• ZURFIN CIKI KASHI NA 3&4 THREE AND FOUR BY BABA MONO
    ZURFIN CIKI KASHI NA 3&4 THREE AND FOUR BY BABA MONO
  • Download Now ZURFIN CIKI BOOK 3 AND 4
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:42
    Inna harira tace, Allah ya kyauta ku tashi mu tafi.
    Suka mike Suka nufi dakin ummi. Duk da ummi a
    da bata tunanin tana da lokacin bishira, yanxu
    kam dole tasan zaman da zasuyi. Su inna saratu
    suka ce ma ummi duk abinda zatayi don allah
    kada ki kulata. Suka ce tayi harkokin gabanta tayi
    biyayya wa mijinta shine abunda zai fisheta.
    Ummi tace To amma a zuciyarta bata tunanin
    zata zuba ido a rainata. Suna tafiya fatima ta
    shigo yiman sallama, ummi tace don allah fati ki
    dan tsaya ni kadai fa zan zauna a dakin nan. fati
    tace wayace kada kisan kawaye? Ummi ta ce
    wane kawaye, auren da a ka daura cikin yan
    mintina? Fati tace, Yau zakiji abinda mata kaji.
    Ummi ta damko mayafin fati, ni fa inajin turo, wai
    da gaske da wahala ko kina tsokanata ne? Fati
    ta kamo kunnen ummi tayi mata rada. Ummi ta
    zaro ido tare da cewa, Da gaske? Fati ta sheke da
    dariya tace sai nazo jin batun. Ummi tace sirrine
    ya za'ayi in fada miki sirrina? Fati tace au ni
    shine na fadamaki nawa ko? Ummi tace kinyi
    haram da kika fada fati tace, "ke kuma kinji
    haram ko? Suka sa dariya. Duk yanda ummi taso
    fati ta tsaya amman taki, don haka sukayi
    sallama. Fati ta shige dakin bishira don yi mata
    sallama. Bishira tace, fati fitar min daga daki
    bana wasa dake, tunda kema naga kin koma
    jam'iyar waccan yar iskar, fati ta fita, cikin ranta
    tana cewa ba zanki yar uwata ba don kishinki na
    banza tayi tafiyata. Ummi tsuru tayi tanaji tsoron
    abinda fati ta fadamata, amman sai wata zucia
    tace keda ba sonki yake ba kila ma bazaibi ta
    kanki ba, sannan ta samu yar natsuwa. Abba ya
    fito zai nufi gida sai kuma ya fasa ya nufi super
    market, ya siyo audugar mata yana tsammanin
    gobe ne zata tashi da al'ada a lissafinsa. Tun
    sanda ta soma bai taba mance ranar ba, haka in
    ya chanza mata lokaci duk yana lissafe. Ya sai
    masu yan kayan masarufi sannan ya fito, gida ya
    nufa amman gabansa yana faduwa kila har
    yanxun ba a kai ummi ba. Da yayi fakin sai kuma
    ya nufi gidan su umma duk kowa ya watse. Yayi
    sallama tsohuwa tana alwala ta amsa. Umma
    daga kicin ta amsa, tsohuwa tace "wane kinibibin
    kuma ya kawoka mai sunan malam? Bayan an
    kai maka ita? Yace kaji tsohuwa da wata magana
    da gurin ummi nake zuwa? Ni gidan mu ne. Tace
    kadaiji shi, takwara dai kada inji kada in gani, don
    nace mata duk abunda kuka mata tazo ta
    fadamin. Yarinyar nan tana kuka wiwi tabar gidan
    nan. Umma cikin dariya tace "toh ai tsohuwa in
    don Abba baza ayi fada ba, ummin ce dai abin
    jama kunnen. Tsohuwa tace 'a' a daina zancen
    nan suwaiba kada ma ya samu nayi. Abba yace"
    Toh bari in zo in hada maki kayanki mu tafi can
    don kada wani ya zafin cewa. Kinga kyafi tare
    mata. Tace ina gana nan din ma zanji. Yace
    Alhaji sun shigo kuwa umma? Tace A'a basu
    shigo ba. Yace toh bari in isa gida. Tace toh
    Abba ummi ma dazun aka rakata. Don allah Abba
    ka kara hankuri a kan na da, sannan matarka
    kuma kada kace zaka nuna mata bambanci a kan
    ummi yar uwarka ce. Ka kwantar mata da hankali
    ka mata adalci, sannan kada ka bawa ummi kofar
    da zata raina bishira. Yace zan kiyaye insha allah,
    kuma don allah umma ki kara mika godiata gurin
    alhaji. Tace haba Abba yaya kake fadin haka?
