Download Now ZURFIN CIKI BOOK 3 AND 4
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:42
Inna harira tace, Allah ya kyauta ku tashi mu tafi.
Suka mike Suka nufi dakin ummi. Duk da ummi a
da bata tunanin tana da lokacin bishira, yanxu
kam dole tasan zaman da zasuyi. Su inna saratu
suka ce ma ummi duk abinda zatayi don allah
kada ki kulata. Suka ce tayi harkokin gabanta tayi
biyayya wa mijinta shine abunda zai fisheta.
Ummi tace To amma a zuciyarta bata tunanin
zata zuba ido a rainata. Suna tafiya fatima ta
shigo yiman sallama, ummi tace don allah fati ki
dan tsaya ni kadai fa zan zauna a dakin nan. fati
tace wayace kada kisan kawaye? Ummi ta ce
wane kawaye, auren da a ka daura cikin yan
mintina? Fati tace, Yau zakiji abinda mata kaji.
Ummi ta damko mayafin fati, ni fa inajin turo, wai
da gaske da wahala ko kina tsokanata ne? Fati
ta kamo kunnen ummi tayi mata rada. Ummi ta
zaro ido tare da cewa, Da gaske? Fati ta sheke da
dariya tace sai nazo jin batun. Ummi tace sirrine
ya za'ayi in fada miki sirrina? Fati tace au ni
shine na fadamaki nawa ko? Ummi tace kinyi
haram da kika fada fati tace, "ke kuma kinji
haram ko? Suka sa dariya. Duk yanda ummi taso
fati ta tsaya amman taki, don haka sukayi
sallama. Fati ta shige dakin bishira don yi mata
sallama. Bishira tace, fati fitar min daga daki
bana wasa dake, tunda kema naga kin koma
jam'iyar waccan yar iskar, fati ta fita, cikin ranta
tana cewa ba zanki yar uwata ba don kishinki na
banza tayi tafiyata. Ummi tsuru tayi tanaji tsoron
abinda fati ta fadamata, amman sai wata zucia
tace keda ba sonki yake ba kila ma bazaibi ta
kanki ba, sannan ta samu yar natsuwa. Abba ya
fito zai nufi gida sai kuma ya fasa ya nufi super
market, ya siyo audugar mata yana tsammanin
gobe ne zata tashi da al'ada a lissafinsa. Tun
sanda ta soma bai taba mance ranar ba, haka in
ya chanza mata lokaci duk yana lissafe. Ya sai
masu yan kayan masarufi sannan ya fito, gida ya
nufa amman gabansa yana faduwa kila har
yanxun ba a kai ummi ba. Da yayi fakin sai kuma
ya nufi gidan su umma duk kowa ya watse. Yayi
sallama tsohuwa tana alwala ta amsa. Umma
daga kicin ta amsa, tsohuwa tace "wane kinibibin
kuma ya kawoka mai sunan malam? Bayan an
kai maka ita? Yace kaji tsohuwa da wata magana
da gurin ummi nake zuwa? Ni gidan mu ne. Tace
kadaiji shi, takwara dai kada inji kada in gani, don
nace mata duk abunda kuka mata tazo ta
fadamin. Yarinyar nan tana kuka wiwi tabar gidan
nan. Umma cikin dariya tace "toh ai tsohuwa in
don Abba baza ayi fada ba, ummin ce dai abin
jama kunnen. Tsohuwa tace 'a' a daina zancen
nan suwaiba kada ma ya samu nayi. Abba yace"
Toh bari in zo in hada maki kayanki mu tafi can
don kada wani ya zafin cewa. Kinga kyafi tare
mata. Tace ina gana nan din ma zanji. Yace
Alhaji sun shigo kuwa umma? Tace A'a basu
shigo ba. Yace toh bari in isa gida. Tace toh
Abba ummi ma dazun aka rakata. Don allah Abba
ka kara hankuri a kan na da, sannan matarka
kuma kada kace zaka nuna mata bambanci a kan
ummi yar uwarka ce. Ka kwantar mata da hankali
ka mata adalci, sannan kada ka bawa ummi kofar
da zata raina bishira. Yace zan kiyaye insha allah,
kuma don allah umma ki kara mika godiata gurin
alhaji. Tace haba Abba yaya kake fadin haka?
Alhaji ai mahaifinka ne karka dinga kallon
alakarka da ummi. Yace haka ne duk da haka dai
a min godia, tsohuwa tace yaki godia ya samu
mata a sama don rashin imani mai sunan malam
ko gyauto bai sa mata ba, toh kasani tana binka
bashin lefe. Abba Yace umma ni dai na wuce.
Umma cikin dariya tace "Toh Abba. Yace tsohuwa
ni nayi gaba, don in na cika tsayuwa a nan kila
mu dambace, Tsohuwa tace kai dai jeka na baka
amana ya tafi yana dariya. Koda ya kai kofar
gidan sai ya bude mota ya dauki kayan
masarufinshi ya nufi cikin gidan salam dai duk da
jarumta irin tashi gabansa ne ke faduwa. Bai san
wace irin masifar bishira ta tanada ba. Ya shiga
da sallama. Bishira tana zaune akofar daki tana
goye da muhibba, amman bata amsa ba. Duhun
magriba ya soma dan daf da a kira sallah a ke,
yace bishira ya ba a tada inajin ba? Tace tunda
kazo yanxun ai sai ka tada kai. Da kafin wata
tazo ai baka taba zuwa kace a tada inji ba. "Abba
ya kalleta a zuciyarshi Yace" mata kenan masu
manta alhaji. Ya aje ledodin hannunshi ya nufi
injin. Bishira ta mike ta nufi ledodin tana fadin
Tun yanxu a aka shigo mata da kazar, alamun ba
za'ayi ada ba kenan. Ni lokaci na sa wuraren tara
ya shigo ina lissafe da komai, ta bude ledodin sai
taga kayan masarufi d kuma audugar mata. Tsaki
taja tare da dangwarar dasu yana kallonta da ya
kara mai ya tada injin sa yazo ya kwashe ledodin
ya shiga falonta.vels / ZURFIN CIKI book 4 part 2
ZURFIN CIKI book 4 part 2
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:44
Kujerun da aka chanza mata masu kyau, amman
a ran abba yace ya basu sati biyu. Ya cire riga ya
fito yana son yayi wanka ne kafin a kira sallar
magana,yaja ruwa da sauri da sauri yayi ban daki
ya fito ya shiga falo ya kwalama bishira kira.
Tace minene kake damuna? Yace ina aka kai min
akwatuna na? Tace tace ina kuwa gasu can a
kicin da sauri ya fito, kicin din lafia? Ya tsaya
yana kallonta bani da mutuncin da za'a sa min
kayana a daki? Tace ni da aka guji dakina da
kayan a kace ni kazama ce, me zaisa in sake
kaine? Daga baice komai ba ya nufi kicin ya
kwaso akwatuna shi da takalmin shi ya kai
falonta. Bai tsaya chanza kaya ba, ya nufi
masallaci don zai rasa sallah. Bai baro masallaci
ba sai bayan isha'i amman bishira tana zauna.
Ummi kam ta kasa fitowa don tana kyankyamin
ban dakin, gashi al ada ta sameta da yamman
nan, sannan duk tanajin abin da sukeyi da
matarshi. Ya shigo gidan ya chanza kaya sabi fil,
ya feshe jikinsa da turarukkanshi wayar shi ta
soma ringing ya daga salis ne. Yace aboki in ba
sallama akwai daga hannu ko? Kace an kai maka
rabin ranka koda ba zamu rakaka ba ai kayi
mana sallama. Cikin dariya Abba yace na yafe
salis yace To Allah ya bada zaman lafia. Suka yi
sallama zai aje wayar kenan sako ya shigo. Ya
duba ummi ce da wayar nan da ya bata ajiya
cewa tayi, ina da matsala, ina bukatar taimako.
Gabanshi ya fadi, sai kuma ya tuna kila al'adar
ce, don haka sai ya saka hularshi ya dauki ledar
audugar ya nufi dakinta. Har lokacin bishira nan
zaune inda take, tace au tun daga yanxu za'a
soma rashin adalcin? An dauki leda an nufi
dakinta? Sam baiko waiwayo ba, yayi sallama ta
amsa tare da gyara mayafinta, ya shiga suka kalli
juna Cikin ido zukatansu sukayi fari kal. Cikin
taushin murya yace, wane taimako kike bukatar?
Ta lumshe ido sannan ta juya masa baya domin
kunya ta rufeta. Yace To karba ya mike mata
ledar ta waiwayo ta ansa da hannu biyu. Mamaki
ya cikata ganin audugar, ya yayi har ya san tana
bukatar audugar kuma a ina yake sanin lokacin
al'adarta har idan ya chanza? Tace nagode yayi
dan murmushi nima ina godia. Ya juya har ya
daga labule tace "Em na ce....." ya waiwayo yace
kika ce mi? Tace don allah inason maganin
wanke bayi ne, tayi maganar Cikin kyankyami,
sakamakon irin dattin da tagani a bandaki tare da
gamsa kuka. Yayi murmushi wane iri kikeso?
(IZAL) yace ai akwai amman yanxu Bai kamata ki
shiga wankin bayi ba. Tace zan wanke in dai
akwai. Yace bari in wanke maki, da sa tace a'a
yaya Abba zan wanke. Falon ya koma ya cire
rigarshi ya shiga jan ruwa. Bishira tana zaune ta
mike ina badai abokitaina ba, in zaka kwashe
mata rijiyar kwashe, amman a juye ko in baras
kuma in dai ruwan da za'ayi amfani dashi ne
kakeja, To kesani nima duk lokacin da zanyi
amfani da ruwa saika dibar min, ehee. Ummi ta
fito da bokitai don duk tana jinsu, tazo wurin
Cikin sanyin murya tace, Ya Abba don allah ka
bari in ja ruwan nan. Ya kalleta, take ya manta da
duk bakin Cikin da bishira ta kunsa mashi.
Yanxun daga zuwa saiki fara jan ruwa? Ummi
tazo ta kama igiyar gugar, ai ba zama nazoyi ba,
Ya Abba bauta nazo yi, Aljanna sai an dage. Ya
saki dariya bishira ta dakatar dashi da ce wa
"Karuwanci za'a gwadaman? Ta daga ruwan da
ya zuba a bukati zata watsama ummi, yace kina
watsa mata zan baki Mamaki. Cikin tsawa yayi
maganar ta tsaya cak da bokitin yace, Sakarya
mai kishin hauka. Yaci gaba da jan ruwan yana
zubawa abokitan da ummi ta fito dashi. Bishira
ta aje ruwan sannan ta hankadar dashi a kasa,
Bai ko kalleta ba. Ya zuba ruwan sannan ya fito
da izal da omo. Daki ummi ta koma ta dauko
tsinsiyar da aka sai mata don wankin bayi, kin
tafiya Abba yayi tana wankewa yana zuba mata
ruwa har sai da taga bayin yayi yanda take
bukatar sannan ta hankura. kyankyami jikinta
takeji don haka taje ta hada kayan wanka har
lokacinzurfin Ya Abba yana wurin rijiyar. So take
ya matsa taja ruwan amman yaki, don ya lura
bishira shi kadai take shakka zata iya zartar da
komai kan ummi. Shine ya sake zuba mah ummi
ruwan wanka, sannan ya coge har ta gama ta
fito rufe da hijabi tayi dakinta, sannan ya dauraye
jikinsa yaje ya maida kayanshi ya nufi wane.
Bishira tana nan wurin kofarta ta kasa zaune ta
kasa tsaye, bakinta kuma Bai fasa sambatu ba
sai kace sabon kamun hauka. Fadi take kuma a
zo a biyani duk basisikan da nike, ehee. Kuma in
yarinya tamin in murji bukina. Ummi kam ta
gyara jikinta tsab ta saka sabbin kaya ta feshe
jikinta da turarokan da umma ta sai mata. Tunda
ba lefe aka mata ba bare ta samu kayan shiga.
Kan doguwar kujera ta mike, salam yanzu taji
yinwa tana tsammanin rabonta da abinci tun
karin safe. Ta shafa Cikin ta ina ma umma na
aiko man da abinci. Ta furta a fili WAYA nan ta
jawo tana tunanin sanar da Abba cewa tana jin
yunwa. Sai wata zucia ta hanata wannan ba
girman amarya bane. don haka ta share ta bude
shafin game tana ta bugawa. Sai sha daya Abba
ya shigo gidan, ya rufe gidan. Nufinshi ya wuce
kai tsaye dakin ummi, amma sai ya tuna da kazar
da ita bishira ya sawo mata. Duk da baya tunanin
ta karba ga mamakinsa tana tsaye a tsakar daki
har yanxu da daurin kirji take. Wannan ya nuna
batayi sallah ba, bare wanka. Ya mike mata wata
harara ta zabga masa banaci, ya juya batare da
yace mata kala ba, ta biyo bayan shi, A bani
basussukana da nike bi malam. Ya nufi dakin
ummi taba biye dashi, ummi ta turo kofa dama
yana kokarin tura kofa dama yana kokarin tura
kofar bishira tana rike masa riga ta baya. Ya
waiwayo Cikin zafin nama zai wanka mata mari
sai taci sa'a ta tsugunna, Cikin azama ta yunkura
tayi baya da gudu. Banda tsaki da yaja Bai ce
komai ba. Ya shige dakin ummi da sallama, ummi
bacci ya dan dauketa saboda gajiya. A kan kujera
take da waya a hannunta. 4rm Shamsy bello
balarabe.IKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 3
ZURFIN CIKI book 4 part 3
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:48
Niyyarta yau sai taji komai, don haka ta kai yarta
ta kwantar, dai dai lokacin ne abba ya fito don
kashe injin. Sake fitowar da tayi ne taganshi zai
koma. Wayan cewa tayi da daukar buta ta shiga
bandaki, shi kuma ya shiga daki ya kulle kofa,
tazo ta manne jikin kofar. Fitar abba shine yaba
ummi damar saka kayan baccinta, don bata iya
bacci da kaya masu nauyi. Fargabarta yaya
kwanciyar tasu zata kasance? Kan kujera ta
zauna tare da kwantar da kanta a hannun kujera.
Shima abba yana da jin zafi don baya iya bacci
da kaya sai da gajeran wando kurum, idanu ummi
ta kulle lokacin da taga ya abba ya soma cire
tufafinsa ga hasken cocilar da ya kunna. Filo ya
dauka ya jefa Kan doguwar kujera ya kwanta
rigingine, ganin haka sai ummi ta mike ta nufi
gado addu'a tayi sannan ta lumshe ido har bacci
ya dauketa. Fuskarta cike da murmushi zuciyarta
cike da godia allah yau gata dakin ya abba a
matsayin matarsa. Abu daya ya rage mata shine
ta koya masa yarda zaya sota. shima farin ciki
ne a ranshi yayi da idanuwanshi sukayi kuri a Kan
gado yana hango ummi ya ta zama halalinsa Abu
daya ya rage shine ya koya mata sonsa. Bishira
data labe bata jiyo komai amman kunnuwanta
suna jiyo mata magana kasa kasa,,hawaye na
zuba a idonta batasan iya adadin awanin data
dauka a kai ba. Koda ta koma daki juyi kawai
take a gado. Abbanta abun sonta yana can
kwance da wata, watar ma makiyiyarta wadda ta
tsana. Wata zuciya tace kije ki watsa masu man
petur wata tace ki bari da safe ki caka masu
wuka babu abinda bata rayaba har asubahin
farko. Labule ta daga ta shiga leke taga ko zasu
fito, lokacin ne kuwa abba ya fito yaja ruwa a
bokitai yayi wanka da alwala. Ba zata gane ko
wani Abu ya faru tsakaninsa da ummi ba don
wanka al'adarshi ce Koda bai dauki najasa ba.
Nafila ya shiga yi da rokon allah yasa ummi ta so
shi, ya kuma hada masa kansu. Koda zai tafi
masallaci bai tashi ummi ba tunda yasan ba
sallah zatayi ba. Bishira ta fito tasa kujera kofar
daki ta zauna, saboda tashi bai bar ummi bacci
ba, don haka ta tashi in tana al'ada yini take
wanka gaba daya sai ta tah ktankyamin jikin ta.
Ta fito da bokitai duk ta cika d ruwa, Bishira tana
kallonta sai da ta wanke bayi tas, sannan tayi
wanka. Sauri take tayi kwalliya don a cikin
nasihohin da umma tayi mata a safiyar da za'a
kawota gidan miji tace kada ta sake mijinta ya
ganta cikin kazamin yanayi. Kuma kada ta bari ya
shaki wari daga gareta, tayi shafe shafenta.
Atamfa ta saka riga da siket mai ruwan hoda
hoda da ruwan kwai. Daurin dan kwali ta kafa
sannan ta feshe jikinta da turaruka masu kamshin
gaske, sannan ta shiga gyaran dakin duk da ba
datti yayi ba. kayan da abba ya cire ta ninke don
da jallabiya yake zuwa masallaci, sannan ta dau
kujera ta kishingida saida gari yayi haske sannan
ya nufo gida. Tsaki bishira ta jamashi maimakon
amsa sallamar ta kara da cewa an girma ba'a
san an girma ba, an kwana da yar ciki abin
kunya. Ai wallahi baka cika dan halas ba da ka
auri yarinyar datayi sanadin kulleka kaci duka har
aka ballaka ba. Ya kalleta dalilin kenan da ban
cika dan halas ba? Tace eh baka cika ba, yace
toh jeka naji ni shege ne, in don dai na auri ummi
ne, tace munafuki dama can kana sonta. Ya sake
wai wayoowa yace so kuwa mai tsanani. Takaici
ya cikata ta daga murya allah ya isa munafuki.
Ya nufi dakin ummi wadda ke sauraren duk
abunda ake. A cikin ranta tace ina ma son da
gaske ne? Tasan ya fada don kawai yaba
matarsa haushi. Da sallama ya daga labulen,
ummi ta amsa tare da tashi daga kishingida da
tayi, ya zauna tare da lumshe ido. Lokacin daya
kuma ya shaki kamshin turarukan data fesa. Ya
kalli Fuskarta labbanta da yake matukar so sun
sha jambaki ruwan hoda. Take abba ya manta da
duk wata damuna koh kalma marar dadi da
bishira ta fada masa. Daga inda take zaune ta
dan rankwafa don girmamawa tace ya abba ina
kwana? Lafia qalau ummin abba ya bakon wuri?
Ta lumshe ido saboda jin dadi sunan daya fada
mata. Alhmdllh ya sake karkatawa yana kallonta
sosai yace to masha allah, yanxu kinsan minene?
Ta tattara hankalinta gareshi tace a'a? Yace kiyi
hnkr nasan a al'adar ta hausawa amarya ta Kan
yi sati daya cir ba tare data yi ko cangal ba. Toh
hnkr zakiyi kinga ke tun daga kawoki jiya kin
soma da wanki toilet. Sannan yanxu ma ina son
ki ciro rishonki a hada shi a sa kalanzir mu karya.
Kin dai ga yanayin yanda matar gidan take
gudanar da nata kishin. Ummi ta gyara zama ta
tuna nasihar ummanta da tace in zaki yima
mijinki magana kalaman ya zamana kin zabo su
ne ba wai kin sakesu ba. Ta kalle shi, shima ita
yake kallo, tace ya abba don wannan ne kake ban
hnkr? Yayi murmushi tare da lumshe ido ya kuma
budesu lokacin guda, a yaran soyayya yana nufin
eh, itama ta fahimci yaren don haka taci gaba da
cewa. Ya abba ni dama ba zama nazo ba, neman
aljanna nazo kuma zanyi komai don na sameta.
Don haka kadaina bani hnkr umurni kawai zaka
bani. Tun daga tsakiyar Kan abba har zuwa
babban yatsansa sai da ya motsa, don sanyin
muryar da ummi tayi amfani da ita tare da
kyawawan kalaman ta. A zuciyarshi yace tabbas
ummi haihuwar ummanshi ce, duk rainon umma
dole zai zama daban ciki ya'ya. Ya kalli ummi
allah yayi maki albarka tace amin. Ta mike ya
bita da kallo taje gurin da a ka shirga mata
kayan aiki ta zakulo risho yace to muje kicin dinZURFIN CIKI book 4 part 4
ZURFIN CIKI book 4 part 4
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:13
Ta mike ya bita dkallo tje gurin da aka shirge mta
kayan aiki ta zakulo risho yce to muje kicin din.
Tkarya murya, ya Abba amin afuwa, bna son in
shiga kicin din can kmin hakuri insa rishona
akofar daki. Ykalleta, bazai tkura mta ba domin
ysan duk wnda yzauna da umma dole zai zama
me kyankyani, yce indai zai miki kiyi kawai , in na
smu ynd da nke so dga baya sai ayi miki kicin a
gurin, tce ngd. Shi kan da kanshi yfito darisho yn
budewa ya hadashi, tafito da tukunya tanufi rijiya,
ta dauraye sannan tazubo ruwa.Bishira kuwa
dma tazo talabe duk tji maganganun dsu kayine,
jin abba zai fito da risho sai ta gudu daki. Sintiri
ta dinga yi tna magana ita kadai, wato abban
walid nece mazai ce anga irin nawa kishin?
Yarinyar dya ce bsonta yke ba dole akayi masa
shine har ysoma kai mta gulmata. Har dawani shi
mata albarka , tunda uwarta ta kitso mata ynda
zata ce ai dole yashi mta albarka, to ni ya tsine
min kawai. Ummi ta amshi galan din kalanzir din
dga hannunshi tre da cewa ya abba kawo inzuba
zai ce ta barshi kenan wayarshi ta soma ruri,
yadaga. Anty ce, suka gaisa tce tna son yin
magana da bishira ya mike ytafi kaimata ummi
kam ci gbata yi dasa kalanzir dinta takunna
rishon tdora ruwan zafinta takoma daki, shima
yna bt wayar ydawo. Anty tce bishira dm na kira
kine inji bakuwar dta kwana a gidan da safennan
kin bta abin kari ko? Bishira tahade rai tamkar
tana gabanta, anty tome mexan bta, ina ruwana
ma da ita? Dazunnan fa suka gama gulmata wai
har yna ce mta tye hakuri tdai ga irin mtar gidan.
Anty tce hauka kike tyi shi ysa ai dole yce haka.
Ynzun dai sai ki tashi kibsu abin kari, hka da rna.
Karki sake yarinyar nan ta dora tukunya sai byan
sati daya, kina jina ko? Bishira tace to bdan
zancan ykai ranta ta amsa ba. Sai don tunanin
kada zancan zuwa makkanta yafasu . Sunayin
sallama ta aje wayar tre da cewa, koda uwarta
tke ywo bzan dfa mta abinci ba. Sai da ummi ta
wanke flas din shayin sannan tazuba ruwan, falon
bishira yje ydauko kayan shayin dbiredi. Tace,
itama kakai mta ruwan zafin. Yce ta dafa, ygama
yashirya tsaf don zuwa gurin aiki, harbakin kofar
daki tarakashi. Yce, ummi naroke ki koda bishira
tna zaginki ne don Allah kda ki kulata, sambana
ganin laifinta don nasan sboda sona tkeyi. Nan
da wni lokaci komai zai daidaita. Ummi tce kada
kadamu insha Allah ba abin dazai faru, allah ya
tsare yace amin nagode. Dakin bishira yaleka ya
amshi wayarshi, sannan yce mezakuyi drana?
Tzabga mishi harara, ina ruwana dawani abinci.
Ya aje mata dari hudu. Gashi kusai nama nasan
akwai komai ko? Tsaki taja, gara maka dauki
kudinka don bzan dafa ma munafukai suci suji
dadin zagina. Yakalleta, Allah yganar dke. Tdg
murya yganar dakai dai maci amana sainaga
bayanku. Bki yataba kafin yafita, baice mata kala
ba. Ummi ta kinkimi akwatinan kayan abba dya
kawo mt tgyara msu mzauni, sannan takwashe
'yan kofunan dasuka sha tea ta wanke. Sannan
takoma dki tna jin wsu kawayen bishira sunzo
sunata habaice dazage-zage, ummi bt fito ba
bare ta tanka. **** **** Bashir abin duniya ya
ishe shi, ykasa sukuni sbd son ummi, yzuga
ummanshi sun kai suka gidan su sahabi don
afasa auran anfasa kuma duk da hk ummin
tzama btashiba. Jinshi yke tamkar ykashe abba
don tsana, don hka koyaushe cikin zuga umma
yke dan kawai tatsani Abb. Guraran sha biyu
ummi bacci yasoma dibanta sai tji muryar
umman bashi akofar dakinta tna cewa ina ummin
tke munafauka, fitsararriya tadaga labulan kofar
tarike. ummi takalle ta. Kin kalle mi mna 'yar
makirai. Kin bar smun zman lfy a gidannan, kuma
uwarki ko tn tsafi dbakin kare dbakin dodo sai
kinbar gidan dana. Ke inzan tafi dazani daya
mtsawar bokaye da 'yan bori suna nunfashi kin
smun nutsuwa agidannan. Bishira tace, umma
shima munafuki ne shida yce bai sonta amma
dazun haryi dni sukayi. Umman bashir tce shi
Abba kimasa uzuri, duk abinda ykeyi byin knshi
bne, anriga an rikita shi, bakya ganin shi duk
afirgice yke? 'yar bori tafada min komai, ynzun
karya tambaya muke nema. Bishira tce duk dhaka
ma ynso, ai ance asiri yan tarad dahali. Umman
bashir tce hk ne, shi dinma ai ubansa zaici ba
dagin kafa. Ummi datna zaune kai duke, sam
zantukansu bsu dme tba, abu dya yagirgizata
btun asiri. Bta son ashiga tsakaninta da mijinta
tun kafin su fara son juna. Saidai kuma dta tuna
da addu'o'inta da takeyi bta fsa yi ba. Ga Azkar
safe dayamma, saitasamu ntsuwa tsan Allah
yafisu.ovels / ZURFIN CIKI book 4 part 5
ZURFIN CIKI book 4 part 5
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:33
Umman bashir tagama jarabarta tafita, karfe daya
drabi Abba ykira wayar dke hnnun ummi tdaga.
