Alhaji Karami ya
karaso gurin su yana cewa, "Kai Abba ina ka
shige ne?" Abba ya dube shi "Nan dan Agundi na
shiga". Alhaji ya ce, "Oho, shi yasa aka yi ta
nemanka. To ka ji kuma yadda lamari ya sauya
ko?" Alhaji Babba ya amsa tare da cewa, "Shi ne
nake massa bayani, wato Abba iyayen yaron nan
Sahabi muka yi ta jiransu su zo gurin daurin
aure, wai ashe su sun fasa. Amma ba su shaida
mana ba har bin su fa nasa aka yi, gashi mun
tara jama'a kawai sai Aminu da Ummanka suka
ce a daura da kai, da ni na ce a daura da Bashir".
Dadi ya lullu6e Abba irin wanda bai ta6a ji ba,
Alhaji ya ci gaba da cewa, kayi hakuri mun kara
maka nauyi ba tare da mun ji ra'ayinka ba". Abba
cikin matukar murna ya ce, "Haba, ai ko ba 'yar
uwata ba ku ka daura min aure da ita zan aminta
bare jinina. Nagode". Sun ji mamakin yanda Abba
yayi murna, duk da sun san biyayya irin tashi ba
zai 'ki ba, tare suka rankaya gidan su Umman, so
kurum yake yaga Ummi. Ba mutane sosai, don
haka har ciki ya kutsa, sai dai suna hada ido da
Umma sai ya ji nauyinta, ta fada da fara'a. "Ina
ka shige Abba?" Yayi dan murmushi, ta ci gaba
"Sai kuma ka ji yanda abu ya kasance?" Ya ce,
"Na ji Umma, Allah yasa haka shi ne alkairi". Ta
ce, "Amin, Insha Allahu". Tamkar ya tambayi ina
Ummin, amma ya kasa. Umma ta ce "A baka
abinci ko?" sai lokacin ya tuna da batun abinci,
amma baya gabanshi, ya ce "Na koshi Umma".
Ta ce, "To ga na 'yan asibiti can in kayi isha'i".
Da sauri ya ce "Wa ke asibiti kuma?" Ta ce,
"Ummi ce, ko 'yan daurin auran ba su watse ba
don ka ji yarintar nan ta hau farin suma don
haushi ko leka su ban yi ba. Tana can it da
Saratu sai Tsohuwa da ta matsa yanzun Alhaji
Karami ya kai ta". Jikin Abba ya yi sanyi, kenan
tsabar rashin sonshi ne ya saka Ummi suma? Ya
ce Umma bani abincin asibitin. Sai da yaje
gidanshi ya dauko dan mukullin motar, a
zuciyarshi yana tambayar kanshi ina kuma
Bishira tayi ne? Zai bude motar kenan muryar
Bashir ta dakar da shi, "Kaci nasarar samun furen
zuciyata, amma ka sani ka kulla abota da rashin
zaman lafiya a novels / ZURFIN CIKI book 3 part 7
ZURFIN CIKI book 3 part 7
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:33
kulla abota da rashin zaman lafiya a gidanka". *
52..A fusace abba ya dubeshi"xansa yan sanda
su rufe min kai inhar zaka cigaba da kiran matata
da furen zuciyarka,rashin zaman lfy kake cewa?
An dade ba'ayi yaki abgdn ba kullum,bashir yace
oho dai ni zanta zuga umma abba yaja tsaki
tareda shigewa motarshi. Bashir yashiga gdnsu
inda su ummanshi dasu bishirabke zaune jugum
jugum tamkar masu zaman makoki,bishira tabi
bashir da kallo lkcn dayace ga ya abba ya can a
waje yashiga mota ya kure wanka,kila ma asibiti
zaije ana fada maku yanaso kuna wani tilasta shi
akayi,bishira cikin dasahhshiyar murya tace aiko
da bala'i don ko bazan yarda ba,umman bashir
tace sha kutuminki bishira,barni dasu zan
maganinsu, bishira tafita fuu,amma saidai. Kafin
ta isa gurin motar tuni ya, Cilla yabar mata
hayaki. Da innna saratu kanwar umma ya soma
cin karo a asibitun suka gaisa,tace ashe kuma
haka abu ya zama? Yace eh"nima dana dawo
dazu nasamu lbrin,tace Allah yasa hakan shine
mafi alkhairi,abba yace ameen inna,ya mai jikin?
Tace dasauki,yace bacci take? Tace a'a ta farka
tun kusan karfe uku,koda fatima ta fada mata
yanda abubuwa zuka zama,tayita yan koke
kokenta,gaban abba yafadi****tabbas ummi ba
son shi take ba inba hka ba meye na kuka? Ya
kalli inna bari in karasa,tace to kaje tshuwa na
ciki,a ranshi yace jaraba road,yasan dai ko yane
sai tshuwa tayi mishi surutu,yana tura kofar
tareda salama suka hada ido da ummi,sun kure
juna da kallo,kowanne nason ya fahimci ya dan
uwansa yadauki abin"tshuwa ta katse su dacewa
to zakin fama sai ynz kaga daman zuwa? Ya
dubeta eh" ai eh ace? To me kikeso ince,tace to
madalla ai na dade da sanin halinka,kuma da ace
iyayenku sunyi shawara dani lallai da baza suyi
wanna hadin ba Domin na tabbata kai zaka
karasa takwara don baka kaunarta, haushi ya
cika abba abba yana kallon tsohuwa yana tuna
amsar data dace da ita, ummi kuwa tsura mishi
ido tayi tana son jin me zaice,yace kamar kin
sani,tace ahaf shiyasa tausan yar nan kebani
tausayi, ta soma matsar ido,yace nima yakamata.
ki tausayamin tnda cusa min ita akayi,ummi
takoma ta kwanta lakwas tareda hakikancewabl
kalaman abba sako ne zuwa gareta,matar cushe
kuma bata daraja,to inaso kasan wani abu
guda,duk randa naji wani abu daidai da
wulakanci, toba kaiba har iyayenka saisun san
naje makura. 52..Dazun nake gaya masu basun
hada kai sun kulla auren nan ba,duk randa suka
kuskura sukazo min da batun warwareshi saina
basu mamaki,abba ya tabe baki tareda kallon
ummi wadda takasa jurewa tashiga rera kuka,ya
isa gaban gadon,"jikin ne ummi? Tayi shuru,kinci
abinci? Nan ma ta share,sai kurum ya nufi wurin
likitan zuciyarshi na kuna bako shakka kukan kin
shi ummi keyi,sun zo da likita ya shiga yimata
fadan kukan da takeyi,a cewar likitan kukan illa
ne ga lafiyarta,tshuwa ta kalli likita dan nan dole
ta koka a dauke ka ahadaka da wanda baya
kaunarka"abba cikin takaici yace subhanallla! Don
Allah tshuwa kibarni inji da abinda ke
gabana,tace ina ruwana da abinda ke
gabanka,likita yayi dariya yace mama yakamata
ki koma gd haka,abba yace bari inkaita
indawo,tace ban binka da can dani kazo? Abba
yace nahuta,likita yayi dariya,da kyar suka lallaba
tshuwa ta tafi da inna saratu,abba yaja kujera ya
zauna gaban gadon,bayan fitan likita Idanu ya
zuba ma ummi,godiya yake ma Allah a zucin shi
daya amsa addu'ar shi yabashi abar sonshi,itako
kai ta dukar a ynz takasa tantance kukan farin
ciki take ko takaicin kalaman ya abbanta? Wani.
Dan zare dake jikin hijabinta take wasa dashi,a
zuciyarta kuma tambayoyi ne da fuska data jefa
masa su,ya katse ta kinci abinci? Ta daga kai
alamun eh" yace to yakamata ki dangana da
kukan haka kisani ni kaina da ina nan bazan bari
su alhji su daura maki aure da wanda bakiso ba.
53..Da sauri ta kalleshi,yace. amma inkin yi hkr
zansame su zamu san yadda zamuyi,ta lumshe
ido a zuciya tace tab! Ai rabamu sai mutuwa,zan
juri duk wani ki dazan gani daga gareka,ya
katsxeta kina zance a zuci fadi abnd kikeson
cewa,tayi tagumi tareda kallonshi,ya abba yakanfi
dacewa sa dan sanda ne ba dan jarida ba,sbd
yanada saurin nazartar mutum,to amma meyasa
yakasa gane tana son shi? Yayi murmushi,zanso
inji abnda kikeb saqawa azuciyarki ko kinn samo
mafita ne? 29. Zancan mafitar nan tana bata
haushi, don haka saita canza zancen da cewa,
tambaya zan maka guda biyu, ya dan yi shiru.
Nazari yake, wace irin tambaya zata masa? Kila
zata tambaye shi ne ko zai amince ya sahale
mata auranshi, ya dubeta amsa daya zan ba ki in
kin yarda, ta ce To dama zance ne ya ka ji
lokacin da labarin sauyawar lamari ya zo gareka?
Ya kura ta da ido, ya tambayi kansa a zuciya, me
yasa take son ji@ yayi dan yake, yi tambayarki ta
gaba, ta tsura mishi ido. Yanzun yaya za ka yi da
maganar Zainab? Ya yi 'yar dariya, wacce amsa
ki ke so a ciki? da sauri ta ce ba ni wannan
amsar. Ya ce, "Kiin manta ni mijin mace hudu ne?
Ta zaro ido kamar ya ya? Ya yi kokarin danne
dariyarsa, sakamakon yanda ya ga ta zarana. Ya
ce, "Ina nufin bayan Zainab har da wata, Ummi ta
hade rai sannan ta zame ta kwanta cike da dana
sanin tambayar. Abba ya yi mamakin kishin
Ummi gare shi, ita da ba sonshi take ba? Ko da
yake an ce mace ko bata son namiji in dai mijinta
ne ta tsani ta ganshi da wata. Duk da haka ya ji
dadin yanda ta nuna kishinta a kanshi, da ya tuna
da Bishira ya ce tab, wata fitinar tana can tana
jirana yau. Sam Ummi bata kara magana ba, shi
kam Abba waya ma yake tayi Inna Saratu ta
dawo, don haka ya mike ya kalli Ummi. Zan tafi
ba tare da ta dago ba ta ce, sai anjima. Ya tafi
yana waiwayonta bayan ya wa Inna Sallama. Kin
shiga gidanshi ya yi sai kusan sha biyu a nufinshi
lokacin Bishira tayi bacci, sannan yaje ya sai
mata wayar da layi don yasan tana son waya.