    Alhaji ai mahaifinka ne karka dinga kallon
    alakarka da ummi. Yace haka ne duk da haka dai
    a min godia, tsohuwa tace yaki godia ya samu
    mata a sama don rashin imani mai sunan malam
    ko gyauto bai sa mata ba, toh kasani tana binka
    bashin lefe. Abba Yace umma ni dai na wuce.
    Umma cikin dariya tace "Toh Abba. Yace tsohuwa
    ni nayi gaba, don in na cika tsayuwa a nan kila
    mu dambace, Tsohuwa tace kai dai jeka na baka
    amana ya tafi yana dariya. Koda ya kai kofar
    gidan sai ya bude mota ya dauki kayan
    masarufinshi ya nufi cikin gidan salam dai duk da
    jarumta irin tashi gabansa ne ke faduwa. Bai san
    wace irin masifar bishira ta tanada ba. Ya shiga
    da sallama. Bishira tana zaune akofar daki tana
    goye da muhibba, amman bata amsa ba. Duhun
    magriba ya soma dan daf da a kira sallah a ke,
    yace bishira ya ba a tada inajin ba? Tace tunda
    kazo yanxun ai sai ka tada kai. Da kafin wata
    tazo ai baka taba zuwa kace a tada inji ba. "Abba
    ya kalleta a zuciyarshi Yace" mata kenan masu
    manta alhaji. Ya aje ledodin hannunshi ya nufi
    injin. Bishira ta mike ta nufi ledodin tana fadin
    Tun yanxu a aka shigo mata da kazar, alamun ba
    za'ayi ada ba kenan. Ni lokaci na sa wuraren tara
    ya shigo ina lissafe da komai, ta bude ledodin sai
    taga kayan masarufi d kuma audugar mata. Tsaki
    taja tare da dangwarar dasu yana kallonta da ya
    kara mai ya tada injin sa yazo ya kwashe ledodin
    ya shiga falonta.vels / ZURFIN CIKI book 4 part 2
    ZURFIN CIKI book 4 part 2
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:44
    Kujerun da aka chanza mata masu kyau, amman
    a ran abba yace ya basu sati biyu. Ya cire riga ya
    fito yana son yayi wanka ne kafin a kira sallar
    magana,yaja ruwa da sauri da sauri yayi ban daki
    ya fito ya shiga falo ya kwalama bishira kira.
    Tace minene kake damuna? Yace ina aka kai min
    akwatuna na? Tace tace ina kuwa gasu can a
    kicin da sauri ya fito, kicin din lafia? Ya tsaya
    yana kallonta bani da mutuncin da za'a sa min
    kayana a daki? Tace ni da aka guji dakina da
    kayan a kace ni kazama ce, me zaisa in sake
    kaine? Daga baice komai ba ya nufi kicin ya
    kwaso akwatuna shi da takalmin shi ya kai
    falonta. Bai tsaya chanza kaya ba, ya nufi
    masallaci don zai rasa sallah. Bai baro masallaci
    ba sai bayan isha'i amman bishira tana zauna.
    Ummi kam ta kasa fitowa don tana kyankyamin
    ban dakin, gashi al ada ta sameta da yamman
    nan, sannan duk tanajin abin da sukeyi da
    matarshi. Ya shigo gidan ya chanza kaya sabi fil,
    ya feshe jikinsa da turarukkanshi wayar shi ta
    soma ringing ya daga salis ne. Yace aboki in ba
    sallama akwai daga hannu ko? Kace an kai maka
    rabin ranka koda ba zamu rakaka ba ai kayi
    mana sallama. Cikin dariya Abba yace na yafe
    salis yace To Allah ya bada zaman lafia. Suka yi
    sallama zai aje wayar kenan sako ya shigo. Ya
    duba ummi ce da wayar nan da ya bata ajiya
    cewa tayi, ina da matsala, ina bukatar taimako.