Cikin girmmawa tce, snnu da aiki ya Abba, ina ftn
kn cikin koshin lpy? Yyi murmushi cikin jindadi
yce, lpy nke ummi, am...in... Dama zan cene kin
ci abinci? Tce A'a, amma bna jin yunwa, dnaji
yunwa zn sha tea ai, kda kdamu kai fa kci? Yyi
dan tsaki, tsiyar bna cin abinci awaje ummi,
abincin umma kdai ke min dadi, Allah ys zki gjeta.
'yar driya ummi tayi, insha Allahu sai mna fita.
Yce anya kuwa? Tce insha Allahu ai nace. Kin
gma mgna yafadi tre dyin murmushi mai sauti,
yawwa bari in kirata ta turo miki da abinci, tce to
ngd. Yce, nima na gode, sai ndawo. Tce, to Ya
Abba kdawo lpy, ka kula min dkanka. Tkashe
wayar, yjima yna kallon wyar tre dmamakin ynda
ummi ta iya zantuka masu kwantar dahankali, irin
wdanda bishira da ta ba ta shekaru bta iya ba.
Ykira lyin ummanshi suka gaisa, yce ummana don
Allah kitura ma ummi abinci, umma tce, kan wani
dlili Abba? Tci gba dacewa, tbdijam!, bza ayi hk
dniba. Abba ymarairaice murya, don Allh ummana
yunwa tke ji. Umma tce, ta tashi tdora mna?
Abba tsaya kaji, dadai wta ce can kke aure ba
ummi ba sai na aika mta, amma ynzun ga
uwargidanka agidan shi kenan sai in aikamata da
abinci? Wannan ba gsky bne, sannan zgin da ake
min ai sai ya linku yfi nada, yce umma duk wnda
yzageki rshin fhimta ne. Kuma fana baiwa bishira
kudin cefane amma tki tdafa musu abinci, tce kila
tgaji ne, shiyasa bta dfa ba. Ita ummi dba saita
amsa tdafa musu ba? Yce, amma dai umma
tsakani da Allah kowacce amary bsai ta kwana 7
bsannan tke fara dfa abinci? Umma tce, ai ba
addini bne al'ada ce, don takama girki ai ba laifi
tyi ba, yce, shikenan umma tunda kin hna sai
anjima, tce mujima dayawa. Shiru abba yyi yna
tunanin mgangnun umma, ysan gsky tfada, amma
dmuwarshi ummi dbta ci komai ba. Ykalli agogo,
saura kusan awa 2 ytashi, wayarta yske kira,
tdaga yce ummi kisha tea din umma bta da
abinci kfin ndawo. Tce, to ya Abba, kkusa
dwowane? Yce, sai nan da awa 2. Tce to Ya
abba, sai ka iso. Bta wni sha tea bdon bta jin
yunwa sam, tshi tayi tasake kakkabe dkinta don
mutane suna tshigowa ganin dki yra dmanya. Tas
tkakkabe ko ina tafito tshare tsakar gidan lungu
dasako, bishira lokacin mbata gidan wsu yra
dsuka shigo tbasu kasko suka smo mt rushi
tzuba turaren wuta mai kyau dkamshi. Tnayi tn
kallon agogo, saura minti ashirin yaya Abbanta
ydwo ta wanke byi tsake wnka, sannan tdibar
masa ruwan wanka shima ta aje akofarta. Trufe
kafin ya iso, tshiga dki tna ta shafe-shafenta, sai
lokacin bishira ta shigo gida. Tna rike da 'yarta
akafada, ita kanta 'yar ba amata wanka ba bre
uwar, tkwabe hijabi trataye, sannan tzauna akofar
dakin tna kallon tsakar gidan. Duk da ita knta
gurin ybta sha'awa, amma bki ta taba tre dcewa,
wahalalliyar bnza. Ummi tayi mtukar kya cikin
wando da riga nawani ydin dshi Abba ydinka mta
a babbar sallar dta gbata. Tasaki gashinta sosai
tyi wani daurin dankwalin da ita ce ta iyashi
amma gshin nta duk yna wje. Tfesa turarukanta
sannan tfada kan kujera, tkalli agogo minti goma
takaru akan lokacin dya fada mta. Zuciyarta tdan
dmu tkosa sosai ta gnshi bta ki yzauna agida tyi
ta kallonshi tre da sauraron muryarshi ba. Sai
dkusan minti 20 sannan Ya Abba yshigo, tsayawa
yyi yna kallon tsakar gidan, yau kam farin cikine
ya mye gurbin bakin cikin dyake ji aduk lokacin
dya shigo gidan ykalli tsakar gidan. Kamshin irin
turaren wutan da umma ke cika gidanta dashi ne
yke shaka. Ysaki murmushi tre dyin sallama,
bishira dke zaune dabas atsakar gidan maimakon
ta amsa sallamar sai tsaki taje dogo tre da cewa.
Aikin bnza. Kallonta kurum yayi ranshi ya baci.
Bai cemata kala ba ynufi dkin ummi, tyi nisa cikin
buga game. Sallamarshi ceta sata yin jifa da
wayar akan kujera tamike tdaga labulan daidai
lokacin dyke cewa inshigo? Ta amsa sallamar
dwata murya wadda bta san ma tna da ita ba,
suka kalli juna cikin ido, lokaci 1 suka ski
murmushi tmika hannu kafadarsh rtaye da wta
jaka wadda bda ita yfita ba. Ya salubo jkar ymika
mt tre dcewa, kirike dakarfi, tce to, sannu
ddawowa. Yshigo rike da leda ahannunshi yzauna
tre dcewa. Yauwa, tnufi robar ruwa data dauraye
jug din data tnda don shi kadai, tzubo ruwa tzo
dakofi tadauraye kofin snnan tzuba ruwan tmika
msa tre dsake cewa, sannu dkokari. Ydubeta,
yauwa kema sannu dkokar, dud da byajin kishi
dole ne ysha ruwan, ybude bki ysoma shan ruwa.
Sai yaji ruwan yfi duk wani ruwa dyasha a tsayin
rayuwarshi gardi dkuma dadi, ydubeta ido lumshe
dama ruwan amare dadin shi dabanne?? ZURFIN CIKI book 4 part 6
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:37
Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa,
yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire
takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan dan
teburin da aka aje don dora abinci ko kofi. Tazo
takwashe tkalman tkaisu kusa da kofar fita tyi
musu ajiya mai kyau, sannan tadauko dan twul
tshare kasar gurin. Ykalleta, yi hkuri nshigo miki
dki datakalmi ko? Tce bkomai aranshi yce nsaba
shiga dakin bishira da tkalmi. Yjanyo ledar dya
shigo da ita tre dcewa ummana tki aiko miki da
abinci ko? Tace, kyi mta mgnane? Ya ciro take
away din yasiyo mata, zo kici, ai dole ta bmu na
dare, zan jene in tsaya mata. Ummi tdubeshi,
anty bishira fa ka bata nata ne? Yyi mta banza,
tduba ledar tga guda daya gakuma wnda yciro
mata. In kaima anti bishira? Ydaka mta tsawa tre
dharararta, ke! Ban aike kiba, tatsaya tna
kallonshi, meye ruwanki da mtata, kin fini snin
meye kamata nayi kenan? Yja dogon tsaki tare
djanyo jakar dta dora mishi akan gado, jikin ummi
yyi sanyi. Ta tuna damaganar da umma acikin
nasihar dta mta, kda kizama dga cikin mtan
dsuke btawa mzajensu rai. Hakan yna sawa miji
yatsani matarsa, kiyi tka tsantsan kinsan hlin
abba yna dsaurin fushi. Dsauri ummi tasulalo dga
kujera. Don Allah kyi hkuri ya abba, ban san
zakaji haushi ba. Ydubeta fuska daure, hwaye
ygni sun cika idonta yace, kda ki sake hawayen
nansu zubo, tsa ytsunta tdanna idnunta, tshi ki
zauna ki dauki abinci kici. Tzauna tarike abincin
tkasa ci. Ykalleta suka hda ido cikin ido, tariga
shi mgna kayi hkuri Yaya Abba, tausayinta
ykamashi amma sai ydake. Bnason kisake mgna
akan abinda yshafi mtata kinji ko? Da sauri tce,
bzan kra ba. Yyi dan murmushi ci abincinki.
Tasauke wta irin ajiyar zuciyar dhar ya klleta da
ido ya tmbayeta lpy? Dabaki tfurta lpy lau, yce ci
abincinki. Ummi tdauki abinci tn ci, jefi-jefi tna
kallonshi, shi kuma yna ta kokarin kunna laptop,
don ymantar da ita. Yce, kinsan menene wannan?
Ta a'a yace computer ce, agurin aikinmu aka rba
mna. Ummi tace, kyauta? Yce A'a za'aringa
cirewa acikin albashinmu, mtso kigani. Tdan
mtsa inda zta iya kallowa, ykunna yna nuna mta
abubuwa, yce ai nsan ki zaki iya sarrafata, tce
wai, bazan iya ba Yaya Abba. Yce, nima sai
nshiga mkarnta akwai tnan cikin gri zan shiga nyi
diploma, salis shi tuni yyi. Ummi tce amma gshi
ynzun mkana sarrafata, yce ina dan hwa ta office
dinmu ai tce tayi kyau Allah ysa albarka yce
amin. Ykashe komai ydauki take away din ynaci.
Sannan yce, bri infita. Tdube shi itakam bta son
yfita don umma tce mta tzama mai tsare mijinta
dga zaman majalisa koyawo. Indai ba mkarnta
yke zuwa ba, yma ztayi thana shi fita tatambayi
knta, tdube shi cikin tausasa murya. Ya Abba hka
zka fito bkayi wnka ba? Tmike gruwa nan nadiba
bari inkai mka, shima ymike. Sai anjima zanyi
ummi, ynzun shago nke sn zuwa. Akwai wsu
dinkuna da za a amsa yau ina son ingako yaran
sun gama snnan inson in yanka wsu dunkunan
ciki har dnaki, koda yke saina gwada ma tukunna.
Tce, tokadan huta mana ynzun faka dawo, ygane
bta son yfita ne, don hk yce kda kidamu dg shago
ba inda zanje. Har bkin kofa tarako shi tarike
labule, to sai kdawo, yce to, ynzun mbai kalli inda
bishira tke ba, yyi wje. Datsaki traka shi tre
dcewa, girma dai yfadi warwas, murmushi yyi mai
sauti yfice abinshi. Ita kuwa sai thau zntuka,
kinibibi a auran mka miji sannan a nuna anfi ka
sonshi, yrinya lokaci nabaki. Ummi dai sai tkaro
kofarta, koda dre abinci daidai cikinta bishira tyi
taci tba 'yarta shiko Abba bai shigo gidan basai
bayan sallar isha'i. Byan yje sun sha dirama da
umma, tce itafa bta yi abinci dsuba, yce umma
gskiya toki bmu na babanmu. Tyi driya, kasan
abin dakake fada kuwa abba? Inbaku abincin
mijina? Ai kuwa bkwaci ba. Tsohuwa tace, kai ina
mtarka ita bazata dafa fa? Kodon tsoronta
fakakeji ko? Abba yce eh bazata dafa ba ina
ruwanki ke tsohuwa kin cika sa ido. Tce, nasa
din, ai gskiyane kowa ysn uwargida ke yin girki
harsati guda. Abba yce, to mu tsarinmu bhka bne,
tkwashe da driya. Bwani tsarinku bhaka bne kila
ma kinyin girkin tyi, yce oho dai bza kiji bdai, tce
jeka intayi tsami mji. Umma dke tsheka driya tce,
abbana zoka dauka gashi nan yce, yauwa
ummana mungode, tce abba bka shiga gidan
nanne? Yce wai gurin umman bashir? Tce eh, yce
ina zuwa mna, tce todon Allah kadinga shiga, nan
yyi musu sallama ytafi. Lokacin dya shigo gidan
dindim! Sai daya tda injin, aranshi cewa yake yi
lallai mta dakíshi, jimatar dko darana tada inji tke
yi amma ynzun don kda wtan tga hske ko tji iskar
fanka shine taki tadawa.I novels / ZURFIN CIKI book 4 part 7
ZURFIN CIKI book 4 part 7
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:41
Ya aje kular kofar dakin ummi yaleka dakin
bishira, tana kwance kan gado, itafa bata jin cewa
zata dazama dakishiya, dole cikin biyu ayi daya,
kota tada ballin dazai saketa komuma tanemi duk
wata hanyar daza akori wannan 'yar iskar
yarinyar. Yashiga dakin, muhibba daketa wasa
akan gadon da baya zaton tun da aka kafashi
tasake kakkabe shi, yace hibba. Yarinyar ta
waiwayo cikin murna tanufo ubanta da dan
gwaranci, bishira tasa hannu tasuri 'yarta yace,
bishira duk wannan abin daki keyi fabashine
mafita agare kiba. Ki kwantar da hankalinki ki
nutsu ki kama girmanki, yarinyar nan zata biki
amma in kin zabi akasin haka kece zaki koko....
Kai malam! Ta katse shi, bafa wata sauran
magana fanasan komai, ni yanzun saki kurum nafi
muradi, ya ce sakin lafiya? Ni yanzun ma na
soma sonki, tadaga mishi hannu tare da daga
murya, nikuma nadaina sonka, karya ne makace
kana sona kuma kanason waccan banzar. Dole
acikinmu akwai wadda kafi so. Abba yace to ai
kece, ke nafi son kuma ita tasan haka, kalmar
tashi tadan sanyaya mata zuciya. Don haka bata
sake magana ba, yace kina bukatar wani abu ne?
Tace don Allah nidai ka fita kawai, yace to na
fita. Ummi lokacin tana canza kaya zuwa riga
dazani na leshi, sosai tayi kwalliya tamkar
kasureta ka ruga don kyau. Fuskarta sake ta tari
Abbanta dasannu dazuwa, ita ce tasa musu
abinci kowa da plate dinshi, amma sai ya aje
nashi yace suci nata. Dama taso yin hakan amma
tana tsoron kada ya gwasaleta, sai da sukayi
dam sannan yace bari yayi wanka tatashi takai
masa ruwan wanka tadawo. Kafin ya fito ta sake
gyara ko ina, jallabiya mai gajeran hannu yasaka
mara nauyi ya wadata jikinshi da turaruka tana
kallonshi cikin sha'awa. Taso taimaka mishi tun
agurin shafa mai, amma tana tsoron kada yaga
zakewarta, don haka tashare tare da cewa
dasannu za azo gurin. Ysake cewa zai koma
shago, tace haba yaya Abba yanzun kuma?
Yadauko tape dinshi nagwada mutane, zo in
gwadaki, har da kayanki zan yaka yanzun.
Yarannan 'yan shiriritane, badon naje dazun ba
dasun sani nasaba alkawari, dinkunan su kawai
suka yi tayi suka aje wanda nabasu. Ummi
tabata fuska, ya tausasa murya, come on zo in
gwada ki, bazan jima bakinji ko? Tatashi taje
gabanshi ta tsaya. Sai dai mamakinta duk
dunkunan da Ya Abba ya sha yi mata abaya bai
taba gwadata basai yanzun? Koya manta yanda
yake mata ne? Tsawon siket din ta ya soma
gwadawa, tana tunani sai taji ratsawar dan
yatsansa tare da tape din a kwankwasonta, duk
da cewa dariga ajikinta saida hakan yasa taji
wani yanayi ajikinta. Har ma takalle shi, haka nan
ya auna hips dinta da kirjinta, shi kanshi ya shiga
wani yanayi alokacin, haka nan yakoma shagon
cike dakewarta. Kayan bacci tasaka ta kwanta a
gadon tana da yakinin bazai mata komai ba,
tunda yasan bata sallah. Har kusan goma da rabi
tana jiran shigo warshi shiru, waya tadauka ta
rubuta mishi sako da cewa. Ya abba don Allah
kadawo ni dai tsoro nake ji. Ya karanta yayi
murmushi, azuciyarshi yace, don ita ya kwafe,
yayi dunkunan yana son kudin don ya sai mata
akwati da kayan shafa zuwa kayan ciki. Share ta
yayi sai kusan sha daya darabi sannan yatashi
tare da sallamar yaran, haka nan itama sai daya
hado mata duguwa rigarta ta shadda wadda
dama anriga anyi sirfani ajikinta. Dakin bishira
yasoma lekawa, bacci yadauketa sosai agefen
gadon take da alamun baccin yazo mata ba cikin
shiri ba. Abba yayi murmushi tare da cewa, wa ya
fada miki ana cin bashin bacci? Ina zaton matar
nan jiya bata runtsa ba, yau gashi yazo ba shiri.
Har ya gyara mata kwanciya itama 'yar ya gyara
ta amma bishira bata farka ba, don haka yakashe
mata wuta yafita. Yaso kashe injin amma garin
da zafi gashi basu kawo wutar nepa ba, gidan
yarufe yazo ya tura kofar ummi data rufe. Karar
kofar ne ya farkar da ita amma bata motsa ba,
tun daga kofar yatsaya yana kallonta, can
tsakiyar gadon takwanta bata dora kanta saman
filo ba. Amma tana manne da filo daya akirjinta
fuskarta yake kallo, a jikinta taji kallonta yakeyi.
Kusan minti 4 sannan ya aje ledar hannunshi.
Shirin bacci yake amma yakasa daina kollonta,
shikanshi yana mamakin wannar jarababben son
dayake ma ummi, duk da dakewar dayake don
kada yabada kanshi amma sai yadinga jin wani
abu yana fisgarshi. Tamkar yafito mata da zallan
sonshi gareta, tsoronshi inta gano kila tarainashi.
Kadan-kadan takan bude ido ta saci kallonshi, sai
daya gama komai a tunanin ta ya kwanta a
gadon amma sai taga yadauki filo yakwanta a
kan kujera. Haka suka rayu har tsawon sati daya,
ranar yabar dakin ummi ranar kuma tasoma salla,
ita ko bishira satin nan tayi shine tamkar
mahaukaciya sabon kamu. Ranar kuma da abba
yadawo dakinta bata runtsa ba shima bata barshi
ya runtsa ba, daga bisani dole yabar dakin
yakoma falonta yakwanta. Haka gidan yaci gaba
da kasancewa, in Abba yafita ummi bata da
sauran sakewa saboda zagi da habaicin bishira.
Wani sa'in har da kawayenta, ko makota 'yan
jam'iyarta su shigo suyi tayi, ummi bata kula su.qnovels / ZURFIN CIKI book 4 part 8
ZURFIN CIKI book 4 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:50
Duk abinda bishira zatayi kada takulata. To ita
duk bawannan bne damuwarta ba, damuwarta
ynda Abba sam yaki nuna sha'awarta gare shi,
duk dayasan tana sallah, hka nan duk lokacin
dakwananshi yajuyo kanta sai dai ya jefa filo
akan kujera ya kwanta. Takasa gane ma'anar
hakan, tun tanajin dadin ynda bai nemeta ba
saboda tsoronsa da take harta dawo tasoma jin
haushi. Ita ma fa mutum ce cikakka mai lafiya,
sannan tana kwana daki daya da san kacecen
abun sonta ya ya ba zata damu ba? Sai dai tayi
wa kanta alkawarin a yau in zasu shekara ahaka
ba za ta taba yi masa tallar kanta ba ma'ana
baza takai masa kanta ba. Sai dai zatayi masa
kyale- kyale taga karshen girman kai, ta kosa su
hadu da fati don ta bata sakon kananan kaya
tasiyo mata don ta bata labarin cewa ta kwashe
su a wambai. Kwananta goma taso ma girka, duk
tsawon kwanakin nan abincin siyarwa dana
umma suke ci, domin bishira taki dafa abinci.
Ranar da zata fara girki ta haukata gidan da
kamshi, tuwon shinkafa miyar shuwaka, tasan
Abba nason tuwon shinkafa. Tun kafin ya dawo
yamata waya ta aika shagonshi, 'yan shago sun
ci suna santi, haka nan ya gayyaci abokansa
kofar gida ya shimfida musu tabarma suka ci tare
da lemu, zobo da kunun aya. (reall ehem tazubo
mun nawa na koma 1 site ina kimtsa cikina lolx)
ga nama ya wadata a ciki, abba yaji dadin yanda
abokanshi sukayi ta santi, safiyar ranar kuma
kunun gyada ta musu da kosai. Duk wannan
abincin da ummi keyi bishira ko a harshenta ta ki
ci, cewa ma tayi ita fa kowa tayi girkinta don
baza ta ci abincin ummi ba. Kuma ba shegiyar
dazatai wa girki, hakan yayi wa ummi dadi don
nata ganin ta bakin tsohuwa ce, da ta ce ko kwai
bishira tadafa shine dai dai a cikin bawo to baza
ta iya ci ba bare wani abinci. Sun zauna tsawon
wata daya ahaka ummi bata taba leka ko kofar
gida ba, tana kewar ummanta gara ma tsohuwa
duk ranar juma'a in tadawo masallaci takan biyo
gidan taga takwararta. Dakinta Abba yake
yagama karyawa ya shirya zai tafi aiki, ummi ta
kalle shi tana son tambayar zuwa gidan umma
tna jin tsoro. Ya dubeta kamar kina son cewa
wani abu ko? Ta ce am dama inaso inje gida in
gaida su umma, yajuyo yadubeta suka hada ido.
Gabanta yafadi, ta sunkuyar dakanta, yace a'a
tadaga ido takalle shi, wani kunci taji aranta, ga
matanshi nan yini take garari a layi bata ko
tambaya amma ita ta tambaya shine ma zai
hanata? Ya dauki jakar shi, ta mike ta rakashi
har tsaka gida tare da yi masa addu'ar Allah
yatsare, yini tayi da takaici dama haka mata suke
ji in an hana su zuwa anguwa? Daran ranar zai
koma ga bishira don haka bata san dawowarshi,
tana kwance kan doguwar kujera tana karanta
littafin hausa ( naleka muku kozanga sunan
littafin amma bangano mukuba) kamshin turaren
shi ne yasa tasan yashigo, don littafin yadauki
hankalinta. Ta amsa sallamar daya sake yi tare
da mikewa zaune, yana sanye da kananan kaya
tamkar wani dan saurayi, yayi kyau a idonta
kamar ta rungumeshi. Tace sannu dazuwa yace
yawwa, dauko mayafinki muje tazura takalma
bayan tagoge sannan ta ciro mayafi, yace a'a
dauko hijabin. Ta maida ta dauko hijabi tafito
sannan yakulle kofar, saida suka fita waje sannan
yadubeta, hannu rabbana zakije musu? Tace yaya
Abba toni bani da kudi ai. Sukabi ta wani super
market suka sai sabulai da turare, akafa suke
takawa sannu ahankali suka jero duk da cewa
bawata hira suke ba, Abba ne yake amsa waya
jifa-jifa na jama'a masu sonshi. Tun daga nesa
suka hangi mahaifansu suna cin abinci a inda
suka saba. Alhaji babba dakarami. Cikin zumudi
ummi ta ce, yauwa gasu alh. Abba yaje haka
zakije musu da rawar kanki ko? Cikin shagwaba
tace, wanne rawar kai nayi toni yaya Abba? Yace,
na gani kinayi kamar zaki kwasa da gudu, kafin
tayi magana sun iso gurin dukkansu suka zube
akan tabarmar daga gefe. Abba ne yasoma cewa,
sannunku alh. Alh. Yace, a'a kune? Alh karami
yace, uwata harda ke? Tace, eh ina yininku?
Sukace lpy lau. Alh. Karami yace, uwata kunanan
lpy ba wta matsala ko? Ta ce, ba komai alh..
Yace to Allah yyi maku albarka, ya azurtaku da
'ya'ya ma su albarka wadanda kuma zasu biku.
Abba yace amin suka hada baki da Alhaji babba,
alh babba yaci gaba da cewa, Abba ya hakurin
shirmen ummi kuma? Ince dai bawata matsala?
Abba yakalleta mun gode Allah alh, amma bwata
matsala, ummi tamike dazumudi bari a karasa.