Kudinshi kenan ma ya kwashe ya sai mata, bai yi
wani motsin kirki ba don kada ta farka, ya bude
dakinshi ya shiga ya fito yana jan ruwan wanka
kenan ta fito daure da zani a kirji. Jikinta ko dan
kwali babu, gaban Abba ya fadi ta ce, "Munafukin
Allah, annamimi dama ashe abinda kuke shiryawa
kenan? To ka sani dole kasa ke ni don ba zan iya
zama da Ummi ba, Allah ya kiyaye in hada miji da
wannan 'yar yarinyar, tunda kai baka ga ai baya
ba". Ya sassauta murya, "Haba Bishira, wannan
abin fa Allah ya kaddaro za a yi haka, matar
murtum kabarinsa. Ta ce, "To wannan ajalinka ce
tunda wancan ya ki shi ne kai a ka cusa maka.
Ya bar jan ruwan ya kama hannunta suka nufi
dakinta, tana ta masifa. Ya ce, kibar maganar
yanzu dare ne duk makota suna ji za su yi, kuma
banga bain da zai sa ki daga hankalinki ba. Kin
san dai ina sonki ko? Ta yi shiru tana kallonshi,
ya ce ina zuwa. Yaje dakinshi wayar ya dauko
mata, ga wayarki. Ta ce, "Eh don ka toshe min
baki k? to bana so, ita wa ya san abinda ka sai
mata? Ya ce, ya ki ke wannan maganar? Ban sai
komai ba ko lefe ma tukunna. Ta mike tare da
jefa mishi kwalin wayar, Ga tsiyarka nan
matsiyaci, dole ka saka min da haka, tuni a ka
gaya min tsiyar talaka na tafe. Haushi ya kama
Abba ya dauki wayarshi ya tafi ya maida yazo ya
dau ruwanshi yayi wanka, yana jiyo kukanta da
duk zage-zagen da take yi. Shi kam katifarshi ya
fada tare da rungume fito yana tunanin ranar da
Ummi zata maye gurbin filon. 30. Har an tada
sallah a Masallaci lokacin da ya farka, ya jima
bai yi irin wannan baccin ba, da hanzari ya fito
ya nufi ban daki don alwala. Abin mamaki Bishira
ce zaune kan kujera a kofar dakinta, matar da sai
ta kai takwas bata farka ba, amma yau bala'in
kishi ya hanata bacci. Ta ce, "Eh na fito a ba ni
takardata na gama zama da kai, ko in da take bai
kalla ba ya ci gaba da abinda ke gabanshi, ya
nufi Masallaci yana jinta tana ina nan ina jira ba
zan zauna ba. Haba, gaskiya naji na tsani
yarinyar ashe mijina zata aura, tsaki ya yi ya
bude gidan ya fice. Har gari ya soma haske yana
cikin masallacin, tunanin zuwa gidan yake, daga
karshe dai ya fita da niyyar zuwa gidan
Ummarshi. Wata zuciyar ta tambaye shi da cewa,
tsoron ta ka ke ji ne? Kar ka zama soko dai a
gidanka. A fili ya furta cewa, tunda na bita ta
lalama ta ki, bari in koma mata ta zafin, ida din
me? Sai ya sauya hanya zuwa gida rai 6ace,
fuska daure ya shiga gidan, tana ta kai-kawo a
tsakar gida. Ta dumfaroshi sai ka ce sabon
kamun hauka, daga ganinshi ta dinfaroshi. "Ka
ban takardata ba ni ba zama da kai, tafiya zan
yi". Ya harareta "Sai da takarda za ki tafi? Lallai
ba ki ji tafiyar ba. To ba zan bada takarda ba,
don ki sani, sai dai in kotu za ki kai can Alkali ya
baki". Ta nufo shi da zummar shako masa kwala,
ya ce Kina ta6a ni sai na zane ki, in yaso ki tafi
da hujja". Ganin yanda Abba ya bude mata wuta
sai taja baya, Ka isa ka zane ni, ai da ka san ka
dake ni, don ko sai ka sha dauri. Ya nufi dakinshi,
wanka ya fito yayi sannan ya yi shirin tafiya aiki,
amma har lokacin tana nan, ga 'yarta ta tashi
daga bacci sai kuka take yi. Ta dauke ta ta goya,
ta shiga dakinta can kuma ta sauke 'yar tasa
kaya ta fito ta dauraye fuska da kafa ta goya 'yar
tasa kaya ta fito taja kofar tana fadin." "Tafiya
zan yi". Ta fito ta same shi yana goge gilashin
motarsa na gaba. Ta ce, Tafiya zan yi sai an
kar6ar min hakkina". Murmushi ya saki, sannan
ya kalleta, ta ina za ki bi in rage miki hanya? Ta
dawo ta duki motar, Ba zan shiga wannan
gwanganin motar ba, kai ne bakon mota. Kafi
kowa sanin daga gidan da na fito, ko motar zuwa
cefanen gidanmu tafi wannan tsarri. Ya ce.
"Gurinki ko? Ni ai bani da wadda ta fita tunda
bata gidan naku nike hawa ba. Sannan kuma
tunda ba za ki zo in rage miki hanya ba shi
kenan sai naga sammaci. Ya shiga motar ya
tasheta yayi gaba, ba tare da ya saurari abinda
take cewa ba. Ta isa gidansu cikin tashin hankali,
Hajiya Zainu ta saurare ta tsaf, sannan ta ce "Kin
dai ga abinda a ke fada miki, kina ganin ba zai
faru ba ke so ya rufe miki ido, to yanzu an zo
gurin. Bishira ta ce, "Ai na gane komai yanzun,
Momy nayi nadama. Ta ce, "To zan tsaya miki
matsalata Babanku, yana nan a gari na kuma san
za su zo iyayen Abba. Amma wannan karon shi
kanshi Babankun zan iya ja da shi, Bishira taji
dadi sosai, don kuwa duk son da ta ke wa Abba
yanzun kishi yasa ya koma 'ki. Gidansu Umma
yaje a gurguje suka gaisa, ya kwashe su da Alhaji
da Alhaji Karami zuwa asibiti, a motar nema ya
ke fada musu cewa Bishira ta tafi gidansu Umma
ta ce a kan me Abba, me ka mata? Ya ce, "Ban
mata komai ba, ya fada musu duk yanda aka yi.
Alhaji Karami ya ce, Sahura ke zugata, itama ai
kwana tayi bala'in. Don haka kada kaje bikonta,
Alhaji Babba ya ce, "Ba za a yi haka ba, da dare
kazo muje, Abba ya ce To. Sun isa asibitin tana
wanka, sun gaisa da Inna Saratu ta fada musu
tana wanka, sannan likitan ya sallame su amma
sai sha biyu za su tafi gida, lokacin an karasa
mata allura. Abba can baya ya tsaya kusa da
kofar shigowa ya jingina da bango idanunshi suna
fuskantar kofar bayin, matuka ya kosa yaga
Ummi. Sanye da hijabi da zani daurin kirji ta fito,
da Abba suka soma hada ido, bai ta6a kallon
Ummi da sha'awa ba sai yau. Kamshin turaren
Abba ya ratsa ko'ina a dakin, ta zare idanunta
daga nashi, ta kalli Ummanta sannunku Umma.
Suka ce Yauwa. Ta gaida su sannan ta zauna
bakin gado tare da sunkuyar da kai, Alhaji Karami
ya ce, "Uwata jiki kuma ya yi sauki ko? Kanta na
kasa ta ce, Eh, ta kasa dago kanta, gani take
Abba ya cika dakin. Abban ya ce, "To ni zan tafi
don lokacin aikina ya kusa, Alhaji zamu je ne in
sauke ku? Suka ce To, Umma ta ce In an yi mata
Allurar anjima ma nemo mai Taxi. Alhaji ya ce, To
shi ke nan. Umma ta dubi Ummi ba za ki gaida
Yayan naki ba? Ta saci kallon Abban tare da
cewa, Au, ban ganshi ba. Ina yini? Ya ce, Umma
me yasa za ki rokar min gaisuwarta? Inna Saratu
ta ce, Kai Ummi da iya shege take, ina kallonta
shi ta fara kare ma kallo sannan ta kalli kowa
amma wai bata ganshi ba. Su Alhaji dai 'yar
dariya suka yi sannan suka fita, Abba ya bi su
tare da yi wa su Umma sallama. * 31. Bayan
fitarsu, Umma ta dubi Ummi fuska daure, ina
fatan baki nuna damarar nuna kiyayya ga Abba
ba ne? Ummi ta sunkuyar da kai, a ranta ta ce,
"Kin ji Umma da wani zance, ai ina zaton nafi
Mahaifiyarshi sonshi ma bare ku. "Amma a fili sai
ta ce, To Umma shi ma fa Ya Abban bai ce yana
sona ba, Umma ta ce Saratu ji ta da wani shirme.
Ina ce ita ce zata janyo ra'ayinshi gareta? Inna
Saratu ta ce, Kwarai kuwa, ta hanyar ladabi,
biyayya da girmamashi, musamman shi da ke da
matsalar mata. Ummi ta ce, Kuma ina tsoron
masifar matarsa ba dai guri daya zamu zauna ba
ko? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?
Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai
kama? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?
Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai
kama? Kada ma in ji kin kuma zan nan, Ummi dai
tayi shiru. Da dare Alhaji ya tasa Abba zuwa
gidan su Bishira, zuwan su ne ma Alhajin yasan
'yarshi tayo yaji, cikin 6acin rai ya kira wayar
Hajiya Zainu ya ce su zo ita da Bishira. Ba tare
da ya jira amsarta ba ya aje wayar, ba tare da
yasan abinda ya faru ba ya shiga ba su hakuri.