    Gabanshi ya fadi, sai kuma ya tuna kila al'adar
    ce, don haka sai ya saka hularshi ya dauki ledar
    audugar ya nufi dakinta. Har lokacin bishira nan
    zaune inda take, tace au tun daga yanxu za'a
    soma rashin adalcin? An dauki leda an nufi
    dakinta? Sam baiko waiwayo ba, yayi sallama ta
    amsa tare da gyara mayafinta, ya shiga suka kalli
    juna Cikin ido zukatansu sukayi fari kal. Cikin
    taushin murya yace, wane taimako kike bukatar?
    Ta lumshe ido sannan ta juya masa baya domin
    kunya ta rufeta. Yace To karba ya mike mata
    ledar ta waiwayo ta ansa da hannu biyu. Mamaki
    ya cikata ganin audugar, ya yayi har ya san tana
    bukatar audugar kuma a ina yake sanin lokacin
    al'adarta har idan ya chanza? Tace nagode yayi
    dan murmushi nima ina godia. Ya juya har ya
    daga labule tace "Em na ce....." ya waiwayo yace
    kika ce mi? Tace don allah inason maganin
    wanke bayi ne, tayi maganar Cikin kyankyami,
    sakamakon irin dattin da tagani a bandaki tare da
    gamsa kuka. Yayi murmushi wane iri kikeso?
    (IZAL) yace ai akwai amman yanxu Bai kamata ki
    shiga wankin bayi ba. Tace zan wanke in dai
    akwai. Yace bari in wanke maki, da sa tace a'a
    yaya Abba zan wanke. Falon ya koma ya cire
    rigarshi ya shiga jan ruwa. Bishira tana zaune ta
    mike ina badai abokitaina ba, in zaka kwashe
    mata rijiyar kwashe, amman a juye ko in baras
    kuma in dai ruwan da za'ayi amfani dashi ne
    kakeja, To kesani nima duk lokacin da zanyi
    amfani da ruwa saika dibar min, ehee. Ummi ta
    fito da bokitai don duk tana jinsu, tazo wurin
    Cikin sanyin murya tace, Ya Abba don allah ka
    bari in ja ruwan nan. Ya kalleta, take ya manta da
    duk bakin Cikin da bishira ta kunsa mashi.
    Yanxun daga zuwa saiki fara jan ruwa? Ummi
    tazo ta kama igiyar gugar, ai ba zama nazoyi ba,
    Ya Abba bauta nazo yi, Aljanna sai an dage. Ya
    saki dariya bishira ta dakatar dashi da ce wa
    "Karuwanci za'a gwadaman? Ta daga ruwan da
    ya zuba a bukati zata watsama ummi, yace kina
    watsa mata zan baki Mamaki. Cikin tsawa yayi
    maganar ta tsaya cak da bokitin yace, Sakarya
    mai kishin hauka. Yaci gaba da jan ruwan yana
    zubawa abokitan da ummi ta fito dashi. Bishira
    ta aje ruwan sannan ta hankadar dashi a kasa,
    Bai ko kalleta ba. Ya zuba ruwan sannan ya fito
    da izal da omo. Daki ummi ta koma ta dauko
    tsinsiyar da aka sai mata don wankin bayi, kin
    tafiya Abba yayi tana wankewa yana zuba mata
    ruwa har sai da taga bayin yayi yanda take
    bukatar sannan ta hankura. kyankyami jikinta
    takeji don haka taje ta hada kayan wanka har
    lokacinzurfin Ya Abba yana wurin rijiyar. So take
    ya matsa taja ruwan amman yaki, don ya lura
    bishira shi kadai take shakka zata iya zartar da
    komai kan ummi. Shine ya sake zuba mah ummi
    ruwan wanka, sannan ya coge har ta gama ta
    fito rufe da hijabi tayi dakinta, sannan ya dauraye
    jikinsa yaje ya maida kayanshi ya nufi wane.
    Bishira tana nan wurin kofarta ta kasa zaune ta
    kasa tsaye, bakinta kuma Bai fasa sambatu ba
    sai kace sabon kamun hauka. Fadi take kuma a
    zo a biyani duk basisikan da nike, ehee. Kuma in
    yarinya tamin in murji bukina. Ummi kam ta
    gyara jikinta tsab ta saka sabbin kaya ta feshe
    jikinta da turarokan da umma ta sai mata. Tunda
    ba lefe aka mata ba bare ta samu kayan shiga.