Tun daga soro take kwala ma umma kira. Umma
tce, A'a muryar wa nake ji haka? Ummi tashigo
da gudu ta cakume umma, tsohuwa tafito tana
fadin lale. Dakin tsohuwa tasoma shiga suka
gaisa sannan tadawo dakin umma, sun gaisa
umma tasake mata nasiha, ummi tace umma ni
matsalata daya matarsa. Kullum saitayi min
habaici tana zagina wata rana r harda kawayentaRFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 9 ZURFIN CIKI book 4 part 9 Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:54 Ita ko bishira gidan su umman bashir ta tafi dakuka wiwi, tace Abba yamata duka takan sun taka hakkinta sun fita ranar girkinta. Tayi magana ummi ta mata tsaki shi kuma yazo yazo yahauta da duka, umman bashir tace duka! Duka akan ummi? Tabdi, tashi muje gurin wadanda suka daure masu gindi. Umma na kokarin shiga daukin alhaji taji sallamarsu sama-sama, gabanta yafadi ta amsa tare da dawowa baya. Sahura tace to suwaiba, abinda kuka shiirya yasoma tasiri. Abba yayi wa bishira shegen duka saboda 'yarku, umma tace haba sahura, yaya ki ke irin wannan maganar? Mu ne zamu sa Abba ya cutar da iyalinsa? Sahura kiyi nazari. Alhaji yafito, me yafaru ne ni kejin hayaniya suwaiba? Umma tace, oho. Sahura tace, bishira fada musu. Nan bishira ta shaida masu yanda ta tsara ma umman bashir, alhaji yadaga waya yakira Abba, Abba yana dagawa alhaji cikin zafi yace Abba maza kazo yanzun duk in da kake. Abba yace to alhaji, ummi ta mike zan bika tsoro nake ji ni daya, cikin zafin rai yace abin daki ke tsoro ya cinye ki, ya fita fuuu. Cirko-cirko ya same su a tsakar gida, sai muryar sahura kake ji tana rashin mutunci. Alhaji karami yadawo gidan shi sai ya jiyo muryar sahura a can gidan, ya nufi gidan don haka kusan tare suka shiga gidan da Abba. Alhaji cikin bacin rai yafada Abba da fada, abba bai katse shi ba har sai daya kai ga tambayarshi cewa me yasa yayi mata duka? Yace, banyi mata duka ba alhaji marinta kawai nayi, umma ta ce mari kawai ne Abba? Alhaji karami yace, to kan wane dalili ma zaka mare ta? Abba ya koro musu komai, ya kara da cewa, wannan har zata ce an mata tsaki, zata yi duka ni wane irin zagi ne bata min ina hakura darajar iyayenta? Ya nuna ta, wallahi in kika kai ni bango zaki koma gidanku don bazan iya ba na gaji, nan kuma su alhaji suka shiga bashi hakuri. Ita kuma suka bata rashin gaskiya, sai dai duk da haka umma tai masa fadan kada ya sake daukan ummi ranar girkin bishira ya fita da ita, yace to. Umman bashir taja bishira zo muje ai dama nasan baza suga laifin 'yar su ba. To wllh marin da yamiki ki tabbata bashine. Ko nan da yaushe ne ki rama shi kan ummin, in ba haka ba duk da banice uwar data haife kiba sai na tsine miki. Alhaji karami yace, to katuwa mara lissafi, ke dai kinji haushin rayuwarki, to ki sani duk randa ta rama duka akan ummi ni kuma akan ki zan rama wa ummin inga ta tsiya. Alhaji babba yace, kada kai ma kazama su mana aminu. Tsohuwa tace, gskiya ne, in har tazama silar dukan ummi itama sai ya mata taji. Umma tace, a'a duk abin ba zai kai haka ba insha Allahu, kai dai abba kayi ta hakuri sannan kadaina sa hannu kana dukan mace. Yace, umma dukana fa tayi, sai kace wani soko zan tsaya mce tna dukana, umma tace, to ai tace ummi taje duka, yace ummin 'yarta ce? Alhaji yace, tafi gidan kahadasu kayi masu nasiha, Abba yace ai baza ta tsaya ba, wannan yarinyar fa sai dai addu'a ni in nagaji kawai hakura za ayi, umma tace bana son jin wannan zancan, alhaji karami yace ai gskiyarshi ne, shi yasan irin zaman dayake da ita. Alhaji babba yace, ai kuma darajar mahaifinta za aduba, da mutuncinsa, Abba yace ai dama alhaji ni banda mahaifinta da tuni nayar da kwallon mangwaro na huta da kuda. Umman tace je ka gida Allah ya kyauta. Nan dai ya musu sallama yanufi gida. Ummi da gske tsoro ne da ita, da rana in ba kowa bta damuwa, amma da dare tfi son tdinga jiyo motsin bishira koda habaicin dta sabayi mata. Soro taje ta tsaya tana yi tana leka waje, can ta hango bishira, don haka takoma daki ta kullo kofa aranta ta ce kada tazo tayi min duka. Ummi tna jiyota lokacin data shigo tana cewa wllh kan yarinya zan rama marina, wannan dole ne koba dade saina ramashi. Abba kan bai nufo gida ba, shagonsa ya wuce lokacin goma ta gota, yaran sunyi shirin tafiya, don haka ya amshi makullin ya shiga shagon saman teburin da suke yin yanka da guga ya hau ya zauna. Tagumi ya zuba hummu biyu tare da sauke wata ajiyar zuciya mai karfi, me yasa ummi ta furta kalmar data tuna mishi cewa bata sonshi? Sakankancewa dayanda ummin kenuna mishi yasa shi jin kamar sonsa take ashe dai shi yake shermenshi. Ya tuno wani labari yaya tabaji na wani mutum da aka ara masa mata wadda bata sonsa, tazo tazauna dashi tsawon shekaru kuma tayi masa biyayya matuka. Ga 'ya'ya sun haifa yaran sun yi girma sosai, suma sun zama magidanta, sai wata rana mutumin nan suna hira da matar, yace oh, wance dafa ba kya sona, yanzun gashi harmun tsufa kin manta dawata kiyayyah. Tadubeshi, inji wa yace maka na manta? Biyayya kurum nake maka amma har gobe bana sonka. Abba yajinjina kai, lallai dole ne ya nutso, yadaina tunanin ummi tana sonshi kokuma zata soshi, shidai da kaddarar sonta tafada mishi sai yayi ta addu'a Allah ya bashi hakurin jure zama da ita ahaka. Bai san adadin lokacin daya dauka awaje ba kuma baisan adadin tunanin dayayi ba. Daga karshe yarufe shagon yanufi gida. Ganin yanda garin yayi tsit shine yasa shi kallon agogon hannunshi, daya da minti shabakwai, lallai lokaci yatafi. ZURFIN CIKI book 4 part 10
ZURFIN CIKI book 4 part 10
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:55
Yanufi dakin bishira aranshi yce da wanda yake
kinka gara mai sonka ko mahaukaci ne. Gdon
yahau tagefe ya kwanta suka saka muhibba
atsakiya, ummi kuwa duk tsawon lokacin nan
tkasa bacci domin bata ga shigowarshi ba. Idonta
biyu har sai daya shigo ta leka ta windo tana
kalloshi har yashiga dakin bishira ya rufo kofa,
sannan ta kwanta tare dayin ajiyar zuciya. A fili
tace ina ga fa har dani alaifin nan, amma bari
gari yawaye inba shi hakuri durkusa ma wada ai
ba gajiyawa bane. Bishira tafarka cikin dare taga
Abba kwance hannunsa na dama dore kan jikin
'yarsu, ta tsura mishi idanu tana son mijinta
sosai. Ban dahaka data kaishi koto ya bata
takardarta koda mahaifinta xaimata baki
sanadiyar haka, amma shi yanzun yadaina sonta.
Takai hannu tadora a kumatunshi, ahankali
yabude idanu, suka kura majuna ido yace bishira
me yasa kike yin abinda zai samu mu samu
sabani bayan kinsan sone ya hadamu?
Idanuwanta suka kawo ruwa, Abba dane ka soni
kaji dani har alokacin ina ganin ba Wata mace
data kai ni dacen gwanin iya soyayya. Amma
yanzun duk ka zuba ni a kwandon shara har kana
marina saboda ummi. Ya ce, a'a ba sbd ummi na
mare kiba, saboda kin dukeni ne amma kiyi
hakuri. Banason kina zubar da kanki a gurinta,
yawan fadanku zai sa raini ya shiga tsakaninku,
ni kuma ba zan so ta rainaki ba. Kuma da kin
kwantar da hankalin ki ummi fa ba wai tana sona
bane, ita fa an matsa ma tane, kuma su umma da
kike zagi na rantse miki masoyan kine. Ta ce
tokai kana son ummi ne ? Ya dan yi jim, sannan
ya ce ai dai kin san yanda auran namu da ita
yakasance bagatatan bai dace ace kinma tsaya
yin wannan tambayar ma. Tadan yi shiru, zancen
nan ya shige ta bakamar yanda ta zata da farko
ba, ko dadin baki zaimata? Sannan ta tuno da
ranar da fati tazo. Ta labe taji koza suyi
zancenta sai taji suna ta hirarsu, acikin harar fati
ke cewa wai kuwa ya kuka kaya ne ummi? Nasan
yanzun ai kin warke, kema kin goge. Ta ce
damefa? Fati tace, a'a ki gane mana, batun
kwanciya. Ummi tace, kin san cewa yaya Abba ko
gadona bai taba kwana ba? Fati tace kai haba?
Ummi tadinga yimata rantsuwa, tuno da wannan
sai bishira ta yarda mijinta ma baya son ummi,
don haka sai ta saki murmushi. Yace, tunanin me
ki ke yi? Tace da ina ga kamar dadin baki kake
min, amma dana tuno naji ummi tana fadama fati
wai baka taba ko kwanciya a gadonta ba, bare ka
hada jiki da ita sai na yarda. Abba ya zaro ido, a
ina kika ji suna zancan? Ta ce, a'a tazo mata
rakiyane naji suna maganar a soro. Abba ya
girgiza kai. Bishira tace, kuma da gske hakane,
yakai hannu yakama nata tafin hannun, wannan
wani sirri ne tsakanina da ummin. Ynda ba zan
fada mata komai tsakanina dake ba, haka itama
zan sakaya nata sirrin, tadai fahimci hakane, don
haka sai ranta yayi mata dadi har ma ta baiwa
Abban kanta a daran. Ynda taga yna rawar jiki ya
tabbatar ma ta ba wani angwanci da yayi, don
haka zuciyarta fes ta wayi gari. Duk da cewa
abba ya tashe ta cewa taje tayi wanka harda
Allah yahadata amma tayi niyar baza tayi hakan
ba sai gari yayi haske. Ummi ta fito don tanuna
mata cewa Abba ya kwana da ita. Bishira an dafa
ruwan tea an kai falo sai wannan rawan kai ake
yi. Sai data lura ummi ta dauko tsintsiya tasoma
sharar gidan kamar yanda tasaba, sannan tafito
da buta aka nufi bandaki, kai ko dankwali babu
aka yiwanka aka fito. Gashi yna ta digar ruwa,
ummi ta fahimta kuma tagane cewa tayi hakan
don ta nuna mata ne. Kuma taji zafi aranta
kamar ynda bishiran taso, ta amma azuciyar ta
sai tace na banza jiya nan yakora miki mari.
Lokacin da abba ya shigo gidan tagama shara
tana kwashewa, bai ko dubeta baya shige falon
bishira, kan ummi yasake daurewa, me yake
faruwane haka da zafi? Ta tambayi kanta. Data
koma daki tagumi ta zabga tana tunani ita da
suka yi kaca-kaca ma sun shirya bare ni? Kamar
tabi shi har falon bishiran ta gaida shi, amma sai
tafasa. Tazuba ido taga zai bar gidanne ba tare
daya leko dakinta ba? Sun gama karin
kumallonsu tsaf yayo wanka don tafiya gurin aiki,
sai dai kayan dazai saka suna dakin ummi. Ya
fito yanufi dakin. Ciki- ciki yayi sallama ita kam
tsoro ne ya tsirga mata, tasake tambayar kanta
mekuma yafaru? Ta amsa tare da gaida shi. Nan
ma a ciki ya amsa, yadauki kayan sai dazai fita
sannan yace ba kya bukatar komai ko? Tayi
karfin halin cewa sugata ceta kare. Ya dube ta
furka tsuke me yasa baki fada minba? Ta ce, na
manta ne, yace to sai kije gurin bishira da dibar
miki inzan dawo na siyo. Ba kya neman komai da
rana ko? Tace a'a sai nama kawai ya daga
murya, kullum ne ya zama dole a saka nama a
abinci? Jikinta har bari yake don tsoro, ta ce a'a
yaja tsaki ya fita. Ummi tasaka kanta cikin cinya
tana furta 'inna lillahi wa inna ilaihir raji'un.'
hawaye suka soma yi mata sintiri.KI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 11
ZURFIN CIKI book 4 part 11
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:57
Dadi tamkar yakashe bishira don tna labe tana
jinsu afalon ya saka kya yashirya tsaf, sannan ya
nufo dakinta don dauka jakar laptop dinshi. Jin
sallamarshi tayi mza tashare hawaye sannan ta
amsa, yshigo ya dauko dari biyu ya aje mata
akan gdo, ga kudin maman nan kura, kada fati
tzo kifada mata baki kudin nama kullum tunda
har kin iya shaida mta cewa ban tba kwana
agadonkiba. Kin kosa inkwanta dakene? Yadauki
jakar yarataya sannan yayi mata wani kallo sama
dakasa, to banga gurin kwana agadon naki ba.
Hakanan banga abin kwanciya ajikinki ba, yafice
yabar ummi tsaye tazaro idanunta cikin matukar
al'ajabi da kunya. Ina ya Abba yaji zancen nan?
Kodai fati ceta fada masa? Wata zuciyar tace fati
baza ta iyayi masa zancan nanba saidai in
ummarsu tafada mawa ita kuma tafada masa.
Inko hakane fati batayi mata adalci ba, ai hira ce
irinta aminta tsakaninsu, gashi ta bata kunya har
tasa ya Abba naganin tazaku. Tokuwa tasha
alwashin nuna mishi bahaka take nufi ba, afili
tace Allah yabamu rai da lpy. Sai kuma tasoma
kuka. Bishira tafadi kan dadi ashe gara data fada
masa zancen dataji suna yida fati, gashi yanzun
yayi mata rana. Lallai labe yayi mata amfani sai
kawai tasabi 'yarta tazari mayafi tafice makota,
yau kan tana da labari mai dadi sai yawon raba
shi take bata manta ko kalma daya. Sannan
darana tazo tahau kici-kicin dora girki, lokacin
ummi tafito don yin alwala, ita ko karyawa batayi
ba don tawuni da takaici ya Abba. Tana kallon
yanda bishira tazubu kayan miya tana jajjagawa
batare data wanke ba hancin kawai ta cire. Ummi
tayi alwala tashige daki, ranar har dare ummi
bataci komai ba, duk da tanajin yunwa. Zantukan
abba kawai kemata yawo a kwanya. Tayi kuka
harta gaji fuska ta kumbura. Tun uku yadawo
baiga ummi ba, bishira tagabatar masa da abinci
dakyar yayi cokali uku. Dama yazo dafura, yasha
sannan yanufi shago, yini yayi yana tunanin
kamar bai kyauta ma ummi ba, amma yana
mamakin yanda ummi ta iya cewa bai hau
gadonta ba. Kenan inyahau din dakuma abinda
yabiyo bayan hawa gadon duk zata ringa fesarwa
ne? Kai yafaji haushin abu biyun nan dacewa
bada sonta aka daura masu auran suba dakuma
fada ma fati sirrinsu. Saidai duk dahaka zuciya
da idanunshi suna matukar kewar ganin ummi,
sai shida yadawo gidan. Ruwan wanka ya diba
yanufi bandaki, man shafawarshi dasauran su
suna dakin ummi, don haka yakalli bishira. Bari in
dauko kayana can dakin ummi kozaki dauko min?
Tace, bazan jeba kaje da kanka. Tana kwance
kan doguwar kujera lokacin kanta yana matukar
sarawa, don kuwa yanda yayi sallamar da kyar
itama dinda kyar ta amsa. Saidai ita badon
wulakanci tayiba, saidai don yanda take jin
jikinta. Yashafa mai tare da feshe jikinsa da
turaruka. Idanunshi suka sauka kan darinshi biyu
daya aje mata. Yakalleta, ke ina abincin da kika
dafa? Batare data dubeshiba tace, bandafa ba.
Yace sbd me? Tace banjin yunwa, kaikuma naga
ba anan kake ba, baki ya taba yasa kaya yafice.
Har tayi sallar isha'i lokacin tasoma jin jiri, amma
bata da niyar shan ko tea tanajin ya shigo ya aje
mata ledar ta kusan minta 30 kafin tataso tazo
tatura kofarta. Sannan taduba ledar, nama ne
balango yaji albasa da tumatiri, sai sugar da
madara, nan ta aje su tayi kwanciyarta afili tace
natabbata kurar kenan indai naci maman nan.
Bacci yadauketa can kusan ukun dare fa yunwa
fatakai yunwa, kowa yasan yunwar dare yanda
take jigata bawa, a gigice ummi ta tashi tahada
tea tahau sha da gaggawa. Tagama kamar taci
naman sai kuma tafasa ( tamiko min ninkuma
nayi fuska nacinye au namanta madawani azumi
lolx) ta kauda kayan ta koma ta kwanta, aikonan
fa cikinta yahau hautsinawa. Dagudu tatashi
tanufi fita tana bude kofa kafin takai bandaki
tasoma sheka amai, tun bude kofarta abba
yafarka dasauri yafito. Riketa yayi ganin yanda
take sheka amai kamar zata amayar da hanjin
cikinta, sai sannu yake mata. Data gama yajanyo
ruwa ya wanke mata fuska ta kuskure baki.
Yawanke gurin gurin tana gefe tsugunne, cikinta
da kanta sai ciwo sukeyi tana mikewa sai jiri.
Nan tafadi ragwaf, shine yadauketa tamkar ya
dau jaririya don rashin nauyi yace duk kece kikayi
makanki sanadin wannan matsalar. Don kina
fushi saiki yiwa abinci yaji, ai gashi nan kema
kina ji ajikinki, kan kujer yadorata ya cire mata
siket din atamfar dake jikinta, don duk sun jike sai
na ciki. Yajuyata zai zage mata zif din rigar tana
son ta hana amma bata dawani karfin hanawa.
Tanaji tana gani abba yacire mata riga, gashi ko
best bata saka ba sai breziya. Takai hannuwanta
tarufe kirjinta. Shikam ganinta ahaka yasa tsigar
jikinsa tashi, tun daga karamin yatsansa har
tsakiyan kansa ruf da ciki ta juya tayi, shi kuma
ya kunna mata fanka yafita. Zaune ya samu
bishira atsakiyar gado, ta kalle shi da tuhuma, me
kaje yi dakinta? Yce amai naji tanayi shiyasa
nafita, bta dlpy ne, tsaki taja sannan ta kwanta.
Shi kam bai runtsa ba, kunnanshi da hankalinshi
suna can, dga bisani madayaga baccin yaki sai
yatashi yayi alwala yasomayin nafila. Dazai tafi
masallaci yske lekawa yaga IKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 13
ZURFIN CIKI book 4 part 13
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:05
shikenan yanyun bata dawani aji agurin Abba
ummi da tsoron allura sam taqi tsayawa jiya ma
don agalabaice take Nurse din tace ke dai
shagwaba ta miki yawa A ce allura ma kin kasa
tsayawa kefa mace ce Wata rana ma haihuwa
zakiyi ummi fa taki tsayawa nurse tazo tace ma
Abba taki tsayawa abba yaleka dakin allura
menene haka ummi tsoron alluran ki yayi yawa
kitsaya mana Tadube shi fuska a shagwabe ya
Abba dazafi nikam na hakura da allurar nan Abba
ya shiga dakin ya kalli nurse din zo kimata ba
zanyi asarar kudina ba Ummi bata ankara basai
jinta tayi atsakiyar kirjin Abba shi kanshi sai jin
wani abu yayi yataso daga tafin kafarshi zuwa
tsakiyar kanshi Har yayi baya dasu tamkar zasu
fadi to bare ummi wadda jikin nata ya dauki rawa
Ya kalli nurse dinda idanuwanshi wadanda suka
canza kala nan da nan zo kiyi mata Yadaga
hajabinta tare dazame zanin daidai inda za ayi
mata allurar shigar allurar ta saka ummi cewa
wash tare da sake makalewa jikin Abba Don kuka
tasaka wanda daga jinshi kasan shagwaba ce
zalla ya lumshe ido lokaci daya ya kuma budesu
nurse din tace kai ke kam kin cika shagwaba
Abba ya dora yatsunshi guda adaidai gurin da
akayi allurar yana murza mata tare da rada mata
'sannu' akunnenta Rekicewa tayi sannan ta
kwace jikinta daga gare shi wani yanayi ta tsinci
kanta mai girgiza bawa Ya sauke ajiyar zuciya
sannan yace mu tafi suna cikin mota dukkansu
sunyi shiru Abba kasala ce da muradin matar shi
yasa shizama hakan Ita ko ummi mamakinta ba
yau Abba yasoma taba jikinta ba can baya yasha
rike ta yazane ta, yasha rungumeta ayi mata
allura, bata taba jin irin abinda taji yanzun ba Ta
jingina da kujera tare da lumshe ido sai take ta
tuno yanayin dataji lokacin daya mannata
ajikinshi. Tsayawar motar ne ya sata bude
idanunta, azatonta gida suka zo,sai taga ashe
gurin kayan kwalama ne Ya kalleta, ina zuwa Ya
fita ya nufi zuwa ciki jim kadan ya fito da ledoji,
kaji ya siyo da madara mai tsafta, har da
kankarar dayaji tana tambayar umma yasai
musu. Tace, gama fa kankarar umma tasai mana.
Bishira ta cika fam don takaici, kamal kaninsu
Abba yaduba mata ko ummi tana gidan umma, ya
fada mata bata nan. Ta tabbatar suna tare, ta
cema umman bashir tunfa safe suka fita tare
umma tace tun safe wane iri? Tace wai bta da
lpy yaje kaita asibiti Umman bashir tace Allah ya
tashe mu lpy Goben nan zan tafi kauye dama
gobe ta ce indawo gaje 'yar bori, ina fada miki
ummi dakanta zata bar gidan basai ance mata
ba. Bishira tace dahaka zata faru zanfi kowa farin
ciki, umman bashir tace kece aida shegen kyamar
'yan kauye bakison mutane Matsalarki kenan da
ace zaki jure muje tare kiyi kwana 2 'yar bori da
bokan tsauni zasu cika miki aiki Bishira tace
zanje umma. Biyan bukata ai yafi dogon buri
umma tace taki turo minshi ince masa sha'ani
zamu don kada yace zai hana, bishira tace to.
Sun sameta agidan ummi tayi dakinta da ledar ta
shikuma yashiga gurin bishira. Ranar daya dawo
dakin ta kuwa tayi kyau cikin doguwar rigar
shadda ruwan kunkumadi, tun yana kallon ummi
asace harya kasa dauke idonsa Ummi talura ta
birgeshi sosai don haka tazauna bakin gado tana
fuskantarshi hira ce suke yi jifa- jifa itace ma
tasoma sako zancen Ya Abba zance ma alhaji
yasai min TV nagaji dazama shiru Abba yace a'a
banason haka ina sane zansai miki, tace to
Bishira dake labe ta girgiza kai aranta tace ashe
za ayi bala'i duk randa yakawo TV ai itama ai
iyayenta suka sai mata. Tace to yaya abba
inason makaranta ya aje laptop din daya soma
budewa yamaimaita kalmar makaranta? Ta ce eh,
yace sai nayi tunani Ummi ta marairaice tunani
ya Abba? Kai dakake son inyi karatu? Yace
shikenan haka sukayi ta hira har lokacin
kwanciya ummi tayi shafa'i da wuturi tayi shirin
baccinta takwanta Abba yau yakasa nutsuwa
tamkar yaje ga ummi, amma girman kai ya
hanashi. Ranar sama-sama yayi bacci sau biyu
yna fita yana watsa majikinshi ruwan sanyi kozai
dan samu nutsuwa. Har lokacin daya tafi gurin
aiki bashi da wani kuzari. Ranar fati tazo lokacin
bishira ta tafi badadinta, ummi tahau fati
damasifa tare da fada mata yanda sukayi da ya
Abba. Fati ta rantse tamaya kan cewa ba wanda
yasan zancen nan don bata fada ma kowa ba,
sukayi ta tunanin ta ina ne zancan nan yafita?
Fati tace to ko kiyi hankali koda Anty bishira tana
miki labe? Ummi tayi shiru tna nazari, can tadubi
fati Bazan zargeta ba, domin ban taba ganinta ba
amma zansa ido fati tace gara kisa kam yanzun
harzuwa yau baku sasanta ba? Ummi tace aini
bana bukatar sasantawa dashi tunda yace baiga
gurin kwanciya agadona ba Fati tasaka dariya ke
dai kada kicika baki,ummi tace kedai mu bar
wannan zancen inbaki kudin kayan don Allah?
Tati tace kibani dan bnida matsala mijina she ne
yakaini nasai nawa zance yakaini insai miki
kinason wanduna Ummi tace kinjiki da siket zaki
debo min Ai har gajerun wanduna ki kwaso min,
wulakanci zanyi a gidan nan.vels / ZURFIN CIKI book 4 part 15
ZURFIN CIKI book 4 part 15
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:12
Saidatayi sallah sannan tazauna gaban madubi
duk da shirin bacci take yi Saida tashafa manta
da hoda sannan tadan goga jan baki. Tafesa
turarenta ta isa gurin kayan baccinta dake cikin
dirowar dora akwati, ta dauko duguwa tazira
sannan takama karshen kitsonta tahada su guri
daya ta tufke. Zata ha gado yace, ga nama kizo
muci. Ta fada gado tare da jan filo ta dora kanta
da kirjinta sannan tace nama saikace wata kura?
Dazun fana danci amiyar danayi. Yace nida na
siyo shine nazama kuran ko? Tace, a'a ya Abba
kaine ranar nan naji kace kura. Kullum ake cin
nama? Yayi murmushi aranshi yace, ok nan na
rama ne kenan, sannan yace toshi kenan bari in
ajiye miki naki. Nan tayi kwanciyarta. To 'yar
gidan tsohuwa, yafada danufin zolaya, tace kai
kuma dan gidan ummanka. Cigaba yayi dashiga
yanar gizonsa, ita kam a gajiye take bacci
yasoma fizgarta. Lokacin dayazo shima ya
kwanta akan gado, ta bude ido lpy Yaya Abba?