Hajiya Zainau taje dakin su Bishira ta kira, suka
nufi sashen Alhajin tana mitar cewa munafukai
sun zo kenan, ai za'ayi ta bari muje mu ji. Suna
shiga Alhajin ya kalli Bishira, "Me ki ka zo min ki
yi a gida? Ta ce, Daddy cin amanata ya yi, aure
fa ya yi da yarinyar da suka tsane ni. Alhajin ya
daukin da ke gabanshi na plastik ya jefe ta da
shi, auren shi ne cin amana don uwaki? Hajiya
Zainu ta ce, "A'a Alhaji, zan cen gaskiya a duba
hakkinta itama, ya ya za a dau 'yar da bata
kaunarta, iyayenta basa kaunarta a ba shi.
Sannan ta yi magana ya hauta da zagin iyaye?
Ya ce, "Ke yi min shiru ban tambaye ki ba". Ya
kalli Abba, Ya abin ya faru? Ban ji ta bakinka ba?
Nan dai Abba ya fadi komai har ta taho, daidai da
cewa tazo ya rage mata haya da abin da ta ce
duka. Alhajin ya yi tsaki ya dubi Alhaji Babba, irin
wannan ai ba a biyo su, tayi ta tafiya sai dai
nima in ba zata koma gidanta ba, to ba gidana
ba. Ya zura hannu cikin aljihu ya ciro rafar 'yan
dari bibbiyu, Ga shi Abba, dama nayi maka
alkawarin baka sadaki duk lokacin da ka nemo
aure. 57..... Abba ya ce, "A'a ka bar su ai an riga
an yi. Mahaifin Bishira ya ce, "Ni nayi alkawari.
Suka yi godiya. Ya kalli Bishira, Ko ki bi mijinki,
ko ki bar gidana. Hajiya Zainu ji take tamkar ta
shake Abba. Ta ce, "Haba Alhaji, gaskiya ban
yarda da wannann hukuncin..." Ya katse ta da
cewa, Ke! Da Allah fita anan. Su Abba suna shiga
mota Bishira na fitowa da kukanta, dole ta zo ta
shiga motar. Alhaji Babba ke ta bata baki har
suka kai gida, shi kam Abba da suke sauke Alhaji
ya yi nasu gidan, suna shiga ta soma zantuka. Ba
za ka ta6a samun kwanciyar hankali ba a gidan
nan har abada, ba dai ka matsa an dawo da ni
ba? Abba ya yi murmushin mugunta, ai ni
wannan yajin naki naji dadinsa, gashi har na
samu gudunmawa, kin ga sai naje kasuwa in
soma darzo wa Amarya zannuwan lefe. Ya nufi
dakinshi ya barta nan tsaye tana zage- zage,
lefen banza, in ma uban lefe ne kai da ita sai na
koya musu hankali. Kusan goman dare Ummi
tana kan doguwar kujera, addu'a take yi Allah
yasa Abba yazo ta ganshi kafin tayi bacci. Can
kasan zuciyarta kuma kishi ne don tasan sun je
gidansu Bishira ne biko ganin Alhaji ya shigo shi
daya sai ta debe tsammani da zuwanshi. A ranta
take raya cewa yanzun haka suna can suna cin
soyayyarsu, kamshin turaren shi ne ke mata gizo
a hanci. Amma sai kunnuwanta suka tsinkayi
sallamarshi, a hankali tamkar ba ya son a san ya
shigo. Umma tana ciki? Tambayar da ya yi kenan
ba tare da ya jira ta amsa sallamar ba, ta tashi
zaune da sauri a'a tana gurin Alhaji. Ya shigo ya
zauna ta ce, "Sannu da zuwa". Ya amsa yana
kalonta, ta sunkuyar da kai, gabanta ke wata irin
faduwa. Shi kam ji yake tamkar ya manne ta a
jikinshi, sai dai yana jin nauyin hakan tunda ba
suyi wannan sabon da ba rin haka zata faru
tsakaninsu ba. Dakin yayi shiru, ita tana wasa da
yatsunta shi kuma yana kallonta, can ya ce
"Ummi". Ta dube shi "Yaushe za ki tare? Ta ce,
Nima ban sani ba, sai yanda su Umma suka ce.
Ya dauko kwalin wayar da ya sai ma Bishira ta
jefe shi da shi ya ciro wayar ya hadata da batir
din bayan ya 6are sim din ya saka. Ummi dai
tana ta kallonshi, ya manna chajar a jiki, ya mika
ma Ummi jona min can, ya nuna mata soke din
da ke bayanta. Ta amsa cike da sha'awar wayar
duk da bata nuna hakan ba sannan ba ta ce kala
ba. Ya ci gaba da cewa, "Karfe nawa a ke kashe
inji? Ta ce, har yanzu ba a canza daga yanda ka
ke kashewa ba. Ya ce, "Sha daya zuwa sha biyu?
Ta ce, "Eh, ya ce in har zuwa wannan lokacin ba
kiyi bacci ba to ki cire in an kashe, ki kunna ko da
yake in dai ke ce ba sai na ce ki kunna ba. Ta
dago ido ta kalle shi, ya ce, Eh kunnawa za ki yi
ko za ki musa ne? Don kin fi ni ma sanin kan
waya. Ta ce, Wayar Umma kadai na iya kunnawa,
sai taka. Ya ce, Oho, cikin dan murmushi, na za
ci ba za ki fadi tawa ba in tuna miki lokacin da
kika kunna tawa. Haka nan don tsabar iya sarrafa
wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin
Kaduna. * 58....Haka nan don tsabar iya sarrafa
wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin
Kaduna. Ta zuba fuskarta cikin tafukan
hannayenta, sam bata son Ya Abba yana tada
wannan zancen, Umma ta shigo da sallama tana
cewa, Yuwa Ummi, ina ki ka sa min 'yar kwalbar
turaren nan? Ummi ta dago fuska, "Cikin jakarki
ta rataye. Umma ta dubi Abba, "A'a ha, yaushe
ka shigo? Ya ce Ban jima sosai ba. Ta zauna ya
gaisheta, sannan ta ce masa dama Alhaji yanzu
yake ce min zaman me Ummi ke yi a gidan nan?
Ya zaci tun daga asibitin zata wuce dakinta,
Ummi ta turo baki. Umma Alhaji ya gaji da ni
sosai, suka kalle ta, Umma ta ce, Ji wani shirme,
me ya yi na gajiya? Ta ce To dubi fa daga cewa
an fasa aurena sai da ya matsa ya daura min
aure. Sannann kuma yanzun wai ya zaci daga
asibiti zan tare? Abba ya ce, Ai yana daki yi
hanzari ki same shi don shi ya san amsarki ba
Ummata ba. Umma ta ce, "Wallahi daga nan suka
share Ummi. Ta kalli Abba ta ce, "To kawai
yanda za a yi gobe ka kwashe kayanka daga
dakinka sai a kai na Ummi din kawai. In yaso
zuwa yamma ko Saratu da sauran makota sai su
rakota. Abba ya kalli Umma, ni da so nayi a dan
yi kwaskwarima a gidan kafin sannan na dan
samu na sai ma Ummin Zannuwa. Umma ta ce,
"Zancen wofi, yanzun tsirara take yawo? Kawai in
kana da fenti a hannu a goga a kawo ta haka, in
babu ma dai goben nan zata tare don ba zan
amince ran mijina ya 6aci ba. Abba ya yi
murmushi, to shi kenan Umma da safe kafin na
fita zan nemo masu aiki ina da fenti da siminti
sai ayi 'yar kwaskwarima shi ke nan. Dama ga
kudi nan da Mahaifin Bishira ya bani, wai dama
ya yi min alkawarin biya min sadaki. . 59...
Umma ta ce, "Yanzun Alhaji ya gama bani labari,
Mahaifin yarinyar nan mutumin kwarai ne, don
Allah Abba ka rike yarinyar nan ko don darajar
mahaifinta. Ummi ta ta6a baki, kishi ya motsa.
Abba ya ce "In sha Allahu Umma nima abinda
nike dubawa kenan, ni ke hakuri da ita. Ta ci
gaba da cewa, Sannan kada kaga Ummi yar
uwarka ce ka ce zaka fifitata, sam ba zan yarda
da haka ba. Kayi adalci a tsakaninsu ka dinga
addu'a Allah ya hada maka kansu. Ya ce, "In
Allah ya yarda Umma zan kula. Ta ce, "To maza
ka tashi ka tafi gurin iyalinka. Sam bai ma dace
ka fito ba, kamata ya yi a ce ka zauna gida ka
kara ba matarka baki, ya cee To Umma. Ta mike
tana cewa, tashi maza. Ya mike yana kallon
Ummi, yayin da ita kuma ta juya fuskarta cike da
6acin rai. Ya ce, Ummi ki fa kunna in an kashe
injin? Sam ba ta tanka ba don haushi, sai da ya
tafi sannan Umma ta dubi Ummi. Ki tashi ki
kwanta don gobe ki tashi da wuri, kiyi duk shirin
da ya dace saboda babu daga kafa a tarewarki
gobe. Ki ta fasha-fishenki ba zamu kuma yarda
da kalace-kalacen ciwonki ba, ta tafi abinta. A
zaton Umma, Ummi tana fushin ba zata tare ba
ne, ita ko haushinta korar mata miji da Umma
tayi ya tafi gurin kishiyarta. Koda ta kulle kofar
ba ta shiga uwar dakin ba, nan kan doguwar
kujeta ta mike abinta. Jira ta ke a kashe Injin ta
kunna waya. Abba ko kafin ya isa gida sai da ya
fita titi ya fanshi kaji guda biyu da madara mai
tsafta.I novels / ZURFIN CIKI book 3 part 8
ZURFIN CIKI book 3 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:37
Jira ta ke a kashe Injin ta kunna waya. Abba ko
kafin ya isa gida sai da ya fita titi ya fanshi kaji
guda biyu da madara mai tsafta. 60...Sai dai
yana shiga gidan ya iske mahaifiyarshi da matar
tashi suna ta zage- zage. Ya nufi gurinsu, Sahura
ta ce, Sai yanzun suka barka ka taho? Ya ce,
"Umma dama ban dade da zuwa ba". Ta ce, "Ina
ta aiken kazo ina nemanka shi ne ka 'ki zuwa
saboda ka maida ni 'yar iska ko? Ya ce, A'a
Umma ba a fada min ba. Sannan aiki ne yasha
kaina... Ta ce, "Rufe min baki, ai baka daga kafa
da zuwa gun Suwaiba. To saurare ni da kyau ka
ji, nazo ne in fada maka cewa ka rubuta saki ka
ba wannan 'yar iskar yarinyar. Ya ce, Kiyi hakuri
Umma, ki bari sai a hankali. Bishira ta ce, Umma
yana sonta fa, jin ku kawai nake. Maganar Bashir
gaskiya ce da ya ce da shi a ka shirya hakan.