Ya dubeta tsakaninsu mutum daya zai iya
kwanciya. Wace irin tambayace wannan mutum
da dakin matarsa da gadonta atambaye shi lpy?
Tatashi zaune, gani nayi ba guri agadona, yayi
shiru, wato ummi bata barin bashi, ta tsura mishi
ido tana jira jin mezaice. Yatashi zaune, idanunshi
akan lebunanta, toni dai ga guri na samu, ta
sulale itama takwanta rigingine tare dajan bargo
tarufe rabin jikinta. Shima hakan yayi, ummi
fargaba ce tasa tanemi bacci tarasa, shikam
addu'ar bacci yakaranta sannan yashafa
yalumshe idanu. Duk su biyun bacci sama- sama
sukayi koda Abba baisamu nasarar kama kayan
ummi ba amma aranshi yace wannan sharar fage
ce. Dasannu za'a kai ga muradi, ko washegari
daya kwana adakin dai bawani cigaba sai sake-
sake Abban yayi tayi azuciyarshi, na cewa
yakauda wata kunya ya fito mata amutum, amma
yakasa hakan. Musamman yanda yaga ummin
tana da shegen wayo, ba kamar yan yazata ba.
Sannan gashi ta iya yin ado irin na tsokana.
Hakan yasa duk ranakun girkinta Abba yana
zumudi amma yakanyi kwanan rashin sukuni.
Wata jumma'a tsohuwa ta riski ummi da irn
wannan shiga tariga da gajeren wando, ta kawo
mata ziyarar data saba inta dawo masallaci.
Salati tasaka tare da cewa, yarinyar nan kece
haka kinzamo sai kace arniya? Ummi ta tashi
tsaye tayi juyi tare da cewa. Ynzun tsohuwa ban
birge kiba? Ta ce kitson naki ne kurum yamin
kyau, amma wannan shiga dame tai kama? Kuma
shimai sunan malam yakasa hanaki koke ma
yasoma tsoron nakine? Ummi ta tuntsure da
dariya, ba tsorona yake jiba, shine ma yake son
kayan don shine ma yasai minsu. Tsohuwa tace,
oho! Eh lallai ta mike Allah ya taimaka, duk abin
ku dai baza ki koma baturiya ba, ummi tace oho
dai ke dai kuma baza ki iya wannan ba. Tace,
Allah ya tsare nida wannan shiga, ummi ta dauko
dari biyu ganin tsohuwa ta mike, nizan tafi in dan
zazzaga in ziyarci jama'a. Ummi ta kama
hannunta ta saka dari biyun, gana goron
jumma'a, Allah ya hadamu aladan ziyarar. Suka
fito tana cewa. Ke kullum nazo sai kin bani kudi
ummi, to Allah ya shi muku albarka, Allah kuma
yasa ki sauko lpy. Murmushi ummi tayi duk 'yan
gidan su kallon mai cike suke mata. Duk hirar
nan tasu bishira najinsu, ta cika tayi fam. Dama
Abba yana kwana da ummi? Ashe shine yake sai
mata kananan kaya? Ashe har tana da ciki shine
yamata karyar cewa baya sonta? Tana dawowa
raka tsohuwa, bishira ta kalleta, karamar yarinya
ta iya karuwanci, dube ki. Ummi ta kalleta babba
fa ya rike girmanshi inba haka ba inhau in taka,
kuma niba karuwa bace, kema kalle ki. Ta taso
zan zane kifa? Ummi ma tadaga murya. Sai kace
wata 'yarki? Ba ki isa ba. Bishira tazo zata
shakota, ummi ta daka tsalle taja baya. Karki
sake ki taba ni. Nan fa gidan ya kacame, bishira
sai ashar take zugama ummi, tana kiranta 'yar
matsiyata. Ummi tace, banga kamannin masu
arziki ba a jikinki, nan makota suka shigo yin
rabo. Ummi ko tana fada mata take ramawa, abin
da yafi yiwa ummi ciwo datace ummanki
matsafiya, nasan komai saboda bakin asirinta ne
sahabi yafasa aurenki aka mannawa mijina. Don
shima ya fada min ba ya sonki, har yanzun bai
taba kwanciya dake ba. Ummi tace, kazama mara
sallah me labe, kina labe min akofan don bakin
kishi, kuma insha Allahu sai Allah yasakawa
ummata tunda kika ce tana asiri. Maman amir
kawar bishira tuni taruga takira umman bashir,
sai dai cikin sa'a tanazuwa Abba nayin parking.
Ganin yanda mahaifiyarshi tashiga gidan cikin
hanzari haka shima agurguje yafada gidan, ranshi
yayi mugun baci yanda yaga gidan cike da
jama'a. Ga bishira mutum biyu sun rike ta tana
zambarmar asake ta ta lallasa ummi, ga ita kuma
ummi tsaye akofarta kanta babu ko dan kwali ta
sha gajeren wando ya dan gota gwuiwarta da 'yar
riga tana maida martani. Yace ma matan dasuka
rike bishira, ku saketa suka sake ta ya daka mata
tsawa da karfi, duk ku fice min daga gida,
magulmata tunda duk yawanku kun kasa sasanta
su. Sum-sum suka wucesuna tabe baki, duk
dahaka bishira bata daina magana ba.ZURFIN CIKI book 4 part 16
ZURFIN CIKI book 4 part 16
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:14
Haka umman bashar batasan yarda komai ya faru
ba. Amman ta shiga zagi da tsine ma ummi har
da ce mata karuwancin ne ya motsa, ai dama
nasan tun kafin kixo gidan nan kinsan maza.
Bishira ta ce umma wllhi ga babban mai laifin
nan, muna funtata sukeyi duk ire ire wadannan
kayan na jikinta shiya sai mata su, ni bai siyo
min ba. Na gaji da hakuri ana cutata gwara
yaban takarda ta. Umma tace daina fadin ya baki
takarda insha allahu saidai ita ya bata, Abba
yayima bishira wani kallo tare da cewa ki tafi
mana sai me? Yarda kika gaji da ni nima Haka na
gaji da ke, ya kalli ummi yace ke kuma mi nake
fada maki kullum? Itama cikin fushi tayi magana
toh shikenan saita ta zagina tana ma ummata
sheri don ita kake so? Bishira ta cafke dama ai
ya fadaman baya sonki. Ummi ta kalleshi ko zai
kare kanshi, amman baya kokarin Haka saima
kara zaro mata ido da yayi yana cewa. Ni kike ma
ihu ummi? Zuciya tazo mata wuya nata ganin an
daketa ne kuma an hanata kuka. Shi kanshi ya
tozarta ta da ya fadama kishiyarta baya sonta.
Duk da tasan da haka ta kalli bishira cikin daga
murya tace, an fada maki na damune don baya
sona bana son ya soni don nima bana son Shi....
Mari Abba ya sakar ma ummi da bayan hannu,
kalmar da ya tsana kenan, zafi yakeji a Zuciyarshi
ko tunowa yayi da ummi bata sonshi. Daki ummi
ta fada, ta fada kan gado tana kuka, ya kalli
bishira kije gidan ku sai nazo, umman bashar
tace ba inda zataje kuma in ka sake na samu
labarin ta tafi saina debe maka albarka. Tasa kai
fuuuu ta fice, tunda ka dauki hukunki mai kyau ka
duki marar kunya ai naji dadi. Bishira ma taji
dadin haka, Shi kuwa ba don su yayi ba zafin
furta bata sonshi ne yasa ya daketa. Yana shiga
dakin ummi lokacin ta mike tana kuka, ta dauko
zane ta daura tana kuka sosai. Ta zari hijabi ta
zura zata fita, yace ina zaki? Taki sauraronshi
zata fita ya rikota, ina zaki nake? Tayi magana
cikin daga murya cikin muryar kuka tace gidan
ubana kai kuma ka zauna da warda kakeso,
tunda ya mareta nan ya gane bai kyauta mata ba,
don yasan ba dole bane ta fahimce Shi, sai ya
samu kanshi da jawota ya rungume. Duk da suna
cikin bacin rai Duk kansu saida sukaji wani irin
yanayi. Yace kada kiyi yaji ummi kinsan dai koh
kinje su umma fada zasu maki. Cikin sanyin
murya yayi maganar, kan ummi ya sara, ta kwace
daga jikinshi ta sake fadawa kan gado. Sabon
kuka ta saki, ya zauna bakin gado ya kamo
hannunta ta sarke ya tsunshi da nata ya dan
matsa, ummi! Ummi!! Tashi kiji, cikin kuka tace
mi zanji yaya Abba, kawai ka rabu dani, ni baka
man adalci ba. Ya za'a yi kaje kana fada mata ni
baka sona kasa tana man gori, umman bashar
harda ceman wai ni nabi maza. Ya sake kwantar
da murya yace ki yarda ni ban fadama bishira
cewa bana sonki ba, kuma batun umma kisashi a
gefe kawai don ni nafi kowa sanin halinki. Nafi
kowa sanin tarbiyar umma na... Duk da haka ai
baka kare kanka ba lokacin da take fada ba,
ummi ta katse kiran da yake mata, yasan ummi
sarai yanzu kam bazata saurari komai ba, koma
ta saurara zata ta kalubatanshi ne, don haka sai
yace to Tashi ki bani abinci. Kin Tashi tayi don
kanta jinsa take kamar ya fado, mi kewa yayi ya
fita, ya rasa sukuni, koda yaje shago kasa yin
komai yayi, sai murza hannunsa da ya mari ummi
yake. Ya ciro wayarsa ya kira ummin tayi ta
ringing kusan sau 3 kafin ummi ta daga yace
haba ummi, inata kira kayi banza dani? Shiru dai
tayi bata tanka ba, ummi cikin disashiyar murya
tace, dama haka ne, sai an kwance ma mutum
zane kasuwa azo gida ace za'a daura masa. Sai
ta kashe wayar. Daga nan gidan umma ya nufa,
tace anya Abba lafiyarka kuwa? Naga Duk ka ya
mutse. Ya zauna suka gaisa yace umma ina fa
lafia, dazun bayan sallar jumma'a ina iso wa gida
da yunwa sai kurum na samu gidan tam d
jama'a. Ummi da bishira na tarar suna ta zage
zage har aka samu wata shedaniya taje ta kira
umman bashar. Umma tace subhanallah! To ya
akayi yanzu? Yace tarwatsa taron nayi, nasan
koda ban tsaya bin bahasi ba ummi ce mai
gaskiya. Domin bata kula bishira, Duk yarda akayi
ta kure ta ne. Tsohuwa daga can gefe tace, wai
bayan zuwa na gidan sukayi fadan? Abba yace
oho ni ban masan mafarin fadan ba. Umma tace
kai wannan abu allah ya dai dai ta maka su.
Amman kyanshi kana zuwa ummin ya kamata
kayi wa fada, koma ka zane ta, don itace karama.
Abba har suna hada baki da Tsohuwa gurin fadin
"Haba dai". Abba yace umma in itace da gaskiya
kuma ai na zalinceta, yanzun da haka fushi take,
Duk na tsorata bana son fushinta, sai taki cin
abinci. Don allah umma bari in kira maki ita ki
bata hnkr, umma tace ba zan bata hnkr ba, abinci
kuwa kada allah yasa taci. Sai dai ayi tunanin
abinda ke cikin ta, Tsohuwa tace, wannan
sakaryar matar taka dama na lura fada takeji.
Sanda nayi sallama tana zaune amman amsawa
ta gagareta, don haka ma ko gaisheta banyi ba
na wuce. Ita kuma takwara ka hanata saka
wadannan kayan na arna. Abba yace, su ake yayi
Tsohuwa, Tsohuwa tace, tafdi lallai yayi ya zama
banza. Abba yake cewa Don allah umma ga nmbr
bari in saka maki a waya, ya dauki wayar umma
ya saka mata lambar wayar da ke hannun
ummin, yace umma na roke ki lallasheta ba wai
fada zaki mata ZURFIN CIKI book 4 part 17
ZURFIN CIKI book 4 part 17
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:17
Duk jumma'a abba yana dawowa gida
musamman in ranar girkin ummi ne don cin
abinci na musamman. Jumma'a biyu kenan bata
fado kanta ba sai wannan, don haka tun alhamis
taje ta yarfo kitsonta, ta biyo ta gidan su gurin
tsohuwa tazo. Don haka suna gaisawa da umma
tace gurin tsohuwa nazo. Suka shige daki tace da
tsohuwa nazo ne indan samu dan wani sirrin.
Tsohuwa tace, name ummi? Ta ce na gyaran jiki
mana. Fati tace min kwanaki kin fada mata wasu
abubuwa. Tsohuwa ta ce, ja'ira, kinga uwar bari?
Dama nace zaki same ni ina kyakkyawan zamana,
bada ina fada miki kina sharewa ba? Ummi tace
haba tsohuwa banaso aji mu yanzun dai ki bani
shawara sannan ki fada min abinda zanyi inja
hankalin mijina. Ta ce, toda farko ki dinga kula da
jikinki ta hanyar rufe shi ruf, kada kibar kofar
iska. Banda tafiya ba takalmi, iska tana shiga
tanan kuma mace narage ni'ima banda zama ba
dankwali inso samu ne hatta tsarki ki daina yi da
ruwan sanyi, ki dinga yida ruwan dumi. Sannan ki
amshi bagaruwa gurin ummarki ki dinga shiga
inkin tafasa da alif dakuma saiwar mata, sannan
inkinyi al'ada kin gama kinyi wanka toki dinga
matsa farin miski a ehem dinki. Sannan ki samu
saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,
mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari
dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi
biyu safe da yamma. Sannan ki aya garinta,
kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,
sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar
ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai
ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,
citta, lemun tsami, ki markada su kisha. In anan
maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum
daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta
musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban
da dukkan sauran mata. Ki hada da biyayya
tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi. Ummi
tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin
nan? Tace, bari zanba matar ado dake yawan
zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu. Amma
su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya
siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin
ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.
Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje
gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi
tasan duk wadannan hadin matan? Tun ranar
alhamis din ta soma aiwatar da darussan da ta
debo daga tsohuwa, safiyar jumma'a ranar zai
bar dakin bishira. Ya fito tana sharar tsakar gida
ta gaidashi, ya amsa da fara'a, tare dawani kallo
mai fassarar in ba keba. Cikin muryar data adana
don shi kadai tace, ya abba ina son in je ayi min
zanen fulawa. Yace jiya kin fita yau kam a'a.
amma ki aika akira mai zanen tazo ta miki. Ta
marairaice, towa zan aika yaya abba? Yace aike
ni, ina ne gidan? Tace layin su umma ne yace to
za'azo ai miki. Bishira tafito daga daki tazabga
ma ummi harara, Tare dacewa kisisina. Abba
yakalleta, kema sai tayi miki. Tace bana bukata,
aikin banza, shikam yafice. Ummi kuwa tace gaba
da aikinta, ita ko sai tasa kujera tazauna tana
sakin zantuka, eh don kwalliyar tabanzanta tunda
ba a iya biyawa miji bukata. Allah dai yasa ya
fada min komai, to ni me zai dame ni don 'yar
aiki kawai na dauki yarinya. Tashare min gida,
tayi wa mijina abinci, daga nan fa? Saita saki
shewa, ummi ta ce aranta yau zan bambance
miki. Birabiskon shinkafa tayi da miya, ta wadata
birabiskon da kayan lambu, miyar ta dauki nama
da bushasshen kifi. Sannan ta hada musu kunun
aya yaji dabino da madara, ta aikawa ummanta
lokacin da kamal yazo daukar na ummarsu.
Tasheka wanka taci doguwar rigar shadda koriya
mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau ne daurin
aurensu. Ga fulawar da yaje ya biya akazo aka
zana mata. Tanajin rigimar muhibba tafito tazuba
mata adan kwano tazaunar da ita akofar falon
mamanta. bishira tafito kicin baki tasaki tana
kallon ummi da tazo wucewa harda bangazar
ummi, nan ko kamshi ya bude ta na turarukan da
ummi ta fesa. Abba yana yin sallama ummi tafito
da sauri, oyoyo yayana, bishira tana daga kicin
dinta tana kallon su. Ummi ta rungume shi,
sannu dazuwa sahibina. Ta amshi ledar
hannunshi dajakar, yace yauwa sannu babyna
tace inazan kai ledar? Yace akwai ta bishira aciki
ki ciro. Ta mika mishi ledar ta wuce dajakar
dakinta. Ya mika wa bishira lemo da abarba da
yayo musu tsaraba sannan ya wuce danasu,
awulakance ta aje. Yana shiga ummi tadan karo
kofar yanda bishiran zata iya lekensu sosai ta
gefen kofan. Ta cire masa hula ta aje akan
madubi sannan ta kunna fanka. Ta shirya masa
abinci, yauni zan baka har ka qoshi. Haka suka
yita baiwa juna abaki har suka qoshi. Yakamo
hannunta mai qunshi yana ta sumbata, wai kamar
kada su goge. Kumatun shi ta shafa nima yau
kamin kyau, koda yake dama kai me kyaune, ina
sonka ya abba sosai. Cikin jin dadi ya mannota a
jikinshi, nima ina sonki, ina manta kowa da komai
in muna tare, tace ina tsoron kada wata rana ka
juya min baya. Ya saqalo hunnuwansa cikin nata
ina fata in mutu kafin lokacin. Ummi tasomayi
masa wasu irin darussa wadanda tasan yana
saurin tada sha'awarshi nanda nan kuwa tasa shi
fita hayyacinsa yakama surutai. Ummi ta tabbata
bishira tana wurin ta labe, don haka tai murmushi
ta bishi suka tafi duniyar ma'aurata. Bishira
tamkar tayi hauka sai kawai ta fado dakin tana
fadin, maciya amana, har yanzun ba afita daga
lokacin girkina ba munafiki. Abba ya tashi sannan
yaja riga yasaka, ok dama kina labewa ne kiji
sirrinmu? Da taga ya sauko da zafin rai saita
gudu dakinta. Yabita yamata tatas, kuma ya fada
mata cewa tazo ta shiga dakin ta zauna ba labe
ba, yanzun zai komane yaci gaba daga inda ya
tsaya. Tayi ta kuka gashi ba damar zuwa gurin
umman bashir dole ta tafi gidansu. Shi kam abba
shareta ya yi kosu umma bai fadawa ba. Sabuwar
soyayya ma ya balle agidan, su ci abinci tare,
wanka tare, su fita yawonsu a qafa ko amota. In
yana gurin aiki bini- bini ya kira waya, ita kuma
ko yaushe cikin kirkirar girki da kwalliya tare da
dadadan kalaman dazata fada masa take.ZURFIN CIKI book 4 part 18
ZURFIN CIKI book 4 part 18
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:19
Ummi tayi alalar gwangwani ta sauke kenan sai
ga aunty farida da yake tunda akayi auren ummi
batazo gidan ba. Har daki ummi ta shiga suka
gaisa tayi masu addu'a zama lafia, tayi mata
nasihar zama da miji. Umman taji dadi tare da
kwadayin ina ma bishira take da halin yayarta, ta
zuba alala ta kaima aunty falon bishira. Ta isko
su tana mata fadan kaxanta, cikin murna aunty
ta anshi alalar taci bishira ta cika fam. Tun tana
jurewa har tace aunty ai kin zubar min da kima,
ya ya za'a yi ki anshi abun kishiya kici. Aunty ta
kalli bishira fuska daure tace ke da ita akwai
bambamci ne? Bishira tace aunty bambamci ma
nifa jininki ce ita fa? Aunty tace a musulunci fa?
Bishira ta hade rai tana kallon aunty, taci gaba
da cewa, A musulunci tama fiki don tana sallah,
Haka nima ina sallah, kefa kin faru? In kin soma
sallar to kin shigo cikin mu ni da ita. Domin
addinin mu ya nuna muna dukkan musulmi dan
uwan musulmi ne. Inji mai tsira da aminci. Haka
zan iya cin abincinta banci naki ba don bakida
tsafta. Ta daka mata tsawa tashi don allah
malama kije kiyi wanka, ki wanke duk jirwayen
nan naki kafin In daukeki da motata. Da zasu tafi
har kudi aunty farida taba ummi, ummi kam
godiya ta dinga yi. Haka nan da abba ya shigo ta
nuna masa tace ai abba ya ciri tuta a zuri'arsu,
halin mahaifinsu ne da ita. Wata rana aunty ta
bugo ma abba waya cewa aisharsu ta haihu don
allah ya fadama bishira koda ya iso gida ya fada
mata nan ta shiga murna. Washe gari tace zata
gida tama mahaifiyarsu barka. Sannan taji randa
zasu abuja wurin aisha. Yace ta shirya ya
sauketa, ta samu aunty tazo nan dai sukeyi wa
juna barka, mahaifiyarsu tace dubi yar uwarki sai
yanxu ta haihu gwanin shawa. Amman kinje kin
gwarje miji ma yayi maki kishiya, dubeki kamar ba
yar gidan nan ba. Aunty tace mummy ai ita taso
ta zama Haka, tunda kaxanta ce sana'arta.
Hajiya zainu tace ni wani lokacin bana ganin
laifinta a kaxanta, don a gida bata saba aiki ba.
Laifinta daya a gurina wannan abba data nace ta
aura, data tsaya ta gama karatunta ta auri wanda
zai dobo mata yan aiki komai saidai ayi mata
tana daga zaune, amman ta likema talakan tela
wanda bashida ko sisi. Aunty ta katse mamarsu
da cewa In tana da yan aiki shine har wanka
zasuyi? Ta cire dan kwalin dake kan bishira kalli
fa mummy har kanta zasu wanke mata. Mummy
tace aiki gida ya mata yawa, yaushe har ta gyara
jikinta? Aunty tace kawai mummy kina goyon
bayanta ne. Bishira tace aunty mummy ta
fahimta kece baki fahimta ba saboda kina da yan
aiki. Mummy tace duk ba kece kika yima kanki ba,
ga kishiya an maki, bishira ta tabe baki nima duk
nadama ta isheni. Kuma shi da matar duk bana
raga masu. Don ban damu ya sakeni ba, yaji ne
dai nace na daina, daddy ko nazo cin mutuncina
yake gabansu. Mummy tace kin man dai dai.
Haka yake bishira kullum cikin tsokanan hayaniya
da ita da miji ko kishiya. Amman ummi yamxun
bata kulata Domin umma ta gargadeta. Bishira
bata bar gidan ba saida mummy ta zugata
Sannan tace mata jibi kizo za a kai su innarku
yin barka abuja kije ki dan huta kafin suna.
Bishira tace daman ban taba zuwa ba, ko anyi
suna sai na huta. Aunty tace kada ku yanke
hukunci ba tare da sanin mijinki ba kije kiji ta
bakinsa. Bishira ta ce ina ruwana da yardarsa
aunty. Haka kuwa data dawo ta shiga tattaro
kayan ta dake jibge a gefen gadonta, don ita zane
ko yau a aka dinka shi In tasa ta cire duk In da
tayar kafin ta dauke shi yaji jiki. Wani ma saita
goge ruwa ne, kamu ne, duk kyan zani saita goge
tsakar daki dashi. Ranar dama abba dakinta
yake, tace mashi jibi zamu abuja Inji mummy.
Taso ya dan sai mata zani sabo wanda zata
danci suna ya dinka mata. Yace akwai wani leshi
dan sai maku yana shago, Tun wancan satin
naso In zauna In dinkashi da kaina don mai tsada
ne. Tace nawa ka siyeshi, yace dubu biyar ko
wane daya, bishira ta tabe baki. Na zaci zakace
sha biyar wai dubu biyar, yace matsalata da ke
rainuwa yace bari zansa a dinka maku gobe ashe
sunan har yazo? Tace a'a jiya pha ta haihu, ya
sake kallonta jiya? Shine zaku tafi jibi? Tace eh
mummy ce tace mu tafi jibi. Yace a'a kibari sai
ana gobe suna kije. Kafin lokacin ma na samu
wasu kudi da nike sa rai. Sai na sai maki kayan
barka zanen maman da kayan baby. Bishira ta ce
gaskia gobe zamu tafi, In ka sayi kayan barkar ka
aika dasu can wurin mummy yan tafiya Ranar
suna su kai mata. Abba yace nifa ban amince da
tafiyar nan gobe ba. Ban yarda ba. Bishira ta ce
ba wai ina neman yardarka bane, ina fada maka
umurnin da mummy ta bani ne, ko ka mance
mahaifiyata ce? Mamakinta ya cika abba, yace
mahaifiyarki ita zata baki izinin tafiya ko ni?
Umurnina da nata yanzu wanene...? Bishira ta
katseshi kada kayi ganganci hada kanka da
mahaifiyata, ita ta haifeni ta raineni har ka ganni
kace kana sona Sannan ka dinga kokarin
kwatanta kanka da ita? An fada maka kowa
baisan darajar mahaifiyarsa ba irinka? Abba ya
mike ni ne bansan darajar mahaifiyata ba? Tayi
shiru yace nagode Kuma suna na hanashi ma
gaba daya. Zan gani Kuma Bishira ta ce zako ka
gani.ls / ZURFIN CIKI book 4 part 19
ZURFIN CIKI book 4 part 19
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:14
Duk ummi tana jiyo su amman bata fito ba, tana
ta mamakin yarda bishira batasan darajar
aurenta ba, bare tasan girman miji. Ranar da
zasu tafi kuwa ko a jikinta ta dibi tsummanta ta
nufi gidan su, Duk ta fadama mummy yarda
sukayi. Mummy tace kinman dai dai talakan
banza shine zai hada kanshi dani, tafiya zakiyi in
yaso in kika dawo ya ce baya auren. Abba ya
dawo ya samu dakinta a rufe, ummi na daka
sakwara a kofar dakinta yace ina bishira? Ummi
tace ina ga ta fita, don ina daki bansan fitarta ba.