Umman Bashir ta ce, "Dama Abba kaima son
Ummi ka ke yi? Ya ce, Umma ba zan ki Ummi ba,
in kun yi la'akari da kaunar da iyayenta suke
nuna min. Amman wallahi ban san komai game
da auranmu ba, ta ce kana nufin kan dole a ka
daura muku aure ba don kana sonta ba? Abba ya
yi dan jim, ta ce kai nake sauraro, don ta tafi sai
ya ce kusan haka dinne, itama kuma ba sona take
ba. Umma ta ce, Ina ruwana da bata sonka, in
bata so iyayenta ai suna so. Ni dai bukatata
yanzun kada ka bari ta tare, sannan ko kusa kada
taga fuska a gurinka. 33. 61... Umma ta ce, "Ina
ruwana da bata sonka, in bata so iyayenta ai
suna so. Ni dai bukatata yanzu kada ka bari ta
tare, sannan ko kusa kada taga fuska a gurinka".
Ya dan yi shiru yana tunanin wannan irin lamari a
zuciyarshi ya ce, bari kawai in lalla6ata, zan yi
yanda ki ka ce sai dai kuma in su Alhaji suka sa
kawo ta ni ba zan iya ja da su ba. Sannann ke
kanki bana so a ce ke ki ka sa ni in ma Ummi
rashin mutunci, amma ki bar ni da ita in har ta
yarda ta tare a nan gidan. Bishira ta ce, "Tab, ba
ko zata tare a nan gidan ba". Umma ta ce "A'a ki
bari in sun matsa ta tare a nan din ta tare, gara
suna kusa muna kallon irin zaman da za su yi.
Can gefe ba sai su rinjaye shi ba". Bishira ta ce,
"Umma na tsani shegiyar yarinyar nan ne, bana
son in ganta ko cikin mafarkina, bare a zahiri".
Sahura ta ce, "Bishira na ce ki nutsu ki bar komai
a hannuna, in ma zan hada da Bokaye ne ba
Malamai ba in sha Allahu sai kin dara a gidan
nan. Ta ce, "To Umma, Sahura ta ce, Yauwa ke
dai ki zuba ido, Abba dai yana tsaye yana
kallonsu. Sai lokacin yayi magana, Umma dare fa
yayi, ta ce to muga ledar hannunka, ya mika
mata. Ta buda ta gani, "A'a kaza? To ku zuba
min nawa". Ya mika wa Bishira, Ki dibarwa
Umma. Ya nufi dakinsa yana jin sallamarta tana
fadin ta wuce, ya fito ya ce "To Umma sai da
safe, ya rufe gidan ya koma dakinsa. Da ya shigo
gidan ne da niyyar lallashin Bishira, amma yanda
abubuwan suka zama sai ya ji ba ma ya son
ganin Bishiran. Zantukan Bishiran da na
Mahaifiyarshi sun saka shi cikin tunani, lamo ya
kwanta a kan katifa yana ta harsaso irin zaman
da za a yi a gidan. Anya kuwa ba zai kama wa
Ummi haya ba? Cak! Hasken wutar dakin ya
dauke tare da tsayawar Injin. A fili ya futa, Mai
ya kare kenan, sai da ya yi shirin bacci ya
kwanta tare da manne filo a kirjinshi, sannan ya
dauko wayarshi ya kira layin da ya hada cikin
sabuwar wayar da ya ba Ummi. 62.. Gabanta ne
ya fadi, lokacin da taga lambar Ya Abba suna
rawa a fuskar wayar, ta haddace lambobinshi tun
shekarun baya. A fili ta ce, kenan ma ya hada
wayar ba yau ya soma hada ta ba, ta sake yin
lamo a kan gado tare da janyo filo ta manna a
kirjinta. Ta daga wayar lokacin tana daf da
tsinkikewa, can cikin makoshinta tayi sallama. Ya
amsa, tsigar jikinsa a tashe sakamon jin muryarta
tana ratsa jikinshi, ya ce "Ummi, ta ce Na'am Ya
Abba. Ya ce, "Kina son ki tare goben? Ta lumshe
ido, ba ni da za6i Ya Abba, duk yanda ku ka ce.
Dadi ya cika zuciyarshi. To shi kenan ki tare
goben, zan yi parking tun Asubahi sai in sa mai
fenti yayi kafin in tafi aiki. Ta ce, "Ba an ce in
mutum ya yi aure ana ba shi hutu ba? Ya yi 'yar
dariya, "To ni ba ki ga yanda auren nawwa yazo
daga sama ba? Amma duk da haka in na nemi
hutun za a bani, ta ce kayi aikin kama kawai ba
sai ka nemi hutu ba.. Ya katseta, "Don ba a sona
shi yasa ba a damu na amshi hutu ba? Ta ce,
"Ba nufina kenan ba, naga kana matukar son
aikinka ne". Ya yi dan murmushi "Kin dai
wayance kawai, to yanzun haka zaki tare babu ko
dan kunshi bare gyaran kai irin na Amare? Koda
yake ba aure so ba ne. Cikin muryar shagwa6a ta
ce, "Ya Abba ka daina, ya ce me zan daina? Kana
cewa bana sona, ai kai ma ba ka sona... Ya dan
yi shiru, yanda ta ke shagwa6ar ne ta tsuma shi.
Ya ce, ok, to goben sai kije ki gyaranki ko? ta ce,
"Umma ba za ta bari in fita ba, amma me yin
fulawa za ta iya ta mini". Ya ce, "To ina ne a ke
gyaran gashin? Ta ce, "Cikin gari ne, ya ce kin
san gurin? Ta ce, "Eh, amma ban ta6a yi ba, ya
ce to ki bari zan shigo gidan kafin na tafi aiki zan
ce Umma ta bar ki, ta ce "To." Suka dan yi shiru.
Can ya katse shirun da cewa, "Me ki ke tunani?"
"Yaushe?" "Yanzun." Ta dan musukuta, "Ina
tunanin yanda abubuwan za su kasance gobe.
Yanda har za'a yi fenti, sannan a jire kuma in tare
duk a gobe". Ya ce "Duk mai sauki ne, ni kuma
kin san tunanin da nake yi yanzun? Ta ce, "A'a,
ya ce gobe kamar yanzun muna tare... da sauri ta
katse wayar, me Ya Abba ke son fada? Ta kashe
wayar sannan ta kudundune. Ita ma yanzun ya
jona mata wannan tunanin, a fili ta furta gobe
kamar yanzun me ya ke faruwa? Shi kuwa sai ya
ji haushin kansa sakamakon furucin da ya yi har
ta yanke wayar, wani gefen kuma sai ya ga kila
don bata sonshi ne shi yasa har ta ji haushin
furucin nashi. Kila ma yanzun tana can tana kuka
in ta tuna gobe tana gidansa, dare ya tsala amma
ya kasa bacci, don haka sai ya mike yayo alwala.
Sallah ya shiga don kara nuna godiyarsa ga Allah
da ya bashi Ummi tare da rokon Allah ya kimsa
mata sonshi, daga karshe ya roki hadin kan
matansa. 34 63..Yana wanka da safe ya jiyo
muryar mum dinsa harta zo gdn, a zuciyarshi
yace innalillahi wa inna ilaihir raji'un, yana fitowa
tace wurinka nazo, Bashir yazo ya fada min cewa
yau za'a kawo fitsararriyar yarinyar nan ko? Abba
cikin damuwa yace umma nima bansani ba, tace
munafiki kasani, bari kaji ko an kawota ko
magana bance ta hadaku da ita ba, kai in ma
kaje girin munafukan iyayen nan nata su ka ce
yau zata tare kace saika shirya. Bishira tace
umma bazan yarda ta tare ba, bai sai min komai
ba, ya kalli Bishira to itama na sai mata wani
abun ne? Sahura tace to ina ruwan wani da baka
sai mata ba? Abba yace toni bani da kudi ma,
Bishira tace to kudin jiya da babana ya baka fa?
Umma tace fito dasu, yace umma dama fa kudin
sadaki ne ya biya min, kuma naba alhji karami
waliyyinta sai dai ki je gun shi ki amsa, tace don
kasan bazan tunkareshi bane shi yasa to tana
binka bashi, zaka chanza mata kayan daki, ka sai
mata zannuwa sannan ka bata jari, yace umma
banyi alkawari ba, in dai na samu kudi kuma ta
kwantar da hankalinta to xan mata, ya nufi daki
yabar su nan sunata zantukan su. Lkcn daya
shiga gdn su umman shi, ummi tana linke kaya
tana sakawa cikin jaka, yana daga bakin kofa ta
dago ta amsa sallamar shi ta kalle shi, ya kalli
kayan sam zuciyarshi bata mishi dadi, ya nufi
wurin umma don yana son neman alfarma abar
ummi zuwa dan wasu kwanaki don yana so ya
dan gyara gidan, rashin galihun zai yi yawa, ba
lefe kuma gida ba gyara? Yayi sallama suka
amsa, bayan ya gaishe su, ya dukar da kai yace
alhji dama nazo ne neman alfarma, suka ce
alfarman me? Yace inaso ne kudan bar ummi
zuwa nan da sati daya, sannan na gyara gdn,
kuma nayi mata sabbin dinki, alhji yace ba kana
da fentin ba? Kaje kasa a goga, sai ka biyo ta
kasuwarmu ka amshi zannuwa, abba yayi shuru
umma tace koda wani abu bayan nan? Yace a'a,
umma tace to an daga maka zuwa gobe, yace to
umma da alhji nagode, ya mike ya zai fita, yace
am umma ummi tace zata je gyaran gashi, suka
yi dariya su kace ai wannan ikon kane, yace to na
tafi alhji sainazo kasuwar, ummi ta jera masa
kayan karin kumallo koda ya leka dakin sai tace
ya abba ka shigo ga break, yace ummi zanyi latti,
tace to da yunwa zaka tafi? Yace akwai shayi a
can, tace come on ya abba zoka karya, ya kalli
agogo minti biyar gareni, ta dau copi ta tsiyayo
kunu ta mika masa, ya fara kurbar kunun, ta zubo
kosai a plate tarike a hannunta dauka kaci, ji take
tamkar ta bashi a baki, tsohuwa ta dago labulen
dakin, tace zura masa a baki za kiyi? Ummi tace
kada ya kware tsohuwa, an hana yin magana in
ana cin abinci, toshuwa tace tafi can da cusa kai
ba kwarjini, abba ya dire kofi tareda mikewa yace
ummi saina dawo, ki bari da dare zan kai ki
gyaran gashi, yasa hannu a aljihu ya zaro yan
dari binbiyu guda biyar ya bata, tayi godiya ya
ciro dari yaba tshuwa yace yar sa ido kema kiyi
kotso da wannan, ta rike baki tana fadin wannan
yara da munafunci suke, ya fita yana murmushi
ummi tace a dawo lfy, ya sake waiwayo wa ya
kalli ummi, suka saki murmushi, 35. 64....
Tsohuwa da ke bin su da ido ta ce, "Kai ban
yarda da ku ba Takwara, dama can ke da me
sunan Malam soyayya ku ke? ---- Umma da ta
tsinci zancen bayan fitowarta daga dakin Alhaji,
ta ce "Ya a ka yi?" Ta ce, "Suwaiba ina ga
yarannan tuni kallonmu kawai suke. Sai wannan
salo suke wa juna, sannan ga Takwara ciwon
barin gida shiru, ina ga dama ciwon nan na mai
sunan Malam ne." Umma ta saki dariya tare da
cewa "Allah yasa haka ne. Ummi kam cikin daki
ta kule zuciyarta zallah dadi. Misalin karfe biyu
Umma ta dan kishingide baya, ta idar da sallah,
tsuwar wayar da da Abba ya ba Ummi ajiya ce ta
farkar da ita. Ta ce, Ummi me ke tsuwa a dakin
nan? Wannan dai ba wayata ba ce. Ummi da ke
tsakar gida ana mata zanan fulawa ta ce, Lah,
Umma Ya Abba ne ya bani ajiya. Kila ma shi ne
ya kirata, ta dubi wadda ta yi mata zanen fulawar
ta ce Sabira don Allah shiga ki dauko min a kan
gado. 2missed call ta gani, ta ce kash! Sai gashi
ya sake kira, kafin ta daga sai da ta leka dakin
tsohuwa ta hango ta kwance a gadonta. Dama a
kofar dakin Tsohuwar take ta biyo inuwa ta daga
wayar tare da sallama, ya amsa cikin dokin jin
muryarta. Ina ki ka shiga ne? Ta amsa a can
cikin makoshinta, ana min fulawa a tsakar gida
wayar kuma tana daki. Ya ce, Ok ana miki zanen
fulawar ne? Ta ce an ma ganin har ya fara
bushewa ya saki murmushi tamkar yana gabanta.
Ana yi miki me kyau? Ta ce, Eh yayi kyau sosai,
ya ce Good, zan dawo kamar karfe uku saboda
zan kwashe kaya za a yi fenti a daki, so kin ga
ba zan samu kai ki gurin gyaran gashin da wuri
ba. 65... Don haka sai mu bar shi zuwa dare ko?
Ta ce, "To Ya Abba, ehm za a dafa maka wani
abu ne? Dadi ya lullu6e shi amma saboda
burinshi na kimanta Bishira a idonta sai ya a'ah.
Na hutar da ke zan ci na Antynki Bishira,
maganar ta soki ran Ummi har ta kasa magana,
ya fahimci hakan don haka sai ya kawo zancen
da cewa sai nazo. Ta tura baki tare da cewa
uhm, tana kashe wayar ta shiga kunkunan cewa
in yaso kaci abinci gidansu bana ta ba. Tsohuwa
da ke sauraronta ta sheka dariya tare da cewa,
ba dai ke kin ce me sunan Malam ba? Sai ma kin
je gidanshi yarinya ban miki baki ba amma za ki
raina kanki. Ummi ta cafke cikin jin haushi ta ce,
wai to Tsohuwa da za ki ce na ce Ya Abba cewa
nayi ina sonshi? Kuma da su Alhaji suka jona ni
da shi da naki har da ke za a dinga cewa ban yi
biyayya ba. Tsohuwa ta ce, Raba ni da gulmarki,
kina sonshi ai ni ba yarinyar goye ba ce, kina
waya kina kashe murya, san nan ciwoce-
ciwancanki duk sun lafa. Sai wannnan rawar kai
ki ke, to ki sani me sunan Malam dai ya aure ki
ne don dole, matar cushe kuwa ba daraja take
ba. Ummi ta ce, "To nima dai ai ba sonshi ni ke
ba, ni dai tsohuwa don Allah ki daina samin ido.
Ta mike, Na ma bar miki kofarki. Ta nufi kofar
dakin Alhaji tana kunkunai. 36. 66... Sai dai duk
da haka kalaman tsohuwa sun tsaya a ranta,
matar cushe bata daraja, Ya Abba kan dole ya
aureta, lallai zancen tsohuwa abin dubawa ne.
Abba ya shigo gidan uku da doriya, tare yake da
yara guda biyu, dayan zai mishi dan face-face,
dayan kuma zai masa fenti. Sune suka taya shi
kwasar kaya, bai samu Bishira a gidan ba, kila
tana gidan Ummanshi, ko makota. Sun kama
aikinsu shi kuma ya shiga kicin don ya dan dafa
abinda zai ci. Bishira gidan Anty ta tafi kuka take
wiwi wai ita fa ba za ta iya zaman gidan nan ba,
ta ce "Aunty Farida tunda kuna shiri da Baban
Walid ki ce masaya sawake min". Anty Farida ta
tsura ma kanwarta ido, tausayin Bishiran ya
cikata. Tabbas kishiya bata da dadi koda
mahaukaciya ce bare mai hankali. Sai dai ita bata
da ikon da zata hana ayi kishiyar koda kuwa
mijinta ne ke son yi, don sunna ce ta mai tsira da
Aminci. Bishira ta katse mata tunani da cewa,
dubi fa Anty hatta Dady yanzu yafi son Baban
Walid fiye da ni. A gabana ya dauki kudi yaba
baban Walid, a halinni kara na kai a kar6ar min
'yancina, kuma Momy zata yi magana ya hanata
cikin tozartawa. Hakan da Daddy yayi ba zubar
min da kima yayi ba, har da ita Momy? Yaushe
Baban Walid zai sake ganin darajarta? Anty
Farida ta sauke ajiyar zuciya, ta ce "Bishira Dady
bai zubar miki da mutunci ba, illa kara tarairayo
miki mutunci da yayi daga ke har Momy. Kuma ni
ba zan ce mijinki ya sake ki ba, haka nan ba zan
ga laifinshi ba, domin aure sunna ce ta Manzon
Allah (S.A.W), sam ba zan yi fushi da wanda ya
raya Sunna ba, koda mijina ne. Kiyi hakuri
kanwata koda bani da kishiya nasan akwai zafi,
amma kema kina da laifi, dube ki fa. Yanzu
Bishira wa zai gan ki ya amince ke kanwata ce ta
hudu? Zato za a yi ke yayata ce, kin saki kin yi
ragwaf, nonuwa har ciki haihuwa biyu jal, dubi
yanda tsabar datti yasa fuskarki da dokin wuyanki
zuwa bayanki duk kyasbi ya miki riga. Da kin
zauna kusa da mutum wari ki ke tashi, hakora
sun miki yalo, kai mijinki fa ya yi kokarin ba
kowane zai dauki hakan ba. Duk ba ki kalli laifinki
ba sai don ya kara aure yanzun? Ina ce kwanaki
garin shegen gantalinki ne ki ka bar danki a gida
ya fada rijiya ya mutu? To hatta Abban Nasir ce
min ya yi da shi ne ba zai yarda ba, saboda haka
ki dawo hankalinki ki zubar da kazantar nan ki
kama Ibadarki. Bishira ba kya jin kunya a ce ba
kya sallah? Kuma a tare da haka kina da wannan
kazantar ki ke kaurace ma shimfidar mijinki.
Kwanan baya ya kira ni a waya ya sanar da
nicewa kin ce min ina wari, don haka ni kuma na
ceya tafi gurin mai tsafta mai kamshi. Shima fa
Anty magana yake dankara min don ba kisan
halinshi ba ne. Anty ta ce, "Bishira kina cikin
hadari, ga kin sallah sannan ga kauracewa miji ki
kwana Mala'iku suna tsine miki. To daidaita
sahunki, ga mijinki dan kwallisan dan Jarida mai
farin jini, ki kalli yanda in yana gabatar da
shirinsa yanda 'yammata kan kira su ce suna son
lambarsa. Amma ke kina sakaci da shi, ki dubi
yanda wata mata ta kawo masa hari kwanaki da
a ce ya yarda ke ba za ki san kina da kishiyar
waje ba. Ki shiga taitayinki zan dai miki taimako
daya in kinamince za ki natsu. 67.... Bishira ta
ce, Anty taimakon me? Ta ce, "Zan samu Momy
su taimaka su canza miki kayan daki, sannan
Dady ya ba mu kujerar Makka ni da ke da Aisha.