Ya daga waya ya kira aunty yace bishira tazo?
Aunty tace bata fada maka zasu tafi abuja bane,
Abba yace ta fadaman amman nace a'a sai ana
gobe suna zataje, ya kwashe komai ya fadama
aunty. Aunty tace kayi hnkr don allah idan ta
dawo da kaina zan hadata da daddyn mu, Abba
yace kiyi hnkr aunty na gaji da halin bishira inga
wannan karo gwara kowa ya huta ni da ita. Aunty
tace kayi hnkr Abba yace sai anjima ya kashe
wayarsa. Zama yayi kan kujera dakin ummi yace
gaskia wannan karo bazai fadawa kowa ba ya
gama auren bishira. In bai nuna mata kurenta ba
nan gaba zata masa abunda yafi wannan don
Haka yabar komai sai ta dawo. Ummi kam
batason ya rabu da matarsa, amman kam saida
taga tarairaya cikin kwanu kan nan matsalarsu
daya, Abba yace ummi kodai asibiti zamuje ne,
ummi tace muce masu mi? Yace muyi masu
bayani mana, ummi tace a'a. Yace to muje mu
fadawa umma, ummi ta zare ido yanxu sai kama
umma wannan zancen? Yayi murmushi. Ai da zan
iya mata wannan maganar da tuni na mata,
asibiti ma abunda yasa banson zuwa sai likita ya
bukaci ganin wurin. Ni kuma ina kishin wani
namiji ya kallan mi al'aurarki, ummi tace nima ai
shine, ya sake janyota jikinshi. Yanzun Haka
zamu zauna? Shine nakeson in fada maka naji
kana ka gaji da aunty bishira kila zaka saketa ne.
Toh don allah ka rabu da ita tunda ko ka saketa
sai ka auri wata. Tunda nasan zama Haka bazai
yiwu ba. Ta soma hawaye ya shiga lallashinta
yace Allah zai yaye masu. Haka sukaci gaba da
rayuwa cikin kwanakin da bishira bata nan, ummi
tanason kalolin wasanin da Abba ke mata,
amman da yaso kwatantawa ko allah ya amshi
addu'a su ta warke saita kwace jikinta ya hau
bari tayi ta kuka. Don Haka sai ya hnkr da
bukatarsa amman ya takura sosai, kuma yana
ganin dole yabar batun bishira yanxu don Haka
ya jaye batun saki amman sai dole ya nuna mata
kurenta. Ranar data dawo kwananta takwas
Ranar ma bata da niyar dawowa sai da aunty ta
kira mahaifinsu ta sanar dashi, ya kirasu a waya
ya zagesu tas gaban mahaifiyarsu harda mai
jego. Tace bishira ta dawo shine ya kira Abba da
waya ya bashi hnkr yace Duk irin wannan ta faru
ya kirashi ya sanar dashi. Abba ya shigo da T. V
guda 2 daya ya kai dakin ummi, daya ya kai falon
bishira wanda ya yanke kwadon. Ummi tayi ta
murna bishira kuma ta daki Duk rashin kunyarta
gabanta sai faduwa yake, batasan ya zasu
kwashe ba. Sai da taga baiko kalleta ba daga ita
har yar sannan ta dan saki jikinta, tasan ba zai
tsaya a fushi ne in taci sa'a. An dauki sati guda
Abba baya ko kallon inda bishira ta ke ko Ranar
girkinta sai dai yayi kwanciyarsa a falonta. Duk
da yana bukatarta Haka kuma ya janye yan
wasanin da yake da ummi don wahalce yake
bacci, ita kuma sai ta damu don ya saba mata
sai tayi tunanin ko laifin tayi masa ne. Ita kam
bishira ganin zura ido ba zai kaita ba, don Haka
ta sauke zafin kai ta iske Abba a falonta wani
dare harda kukanta take bashi hnkr. Wai sherin
shedan ne ba zata sake ba, Abba ya dubeta mi
kikayi? Tace nidai ka yafeman, yace ashe kinsan
kinyi ba dai dai ba? Ai inda ke ce saikin kara,
amman bari kiji na rantse maki duk kika kara
zuwa wani wurin bada izinina ba wllhi sai kinsha
mamaki. Tace na yarda, abun mata da miji nan
dai suka sasanta, hakan nan dakin ta ya kwana,
suna shiri cikin satin don bishira ta fahimci mijnta
ita kadai a matarsa, yarda yake rawar jiki lokacin
kwanciyarsu. ***ummi na zaune idonta kan tv
Abba take kallo yarda yake watso turanci cikin
kwarewa. Kullum kara sonshi take, ta kwantar da
kanta a hannun kujera, kusan sati guda kenan
tana lura da Abba. Baya son ko taba hannunta
sannan ga wani shiri da yake da matarsa, sai dai
yazo yaci abinci ya dauki laptop dinsa ya raba
dare. Inko yazo kwanciya saidai ya juya mata
baya sabanin kwanaki da yake mata makwanci da
hakarkarinsa, lokacin tasan babu inda keda dadin
kwanciya ga matar aure irin hakarkarin mijinta,
sam bata iya bacci sai tunanin abunda tayi masa,
amman yau din nan zata tmbysa ko laifi tayi
masa, Bayan yaci abinci yayi wanka ta dauko mai
zata shafa masa ya amsa da murmushi yace
barshi kawai nagode, ta dawo ta zauna, zaya fita
tace ina zaka ya Abba, yace aski zani, ko zaki
rakkani tace eh yace taso muje. Suna tafe suna
hirar aikin shi, yace An koma kirkirar wani filin
kuma An saka shi ciki, yanxu abubuwa zasu kara
mashi yawa. Sun isa babu layi An suma mashi ya
mika mata wayoyinsa guda biyu tana danne
danne kira ya shigo. Nan take ta hade rai ganin
sunan dake jiki zainab dina, ya tmbyta da ido
waya kira ta sake hade rai, sannan ta mika masa.
Ya kalli sunan zainab sannan ya daga cike da son
ya zolayi ummi yace zainabuna. Can bangaren
Duk da kallaman Sun mata dadi tace da ba
amman yanxu ta wani ce. Yaya salis ya kawo
maka katin aurena? Yace eh yabani tace ya
amarya? Yace gata bari in bata ku gaisa, ummi ta
kauda kai tare da jan tsaki, yayi dan murmushi
yanason yanda ummi ke nuna kishinsa, salon da
take wurin kishinta daban ne. Yace zainab Wai
tana gaisheki, zainab tace to ina amsawa. Ka
gaida umma sannan ka sai masu anko kalla biyu
ne. Abba ya naji ko kalla goma ne zan saya tace
to gobe kazo gidan mu nan ake sai dawa. Ya kalli
ummi yasan kadan ya rage ya kaita bango. Ya
danne dariyar da ta taso masa yace gobe kikeso
nazo gidanku zainab? Tace eh don gobe za'a
kawo wasu kayan, yace to zanzo, ummi ta zaro
ido ta mika tsaye dai dai lokacin da aka gama
askin. Yayi sallama da zainab din sannan ya
shiga karkabe jikinsa. Ummi kam tuni ta kai bakin
kofa. Ya sallami mai askin ya isketa Sun jera
yanxu ba kamar daxun da suke fira ba. Sun kusa
layinsu yace muje mu gaida su umma tace ni
bacci nakeji baice komai ba, Sun iso hijabi kawai
ta cire ta kwanta, yace Wai lafia don zainab ta
kirani tun dazun kin kasa sukuni?URFIN CIKI book 4 part 20
ZURFIN CIKI book 4 part 20
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:17
Ummi ta taba baki, Allah yakawo ta lpy. Ya ce ni
ban soba gsky. Sbd ke ummi tadafa kirji, sbd ni?
Ni ya abba, kada kasa duniya ta zage ni, Tare fa
nasameku? Yace to ni dai kada kiga kamar da
son raina, tace don Allah ya Abba kabar zancen
nan. Kaje kagyar mata dakunanta don su kamal
bazasu iya ba, yanufi gurinsu ganin kamar ya
damu yasa itama taje tasa musu hannu don dai
ya saki ranshi, sun gyara tsaf ummi ta goge
sannan ta rufe dakin. Har magriba bishira bata ji
an ce za'a maida taba, sai ta dauki wayar
kanwarta ta kira shi wai yazo don Allah
yadauketa. Tsakanin mata da miji sai Allah, nan
ya tausaya mata yace zaizo, kafin ya isa sai daya
sai mata waya irin dai ta hannun ummi. Har cikin
gidan ya shiga suka gaisa da babanta, yayi
murna sosai yayi tawa Abba godiya, tare da ba
shi hakuri yace yasan yanda ta horu zai gata
canza da yardar Allah. Yasa aka turo ta yayi
mata nasiha, sannan ya gargadeta da cewa inhar
ta bari mijinta yakawa kararta zatayi mamakin
abinda zai mata. Tace, insha Allahu baza ta kara
ba, yakawo kudi yaba Abba, da kyar ya amsa ita
kuma ya bata wasu zannuwa acikin leda, yace su
raba da abokiya zamanta. Taje tayi wa hajiya
zainu sallama suka tafi, tamkar baquwa haka ta
koma, sai kace basu taba zaman aure da Abba
ba, nauyinsa take ji. Suna tafe ya ciro waya ya
miqa mata, tasa hannu ta amsa yace taki ce, tayi
ta godiya yace ba komai. Sallamarsu tasa gaban
ummi faduwa, ta dake ta fito ta amsa, wani kishi
ya tasho mata amma saita danne. Ta kalli bishira
tare dayi mata sannu dazuwa, ta amsa tana
kallon ummi tayi kyau tagoge daga ka ganta
kaga wayayya 'yar gatan miji. Ta dauko makullin
dakin ta ba bishira, abba kuma ya nufi dakin
ummi. Bishira ta dinga kallon yanda abba ya
gyara gidan yaja gini ta gefen ummi yayi mata
falo da kicin, sannan tsakar gidan an gyare shi da
tiles. Haka bandakin su yagyara shi, nan dai
bishira ta shiga dakinta ta zauna bakin gado tana
yi wa allah godiya tare dayi wa kanta alkawarin
har abada bazata ta kara yin yaji ko ta janyo
abinda zaisa mijinta ya sake ta ba. Ummi tana
kan gado tana karanta wani littafi yazo ya zauna
bakin gadon bata ko kalle shi ba don haushi take
ji. Sai take ganin kamar rawar kai yake yi da
dawowar bishiran, kuma tuntuni yana zuwa gurin
ta ya boye mata. Yace madam ina son in yi
magana da ku ne ke da bishira, ummi tace ina jin
ka, yace can zaki zo muje. Tace, gsky nagaji, kayi
maganar da safe. Yagama gano kishi ne ke
damunta, don haka yayi murmushi yace yanda
kikace hakan za'ayi. Ya fita kamar minti 30
yasake shigowa ya aje mata leda tare da cewa
saida safe aciki tace Allah yabamu alheri. Yana
tafiya taje ta banko kofarta, yau kam bacci ya qi
idanun ummi sbd tayi sabon bacci a haqarqarin
Abba. Dukkan filolinta ta rasa wanda zai maye
mata madadin haqarqarin mijinta, ynzun yancan
da wata tasan yanda yake wannan rawar jikin
ynzun ya manta da batunta. Tarasa me yake
mata dadi, littafin datake karantawa kuwa sam
bata fahimtar abinda ke ciki. Hka ta dinga zubda
hawaye har nisan dare, ganin bata da wata
mafita, tashi tayi ta bude kofa lokacin 2 saura
taje tayo alwala tazo ta kama nafila. Abba jin
bude kofarta ne yasa shi leqowa ta window
aranshi yaji tausayinta don yasan bata iya bacci
sai ajikinshi, ita bata san ya leqo ba don ko
hanyar dakin bata ishe ta kallo ba. Yakalli bishira
wadda bacci yayi gaba da ita ya tausaya mata
sosai yanda tayi tarawar jiki alokacin
auratayyarsu dazun. Yadauko wayarshi yarubuta
ma ummi sako. KI KWANTA KIYI BACCI BABY,
TARE DA QISIMA CEWA KINA LAFE
AMAKWANCINKI (WATO JIKINA) INA CIKE DA
KEWAR LEBUNANKI Tana sallah taji shigowar
saqo amma bata yi ko marmarin dubawa ba, haka
tai sallah har zuwa lokacin da bacci yasoma
fizgarta. Tayi adduo'o'i sannan ta kwanta, saida
asubahi ne datayi sallah sannan ta karanta, dan
tsaki taja tare da cewa, Karya kawai, kishi yasa
ta fadin haka don tasan Abba sosai baya boye
mata komai ynzun. Sai dai abinda yasake qular
da ita da asubahin nan yanda tana fita shi kuma
ya fito wanka, duk da tasan dole wani abu yafaru
tsakaninshi damatarsa, amma sai taga tamkar da
gayya ya tsaya don tafito taganshi. Tna idar da
sallah ta dora ruwa akicin dinta, tadafa ruwan tea
taje kicin din bishira tadauko flask tazo ta wanke
ta zuba musu ruwan zafi taje kofar bishira tayi
sallama bishiran ce ta bude ummi tamiqa mata
tare da cewa an tashi lpy? Cikin sakin fuska tace,
lpy lau, nagode. Ummi ta ce ba komai takoma
dakinta ta kulle kofarta don yau bata da darasin
safe. Abba ma yau bada wuri zai fita ba, don
haka yadan samu baccin safe sai 8 yayi wanka
ya karya, sannan yanufi dakin ummi. Kofarta tana
rufe, ya kwankwasa ta share sai can dai dataji
yaqi tafiya sannan tazo tabude. Takalle shiya yi
kyau cikin kananan kaya, ta kauda kai tare da
cewa, an tashi lpy? Yace lpy lau, kin karya? Tace,
um'um sai anjima, zata rufe kofar yace,
makaranta fa? Tace sai karfe 2 nake da darasi.
Ta maida kofar ta rufe, yayi dan murmushin
takaici sannan yafita. Kwananshi 2 dakin bishira
yayi niyyar dawowa dakin ummi, don ya kosa
yadawo ya lallasheta bazai iya daukar wannan
shariyar da take mishiba. Tsakaninta da bishira
lpy lau amma shi sai tana wani share shi. Ya
shigo da zumudi zai nufi dakinta, tamiqe cikin
fara'a daga wanke-wanken da take yi ta amshi
ledar hannunsa da jakar laptop ta nufi dakin
bishira. Shida bishira suka bita da kallo, ganin
zata shiga bishira tace ummi yau ai dakinki yake.
Ummi tace injiwa? Anty bishara ai kullum ke ce
dashi har sai kin rama duk kwanakin da kika
dauka agida. Kinga kenan kusan wata goma sha
daya kenan. Abba cikin sauri yace ke
mahaukaciya ce? Ina ki kasamo wannan fatawar?
Ta kalle shi, sannan tashiga dakin ta ajiye ta fito
taqara kallonshi gurin malamai, yace to ban
yarda ba, don haka zanci gaba dayi muku kwana
bibbiyunku, ummi tace to ni na yafe mata nawa
kwanakin bishira tace nagode ummi. Haushi ya
cika Abba, amma shi bazai dauki wannan horon
da ummi take shirin yi masa ba. Yadawo dakin
bishira a fili yafurta kema saina baki haushi zakiyi
dakin sanin wannan furucin. Sharewa yayi yaci
gaba da kwana dakin bishira tare da nuna kulawa
ga bishiran. Ummi ta jure duk da duk daren Allah
sai taci kuka ta gode Allah, sannan tashiga zargin
cewa shi ma ya Abban dama can yana son
tarewa dakin bishira, inba haka bame zaisa yayi
saurin yarda kuma yayi ta nuna mata soyayya?
Ganin ummi tana yi tamkar bata damu ba yasa
shi qa rajin haushi, yadawo da yamma suna
zaune kowa A qofarshi. Ummi tayi kwalliya cikin
qananan kaya, bishira kuma tana sanye da leshi,
karatun littafi bishiran keyi ita kuma ummi tana
yin gyaran qumbunanta. Bawai suna wata hira
bane amma suna kula juna sosai musamman
bishira tana son su saba da ummi. Ummin ce.
bata cika son fitowa ba, bishira ta tashi ta masa
sannu dazuwa tare da amsar kayan hannunsa
don yanzun tana koyi da ummi gurin kyautatawa,
ummi ta kalle shi sannu dazuwa, ya amsa da
yauwa baby. Yakalli bishira sweety zanyi wanka,
tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai
tazo tace masa takai nan k sweety zanyi wanka,
tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai
tazo tace masa takai nan kuma yajanyo bishira
jikinshi. Ba wai yana da bukata bane, amma don
ya shaqar da ummi sai ya banko kofar, qaran
kofar ne yasa ummi kallon gurin dakin. Ta duqar
dakai taci gaba da abinda take yi, kusan minti
arba'in suka fito, Abba ya matsawa bishira wai
suyi wanka tare, tace ni bazan iya ba akwai ummi
dama da dare ne inajin kunya. Kuma kada taga
kamar cin fuska ne, yace kenan don kada ki bata
mata rai ni mijinki bazaki faranta min ba ko? Dole
ta bishi suka shiga bayi. Baqin ciki yasa ummi
tashi tashige daki, kuka sosai tayi daga nan bata
fito ba sai magriba, tanayin alwala tarufo kofa,
washegari ma qin bude qofar tayi daga alwalar
asubahi. Abba yayi ta raba ido ya ganta amma
bata fito ba, yasan fushi take, ya kira wayarta
taqi dagowa yayi mata saqo cewa in zata
makaranta tafito inkuma sai darana ta bude ta
amshi kudin mota. Tana gama karantawa tayi
wuri da wayar ba tare data bashi amsa ba, haka
ya tafi. Bishira ta qwanqwasa ma ummi ta bude
suka gaisa, tace naga baki fito bane ina fata lpy?
Tace lpy lau bacci ne, tace yau baza kije
makaranta bane? Ummi tace, zanje sai sha biyu.
Bishira tace kinji dadinki ni gashi nan ina tayi
masa zancen karatun amma ya share ni, ummi
tace inkin matsa zai yarda, tace ko za ki dan sa
min baki? Ummi ta riqe baki, ni a wa? Ke da yake
hannunki ai ke ce zai saurara, ni kin zo ne ma ki
zage ni. Bishira tace wane irin zagi? Ni dama ki
amshi mijinki ummi don gangar jikinshi ce kawai
agurina, amma ruhinsa yana gurinki. Ummi ta ce,
ngd da zagi, bishira ta ce zancan gsky ne ba
wani zagi. Haka suka yi ta rayuwa cikin kwanakin
ummi kam har rama tayi shima Abba ya rage
walwala don wanda yasan kan kula da shi
kamarta. Yayi missing din abincinta. Amma ya
gaji bazai jure ba. Ya tuna bishira tace masa zata
ta yini gidan ummanshi. Don haka yana gama
muhimman abubuwan da zai yi agurin aikin
yanufi gida. Ummi tana shirin tafiya makaranta ta
dauko jakarta sai kurum taga mutum kamar an
jeho shi. Ta daure fuska tamkar bata taba dariya
ba, yace ummi nagaji kin ji ko, na gaji da wannan
horon naki. Laifin me nayi miki? In don na dawo
da bishira ne sai in saketa, duk ba kece kika
takura min sai na dawo da ita ba? Ummi tace, ni
karka doran jakar tsaba kasa kaji su bini, ka saki
matarka sbd ni? Ba ruwana. Yace, to ki dawo
yanda kike, kuma ki janye batunki na wai kin
haqura dani, niban haqura ba. Ke ma kuma nasan
dole ki kasa kanki, ummi ta ce ni ban damu ba,
ya ce qarya ne gashi nan duk kin rame? Ya
canza daga fada zuwa lallashi, ummi don Allah
na roqeki mu koma kamar da, haba bebyna. Ya
lalubo hannunta ta qwace, don Allah ka tafi kada
bishira ta dawo ta same ka anan ta zargi wani
abu. Haushi yakamashi sosai, ya daga murya da
qarfi, kin san Allah ummi zan hadaki da umma, ta
nufi hanya fita, nikaga kada kasa ni yi latti don
lokaci yayi nisa. Ya ficiko ta ta dawo ba zaki
makarantar ba, ke an ma daina karatun tunda yafi
ni. Ta zubar da jakar da hijabi ta nufi gado shi
kuma ya fita cikin zafin rai, gidan su umma yaje.
Bishira tana dakin umma tana sallah yabi umma
kicin, umma gurinki nazo, ta dube shi lafiya
Abba? Ya turo baki, alamun ranshi bace baki,
yace umma ki sallami bishira, tace kamar yaya?
Yace taje can gidan ko muyi maganar agabanta?
Tace, kyale ta muje dakin babanku. Abba ya fada
ma umma komai da ummi ke masa, tun dawowar
bishira ran umma ya baci tace ka barni da ita.
Banda shashancin ta da ita kadai take son
azauna? Baga bishirar nan ba gidan nan ta gane
kuskurenta ko yau yarinyar nan sai da tace in
yafe ta nace ni dama ban riqe ta da wani abu ba.
Shine ita zata qirqiro fitina? Yace, umma ai ba da
bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane
kurenta da dare kuzo kai da ita. Umma ce ta kira
ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu
don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar
isha'i taje gidan. Can tasamu abba, nan ko umma
ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo
umma tafada mata komai sai ta shiga fada. Wai
ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko
ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya. Abba
yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun
in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma
ni abin ya qare akaina? Nan fa umma tayi mata
tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka
kira shi awaya ya fita. Umma ta samu dama
taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki
yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice
kinyi fushi da ita kin barwa kishiya? To kada in
sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke
ganinki da ita. Ta jima tana bata shawara kafin
Abba yadawo suka nufi gida. Ya shiga gurin
Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai
kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,
tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa
s / ZURFIN CIKI book 4 part 21
ZURFIN CIKI book 4 part 21
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:19
Kwanci tashi asarar mai rai, shekara ta zagayo
lokacin bishira da tsohon ciki, Abba nason yara
don muhibba taqi dawowa tafi son umma dole
suka haqura suka bar mata. Ta haifi 'yarta
budurwa tubarkalla ranar suna ta ci sunan sahura
inda suka sa mata walida. Ummi nason yara, don
haka in tana gida to tana manne da walida, Abba
yana damuwa da rashin samun cikin ummi,
wanda ita ummin ta barma Allah komai. Shekaru
uku sun sake biyo baya, lokacin Bishira ta sake
haihuwar habiba takwara Abba yayi wa ummi.
Tsohuwa an qara tsufa, 'yan rigingimu sun qaru
tace ita Abba yama takwara amma bata son ya
duke ta irin yanda yayi wa ummi. Abba kullum
qara son ummi yake, umma ta matsa masa sai
da yayi qoqari ya sai fili rabin filoti tace kuma a
rage ciye ciyen dadin nan agina shì. Haka kuwa
ya gina flat mai daki hudu, daya ummi daya
bishira, sai nashi sannan na yara. Yayi qoqari
gurin gyaran falon ita kuma ummi ya canza mata
kayan daki don bishira an canza mata daza su
tashi agidan su. Yace tabishi bashi in ya samu
zai bata kudi amadadin kayan daya saima ummi,
tace ta yafe. Ummi dake karantar (BUSSINESS)
har ta hada (H.N.D) dinta kuma tayi bautar qasa.
Abba dai yace baza'ayi aiki ba amma ya yarda
tayi kasuwanci, Alhaji babba ne ya bata jari inda
take saro kaya zannuwa, lesuna, takalma zuwa
jakunkuna. Abin ya amsheta don har kayan aure
tana hadawa, tana yin saqo irin su kwatano da
chaina, india, pakistan ko dubai, ta hanyar wani
wan kawarta. Haka kawai ummi ta samu kanta
da zaban abinci, yawan bacci kasala da dai
sauransu, sam bata san takamaiman lokacin
al'adarta ba. Don bata wani lissafi in yazo shi
kenan in bai zo ba bata damu ba tama cire ranta
daga batun ciki. Abba ya kalli nonuwanta, baby
kwanan nan kirjinki ya cika sosai, gashi kinyi
haske ko kin canza mai ne? Tace yaya yaushe
kazama likita? Yace, ummi kin fa canza shirya
muje asibiti, ta ce ya Abba don Allah ka bar ni
nagaji dazuwa asibiti. Yace, to ni zan je inya
tambaya game da yanda ki ka canza. Cikin jin
haushi tace sai ka dawo. Ga yara atsakar gida
sun ishe mu, yace ni naki nake qawar in gani
nasan addu'ar da nike yi bazata fadi kara banza
ba, sannan ga qoqarin danake yi, shiru ta masa.