To sai ya ce tunda ke kin ki kwantar da
hankalinki ki kwantar da na mijinki to ya fasa
naki, mu harmun yi passport. Bishira ta zaro ido,
da gaske Anty? Anty ta ce, Allah da gaske. To
yanzun shi ne ni ke son in ce muje mu ba shi
hakuri kila ya amince. Bishira ta ce, Tashi muje
Anty don Allah, Anty ta ce kin tambayo zuwa can
ne? Bishira ta ta6a baki, nifa ko nan din ban
wani tambaya ba, wallahi gidan ne bakikkirin
nake ganinshi. Anty ta ce, "Ki dinga addu'a, kishi
yayi miki yawa. Sannan ki daina fita ba tare da
izinin mijinki ba, duk in da ki ka je har ki dawo
Mala'iku suna tsine miki. Don haka yanzun tashi
ki tafi gidanki, ni zan samu Hajiya da Dady yau
din nan kuma in sha Allah za amiki gyaran dakin,
sannan tafiyar za ta kasance tare da ke. Bishira
ta ce, Na gode Anty, amma don Allah ki barni na
dan huta a nan gidan duhunsa nake gani, don ba
ki ji yanda ni ke ji ba ne Anty ko da dana Walid
ya rasu ban ji kunci irin wannan ba. Ta sake
rushewa da sabon kuka wiwi, Anty kallonta kawai
take ta ma rasa me zata ce. Wayarta ta ciro
daga chaji ta shiga kiran layin Abba, lokacin ya
kira kananan kannanshi su Kamal suna ta fito da
kayan dakin Bishira saboda ayi fenti har an gama
nashi dakin. Wayarshi da ya ajiye a kan windown
dakinshi ta shiga ruri, ya duba, Anty ce. Ya daga
tare da sallama, ta amsa ya gaida ta cikin
girmamawa da mutuntuwa, ta amsa da fara'a
sannan ta ce, "Abba ga Bishira nan tazo tana
kuka, kuma ta ce min ba ka san ta fito ba". Ya
ce, "Eh haka ne, ta ce don Allah in baka wani abu
ina son ganinka. Ya ce To zan zo Anty, amma
yanzu ina aiki ne kayan dakin ta muke fita da shi
za a yi mata fenti ne, ta ce To ko da dare ne
haka, ya ce to zan zo. * 68.... Ummi tana ta zuba
ido ganin Abba amma shiru har a ka yi Magriba
tayi wanka tayi sallah. Tana zaune har Isha'i tayi
daga Masallaci shima ya nufo gidan su Ummi,
lokacin Ummi tana bakin gado tana 'yan shafe-
shafenta.Ta juyo Abba suna gaisawa da su
Umma, ta shirya cikin leshi mai ruwan lemun
tsami, da dan mayafinta fari haka takalminta. Ta
fito tana zaune kan kujera, ta ce "Sannu da zuwa.
Za ka ci abinci?" ya ce, "Da sauri haka ba muko
gaisa ba?" Ta zauna ina yini? Ya ce, lafiya lau. To
na kawo abinci? Ya ce, daga gida fa nake, ina da
kuma mata. Ummi ta ta6a baki, oh, haka ne ashe
kana da mata, gani nayi da matar taka ka ke
zuwa cin abincin daga nan ta lafe a kujera tare da
hada rai. Ya mike muje ko? itama ta mike, ya
kalle ta da wannan mayafin za ki? Ta ce, eh, ya
ce a'a dauko hijabi ba zan lamunci yafa wannan
dan mayafin ba. Ta kalle shi kamar ta ce ai
matarka tana yafa irin shi sai kuma tayi shiru ta
nufi uwar daki don dauko hijabi. Shi kuma ya nufi
waje, ta yi wa su Umma sallama sannan ta fito.
Yana tsaye jikin mota ya ce, ina wayar nan? Ta
ce, "Gata nan a hannuna ya yi dan murmushi
yace mayyar waya dama nasan sai kin dauko har
yanzun cikin haushin maganar shi ta dazun take
yi. Don haka bata kula shi ba, ya shiga motar ya
bude mata gefen kusa da direba ta zauna cikin
fushi. Lura ya yi da hakan, don haka sai ya ce ba
ni tamata ta ce so nake in loda mata kudi. Ya
guntse baki don kada yayi dariya, ganin yanda
tamiko mishi wayar cikin hanzari gata Allah yasa
bacewa nayi a bani ba. Ta juyar da kai tana
kallon titi, shima bai sake cewa kala ba har suka
shiga cikin gari. Ya dube ta, wane shagon zamu?
Ta ce, duk wanda kaje, ni sanin wani saloon nayi?
Shagon wata mata ya kaita kusa da inda yake
aski, sun samu shagon Musulma ce 'yar
Maiduguri.Shamsy belloRFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 3 part 9
ZURFIN CIKI book 3 part 9
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:40
nayi? Shagon wata mata ya kaita kusa da inda
yake aski, sun samu shagon Musulma ce 'yar
Maiduguri. 69.... Abba ya ce mata ga Amaryata a
gyara mata kai duk da ba wai gashi ne da ita ba
ya yi kyau sosai ko nawa ne zan biya. Mai
shagon tayi 'yar dariya, zan mata yanda ka keso
ya dubi Ummi wadda ta samu kujera ta zauna
fuska daure. Ya ce, "Kanwata zan tafi nayi aski
nima, daga nan sai na dauki matata daga unguwa
na kaita gida, sannan ta san in har ta bude baki
to kuka ne zai kwace mata, don haka sai ta yi
shiru. Ya fita yana 'yar dariya, mai shagon
Yagana saloon ta ce, "Kai kanwata kun dace fa,
kuma da alamayana sonki sosai.Ta kalli mai
shagon hawayen da take makalewasuka zubo, ta
ce "Anty ina so a nan, dubi fa abinda yake
min.Komai sai ya ce min matarsa, matarsa, ko
inaruwana da matarsa? Yagana ta ce, "Yana da
matane? Sam bai yi kama da mai mata ba.Ummi
ta ta6a baki ta ce, "Yana da mata da yakeso ni
bana sonshi, baya sona, iyayenmu ne sukahada
mu.Yagana ta ce, in ma ke ba kya sonshi shi kam
yanadauke da tsantsar sonki a idanunshi n
fuskancihakan. Ummi ta ce, "Anya kuwa? Bana
zaton yanasona ne, in kin ce yabi iyayenmu ne
zan fi yardadon shi din mai biyayya ne.Yagana ta
tura mata kujera, zauna in soma miki,sai da ta
fara gyara mata kai sannan ta ce, "In mamijinki
ba ya sonki to kuwa ba za a yi wuyarshawo kai
ba.Ummi tayi murmushi tare da kallon fuskarta
tamadubin da suke fuskanta, ki ke gani Anty? Ta
cesosai kuwa, ki tarairaye shi da kyau, kin san
shinamiji dai dan shauki ne da son nishadi.
(((KWARAI KUWWA!!!)))Ga kuma son tarairaya
kamar jaririn yaro, ummi tace, "To zan yi hakan in
har yin hakan zai sa ya soni.Yagana ta ce, "Zai
so ki, zan so kiyi gyaran jiki dafata, Umi ta ce,
kamar ya ya? Yagana ta ce, kayanmata zuwa
gyaran fata, wanda za ki sha don 'karinni'ima.
Ummi tayi shiru, don bata son irin
wannanzantukan.Ta ce, "Kin yi shiru, Ummi ta ce
Ummana ta ce bata son in sha komai, tunda ni
budurwa ce, in je wamijina da ainihin halittata.In
yaso daga baya sanin saboda 'yan garinmu sunzo
da shi daga Zamfara. Yagana ta ce, Hakan
mayana da kyau, domin Amare da yawa suna
shanwahala sosai kasancewar ba su saba
ba.Sannan mazajen ba su bambance ainihin
yandamatan suke. Ummi cikin gundira ta ce, Gara
ma nagyara fatar.Yagana ta ce, "Wancan ma za
ki neme shi, ko nangaba Ummi ta ta6a baki, ni
dai fada min na gayarnfatar.Ta ce, "Ina sai dawa
in kina so zan baki kije gida kihada kiyi zan hada
ma angon lissafi da shi Ummita ce, ba ni sai da
suka gama a ka gyara matagashi fes, sannan ta
dauko kayan ta shiga lissafamata kamar haka:-1.
Man Zaitun2. Lalle3. Kurkur4. Madara ta ruwaZa
ki hada su guri daya ki kwa6a, sannan ki
shafejikinki da su kafin shiga wanka, in ya bushe
idan zaki shiga wankan sai ki murje shi tas,
dukwadannan 'yan kurajen na fuskarki za su
mutu,jikinki ya yi laushi da sheki.Ga kuma wani.1.
Sabulun Ghana2. Dettol3. Zogale4. Farar
AlbasaZa ki hada Sabulun Ghanada da Dettol da
garinzogale, da farar albasa, ki hada su ki kir6a
kimurmule shima a jikin za ki ringa shafawa.Da
fuska kafin ki shiga wanka, zan bar ki da biyunin
sun amshe ki ma sun ishe ki. Yanzun ko inwanke
miki kafa? 39. 70.... Ummita ce, "Ina tsoron kada
yazo kuma kudin shi ba su kai ba, Yagana tayi
'yar dariya, kina tausayinsa ne? Ki daina tausayin
mijinki shi ne zai amfana da gyaran da duk za ki
yi. Ummi ta ce, "To wanke mini".Ta hada kayan
wankin kafa ta ce yarana ke yi amma zan miki da
kaina. Sai kuma taga zanen fulawa. Ta ce, "Au,
an riga an yi zanen fulawa ma ba dama ayi,
Ummi ta ce, Ohi ni na manta ma, to ki fada min
yanda zan dinga gyara kafar, ta ce To bari in ba
ki mai sauki ma. 1. Man kwaka 2. Man shanu 3.