Dagaske yake yi yaje yayi wa likita bayani, yace
yadai kawo fitsarinta. Sai da suka yi tsiya da qyar
bishira ta lallasheta ta yarda ta bada fitsarinURFIN CIKI book 4 part 23
ZURFIN CIKI book 4 part 23
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:22
Sam bishira bata damu da barin mijinta da zatayi
gurin ummi ba, tunda ta jima da sanin cewa
ummi bata da wani ammafni. Wannan ne ma
yasa tasha alwashin in taje zatayi addu'a Allah
yakara toshe ummin kada ta warke sam, tunda
umma Bashir ta fada mata duk addu'ar da tayo
kafin ta dawo an karba mata. Ta kuma kara bata
shawara ta roko musu rigima suyi tayi har su
rabu, Bishira tace duk zata roko. Ko ranar da
zasu tafi sai da ta yi wa ummi habaici, kawyenta
sun shigo wato makotansu a tsakar gida take
fada musu cewa mijinta kurum take tunani. Wai
zai sha wahala kafin ta dawo. Wata cikin su tace,
wahalar me ga shi da amarya? Ta ce amaryar da
ta ke a toshe, ai bata da ammfani. Ummi duk
tana ji, takaicin duniya ya isheta sai dai ita zata
so ace bishiran take ta roko ma kanta shiriya ko
Allah zai sa ta dawo ta kama sallah. Dayar tace,
to Bishira ki roko mata sauki mana, cikin zolaya
tayi zancen, Bishira tace ba abinda zai kaini
makka in roko ma kishiya abin arziki. Ummi ta
fito ta ce Anty Bishira zai fi kyau ki roko ma
kanki shirya ko in kin dawo kya fara sallah da
tsafta. To ban san ma yanda zaki kwashe da
ibadar ba ko za a karba tunda ba yin sallah ki ke
ba. Ta taso fuuu, kawayen suka reketa suka ce
kyaleta bakin ciki ne. Abba ya fito wanka yana
cewa, Ok, za kuyi na bankwana ko? Yana da kyau
hakan. Ummi ta koma dakinta. Tun bayan tafiyar
Bishira Abba ya shiga takura musamman irin
wannan lkc na sanyi. Ya dawo da yiwa ummi 'yan
wasanni da ya daina, sai hakan yakara sa shi
damuwa don haka ya shiga lallashin ummi ta
fadawa umma....... Kuyi hkr da typing din banda
lafia sstr dita nake sawa tana maku.els / ZURFIN CIKI book 4 part 24
ZURFIN CIKI book 4 part 24
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:24
Tace ita kam ba zata iya ba ranar wata juma'a
suka tafi da nufun su fadama umma matsalarsu,
sai dai har zuwa bayan isha'i da abban yazo don
su tafi sun kssa sanar da umman komai, har
sunyi sallama abba yayi kunar bakin wake yace
umma ta fada maki matsalarta? Umma tace wa?
Yace ummi tace a'a suka koma suka zauna. Abba
kanshi na kasa Yace umma dama bata da lafiya
ne? Umma tace mike damunta kuma? Yace ummi
fada mata. Ummi ta sunne kai cikin cinya tare da
cewa shiya fada. Cikin sa'a aka kira wayarshi,
nan yayi waje ya barsu, umma tasa ummi saita
fada. Ummi ta rasa ta inda zata dauki zancen,
umma ta soma yi mata fada har tsohuwa ta leko
tambaya take lafiya ba sunyi sallama dama basu
tafi bane? Umma tace wai bata da lafiya ne,
kuma ita da abban sun kasa fadaman shi yayi
waje, ita kuma ta kunshe kai cikin cinya wai injira
ya dawo ya fadaman. Tsohuwa taja hannun
ummi zuwa dakinta, suka zauna bakin gado ta
riko hannunta. Takwara fadaman abunda ke
damunki. Ummi ta sunkuyar da kai ta kasa
magana. Tsohuwa tace inda baki fadaman ba
akwai wanda zai taimaka maki ne? Tunda naga
duk yarda mijinki yake da umman ku ya kasa
fadamata to abun mai girma ne. Ummi ta daure
tace "Gabana ne fa a toshe....." tsohuwa ta rafka
salati, sannan tace yannan badai angurya ba?
Cikin tsoro ummi Tace, ni ma ban sani ba ko
shine. Salati tsohuwa ne ta jawo hankalin umma
tazo dakin da sauri. Tsohuwa Tace ina ga
yarinyar nan angurya ne a gabanta. Umma Tace
shine don wauta daga ke har abban kukayi shiru,
dubi tsawon watanin da kuka dauka, tsohuwa
Tace yanzun yaya za'ayi umma tace ni ina nasan
yanda za'ayi, ai ni na zata yanzun babu masu irin
wannan ciwon. Rabon da inji labarinshi tun muna
yan mata. Tsohuwa Tace kai nima na jima banji
ba, amman kinsan dama wanzamai ke aikin.
Alhaji ya dawo daga sallar isha'i yaga abba tsaye
a waje, Yace a'a babana dama baku tafi ba, Abba
yace eh yanzun zamu wuce, ya biyo bayan Alhaji
suka shigo suka riski zancen dasu dasu umma
keyi. Alhaji Yace lafiya? Umma Tace yaran nan
ashe zaune suka da lalura, tame inji Alhaji, umma
Tace angurya ce ashe ta fito ma Ummi wai suka
zaune. Alhaji yace meye kuma angurya Tace wani
abu ne dake toshe mace. Nan fa suka shiga
tattauna yanda za'a shawo kan abin, tsohuwa
Tace wanzami za a kira ya yanka mata. Alhaji
yace to gobe zai kira wanzami. ZURFIN CIKI book 4 part 25
ZURFIN CIKI book 4 part 25
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:26
Abba da jin haka sai ya fito, kishi fal da
zuciyarshi, ya ce umma wanzami kuma? Ta ce
eh, aikin sune. Yace gsky umma ba za a kai ta
gurin wani wanzami ba , bagara muje asibiti ba.
Tsohuwa ta ce, kaci gdanku da asibiti komai ku
ce asibiti to wannan ba aikinsu ba ne. Abba ya
ce, Nifa gsky ba xa a kai min mata gurin wani
wanzami ba, umma asibiti zamu. Yanzu kai ya
waye wanzamai ba duka suke dafa kayan aikinsu
ba, haka kawai taje ta hadu da wata cutar? Alhaji
yayi murmushi yasan kishi ne ke damun Abba, ya
ce Babana kada ka damu, goben sai kuje asibitin,
in sun ce ba su san shi ba to sai a zo a yi na
wanzam ko ? Kunya ta kama Abba, Sam ya
manta Alhaji yana gurin ya ce to Tsohuwa ta ce
kuje in kun je ma dawowa za Ku yi dan me taurin
kan tsiya. Abba ya ce naji kin ji ummi taso muje
gda Tsohuwa ta ce oho dai, kuyi ta tafiya in dai
akayi mata aikin ai dole ka barta ta warke . Alhaji
da umma dai dariya sukayi ta yi musu, shi kuma
yayi musu sallama, ummi kam kasa magana tayi
don duk ta tsorata. Suna fita ta rike hannun Abba
gam tana cewa. Don Allah ya Abba kada kabari
wanzam yayi mini aikin nan, zan ji zafi. Ya
rungumota, Ba zan amince ba wani ya ganmin
al'aurar mata, likita ma mace zan nema ko nawa
zan kashe . Ummi ta ce, to zan ji zafi ya Abba?
Ya ce, made ki damu, in asibiti ne kila suyi miki
allurar kashe zafi amma in wanzami ne ina za ya
ga wata allura yayi mini. Ummi sarkin tsoro ranar
kwana tayi cikin damuwa, washegari kuwa tun
bakwai suna asibiti. Babban asibiti suka je sun
yanki kati likita me kula da fannin mata aka tura
su. Mata dayawa suna ta kallon su ummi
musamman yanda Abba ke nan-nan da ita,
sannan wasu sungane shi kasan cewar shi dan
jarida mai farin mini. Wasu mazan kuwa sai zuwa
suke suna gaida shi. An kirata dakin ganin likitan,
ta mike zata Shiga Abba shima ya mike, wata
Nurse ta ce, malam jira mana, ya ce ai duk Mu
biyu ne bamu da lfy, ya shige likitan namiji ne ba
yanda ya iya dole ya yi masa bayani likitan yayi
ma ummi tambayoyi in da duk ta bashi amsa/ ZURFIN CIKI book 4 part 26
ZURFIN CIKI book 4 part 26
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:27
Sannan ya bukaci ta kwanta kan gado ya saka
safar hannu, juya kai abba yayi don gaskia ranshi
ya baci, lallai ya kamata mata musulmai su dage
suyi karatun likitanci don su taimaki yan uwansu
mata. Sai da likita ya gama dubata sannan ya iya
dubansa, likita yayi wani rubutu ya mika abba
tare da cewa, an baku gado zayi mata aiki gobe
ko jibi. Abba yace likita zan iya sanin wane ciwo
ne wannan? Likita yace tsirone dake fitoma mata
dai daiku. Sam abba bai fahimta ba don haka yayi
mashi sallama. Umma ce a wurin ummi tana
shan magani kafin ranar aiki inda abba
hankalinshi ya rabu biyu rabi gurin aiki rabi garin
ummi. Don ma umma ta koreshi da so yayi ya
rika kwana, addu'a kam yana yinta. Ranar da
za'ayi aiki abba hankalinshi duk tashe. Yana
zaune bakin gadon da take kwance ita kuma tana
can ana aikin. Wayar umma ce a hannunshi yana
ta danne danne, ba don nishadi ba don kawai ya
rasa me zaiyi. Dript ya shiga yana ta bin abinda
ke ciki, mamaki ya cikashi lokacin da yaga irin
text din da ummi tasha rubuta mashi don ta tura
ma abba, sai kuma ta fasa. Tamkar cikin mafarki
abba ya rika karanta sakwanin dama ummi tana
sonshi zurfin ciki ne tayi? Ya sake bude wani
rubutu cewa, Ya Abba ina sonka, ina kaunarka
duk wani motsi na numfashina kara sonka nake,
ka tausaya mun sonka zai zama ajalina, duk
ciwon da nakeyi na sonka ne. Ko na rantse ba
zanyi kaffara ba, in kaji haushin kalamaina ka
yafeni, nasan ni ba ajinka bace, amman ka daure
kace kana sona koda bada gaske bane. Gama
karanta sakon yayi dai dai da dawowa da ummi
dakin, da sauri suka nufeta idonta biyu saidai
daga gani tasha azaba. Tayi wujiga wujiga. Abba
ya kama hannunta cikin matsanancin sonta da
tausayi. Sannu suka dinga yimata, nurse tabasu
magungunan da za'a rika bata, umma kuma ta
dauki wayarta don sanar da alhaji an gama aikin.
Abba yasa bakinshi dai dai kunnenta yace ina
sonki ummi, ina matukar sonki. Duk da tana cikin
wani hali taji kalaman nasa har a tafin kafarta.
Ta bude jajayen idonta ta dubeshi, ya sakale
hannunshi cikin tafin hannunta ya hade su. Ta
girgiza kai dai dai lokacin da nurse din ta sake
shigowa tace ga kayanta, ya amsa zaninta ne da
siket da sauransu. Tace ka barta tayi bacci kafin
ta tashi zafin gurin ya ragu, kila zuwa dare a
sallame ku. Umma tace to mungode. Nurse tace
yarinyarki nada dauriya, anyi mata allurar kashe
zafi bata kama jikinta ba amman bata yimuna ihu
ba. Likita ma ya yabata da kokarie ta, Abba ya
kalli ummi cikin tausayi. Sai gurin karfe ukku ta
farka wurin kam ya dan lafa da radadin, abba ne
yaje gida ya dafo masu abinci sannan ya nufi
wurin aikin shi. Don ranar bada wuri zashi ba.
Tunda ummi ta farka take ta kokarie tunowa shin
kalaman da taji cikin mafarki ne ko kuwa ido biyu
ne? Bakwai na dare likita ya shigo ya kara duba
ummi sannan yace suna iya tafia gida. Ya basu
maganin sha sannan yace ta rika shiga ruwan
zafi da dettol. Umma ta kira abba ta fada masu
batun sallama. Yace su jirashi yana zuwa. Ummi
tace da ummansu su alhaji pha? Tace sunxo kina
bacci harda ummanku sahura.els / ZURFIN CIKI book 4 part 28
ZURFIN CIKI book 4 part 28
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:30
Bansan lokacin dana dauka ina rigimniya da sonki
danqare a zuciyata.Ummi da ban sameki ba da
tuni bana garin Kano domin lokacin yanke
shawara nayi in nemi canjin aiki zuwa wata jihar
har yau ban daina yiwa Salisu addua ba wanda
shine mutum na farko da ya soma tsegunta min
kin zama mata gareni So, Ummi baya raina
abinda yake so da nayi zaton zubar da kima ne in
furta maki kalmar so musammam in na tuna ke
baki soma, zurfin a so bashida wani amfani don
na sha wahala.Ba zan Qara boye dimbin son da
nike maki ba Ummi ko gaban wa zan nuna kina
jina matsala? Ummi wadda ke zaton mafarki take
sai taji bakinta yana furta wayyo dadi Ya Allah
kada ka farkar dani in har bacci nike Abba yace
ciji yatsanki zakiji zafi Ummi nine Abban ki mai
sonki wanda ya reneki tun kina zanen gobe.
Hawaye suka soma zubo mata cikin muryar kuka
tace Ya Abba da gaske kana sona? Nafi zaton
tausayina yasa ka furta haka, Amma koba gaske
ba ne na gode kuma naji dadi Amma ka sani Ya
Abba ina sonka mai tsanani sai tasa kuka. Yace
ummi yi shiru, in kukan takaici ne kukan ya kare.
Nima na jima ina sonki jiya naga sakonki a wayar
umma da kike rubutawa mai dauke da nuna sonki
gareni. Sai zurfin ciki ya hanaki, don allah ummi
kada ki koma zurfin ciki a sona, ki zazzage min
duk irin sonki gareni. Ummi tace yau kam ji nake
kamar a mafarki. Sun nutsa a cikin hirar so suna
ta baiwa juna labarin halin da suke shiga a baya,
a lokacin daya ganta da wani namiji yace
hankalinsa yayi mugun tashi. Sai lokacin daya
fuskanci bashir na sonta, ita kuma Tace ta tsani
koh mace ta kira layin shi, zainab kuwa data
samu labarin ta kamar ta mutu. Tace ko bishira
bata kishi kamar yarda take kishin zainab, sunyi
nisa basu san sun kwana zance ba, sai da ummi
taji kiran sallah. Tace ya abba kaji abunda naji,
yace sallah ake kira naji, kin sani kwana zance.
Ban gaji dajin muryarki ba amarya tah. Ummi
tace gari yayi saurin wayewa kaje kayi muna
godia ga allah ta hanyar nafita, yace to matata.
Hamdala ta rikayi har bacci ya dauketa, muryar
umma taji tana cewa ummi ki tashi kiyi wanka ki
gasa jikinki. Tana zaune cikin baho wanda umma
ta zuba ruwan dimi da dettol, tsohuwa ta shigo
cikin bandakin. Ummi tace don allah tsohuwa fita,
tace don allah ja can anki a fita din, ta saka
hannu cikin ruwan wankan ummi dake gefe a
bokiti. Tace ina suwaiba? Ai karo mata ruwan
zafi, wannan ruwa yaushe zata gasa jikinta, idan
da dan tawul dauko in danna mata jikin. Ummi
tace nidai tsohuwa ki barshi don allah, sai kace
wata mai jego? Tsohuwa tace tafi can kuda baku
san darajar jikinku ba. Wannan rawar kan da mai
sunan malam keyi idan ba'a gyara kiba saiki ba
sai zance ya dawo baya, idan anyi magana ku
yan zamani kuce bamu waye ba. Alhali ku
wayewarku itace kwalliya amman jiki ba'a san a
gyara ba, umma tazo ta kara mata ruwan zafi a
cikin bokiti. Tsohuwa tace yau a sawo bagaruwa
a tafasa ruwan shigar tata da ita don tayi saurin
warkewa. Kuma ko ina zai hade, in kin koma
gidanki kin kwana biyu ki dinga hada bagaruwa
da alim kina tafasa su kina shiga.IKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 29
ZURFIN CIKI book 4 part 29
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:31
Umma Tace xa'asiyo tafita tabar su ummi
nacewa to tsohowa kije mana tace bantafiya sai
naga yanda xakiyi ganin ummi tabata lokaci nan
tsohuwa ta dauki tawul din tashiga nadar ruwa
tana dannama Ummi, Ummi tanacewa itadai
abata tayi da kanta. Tsohuwa tace gaddamace
daku ya'yan yau kinga duk macce dake rufe
jikinta tafita daban damasu tallar jiki. Ita macce
anfison a sameta ko yaushe da dumi a jikinta,
yawo babu takalmi ko a tsakargidane yana
ragewa mace dumi sbd sanyinda ke ratsa tafin
kafarta har ni'ima yana ragemata. Sannan zama
atantagaryar suminti shima yana rage mace, da a
ace zaku gane kunga masu saka hijabinnan da
safa? bakaramin wayo suke yimukuba. Inda za'a
banbance za a samu sunfiku ni'ima da kyau fata,
don haka sai kin dage Ummi dai tayi shiru, amma
aranta cewa take wannan tsohowa ko ina tasan
wannan duk bayanin? Filo aka ajewa Ummi ta
zauna tana karin kumallo, duk takosa taga
abbanta, koda ta tsinkayi sallamarsa tamkar
tamike ta taroshi. Amma dole yaje yagaida su
alhaji, tsohuwa tace aefa mu kuma bana munga
takanmu don nan zaka dinga likemana. Yace
dadin abundai nima nan gidan ubanane, da
uwata. Umma tana kicin tanamasu dariya. Tunda
ya zama idanunsu sunsarke da juna sun kasa ko
magana Ummi ce tayi karfin halin lumshe ido
sannan tabude tace sannu daxuwa. Tasowa yayi
ya tsugunna kusa da 'its, yajikin babyna?sunan
yamata dadi, naji sauki bari in kawomaka abun
karinka. yamika mata tafin hannunsa tasaka nata
yahadasu ya yasarke, murya kasa kasa yace
barshi na' amso. Ta kula abba mutum ne maison
wasa da tafin hannu. Ita kanta tanason hakan da
akwai wani sako da tafin hannu ke isarwa acikin
duniyar ma'abota so, kila wannan dalilin ne yasa
abba ke kashema tafin hannusa kudi da mayukan
da ke saka laushin hannu har ita mah ya
saimata. Koda umma ta shigo Ummi tayi kokarie
amshe hannunta amman abba yaki saki, kuma a
hakan ya karya. Umma kasa zaman dakin tayi
domin a baki abba yake ba Ummi abinci, umma
nafita taceels / ZURFIN CIKI book 4 part 30
ZURFIN CIKI book 4 part 30
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:33
Daren ranar duk suna kan kujera doguwa a dakin
umma ya bude mata laptop wai yana koya mata
kanta kwance a cinyarsa, umma ta shigo dakin
tsohuwa tace tsohuwa zaifi kyau mu sallami
yaran nan na gaji da ganin wannan aiki nasu ai
tasamu sauki. Tsohuwa tace suwaiba ina laifin ta
kwan goma ma, umma tace anya zasu kwan
goma nan? Gobe bakwai guda ta koma dakin ta,
tsohuwa tace shine nan. Abba yace Ummi kinfa
samu sauki ba zakizo mu koma gidan mu ba?
Tace su umma ne zasu maidani ai nima ya abba
inason in koma yace yau nan zan kwana in sunga
haka sun kuramu, Ummi tace ya abba kayi hnkr
kada ka kwana, shine yace kin yarda goma inxo
mutafi ko ba sanin su umma? Tasa dariya tace
taf inajin kunya bazan iya binka ba yace to kuwa
zan kwana a nan. Suna cikin haka umma ta leko
tace abba bazakaje gida ba yanxo fa sha biyu
saura, yace umma nima nan zan kwana. Ta rike
haba nan din lafia? Yace to umma nima ba gidan
mu bane? Ummi tace dama yafi umma kada yaje
wani abu ya rudashi, umma tace a'a abba tashi
ka tafi insha allah gobe Ummi zata koma yayi
murmushi tare da cewa nagode umma.nan dai ya
tattara yanashi yanashi ya tafi gida cike da
kewar matarshi, itama Ummi lamo tayi a gado.
Bayan umma ta gama yimata fada ta bari ta
warke taki ko, sai cewa tayi umma ni fa na
warke. Umma ta kalli Ummi cike da mamaki tace
yaran yazo saidai a barsu. Shiyasa akace idan
macce ta isa aure ayi mata a huta. Ita kam Ummi
tana ganin a barta tabi mijinta ta faranta mashi
shine abinda yafi dacewa don yanxu ba inda ya
kai mata dakinta dadi bacci. Duk da kashedin da
tsohuwa tasa abba dakinta tayi mashi na cewa
ya bar Ummi sai ta kara sati kafin yace zai
kulata da sunan auratayya, bai sa abba jin zai iya
ba. Don haka koda ta fada mashi cewa yayi kadai
da huruminki da wanda ba naki ba duk sai kin
shiga? To nidai ki lafa man haka. Ya fice a dakin.
Ita kuma tana ta fadanta tana cewa "Na shiga din
dan neman yaro, da kyar ya barta ta kara kwana
biyu ya afka mata don shi hkr sa ya kare, ta
nuna mashi ita fa tsoro take ji kada ta wahala, ya
lallasheta yace ba wani wahala. Ummi tana son
faranta ran mijinta. Don haka ta jure duk da
yarda yazo mata ba sauki, sai dai tasha albarka
kuma ta kara samun wani matsayi na
musammam a gunsa. Cikin satin ta zama yar
lelenshin kafin sati biyu ta hardace duk wani
darasi da abba yake koya mata, abba jinsa yake
kamar wannan lokacin ne ya fara rayuwar
angoncinsa. Sam ya manta yana da wata mata
uwa duniya saida Aunty ta kirashi tace lafia baya
kiran matarsa sai ga abba da girman shi ya girba
karya. Wai ya kira ya kasa samunsu Aunty ta
yanda tunda farkon tafiyarsu yana kiransu sun
gaisa da bishira tana tmbyrshi ina hibbarta? Sai
lokacin ya tuna kwana biyu bai ganta don tana
gidansu umman bashir, amman sai yace tana
lafia in yaje zai kirata taji gwarancin yar tata.
La'asar sur suka jero ita da abba don su dan
zaga kurum. Sun shigo gidan ahmad da muktar
duk basu rabu ba saida sukaji sun saba da ummi.
Don ita haka take yana da wuya kayi zaman awa
guda da ita bakaji ta kwanta maka a rai ba. Abba
yaji dadi yarda Ummi ta nuna kauna ga matan
abokanin nasa, yasan bada jimawa ba matansu
zasu zama kawaye kamar yarda yaso da bishira
amman taki. Daga can suka nufi layin su gidan
su umman bashir Ummi tace su fara shiga su
dauki muhibba abba yace bazata yarda dake ba.
Ummi tace zata yarda muje a ran abba tsoro
yake gada umman bashir ta gwasaleta Ummi, sun
sameta tana shara da sauri Ummi ta amsa ta
soma sharewa hakan ya faranta ran abba sai dai
da ya kalli umman bashir yaga tana hararar
Ummi, saida ta gama taxo ta zauna suka gaisa
abba na rike da hibba tayi kaca kaca da kunu
gashi duk ya dunkule dama ko lokacin da bishira
tana nan haka zakaga yar duk kazanta. Ummi ta
bude post dinta ta cire dari biyu guda biyu ta
mikawa umman bashir gashi umma kin sai goro
saida ta tabe baki ta amsa babu ko godia, sai dai
abba cikin jin dadi yace angode, da hibba taki
binsu Ummi tace kamal xo ka siyo wa hibba
alawa, kinga baba kamal baya nan xo muje in
sayo maki. Cikin sa'a sai taxo zasu fita sai ga
bashir dauke kai yayi tare da jan tsaki daya shiga
gidan sai ya hau umma da fada Wai ta daina
barin Ummi da wannan abba suna zuwa in ba
haka ba zasu kawo mata wani asiri. Umman
bashir tace suta zuwa ma indan ta nine mi jiya
tayi bare yau, ka gansu dari hudu yanxu ta bani
don haka bazan hana zuwa ba amma fa ina nan
yarda nake bazan canza ba, suna shiga gidan su
umma kicin ta wuce ruwan zafi ta zubu ta cude
muhibba tas, ta wanke mata kai ta chajeshi ta
shafeta da mai nan ma basu jima ba suka nufi
gida zanen umma ta ansa ta goye muhibba, shine
ya bude dakin bishira duk kayan yarinyar sun rine
da datti, Ummi dai ta zazzaba yace .ba maidata
za'ayi ba, Ummi tace ta dan kwana biyu mana.
Yace tana fitsari fa. Ummi tace kasawo muna
pampers Yace shikenan duk da ya nuna bayaso
yarinyar ta zauna gurinsu amman yaji dadi sai
lokacin bacci daya shigo ya shigo da pampers din
ta saka mata Sannan ta kwantar da ita can gefe
ta azama mata pillo guda haba guda baya, su
kuma suka kwanta a nasu makwancin suka
cigaba da soyewa. novels / ZURFIN CIKI book 4 part 31
ZURFIN CIKI book 4 part 31
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:36
Ummi tana son yara don haka hibba ta dinga
samun gata, satinta guda umman bashir ta dinga
jaraba sai an dawo da ita. Wai kwadayi ne don in
bishira tadawo ta bata tsaraba, amma koda ta
tafi da hibban yarinyar sai taqi sai kuka har dasu
amai. Dole aka dawo da ita, don alhaji karami
cewa yayi atattara mata kayanta duka inyasake
samun an maido da ita sai ya saba ma umman
bashir. Hakan da babbar sallah abba yakashe
musu kudi ita da hibba, sai dai duk abinda yasai
ma ummi to ya aje ma bishira nata. Ita kam tana
can duk addu'arta akan ummi ne, kafin ta dawo
ummi tafita, don haka data dawo da kwarin
gwuiwarta ce wa bazata samu ummi agidan ba.