Man Zaitun Ki samu man kwakwa da man shanu
da man zaitun ki hada man kwakwa da man
shanu guri daya, ki shafa da dare da safe. Ki dan
gasa kafar sannan ki wanke ki shafa man zaitun,
za ki ga yanda kafafunki za su yi tamkar ta jariri.
Ko ki yi na ruwan ko kumba, lalle ki hada su guri
daya ki shafa a kafafunki da dare. Da safe ki
wanke ki shafa man ridi, wadan nan kurum in kin
rike su za ki ba wani labari, Ummi tace zan
kiyaye in sha Allah. Shi kuma Abba yana fitowa
daga shagon aski kai tsaye gidan Anty ya nufa,
ya samu Bishira Anty ta matsa mata tayi wanka
ta bata kaya ta saka. Ta kira mai kitso tazo tayi
mata ta sata ta shafa turaruka. Tunda Abba ya
shigo yake kallon Bishira, sun gaisa da Anty,
sannan ta ce dama dai na ce kazo ne don Bishira
ta baka hakuri. Sannan in maka tuni da yin adalci
a tsakanin matanka, kuma na yi wa Bishira fada
sosai. Ta dubi Bishira, ki ba shi hakuri, Bishira ta
hada rai tare da turo baki, ta kalle shi cike da
tsananin jin haushin shi. Kayi hakuri ya ce ba
komai dama ni ban yi fushi dake ba, a zuciyarta
ta ce, ba ka isa in baka hakuriba, albarkacin ina
son zuwa Makka ne da kuma canjin kayan dakin.
Ya yi wa Anty godiya ta ce ma Bishira gobe da
wuri kiyi parking din duk kayan ki a waje da mun
zo sai mu shirya miki. Bishira ta ce, Allah dai
yasa su yarda, Anty ta ce,"Za mu su yarda in
Allah ya yarda. Ta dauko wasu kayan sawa da
sabbin kuloli ta ce ma Bishiran je kisa a motarku.
Abba ya ce, "Kawo in kai, Anty na gode sai
anjima, ta ce To Abba ayi ta hakuri". Ya ce, Ba
komai, Insha Allahu. Suka biyo shi a baya tana
kara jawa Bishira kunne kan cewa in har ta
kuskura ta ji wata magana ta 6ullo ta rashin
mutunci sai ta fasa tsaya mata a kan maganar
aikin Hajji ko Dady ya amince sai tasa ya janye.
71.... Sun shigo mata Muhibba tana baya tana
'yanwutsil-wutsil dinta tamkar kurame, haka suke
tafiyar. Ta zaci su nufi gida sai taga sun nufi
cikin gari. Bata tambaye shi ina za su ba, har
suka isa inda yayi parking ya dubeta, Madam ina
zuwa, hum kawai ta ce. Ya bude baya ya dauko
Muhibba ya sa6a a kafada ya nufi shagon saloon
din. Daidai lokacin sun kammala komai, Ummi ta
zari hijabinta da niyyar rufe kanta, Yagana ta ce
a'a kanwata bari ya gani don ya biya ni 'yan
kudina. Abba bai zaci Ummi tana da gashi ba,
domin dai acikin Hausawa 'yan Arewa za a iya
saka Ummi acikin ma su gashi. Yayi laya-laya a
dokin wuyanta baki sidik. Yayi murmushi, lallai
kin gyara da kyau. Nawa ne kudinki? Ta fada ya
ciro ya bata, sannan Ummi tazari hijabinta.
Mamaki take, Gida ya koma ya dauko Muhibba?
Yamiko mata ita, Ga 'yarki. Ta amsheta. Yagana
tace, yarinyar tana kama da ku. Abba ya ce, "Ai
'yarmu ce, suka yi mata sallama suka fito. Ummi
da Bishira a tare gabansu ya fadi lokacin da suka
ga juna. Bishira ta kauda kai yayin da Ummi taja
baya daga mazaunin kusa da direban da ta nufa,
ya bude mata baya ta zauna tana rike da
yarinyar. Ya tada motar suka dauki hanyar tafiya
kowanne zuciyarshi da abinda take karantowa.
Ummi tunaninta Abba ya je ya zo da matarshi ne
don yanuna mata shi fa matarshi yake so. Ita ko
Bishira nata ganin wulakanci ne na karshe da ya
dauko ta yazo da ita gurin wannan karamar
yarinyar. Shi ko Abba addu'a ce a zuciyarshi
Allah ya hada masa kan matansa, sai kuma ya
soma tunanin ina zai soma zuwa? Nashi ganin in
ya kai Bishira gida ya sauke ya tafi kai Ummi bai
mata adalci ba. Amma ya kula Ummi tana fushi
kuma yaso ya lallasheta, yana cikin wannan
tunanin ya tuna dawayar nan. Ya kalli wayar a
gefanshi. Dan murmushi yayi da ya tuna lokacin
da ta dangwarar masa da wayar don ya ce ta
matarsa ce. Yanayin yanda Ummin ke nuna
kishinta yana birge shi, koda bata sonshi tana
kishinshi sannan bata masa raini ko rashin
kunya. Kofar wani gidan saida gasassun kaji da
ire-iren kayan kwalam ya tsaya. Ya kalli Bishira
Madam mu shiga ko? Ta ce, "A'a ni fa ba zan fita
ba, ya ce To bari in dawo, ya nufi ciki. 72.. Ta
waiwayo ta dubi Ummi, ta ce "Ba ni 'yata
fitsararriya. Ummi ta mika mata tare da cewa
nima ai ba cewa nayi a bani ba, ta ce "Kar dai ki
min rashin kunyaki bar ganin an jona ki da mijina
ki zata za ki hada sahu da ni. Ummi ta ce, "Sai
dai kada a kuma in dai batun hada sahu ne, kuma
ban damu don mijinki ba bai sona ba, tunda ni ina
sonshi. Bishira cikin daga murya ta ce, oho?
Dama sonshiki ke yi? Yanzun na gane da nufi aka
yi. To ki sani kin sai ma kanki masifa da bala'i.
Ummita ce, "Kin ga bala'inki can, daga nan
batakara magana ba ta bar Bishira na ta masifa.
Tundaki ka za6i ki auri mijina zan shayar da ke
ruwan dana sani. Sai kin gwammace zama a
kurkuku fiye da gidan mijina, daidai lokacin Abba
ya dawo da ledoji guda biyu. Bishira bata yi shiru
ba sai zagin Ummi take yi,"'Yar iska, 'yar daba...
tsawa Abba ya daka ma Bishira, tare da cewa ba
ki ji kunya ba da ki ke zaginta amma bata kula ki
ba? "Ta ce, "To ka ji abin da ta ce min ne? Tsaki
yaja tare da daukar wayar da ta aje yasa a ledar
Ummi, sannan ya tada motar. Kofar gidan su
Umma ya tsaya, Ummi wadda dama ta kosa tazo
gida, ta bude motar ta fada gida cike da takaici.
Ya kashe motar sannan ya dauki ledarta ya kalli
Bishira, Ina zuwa. Kala bata ce ba. Illa baki da ta
cije, kirjinta na yin wata irin suya. Ban da tana
tsoron Anty kada ta fasa zuwa gurin Dadynsu da
tuni ta shago Ummi ta nadi 'yan kayanta. Dakin
Umma ta shige, Ummar tana shirin fitowa Ummi
na shiga, ta ce kun dawo? Ummin ta hadiye 6acin
ranta."Eh, mun dawo Abba a ya shiga gaida
Umma sannan ya mika ma Ummi ledar, gashi kin
manta Ummi ta amsa tare da cewa, an gode.
Umma ta ce, "Me ku ka siyo in ce dai ka sai ma
Bishira? Ya ce, "Eh na sai mata, kaza ce fa
Umma ba wani abu ba". Ta ce, "To shi ke nan
maza ka koma gurin su, yace "To. Tana fita ya
kalli Ummi akwai waya a cikin zan kira ki, kuma
bana bukatar ki kashe min waya. Ummi ta ciro
wayar da sauri, ta dibe shi ba wayar matarka ba
ce? Ya ce, "Eh tata ce, ta mika mishi cike da
kunan rai, ga abinku ka kira ni da layin Umma. Ya
ce, "Ke ce za ki cigaba da rike ma mata
tawayarta, ba tare da ya jira jin me za ta ce ba
yana murmushi, Ummi ta kasa gane cewa ita ce
matarta shi. Ko kallon kazar bata yi ba illa dai
tayi duk wasu abubuwan da ta saba yi kafin ta
kwanta, sannan ta kunna wayar tana tsammanin
kira. 73..... Shi ko Abba koda yazo Bishira tana
ta mitar don tsohon wulakanci an zo da ita an
shanya ta, bai ce mata kala ba illa dai motar da
ya tada suka nufi gida. Gidan duk kaya saboda
bai maida ba da a ka gama fentin, ya dauki
tsintsiya ya share dakin, sannan ya shimfida
katifa ya fito inda take zaune bakin Rijiya.
Muhibba tayi bacci tana rungume a jikinta, ya ce
kawo ta, ta mike a fusace ta nufi dakin ba tare
data bashi 'yar ba. Ya bi bayanta, so kurum yake
ya lallasheta ba wai don tsoronta ba sai don
tausayinta, yasan mata kan kishi za su iya yin
'yar karamar hauka. Wasu ma sai sun yi babbar
kuma bai dace ana nuna kishinsa ba, shi kuma
yana nuna ko 'in kula a gare ta, gefen katifar ya
zauna ya lalubo hannunta ya rike cikin
nashi."Bishira!" ya ambaci sunanta cikin sanyin
murya, bata amsa ba kuma bata dube shi ba, ya
ci gabada cewa, "Bishira ban ga abin damuwa ba.