La'asar sakaliya, direban gidansu ya iso da ita
gidan kamar yanda mahaifinsu ya umarce shi
cewa in ya dauko su kada yaso dasunan, ya dire
kowa agidanta. Kasancewar unguwa uku suka
soma zuwa sai anty ta taya bishira diban kaya
su shiga. Daidai kofar dakin bishiran abba na
kwance rigingine, 'yar T-shirt ajikinshi fara kar.
Dawandon jeans gajere iyaka gwuiwa. Ummi
kuma dogon wando ne irin mai kama jikin nan
dariga mai kamar singileti kanta yasha kana nan
kitso, tayi filo da kirjinshi yana bata labarin wata
mota da yake son yabada tashi yayi ciko. Ita
kuma tana ce masa ya dai je ya shawarci umma,
muhibba kuwa tana ta faman wasa da sabbin
kayan wasanta da ummi tasai mata. Ita ma cikin
'yar shimi mai kyau, kanta kuwa ummi tayi mata
kitson (3 in 1). Sororo bishira ta tsaya tana
kallonsu, sam bata tsammaci a irin addu'ar
datayi zata dawo ta samu ummi agidan ba. Basu
ganta ba saida anty tayi sallama tare da cewa, ya
naga kin tsaya? da sauri suka waiwayo duk suka
mike. Gaban ummi yayi wata muguwar faduwa,
amma duk dahaka cikin fara'a ta nufe su, bishira
ta hade rai matuqa sannan taqi ko kallon ummi
ta nufi 'yarta. Anty kam cikin fara'a suka gaisa da
ummi harta zage jakarta dake kafadarta tabawa
ummi wani dan agogo mai kyau. Nan dai ummi
tayi ta godiya shima abba ya mata godiya. Abban
ne ya shigar mata da kayan daki, ummi tana
cewa anty kin mana dawowar bazata, dakin fada
da an share miki dakin. Nan ma bata tanka ba,
ummi dai data gaji dayi mata sannu bata amsa
ba sai kurum ta nufi dakinta, zuciyarta babu dadi,
tasan yanzun ya Abba zai raba jin da yake da ita
zuwa su biyu. Bishira tayi kyam tana ta qamshi
don anty baza su barta tazauna masu da qazanta
ba, ga haqorin makka an sako ana ta qwambo.
Ranar dakinta Abba yakwana, yanda bata ga
wata rawar jiki daga gare shi ba tayi zargin ummi
tasamu lafiya. Hakan ya qara dagula mata lissafi,
tayi rabon tsarabarta daga kawayenta sai
maqota, don ko umman bashir daga zam-zam
bata qara mata komai ba. Dama tana cike da
haushin umman data bari ummi ta daukar mata
'ya gashi nan muhibba ta liqe ma ummi. Hakan
ya shaqar da umman bashir har tace amaida
mata zam-zam dinta ita bata sha. Wato don taje
makka shine zato zo ta canza hali? Ita kuma
bishira ta amsa tare da cewa, ai ba ita ta aike ni
makkan bada har sai tazabi abinda zan bata.
Ummi ko zam zam din ba abata ba, kuma ko
ajikinta. Abba kam shita kawo masa dogayen
riguna da T-shirt masu kyau, amma su anty ne
suka matsa mata sai ta saya. Ranar daya dawo
daga dakin bishira ummi tana fashin sallah gashi
yanuna yana dalarura alokacin. Sai tace ta yafe
masa yau dagobe yaje gurin anty bishira, yace
A'a tace ba haramun bane nina amince, yace
nasani. Shiba yason sai yatafi tafara damuwa ko
tazo tana jin haushinsa, tace ba komai saida
yatafin kuwa har kuka tayi don kishi. Amma
tabawa zuciyarta hakuri tasan wata rana wannan
jarumtar datayi zata zame mata alkhairi. Ita ko
bishira koda yazo mata sam bata damu ta
bincika ba, tunda taga ba girkinta ba, saima ta
hau murna yayo satar kwana ya bata musamman
dataga dayayi wanka yakoma dakin ummi, haka
washegari. Don haka sai tashiga daga hanci har
da 'yan habaice habaice, kafin tadawo tun da
dama da namiji dan uwansa yake kwana. Tana
nufin ummi bata ba tayi masa amfanin komai
wannan yasa ummi ta daura aniyar cusa mata
takaici, aranta tace tunda cinikinki labe nikuma
zansa miki hawan jini. Kamal yazo daukar abincin
da ummi ta saba sawa yau har da kunun gyada
tayi. Bishira ta kalle shi, wai kai wannan abincin
na waye kullum kake zuwa dauka? Yace na
ummarmu ne. Ta taba baki, ummar nan taku
kwadayinta yayi yawa, ko kuwa itama asirin ya
kamata ne? Kamal kuwa yaje yafada sai ga
umman bashir agidan suna zage zage da bishira,
tana ce ma bishira dadin abin gidan dana nazo
kwadayin ba gidan ubanki ba. Marowaciyar bnza
ai dama ina da cikinki, lokacin da Abba yasai
maku TV, yace ki bani naki sai ki kace gara kiyar.
Bishira tace, Eh na hana TV aiba wani shegen ya
sai minba, ubana yasai min, kuma nace mai
kwadayin yarinyar daki kace uwarta mai asiri,
menene na amsar abincinta kici banda kwadayi?
Shiyasa kika bata 'yata ashe don asami abinci
ne, umman tasa kuka ni ke ke zagi? Yau ko abba
zai zo gidan nan zai zaba ko ni ko ke. Ummi dai
tana daki tana jinsu. (aranta tace dadi na da
gobe saurin zuwa). Bishira tace dama ya darajaki
ne shine za kice haka, yazo din nace mai kwadayi
harda rainawa na baki zam zam butulu duk
abinda na miki kin manta kece kika aikeni
makkan? Umman tace, zuwa makkan naki dashi
gara babu, don nasan da kyar ne in za akarbi
wannan aikin nani ke da bakya sallah arniyar
banza qazama. Ummi harda riqe ciki don dariya,
haka dai suka yi tayi wajuna gori har dai 'yan
kallon da suka taru suka soma bda haquri,
umman bashir tayi gida cikin kuka. Tagayawa
'ya'yanta komai su bashir dasunce sai sunje sun
zaneta umman bashir din tace barta ku barta
kawai bari abban yadawo. Da dare ta ritsa shi
agidan yasha mamakin wai yau mahaifiyarshi da
bishira ne suke fada yace hakane dama duk
zamantakewar da ba'a kafata don Allha ba wata
rana sai ta rushe. Nan yayi tawa bishira fada da
cewa uwarshi sa'arta ce dazata tsaya ta dinga
gaya mata magana? Nan fa aka sake kacamewa
har abba. Yakai ga kwasa wa bishira mari,
sakamakon irin rashin kunyar data rike qugu take
tsulawa umman bashir din. Ummi ganin abin yana
tsawo ta fita taja umman bashir tana bata haquri
ta zaci zata hantare ta amma sai taji tana cewa
ba komai ummi sakayya ce tunda na nuna ina
sonta dole tamin haka. Abba yace ummi tasa
mayafi taraka umma gida, hakan ya qara qona
ran bishira gashi yanda taga Abba ya bata rai zai
iya yin komai, dole ta koma daki tana cizon yatsa
tare da tunanin mafita. Ummi kuwa ahanya sai
lallashin umman take tare dayi mata alqawarin
cewa duk abinda take so ta tambayeta zata mata
shi tarakata har gida sannan tadawo. Sabon kuka
umman bashir tazauna tanayi, takaicinta yanda
bishira ta zage ta taci mata mutunci agaban
ummi, tashare ido tare dayin ajiyar zuciya a fili
tace dani take magana. Ynzun ummi tasan kishi
fiye da baya, don ta hau turbar ma'aurata kuma
tasan muhimmancin abinda ake yiwa kishi, don
haka zatayi komai na jan hankali don ganin taja
mijinta gareta. Kuma inta lura cewa bishira ta
maqale mata aqofar daki sai tayi ta jan abba da
wasanni, don ta quntata ma me labe. Amma
hakan baisa ta daina ba, don haka ta daura
aniyai saita mata abinda zata tona kanta ha abba
yasani. Duk jumma'a abba yana dawowa gida
musamman in ranar girkin ummi ne don cin
abinci na musamman. Jumma'a biyu kenan bata
fado kanta ba sai wannan, don haka tun alhamis
taje ta yarfo kitsonta, ta biyo ta gidan su gurin
tsohuwa tazo. Don haka suna gaisawa da umma
tace gurin tsohuwa nazo. Suka shige daki tace da
tsohuwa nazo ne indan samu dan wani sirrin.
Tsohuwa tace, name ummi? Ta ce na gyaran jiki
mana. Fati tace min kwanaki kin fada mata wasu
abubuwa. Tsohuwa ta ce, ja'ira, kinga uwar bari?
Dama nace zaki same ni ina kyakkyawan zamana,
bada ina fada miki kina sharewa ba? Ummi tace
haba tsohuwa banaso aji mu yanzun dai ki bani
shawara sannan ki fada min abinda zanyi inja
hankalin mijina. Ta ce, toda farko ki dinga kula da
jikinki ta hanyar rufe shi ruf, kada kibar kofar
iska. Banda tafiya ba takalmi, iska tana shiga
tanan kuma mace narage ni'ima banda zama ba
dankwali inso samu ne hatta tsarki ki daina yi da
ruwan sanyi, ki dinga yida ruwan dumi. Sannan ki
amshi bagaruwa gurin ummarki ki dinga shiga
inkin tafasa da alif dakuma saiwar mata, sannan
inkinyi al'ada kin gama kinyi wanka toki dinga
matsa farin miski a ehem dinki. Sannan ki samu
saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,
mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari
dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi
biyu safe da yamma. Sannan ki aya garinta,
kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,
sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar
ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai
ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,
citta, lemun tsami, ki markada su kisha. In anan
maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum
daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta
musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban
da dukkan sauran mata. Ki hada da biyayya
tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi. Ummi
tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin
nan? Tace, bari zanba matar ado dake yawan
zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu. Amma
su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya
siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin
ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.
Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje
gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi
tasan duk wadannan hadin matan? Amma data
tuna cewa 'yar katsina ce sai tace ba mamaki.
Tun ranar alhamis din ta soma aiwatar da
darussan da ta debo daga tsohuwa, safiyar
jumma'a ranar zai bar dakin bishira. Ya fito tana
sharar tsakar gida ta gaidashi, ya amsa da fara'a,
tare dawani kallo mai fassarar in ba keba. Cikin
muryar data adana don shi kadai tace, ya abba
ina son in je ayi min zanen fulawa. Yace jiya kin
fita yau kam a'a. amma ki aika akira mai zanen
tazo ta miki. Ta marairaice, towa zan aika yaya
abba? Yace aike ni, ina ne gidan? Tace layin su
umma ne yace to za'azo ai miki. Bishira tafito
daga daki tazabga ma ummi harara, Tare dacewa
kisisina. Abba yakalleta, kema sai tayi miki. Tace
bana bukata, aikin banza, shikam yafice. Ummi
kuwa tace gaba da aikinta, ita ko sai tasa kujera
tazauna tana sakin zantuka, eh don kwalliyar
tabanzanta tunda ba a iya biyawa miji bukata.
Allah dai yasa ya fada min komai, to ni me zai
dame ni don 'yar aiki kawai na dauki yarinya.
Tashare min gida, tayi wa mijina abinci, daga nan
fa? Saita saki shewa, ummi ta ce aranta yau zan
bambance miki. Birabiskon shinkafa tayi da miya,
ta wadata birabiskon da kayan lambu, miyar ta
dauki nama da bushasshen kifi. Sannan ta hada
musu kunun aya yaji dabino da madara, ta
aikawa ummanta lokacin da kamal yazo daukar
na ummarsu. Tasheka wanka taci doguwar rigar
shadda koriya mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau
ne daurin aurensu. Ga fulawar da yaje ya biya
akazo aka zana mata. Tanajin rigimar muhibba
tafito tazuba mata adan kwano tazaunar da ita
akofar falon mamanta.bishira tafito kicin baki
tasaki tana kallon ummi da tazo wucewa harda
bangazar ummi, nan ko kamshi ya bude ta na
turarukan da ummi ta fesa. Abba yana yin
sallama ummi tafito da sauri, oyoyo yayana,
bishira tana daga kicin dinta tana kallon su.
Ummi ta rungume shi, sannu dazuwa sahibina.
Ta amshi ledar hannunshi dajakar, yace yauwa
sannu babyna tace inazan kai ledar? Yace akwai
ta bishira aciki ki ciro. Ta mika mishi ledar ta
wuce dajakar dakinta. Ya mika wa bishira lemo
da abarba da yayo musu tsaraba sannan ya wuce
danasu, awulakance ta aje. Yana shiga ummi
tadan karo kofar yanda bishiran zata iya lekensu
sosai ta gefen kofan. Ta cire masa hula ta aje
akan madubi sannan ta kunna fanka. Ta shirya
masa abinci, yauni zan baka har ka qoshi. Haka
suka yita baiwa juna abaki har suka qoshi.
Yakamo hannunta mai qunshi yana ta sumbata,
wai kamar kada su goge. Kumatun shi ta shafa
nima yau kamin kyau, koda yake dama kai me
kyaune, ina sonka ya abba sosai. Cikin jin dadi
ya mannota a jikinshi, nima ina sonki, ina manta
kowa da komai in muna tare, tace ina tsoron kada
wata rana ka juya min baya. Ya saqalo
hunnuwansa cikin nata ina fata in mutu kafin
lokacin. Ummi tasomayi masa wasu irin darussa
wadanda tasan yana saurin tada sha'awarshi
nanda nan kuwa tasa shi fita hayyacinsa yakama
surutai. Ummi ta tabbata bishira tana wurin ta
labe, don haka tai murmushi ta bishi suka tafi
duniyar ma'aurata. Bishira tamkar tayi hauka sai
kawai ta fado dakin tana fadin, maciya amana,
har yanzun ba afita daga lokacin girkina ba
munafiki. Abba ya tashi sannan yaja riga yasaka,
ok dama kina labewa ne kiji sirrinmu? Da taga ya
sauko da zafin rai saita gudu dakinta. Yabita
yamata tatas, kuma ya fada mata cewa tazo ta
shiga dakin ta zauna ba labe ba, yanzun zai
komane yaci gaba daga inda ya tsaya. Tayi ta
kuka gashi ba damar zuwa gurin umman bashir
dole ta tafi gidansu. Shi kam abba shareta ya yi
kosu umma bai fadawa ba. Sabuwar soyayya ma
ya balle agidan, su ci abinci tare, wanka tare, su
fita yawonsu a qafa ko amota. In yana gurin aiki
bini- bini ya kira waya, ita kuma ko yaushe cikin
kirkirar girki da kwalliya tare da dadadan kalaman
dazata fada masa take. Duk lokacin datayi masa
zancen bishira sai ya ce, don Allah ta bar ta ta
huta, ummanshi kuwa 'yar bin qwaqqwafi sai da
tabi ta gano bishira bata nan. Don haka koda ya
shiga gaisheta sai tace kada ya yarda yaje yama
bata takardarta. Ita ko tana can uwarta tace ma
mahaifinta abba sakinta yayi, shi kuma yace to
sai tazauna tunda zaman gidan take so. Amma
su sani daga abinci sai ruwan gidanshi ya amince
tayi amfani dasu sai ko gurin kwana, amma bnda
wannan ko makilin dinshi ta taba bai yafe mata
ba, wannan hukunci yayi musu tsauri. Ko wata
bata rufa ba taji gidan ya isheta don hajiya zainu
taso maidata makaranta amma yace tagama
boko. Bishira na zaune ta zuba tagumi hajiya
zainu ta shigo dakiki tace tagumin menene kuma?
Tace, su sumayyah ne wai nace suyi ma muhibba
wanka sukace Allah yakiyaye. Wai tunda nazo
dakinsu ya lalace da kazanta, hajiya zainu tace
aiba karya suka yiba, don haka ma maida
yarinyar nan za ayi ke kuma ki koma gidan
antynku ko ki tafi abuja gidan aisha. Tace
baxanje gidan aisha ba, don itama bama shiri,
gara gidan antyn amma gsky ni abarmin 'yata
kuma fakinsan bai sakeni ba. Tace, inda ubanki
yasan ba saki bne da tuni bai kora kiba? Don
haka mubarshi haka amma batun 'ya nice zan
maidata. Ranar da ummi takira ummansu tafada
mata cewa bishirafa tuntuni tayi yaji amma Abba
yaqi zuwa, umma ta kira shi tace inya dawo gurin
aiki tana son ganinshi. To kafin yadawo ma saiga
hajiya zainu da direba tazo gidan su umma tadire
musu 'yar, sannan tashiga gidan umman bashir
tace, in kin haifi danki na halas ne ba shege ba to
kisa shi ya aiko wa 'yata saki. Umman tace zoko
kiga dan halas ne in yaso kuje ku nemi arne mara
sallah dan uwanta kazami kubashi. Nan fa zage-
zage ya tashi har su umma dasauran makota
suka shigo. Dakyar aka tura hajiya ta tafi, tace
kuma saita kira 'yan sanda anzo antafi da umman
bashir. Alhji qarami ma cewa yayi maza abba
Abba yarubuta takarda ya aika ma bishira.ZURFIN CIKI book 4 part 32
ZURFIN CIKI book 4 part 32
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:37
Shiko alhji babba da umma suka ce a'a abari
qura ta lafa sannan aje. Koda aka kwana 2 abba
kin bin alhaji yayi sai wani abokinshi alhaji
yasamu suka tafi tare. Mahaifin bishira yaji
mamaki cewa ba sakinta abba yayi ba. Kuma bai
san sun maida 'ya ba, tadai ce mishi kunzo kun
amshi 'yarku, to yanzun tunda haka ne kunga
kenan bishira da uwarta basa son takoma gidan
mijinta ko? Su alhaji suka ce eh, yace to ku sa
shi ya rubuto takardarta ku kawo min, su alhaji
sukace ba za'ayi haka ba. Yace, to kuje ku barta
zata gane gidan ubanta bananne yadace tazauna
ba. Sukai godiya suka tafi. Harta koma gidan
anty farida mahaifinsu yace tadawo nan gidanshi
badashi take takama ba? Wato ta kashe auranta
zata je ta kashe na yarta dole ta dawo, tsohuwar
dake musu aiki yace ta koma gida tahuta amma
duk wata tazo ta amshi albashinta. Sannan yace
bishira itace zata dinga wannan aikin duka ita
kadai, lamarin yayi wa bishira tsauri da yawa,
gashi ba fita duk ta rame ta lalace ga tunanin
'yarta. Muhibba kuwa tana gurin umma, ummi
ma takan daukota sannan ummi tasamu nasarar
rufe bakin umman bashir, ta hanyar yi mata
kyautuka ko me sukace sai ta aika mata. Tasa
Abba ya canja mata gado don nata ya lallace,
sannan da fati ta haihu tasa Abba ya sai mata
garar abinci, ita kuma tasa zani da rigunan yara.
Nan fa sai ga sahura babu ko kunya tana shima
ummi albarka, ko bashir ne yakawo gulmarsu
ummi sai tace ai ita bata yo halin uwarta ba.
Tafi-tafi ma in ya kawo sai tace ai su umma da
ummi sun gane kuransu. Haba sahura kodai ki
gane kuranki? Abba yasoma damun ummi da
batun ciki, wai shifa yana tsoro kada su gaji su
umma, ummi tace su dai yi addu'a sunje asibiti
ba wata matsala, likita yace in rabonsu yazo zasu
haihu. Da kyar ummi ta shawo kan Abba ya
amince ta zana (JAMB) don ci gaba da karatu,
sannan ta shiga islamiya. Abba yayi kyau yayi
kiba ya kara gogewa, haka nan ummi duk wanda
yaganta saita birge shi, daka ganta kaga wayayya
wadda mijinta yasan da ita. Taci nasarar samun
(POLY) saboda bata samu abinda take so don
zuwa (UNIVERSITY) ba, sai dai ba tasha dokoki
kafin ta fara zuwa. Bayason kawaye baya son
abokai, irin wanda wasu matan keyi sannan
yadinka mata manyan hijabai, kuma banda hawa
acaba, inya samu sarari zai dinga zuwa da kansa
yana daukarta. Sai kuma gargadi na karshe kuma
da babbar murya, in har ya daina samun kular
datake bashi ta kowane fanni wai saboda karatu,
to kuwa za adaina karatun gaba daya. Tace,
insha Allah sai abinda yai gaba. Ya canja mota,
umma tayi ta fada wai tafi son yasai fili yayi dan
gidanshi irin na zamani yace za'azo gurin
ahankali kada ki damu umma. Bishira ta sulale ta
tafi na'ibawa gidan anty da kukanta wiwi don
Allah ta taimaka mata taba Abba hakuri ya maida
ta, wlh tagane kuskurenta. Anty tace, nifa bazan
iya kiran Abba ba don kin riga kin bmu kunya, sai
dai in ke ce zaki kira shi ga waya can. Ta dauko
ta kira, shikuma ganin kiran anty sai yayi parking
yadauko ummi daga makaranta, ya daga sai yaji
muryar bishira. Cikin kuka tana cewa, don Allah
abba nice, kayi hakuri indawo dakina, wallh zan
canza, yace ok baki riga kin canza din ba, to bari
inkin canza din sai muyi magana. Yakashe haka
tayi ta kuka tagama anty tabata wasu kayan
sawanta sannan ta tafi. In lokacin labarai yayi
haka take zuwa ta tasa TV tayi ta kallonshi tana
kuka, kullum kara sonshi take gashi yayi kyau
idanunshi sun qara haske. Wata ranar jumma'a
wuraran karfe sha daya ta saci jiki tanufi gurin
aikin Abba, yana fitowa dakin daukar labarai
akace wata tana nemanshi. Baiji wani mamaki ba
don mata kanzo neman shi wasu suce suna
sonshi wasu suce ganinshi kurum zasuyi don
yana birge su. Yana zuwa sai yaga bishira, nan
take ya daure fuska tamkar bai taba dariya ba,
duk da cewa acan kasan zuciyarshi yatausaya
mata. Ta tsugunna gwuiwa 2 tana rokonsa, yace
ke tashi kada ki janyo min mutane, jeki zanzo.
Koda ta tafi cikin murna shi ko harkokinsa
yakama. Shiru-shiru tana saka rai bashi ba
alamarsa. Nan kuma tashiga daukar waya
kannanta tana kiranshi, harma yadaina dagawa.
Wataran taje tasamu ahmad tana kuka, ahmad
yace taje zai ganshi. Rannan kuwa har gida
ahmad yiyi sallama da abba yashiga rokon Abba
ya maidota. Abba yace taje taroqi mahaifiyarsa
dasu umma insun yarda shikenan. Har gida
ahmad yaje ya fada mata, bata yi sanyi ba tanufi
gurin umman bashir. Umman tana zaune da
'ya'yanta suna shan farfesun kifin da ummi ta
aiko musu dashi, tana ganin bishira ta hade rai.
Tace, lapiya? Bishira tace lpy lau umma zuwa
nayi in roqi gafararki. Tace nime kika min? Tace
don Allah dai ki yafe ni, ina son indawo dakina
Abba yace sai kin hakura, tace oho, yanzun kin
yarda ina da kima agurinsa? To bari kiji bazaki
dawo ba, mai baqar rowa kince nimai kwadayi ke
kuma mai rowa ko? To kin gani wannan ummi ce
ta dafo mana ta nuna mata kular kifi, sanda
kinanan bana cin komai bansan dana yana samu
ko baya samu ba. Yanzun abin arziki iri-iri
kidawo ki toshemana kofar samu? Tace, wlh
bazan toshe ba, umman bashir tace dukda haka
dai bazaki dawo ba. Tayi takuka sannan tafita,
har zata wuce gidan su ummanshi sai ta tuna
kada suyi mata dariya sai tace baridai ta shiga.
Kyakkyawar karba umma tayi mata suka gaisa,
tazauna umma ta kawo mata ruwa ta amsa
tasha. Muhibba tana ta tsalle tsallenta kan kujera
zuwa jikin umma, umma tace ji hibba ki gaida
mamanki, ga mamakin bishira sai yarinyar ta
kalleta tace. Umma niba wannan bace ba
momina, momina sun tafi da babana zaya kaita
makaranta. Umma tace, wannan ma ummarki ce
yarinyar taruga dakin tsohuwa tana cewa, ita ba
ummarta bace. Bishira ta bita dakallo, yarinyar
tayi bulbul gata cikin shiga mai kyau da tsafta
kanta yaji kitso da 'yan duwatsu. Saita soma
kuka tana fadin mahaifiyata ta cuce ni, umma
tace a'a kece kika cuci kanki, inbaki dauki
damuwarki kin kai mata ba yaushe zatasan anyi?