Ko damata uku a ka daura min aure da su bare
daya, inkin yi la'akari da irin son da nake miki ke
kin san Bishira ba kiyayya ta hada mu ba. Kina
manta wannan ne? Ta dago ta dube shi ta dan
soma saukowa, yayi murmushi har yau ban daina
sonki ba, ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta turo
baki sai kace 'yar yarinya. To ai na sha jin a ana
cewa so daya ne tak, ya cehaka ne, ta ce "To
tsakanin ni da Ummi wa ke keyi wa? Da sauri ya
ce ke, ta ce Allah?Ya sake tausasa murya, haba
Bishira ya ki ke wannan zancen kema kin sani,
kuma don Allah na roki ki in muna tare ki daina
min zancen Ummi, ke kadai ce za6i na. Bishira
taji dadin wannan kalamai, don haka sukaci
namansu suka kwanta, ya bukace ta a nan masai
da ta ce kaje gurin Ummin mana. Ya ce, "Na ce
in muna tare bana son kina min zancenta. Sai dai
in kina son ci gaba da horon daki ke min ne.
Haba Bishira, ko tausayina bakya yi?An fi wata
uku kina haramta min halas dina. Kullum sai dai
ina azumi sai ka ce gwauro? Yajawota jikinshi, ya
rungume da kyar dai ya samu yadan rage
matsala, sai dai ita ma ya lura tayi missing
dinsa. Suna kwance har kusan sha daya saura
tuni ita tayi bacci, shi kam daman so yake tayi
bacci yakira Ummi. Ya mike yaje yayo wanka
sannan ya nufi dakinshi. Yaja katifarshi ya kai
dakin, sannan ya kwanta akai, ya kira Ummi
lokacin bacci ya soma figarta. Ringing din ne ya
farkar da ita, sai da ta kusa tsinkewa sannan ta
daga, kafin ta amsa sallamarshi sai da tayi wata
doguwar hamma.Ya ce, "Ke baccin ki ma ki ke
alhalin na ce zan kira ko? Ta ce, "Amma ka san
bacci ba ya jira in ya zo,ni kuma ba zan iya yiwa
bacci gardama ba". Ya ceto sarkin iya zance, yayi
nufin zolayar ta. Yanzun dai na soma tunanin kin
soma sona, gabanta ya fafi, sam bata son ya
gano hakan yanzu. Tafi son sai lokacin da shima
ya soma sonta. Ya katse mata tunani, hasashe
na haka ne? Ta ce, ko kusa, mene hujjarka da
fadin haka? Ya gyara kwanciya. Na farko naga
ana ta kishina, sannan tun da a kadaura aure da
ni sai ciwo ya kame kansa, kuma nalura kina ta
zumdin tarewa a gidana.Ya saki 'yar dariya,
yasan ya cika mata ciki da takaici, shiru tayi
nazari take wacce amsa zata bashi, ko dai wayar
zata kashe? Tamkar ya shiga zuciyarta, sai ya
ce.... 41 Tamkar ya shiga zuciyarta sai ya ce,
"Koda wasakada a kashe waya. Ranta ya sake
6aci, ta ce Ya Abba ka tafka kuskure da kayi
zaton ina sonka,sam ni bana wani kishinka. In
don ka ce wayar matarka ce na ce ka rike abinka,
sanin kanka ne ba ma shiri da matarka, kuma duk
abinda ka ce nata ne dole na guje shidon ba zan
dauki wulakanci ba. Batun ciwo kuma daka ce
tunda aka daura mana aure ka neme shi ka rasa
dama bani na dora makaina ba, kaima ina naka
hawan jinin ya tafi? Sannann kuma wane zumudi
na nuna na tarewa a gidanka, Ya Abba ka sani
yanda a ka tilasta maka aurena, to ni ma fa dole
tasa na hakura. Amma ka rike a ranka bana wani
sonka bani kamarina ina sonka, kalaman nata na
karshe sun burgeshi har sun sa shi yin da ya
sanin tsokale zancen. Sai kuma ya canza salo da
cewa, haka dai ki ka ce amma ina da ja mu dai
bar zancen, shin dazun kafin ki soma wannan
tunanin me ki ke yi? Ta danyi shiru tana
tambayar kanta. Dama mutumin nan haka ya ke?
Oh yanzun dabara zai min sai ya gano ko ina
sonshi dole, to kuwa bazai ji ba, ya katse ta da
cewa ban san ki da karya ba. Ta ce, ina tunanin
irin ukubar da zan sha a gidanka ne ta
wulakancin da zaka min, ya yi shiru zuciyarshi
tana cewa yarinyar nan ba ta san irinson da ka ke
mata ba ai ta ma dauke ka mugu kenan. A fili sai
ya ce, "Kuma fa kin yi tunani, Allah yabaki ikon
daukar ukubar da zaki sha tare kuma dajure
wulakancin da na tanadar miki goben Ummi. "Ya
fadi, wai dama da gaske wulakancin zai mata.
Gyara kwanciya kawai tayi bata kara cewa komai
ba, kuma bata da nufin cewa wani abu, yasa taji
haushi sosai, don haka sai ya tausasa muryarshi.
"Ummi kina ji na?" Uhm" Kurum ta ce, don ya
gane tana jin shi. Alkawari ta dauka ba zata sake
cewakala ba, tunda ya hanata kashe wayar. "Ba
ni da nufin miki..." Sai layin ya yanke daga
gefanshi, ta ce, "Gara ma haka". Tana kokarin
kashe wayar gaba daya kiranshi ya sake shigowa.
Tsaki taja kafin ta daga, kuma a ciki ta amsa
sallamarshi, sannan cikin murya mai kamar zata
rushe da kuka ta ce "Ya Abba ni fa bacci nake
son in yi". Ya ce, "Sam ba wani bacci da za ki iya
yoa sai tunani". Ta ce "To na ji, ina son yin
tunanin please".Ya ce, "Tunanin me za ki yi".
Cikin gundira ta ce,"Dole in yi tunanin yanda zan
kare kaina daga wulakancinka, don bana
tsammanin zan dauka" .Ya ce, "Wasa nake miki
fa." Ta ce, "Uhum, ban amince da cewa wasa ka
ke min ba, don na tabbata mu ba abokan wasa
ba ne".Ya ce, "To shi ke nan bari in bar ki kiyi
tunanin, amma tunanin yanda za ki faranta min
za ki yi". Muryar Bishira ce ta katse shi. "Oho! Ai
tun da na farka ban ganka ba na san ana nan
ana cin amanata". Ya kashe wayar da sauri, duk
da dai Ummi ta riga ta jiyo muryar Bishiran. Sai
dai bata fahimci me Bishirar take cewa ba,
ringingine tayi tare da dora filo a kirjinta, tunani
take yi wane irin zama za su yi? Koda bata da
amsa ta kudurce har abada ba za ta dauki
wulakanci ba, a shi ko a matar shi. Sai dai
alkawari ta dauka ba za ta musu raini ba,
matsawar ba su suka 6ullo da hakan ba. *
************************************** Shi ko
Abba rigima suka dinga yi da Bishira cikin tsohon
daren wai ya cuce ta ya kwanta da ita yazo yana
hira da wata banza. Kila ma ya saba kwanciya da
Ummin ne yau bai samu dama ba, Abba ya ce kin
so kanki in ki ka yimin wannan zaton, don ban
ta6a nemanki ba, kafinki shigo gidana, ko na
ta6a?"Ta ce, "Don ka san dai ni ba fuska". Da ya
gaji da iya korata ya rufe kofar ya koma can
dakin. 40. 74... Washegarin ranar, ga mamakin
Ummi tun misalin karfe goma jama'asuka cika
gidansu, a ka dora abinci. Can kuma saiga yaran
shagon Abba da dinkunan zannuwan daAlhaji
Babba ya sai mata.Ranar Abba bai shigo gidan
ba a waya ya kiraUmma suka yi magana, zuwa
karfe uku angama yiwa Ummi jeren dakin da yake
yana da girma yacinye komai tsaf.Fitar 'yan jere
babu jimawa sai ga Anty Farida dakannasu motar
tana da kaya tana biye da su, gadoda kujeru a ka
canzo mata.Suka jera mata sannan suka lodawa
motar na dasuka dauki hanya suka koma, Abba
kam yana gurinaiki amma zuciyarshi tana
gida.Fatanshi Allah yasa yana zuwa ya tarar an
kaimishi Umminshi, kawayen Bishira da
makotansu'yan jam'iyyarta duk sun shigo gidan
sun hadu saizugata suke yi tare da nuna mata
koda wasa kadata sakar ma Ummi fuska, kuma in
ta mata takamata ta duki 'yan kayanta.Suna
gidan a ka kawo Ummi, 'yan kawo Amaeyakam
suna jiyo habaici da zagin da su Bishira ke yi,don
haka suka ce kada a kai musu yarinyar.Inna
Saratu da Inna Harira suka ce ai kuwa sai
ankaita.Ba ko kunya Bishira ta zabga musu
harara lokacinda suka fada mata cewa ga
kanwarta sun kawomata, don Allah su zauna
lafiya tare da Aminci.In yarinyar tayi ba daidai ba
ta sata a hanya... takatse su cikin tsawa da
mikewa tsaye. "Don Allahku fice min daga daki
amanar kishiya? Har wai muzauna da aminci ku
ke cewa?Tayi 'yar dariyar yake "Kun yi kuskure,
ai batacanza daga sunan ta na kishiya ba, kuma
kowa yasan kishiya abokiyar gaba ce."Inna
Saratu ta ce, "Baiwar Allah jahilan mata sunesuke
yin irin wannan tunanin, amma ga masu ilimisuna
koyi da gidan mai tsira da Aminci
(S.A.W)ne".Bishira ta ce, "To kawai dai ki ce min
jahila ki huta,bari ku ji ba za n ba ku a 6oye ba,
zama ne za muyi shi na rashin mutunci, na kowa
ya iya allonshi. Don ina kishin mijina, kuma zan
nuna". Tirkashi! Lallai akwai daru kenan. To
masu karatu ku biyo ni cikin littafi na 4, kumana
karshe domin jin yadda za ta kasance atsakanin
Bishira da Ummi da kuma Oga kwata-kwata wato
@BABA MONO HAXOR
No comments:
Post a Comment