To ynzun dai dubi 'yarki tana gudunki sbd bata
sanki ba, ina amfanin wannan? Tsohuwa tace
kukan wanikeji ta shigo tana kallon bishira cikin
mamaki tace. 'yar nan kece haka? Ciwo kikayi ko
ko duniya ce ta juya miki baya? Kai jama'a dubi
yanda kika kare kikayi bikinkirin. Ita da tadukar
dakai tare da cewa bnyi ciwo ba nidai nazo ku
yafe ni, sannan ku roqa min abba ya yafe min in
dawo dakina. Yace, bazan dawo ba har sai kun
yafe min, amma naje gurin umman bashir ta kore
ni tace bazata bari in dawo ba. Kuma gidanmu
wuya nake sha, kusan rabin aikin gidan nikeyi ga
qannaina duk sun raina ni. Umma tace, yi shiru
share hawayenki bari zaki koma. Tsohuwa tace,
ke dai kin cika sa kai a uku suwaiba, gashi abin
kirki bai karbe kiba. Kina yi ana zaginki ana zagin
'yarki, bishira ta ce wlh duk na daina, yanzu na
gane kune masu sona, umma tace ba komai.
Tadaga waya ta kira alhaji ta fada masa komai
yace to yana zuwa donshi ya qosa asulhunta
yarinyar ta koma dakinta saboda darajar
tsohonta. Yana zuwa yaji komai nan ya daga
waya yakira Abba, yace yana zuwa yana hanya
ne yace to ya same su gida. Abba yana shigowa
ganin bishira yahade rai ya zauna nan dai alhaji
ya hada su yayi musu fada da nasiha, sannan
yace baya son abba yace komai komai kuma ko
sun koma gida banda tashin tashina. Bishira tayi
ta godiya alhaji babba yace su tashi ashiga gurin
umman bashir din tana ganinsu tahau cewa alhaji
dakanka? Maimakon ace in zo? Umma tace, a'a
keda zamu zo baki hakuri ai mu ya dace mu
shigo. Nai dai alhaji yayi bata hakuri tace taci
albarkacinta na hakura, amma da sharadi inta
sake maimaita halin da tayi abaya ko taje ta
takurawa ummi tofa saita tabar gidan. Bishira
cikin kuka tace ta daina insha Allahu, nan itama
umman bashir din tace dasu umma su yafe mata
sharrin shaidan ne da qaryar barayin imani wato
bokaye da 'yan tsibbu suka ce ba komai. Nan
alhaji yace da abba yakai bishira gida, ba don son
ranshi ba yadauke tazuwa gida, sam bata damu
da daure fuskarshi ba, dadi da murna fal ranta.
Yana sauke tazai wuce tace, don Allah ka yafe
min sannan ka gaida min ummi, yace zataji. Tace
to yaushe zan dawo? Yace, duk lokacin dasu
alhaji suka zo gurin dadynku. Nan yatafi, ita
kuma ta shiga gida, hajiya zainu ta tsareta wai
sai ta fadi inda taje, tunda ta kira anty tace, bata
can. Bishira tace naje ba mijina da surukaina
hakuri ne, hajiya zainu tace ni dazai maida ki ai
sai nafi kowa murna. Na gaji da zamanki da
qazantarki, tunda babanku yaqi ki koma
makaranta yakashe miki kudi ki goge ko kya
samu mai kudin dazai aure ki, to gara kin koma
can kin qarata. Abba kam shi tunaninshi ta ina
zai soma sanar da ummi dawowar bishira? Don
baya son ko kusa hankalinta yatashi, baya son
wani abu yayi musu katsalandan a cikin
daddadan zamansu, don haka ya share bai fada
mata ba. Da dare alhaji da umma suka je, an
sasanta sannan suka taho da alkawarin cewa
gobe zata dawo dakinta. Washegari umma ta kira
Abba tace ya share ma bishira daki yau zata
dawo, yace umma nifa gsky dabata hankalina yafi
kwanciya. Sannan ina ta tunanin yanda zan
tunkari ummi da wannan zancen, umma ta riqe
baki tare da rafka salati, yace ynzun tsoron
ummin ka koma ne? Yace, a'a umma kin gata
sakankance ynzun hankalinta yakwanta sai kuma
taji nazo mata da zance dawowar bishira? Tace,
shi kenan nina fada mata. Awaya ta kira ummi
tafada mata cewa bishira zata dawo, duk datasan
cewa matar mijinta ce dama, amma sai da
gabanta yafadi. Umma taja mata kunne da cewa
kada taji kada tagani, abba ranar sai kusan sha
biyu zaije gurin aiki. Don haka yace kannanshi
suje su soma fito da kayan kafin yazo sunzo sun
fada ma ummi, ita ce ta bude musu dakunan don
abba ya canza makulli bayan tafiyar bishira. Abba
ya shigo tana zaune kan kujera sai tunani take yi
na irin zaman dazasu yi in bishira tadawo.
Yazauna tare dariko hannunta, tunanin me ki ke
yi? Takalle shi, halin rayuwa nake tunani, yace
yanzun umma ta kira ni jiya sun je gidan su
bishira wai yau zata dawo. Ummi ta taba baki,
Allah yakawo ta lpy. Ya ce ni ban soba gsky. Sbd
ke ummi tadafa kirji, sbd ni? Ni ya abba, kada
kasa duniya ta zage ni, Tare fa nasameku? Yace
to ni dai kada kiga kamar da son raina, tace don
Allah ya Abba kabar zancen nan. Kaje kagyar
mata dakunanta don su kamal bazasu iya ba,
yanufi gurinsu ganin kamar ya damu yasa itama
taje tasa musu hannu don dai ya saki ranshi, sun
gyara tsaf ummi ta goge sannan ta rufe dakin.
Har magriba bishira bata ji an ce za'a maida
taba, sai ta dauki wayar kanwarta ta kira shi wai
yazo don Allah yadauketa. Tsakanin mata da miji
sai Allah, nan ya tausaya mata yace zaizo, kafin
ya isa sai daya sai mata waya irin dai ta hannun
ummi. Har cikin gidan ya shiga suka gaisa da
babanta, yayi murna sosai yayi tawa Abba
godiya, tare da ba shi hakuri yace yasan yanda ta
horu zai gata canza da yardar Allah. Yasa aka
turo ta yayi mata nasiha, sannan ya gargadeta da
cewa inhar ta bari mijinta yakawa kararta zatayi
mamakin abinda zai mata. Tace, insha Allahu
baza ta kara ba, yakawo kudi yaba Abba, da kyar
ya amsa ita kuma ya bata wasu zannuwa acikin
leda, yace su raba da abokiya zamanta. Taje tayi
wa hajiya zainu sallama suka tafi, tamkar
baquwa haka ta koma, sai kace basu taba zaman
aure da Abba ba, nauyinsa take ji. Suna tafe ya
ciro waya ya miqa mata, tasa hannu ta amsa
yace taki ce, tayi ta godiya yace ba komai.
Sallamarsu tasa gaban ummi faduwa, ta dake ta
fito ta amsa, wani kishi ya tasho mata amma
saita danne. Ta kalli bishira tare dayi mata sannu
dazuwa, ta amsa tana kallon ummi tayi kyau
tagoge daga ka ganta kaga wayayya 'yar gatan
miji. Ta dauko makullin dakin ta ba bishira, abba
kuma ya nufi dakin ummi. Bishira ta dinga kallon
yanda abba ya gyara gidan yaja gini ta gefen
ummi yayi mata falo da kicin, sannan tsakar
gidan an gyare shi da tiles. Haka bandakin su
yagyara shi, nan dai bishira ta shiga dakinta ta
zauna bakin gado tana yi wa allah godiya tare
dayi wa kanta alkawarin har abada bazata ta
kara yin yaji ko ta janyo abinda zaisa mijinta ya
sake ta ba. Ummi tana kan gado tana karanta
wani littafi yazo ya zauna bakin gadon bata ko
kalle shi ba don haushi take ji. Sai take ganin
kamar rawar kai yake yi da dawowar bishiran,
kuma tuntuni yana zuwa gurin ta ya boye mata.
Yace madam ina son in yi magana da ku ne ke da
bishira, ummi tace ina jin ka, yace can zaki zo
muje. Tace, gsky nagaji, kayi maganar da safe.
Yagama gano kishi ne ke damunta, don haka yayi
murmushi yace yanda kikace hakan za'ayi. Ya
fita kamar minti 30 yasake shigowa ya aje mata
leda tare da cewa saida safe aciki tace Allah
yabamu alheri. Yana tafiya taje ta banko kofarta,
yau kam bacci ya qi idanun ummi sbd tayi sabon
bacci a haqarqarin Abba. Dukkan filolinta ta rasa
wanda zai maye mata madadin haqarqarin
mijinta, ynzun yancan da wata tasan yanda yake
wannan rawar jikin ynzun ya manta da batunta.
Tarasa me yake mata dadi, littafin datake
karantawa kuwa sam bata fahimtar abinda ke
ciki. Hka ta dinga zubda hawaye har nisan dare,
ganin bata da wata mafita, tashi tayi ta bude kofa
lokacin 2 saura taje tayo alwala tazo ta kama
nafila. Abba jin bude kofarta ne yasa shi leqowa
ta window aranshi yaji tausayinta don yasan bata
iya bacci sai ajikinshi, ita bata san ya leqo ba
don ko hanyar dakin bata ishe ta kallo ba. Yakalli
bishira wadda bacci yayi gaba da ita ya tausaya
mata sosai yanda tayi tarawar jiki alokacin
auratayyarsu dazun. Yadauko wayarshi yarubuta
ma ummi sako. KI KWANTA KIYI BACCI BABY,
TARE DA QISIMA CEWA KINA LAFE
AMAKWANCINKI (WATO JIKINA) INA CIKE DA
KEWAR LEBUNANKI. Tana sallah taji shigowar
saqo amma bata yi ko marmarin dubawa ba, haka
tai sallah har zuwa lokacin da bacci yasoma
fizgarta. Tayi adduo'o'i sannan ta kwanta, saida
asubahi ne datayi sallah sannan ta karanta, dan
tsaki taja tare da cewa, Karya kawai, kishi yasa
ta fadin haka don tasan Abba sosai baya boye
mata komai ynzun. Sai dai abinda yasake qular
da ita da asubahin nan yanda tana fita shi kuma
ya fito wanka, duk da tasan dole wani abu yafaru
tsakaninshi damatarsa, amma sai taga tamkar da
gayya ya tsaya don tafito taganshi. Tna idar da
sallah ta dora ruwa akicin dinta, tadafa ruwan tea
taje kicin din bishira tadauko flask tazo ta wanke
ta zuba musu ruwan zafi taje kofar bishira tayi
sallama bishiran ce ta bude ummi tamiqa mata
tare da cewa an tashi lpy? Cikin sakin fuska tace,
lpy lau, nagode. Ummi ta ce ba komai takoma
dakinta ta kulle kofarta don yau bata da darasin
safe. Abba ma yau bada wuri zai fita ba, don
haka yadan samu baccin safe sai 8 yayi wanka
ya karya, sannan yanufi dakin ummi. Kofarta tana
rufe, ya kwankwasa ta share sai can dai dataji
yaqi tafiya sannan tazo tabude. Takalle shiya yi
kyau cikin kananan kaya, ta kauda kai tare da
cewa, an tashi lpy? Yace lpy lau, kin karya? Tace,
um'um sai anjima, zata rufe kofar yace,
makaranta fa? Tace sai karfe 2 nake da darasi.
Ta maida kofar ta rufe, yayi dan murmushin
takaici sannan yafita. Kwananshi 2 dakin bishira
yayi niyyar dawowa dakin ummi, don ya kosa
yadawo ya lallasheta bazai iya daukar wannan
shariyar da take mishiba. Tsakaninta da bishira
lpy lau amma shi sai tana wani share shi. part 33 the end
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:45
Ya shigo da zumudi zai nufi dakinta, tamiqe cikin
fara'a daga wanke-wanken da take yi ta amshi
ledar hannunsa da jakar laptop ta nufi dakin
bishira. Shida bishira suka bita da kallo, ganin
zata shiga bishira tace ummi yau ai dakinki yake.
Ummi tace injiwa? Anty bishara ai kullum ke ce
dashi har sai kin rama duk kwanakin da kika
dauka agida. Kinga kenan kusan wata goma sha
daya kenan. Abba cikin sauri yace ke
mahaukaciya ce? Ina ki kasamo wannan fatawar?
Ta kalle shi, sannan tashiga dakin ta ajiye ta fito
taqara kallonshi gurin malamai, yace to ban
yarda ba, don haka zanci gaba dayi muku kwana
bibbiyunku, ummi tace to ni na yafe mata nawa
kwanakin bishira tace nagode ummi. Haushi ya
cika Abba, amma shi bazai dauki wannan horon
da ummi take shirin yi masa ba. Yadawo dakin
bishira a fili yafurta kema saina baki haushi zakiyi
dakin sanin wannan furucin. Sharewa yayi yaci
gaba da kwana dakin bishira tare da nuna kulawa
ga bishiran. Ummi ta jure duk da duk daren Allah
sai taci kuka ta gode Allah, sannan tashiga zargin
cewa shi ma ya Abban dama can yana son
tarewa dakin bishira, inba haka bame zaisa yayi
saurin yarda kuma yayi ta nuna mata soyayya?
Ganin ummi tana yi tamkar bata damu ba yasa
shi qa rajin haushi, yadawo da yamma suna
zaune kowa A qofarshi. Ummi tayi kwalliya cikin
qananan kaya, bishira kuma tana sanye da leshi,
karatun littafi bishiran keyi ita kuma ummi tana
yin gyaran qumbunanta. Bawai suna wata hira
bane amma suna kula juna sosai musamman
bishira tana son su saba da ummi. Ummin ce
bata cika son fitowa ba, bishira ta tashi ta masa
sannu dazuwa tare da amsar kayan hannunsa
don yanzun tana koyi da ummi gurin kyautatawa,
ummi ta kalle shi sannu dazuwa, ya amsa da
yauwa baby. Yakalli bishira sweety zanyi wanka,
tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai
tazo tace masa takai nan kuma yajanyo bishira
jikinshi. Ba wai yana da bukata bane, amma don
ya shaqar da ummi sai ya banko kofar, qaran
kofar ne yasa ummi kallon gurin dakin. Ta duqar
dakai taci gaba da abinda take yi, kusan minti
arba'in suka fito, Abba ya matsawa bishira wai
suyi wanka tare, tace ni bazan iya ba akwai ummi
dama da dare ne inajin kunya. Kuma kada taga
kamar cin fuska ne, yace kenan don kada ki bata
mata rai ni mijinki bazaki faranta min ba ko? Dole
ta bishi suka shiga bayi. Baqin ciki yasa ummi
tashi tashige daki, kuka sosai tayi daga nan bata
fito ba sai magriba, tanayin alwala tarufo kofa,
washegari ma qin bude qofar tayi daga alwalar
asubahi. Abba yayi ta raba ido ya ganta amma
bata fito ba, yasan fushi take, ya kira wayarta
taqi dagowa yayi mata saqo cewa in zata
makaranta tafito inkuma sai darana ta bude ta
amshi kudin mota. Tana gama karantawa tayi
wuri da wayar ba tare data bashi amsa ba, haka
ya tafi. Bishira ta qwanqwasa ma ummi ta bude
suka gaisa, tace naga baki fito bane ina fata lpy?
Tace lpy lau bacci ne, tace yau baza kije
makaranta bane? Ummi tace, zanje sai sha biyu.
Bishira tace kinji dadinki ni gashi nan ina tayi
masa zancen karatun amma ya share ni, ummi
tace inkin matsa zai yarda, tace ko za ki dan sa
min baki? Ummi ta riqe baki, ni a wa? Ke da yake
hannunki ai ke ce zai saurara, ni kin zo ne ma ki
zage ni. Bishira tace wane irin zagi? Ni dama ki
amshi mijinki ummi don gangar jikinshi ce kawai
agurina, amma ruhinsa yana gurinki. Ummi ta ce,
ngd da zagi, bishira ta ce zancan gsky ne ba
wani zagi. Haka suka yi ta rayuwa cikin kwanakin
ummi kam har rama tayi shima Abba ya rage
walwala don wanda yasan kan kula da shi
kamarta. Yayi missing din abincinta. Amma ya
gaji bazai jure ba. Ya tuna bishira tace masa zata
ta yini gidan ummanshi. Don haka yana gama
muhimman abubuwan da zai yi agurin aikin
yanufi gida. Ummi tana shirin tafiya makaranta ta
dauko jakarta sai kurum taga mutum kamar an
jeho shi. Ta daure fuska tamkar bata taba dariya
ba, yace ummi nagaji kin ji ko, na gaji da wannan
horon naki. Laifin me nayi miki? In don na dawo
da bishira ne sai in saketa, duk ba kece kika
takura min sai na dawo da ita ba? Ummi tace, ni
karka doran jakar tsaba kasa kaji su bini, ka saki
matarka sbd ni? Ba ruwana. Yace, to ki dawo
yanda kike, kuma ki janye batunki na wai kin
haqura dani, niban haqura ba. Ke ma kuma nasan
dole ki kasa kanki, ummi ta ce ni ban damu ba,
ya ce qarya ne gashi nan duk kin rame? Ya
canza daga fada zuwa lallashi, ummi don Allah
na roqeki mu koma kamar da, haba bebyna. Ya
lalubo hannunta ta qwace, don Allah ka tafi kada
bishira ta dawo ta same ka anan ta zargi wani
abu. Haushi yakamashi sosai, ya daga murya da
qarfi, kin san Allah ummi zan hadaki da umma, ta
nufi hanya fita, nikaga kada kasa ni yi latti don
lokaci yayi nisa. Ya ficiko ta ta dawo ba zaki
makarantar ba, ke an ma daina karatun tunda yafi
ni. Ta zubar da jakar da hijabi ta nufi gado shi
kuma ya fita cikin zafin rai, gidan su umma yaje.
Bishira tana dakin umma tana sallah yabi umma
kicin, umma gurinki nazo, ta dube shi lafiya
Abba? Ya turo baki, alamun ranshi bace baki,
yace umma ki sallami bishira, tace kamar yaya?
Yace taje can gidan ko muyi maganar agabanta?
Tace, kyale ta muje dakin babanku. Abba ya fada
ma umma komai da ummi ke masa, tun dawowar
bishira ran umma ya baci tace ka barni da ita.
Banda shashancin ta da ita kadai take son
azauna? Baga bishirar nan ba gidan nan ta gane
kuskurenta ko yau yarinyar nan sai da tace in
yafe ta nace ni dama ban riqe ta da wani abu ba.
Shine ita zata qirqiro fitina? Yace, umma ai ba da
bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane
kurenta da dare kuzo kai da ita. Umma ce ta kira
ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu
don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar
isha'i taje gidan. Can tasamu abba, nan ko umma
ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo
umma tafada mata komai sai ta shiga fada. Wai
ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko
ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya. Abba
yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun
in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma
ni abin ya qare akaina? Nan fa umma tayi mata
tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka
kira shi awaya ya fita. Umma ta samu dama
taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki
yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice
kinyi fushi da ita kin barwa kishiya? To kada in
sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke
ganinki da ita. Ta jima tana bata shawara kafin
Abba yadawo suka nufi gida. Ya shiga gurin
Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai
kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,
tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa
aranar. ** ** ** ** Kwanci tashi asarar mai rai,
shekara ta zagayo lokacin bishira da tsohon ciki,
Abba nason yara don muhibba taqi dawowa tafi
son umma dole suka haqura suka bar mata. Ta
haifi 'yarta budurwa tubarkalla ranar suna ta ci
sunan sahura inda suka sa mata walida. Ummi
nason yara, don haka in tana gida to tana manne
da walida, Abba yana damuwa da rashin samun
cikin ummi, wanda ita ummin ta barma Allah
komai. Shekaru uku sun sake biyo baya, lokacin
Bishira ta sake haihuwar habiba takwara Abba
yayi wa ummi. Tsohuwa an qara tsufa, 'yan
rigingimu sun qaru tace ita Abba yama takwara
amma bata son ya duke ta irin yanda yayi wa
ummi. Abba kullum qara son ummi yake, umma
ta matsa masa sai da yayi qoqari ya sai fili rabin
filoti tace kuma a rage ciye ciyen dadin nan agina
shì. Haka kuwa ya gina flat mai daki hudu, daya
ummi daya bishira, sai nashi sannan na yara.
Yayi qoqari gurin gyaran falon ita kuma ummi ya
canza mata kayan daki don bishira an canza
mata daza su tashi agidan su. Yace tabishi bashi
in ya samu zai bata kudi amadadin kayan daya
saima ummi, tace ta yafe. Ummi dake karantar
(BUSSINESS) har ta hada (H.N.D) dinta kuma
tayi bautar qasa. Abba dai yace baza'ayi aiki ba
amma ya yarda tayi kasuwanci, Alhaji babba ne
ya bata jari inda take saro kaya zannuwa, lesuna,
takalma zuwa jakunkuna. Abin ya amsheta don
har kayan aure tana hadawa, tana yin saqo irin
su kwatano da chaina, india, pakistan ko dubai,
ta hanyar wani wan kawarta. Haka kawai ummi
ta samu kanta da zaban abinci, yawan bacci
kasala da dai sauransu, sam bata san
takamaiman lokacin al'adarta ba. Don bata wani
lissafi in yazo shi kenan in bai zo ba bata damu
ba tama cire ranta daga batun ciki. Abba ya kalli
nonuwanta, baby kwanan nan kirjinki ya cika
sosai, gashi kinyi haske ko kin canza mai ne?
Tace yaya yaushe kazama likita? Yace, ummi kin
fa canza shirya muje asibiti, ta ce ya Abba don
Allah ka bar ni nagaji dazuwa asibiti. Yace, to ni
zan je inya tambaya game da yanda ki ka canza.
Cikin jin haushi tace sai ka dawo. Ga yara
atsakar gida sun ishe mu, yace ni naki nake
qawar in gani nasan addu'ar da nike yi bazata
fadi kara banza ba, sannan ga qoqarin danake yi,
shiru ta masa. Dagaske yake yi yaje yayi wa likita
bayani, yace yadai kawo fitsarinta. Sai da suka yi
tsiya da qyar bishira ta lallasheta ta yarda ta
bada fitsarin. Rungume likitan yaya lokacin da
yake fada masa ciki ne in dai har fitsarinta ne.
Afalo gaban bishira da yara abba ya rungume
ummi yana murna, ji tayi tamkar tsokana amma
ganin ya zauna yana ta buga waya yanata
yadawa ta amince cewa gske ne. Don haka ta
tashi ta shiga dakinta tayi alwala tazo tayi nafila
raka'a 2 cikin kuku take godewa Allah tare da
addu'ar ya raba lpy. Ya bata mai albarka.
Tsohuwa ma kuka ta saka lokacin da labarin ya
riske su. Ummi taga gata musamman daya
kasance cikin yazo da kumburi tayi sumtum. Duk
kowa ya tsorata sbd tunanin ko hawan jininta ne
ya tashi. ALLAH cikin Ikonshi data tashi haihuwa
saita santalo danta cikin gajeriyar nakuda, sak da
abba kwabo da kwabo. Rungume ummi abba yayi
don murna, sunan alhaji babba ya sake maida wa
kuma walid din dai suke kiranshi. Watan yaron
bakwai ummi ta sake rasa kanta, kuka wiwi ta
dinga yi shiko abba murna kamar yayi rawa.
Tasake samun da namiji inda yaci sunan alhaji
karami suka sa masa hibban. Haka suka ci gaba
da rayuwa cikin haquri da juna, tsakanin bishira
da ummi, bama irin bishira saboda abba baya iya
boye son ummi. Kan 'ya'yansu ahade ba kya
gane bambanci, bishira ta gane umma uwa ce
guda har da rabi, don haka hatta shawara saitaje
gurin umma kuma ko sabani suka samu da abba
gurin umma take zuwa. Ita kuma umma ta dauke
ta babu bambanci da ummi, don bata taba fada
ma ummi sirrin bishira ba. Sahura yanzun ta
yarda umma da alhaji sune rufin asirinsu, kuma
gatan Abba, bashi ma da yayi aure gidan dasu
ummi suka tashi nan ya zauna. Dangin bishira
yanzun sunga bishira ta samu natsuwa sun
sulhunta. Abba agurin aikinshi yana ta samun ci
gaba, lamuran sai godiya. Ummi tashafa addu'ar
da takeyi sannan tamiqe tana linke dardumar tace
kallon me ka ishe ni dashi ne ya Abba, yace ina
kallo ne na kusan samun da na uku wannan
karon takwara zan ma kaina. Ummi ta jefa masa
dardumar hannunta, daina min fata ni, yace ban
karanci likitanci ba amma ni likitanki ne. Ta fada
kanshi, ya rike fuskarta yana kallonta cikin ido,
ummi lokuta da yawa ina zama inta tuna da,
musamman in na kalli 'yan yaranmu wadanda
suke matuqar kama dani, tace me kafi tunawa a
baya? Yace, yanda kikayi ta kirana awaya kina
tsara ni suhaylan kaduna. Suka sa dariya. Ni kam
nafi tuna yanda ni da kai muka yi ta 'ZURFIN
CIKI' dason juna. Yace Allah yabarni da ke har
abada matata. Ta kwantar da kanta
amakwancinta ''Amin mijina''. Muma Allah ya bar
mu da masoyanmu har gidan aljanna, ya bamu
lafiya dazama lafiya. Ya zaunar mana da 'yan
uwanmu lafiya, Amin ya rabbi. ** ** ** ** Bayan
shekara goma naje nasamu yaya Abba nace
inason muhibba yace badamuwa yabani kyautar
gida da mota. Ummi kuma ta hada mun kayan
lefe saboda namijin kokarin danayi na rubuto
maku wannan littafin aka daura mana aure da
muhibbata muka tare muka cigaba da soyayya
fiye dasu ummi ma.
@BABA MONO HAXOR
No comments:
Post a Comment