    Kan doguwar kujera ta mike, salam yanzu taji
    yinwa tana tsammanin rabonta da abinci tun
    karin safe. Ta shafa Cikin ta ina ma umma na
    aiko man da abinci. Ta furta a fili WAYA nan ta
    jawo tana tunanin sanar da Abba cewa tana jin
    yunwa. Sai wata zucia ta hanata wannan ba
    girman amarya bane. don haka ta share ta bude
    shafin game tana ta bugawa. Sai sha daya Abba
    ya shigo gidan, ya rufe gidan. Nufinshi ya wuce
    kai tsaye dakin ummi, amma sai ya tuna da kazar
    da ita bishira ya sawo mata. Duk da baya tunanin
    ta karba ga mamakinsa tana tsaye a tsakar daki
    har yanxu da daurin kirji take. Wannan ya nuna
    batayi sallah ba, bare wanka. Ya mike mata wata
    harara ta zabga masa banaci, ya juya batare da
    yace mata kala ba, ta biyo bayan shi, A bani
    basussukana da nike bi malam. Ya nufi dakin
    ummi taba biye dashi, ummi ta turo kofa dama
    yana kokarin tura kofa dama yana kokarin tura
    kofar bishira tana rike masa riga ta baya. Ya
    waiwayo Cikin zafin nama zai wanka mata mari
    sai taci sa'a ta tsugunna, Cikin azama ta yunkura
    tayi baya da gudu. Banda tsaki da yaja Bai ce
    komai ba. Ya shige dakin ummi da sallama, ummi
    bacci ya dan dauketa saboda gajiya. A kan kujera
    take da waya a hannunta. 4rm Shamsy bello
    balarabe.IKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 3
    ZURFIN CIKI book 4 part 3
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:48
    Niyyarta yau sai taji komai, don haka ta kai yarta
    ta kwantar, dai dai lokacin ne abba ya fito don
    kashe injin. Sake fitowar da tayi ne taganshi zai
    koma. Wayan cewa tayi da daukar buta ta shiga
    bandaki, shi kuma ya shiga daki ya kulle kofa,
    tazo ta manne jikin kofar. Fitar abba shine yaba
    ummi damar saka kayan baccinta, don bata iya
    bacci da kaya masu nauyi. Fargabarta yaya
    kwanciyar tasu zata kasance? Kan kujera ta
    zauna tare da kwantar da kanta a hannun kujera.
    Shima abba yana da jin zafi don baya iya bacci
    da kaya sai da gajeran wando kurum, idanu ummi
    ta kulle lokacin da taga ya abba ya soma cire
    tufafinsa ga hasken cocilar da ya kunna. Filo ya
    dauka ya jefa Kan doguwar kujera ya kwanta
    rigingine, ganin haka sai ummi ta mike ta nufi
    gado addu'a tayi sannan ta lumshe ido har bacci
    ya dauketa. Fuskarta cike da murmushi zuciyarta
    cike da godia allah yau gata dakin ya abba a
    matsayin matarsa. Abu daya ya rage mata shine
    ta koya masa yarda zaya sota. shima farin ciki
    ne a ranshi yayi da idanuwanshi sukayi kuri a Kan
    gado yana hango ummi ya ta zama halalinsa Abu
    daya ya rage shine ya koya mata sonsa. Bishira
    data labe bata jiyo komai amman kunnuwanta
    suna jiyo mata magana kasa kasa,,hawaye na
    zuba a idonta batasan iya adadin awanin data
    dauka a kai ba. Koda ta koma daki juyi kawai
    take a gado. Abbanta abun sonta yana can
    kwance da wata, watar ma makiyiyarta wadda ta
    tsana. Wata zuciya tace kije ki watsa masu man
    petur wata tace ki bari da safe ki caka masu
    wuka babu abinda bata rayaba har asubahin
    farko. Labule ta daga ta shiga leke taga ko zasu
    fito, lokacin ne kuwa abba ya fito yaja ruwa a
    bokitai yayi wanka da alwala. Ba zata gane ko
    wani Abu ya faru tsakaninsa da ummi ba don
    wanka al'adarshi ce Koda bai dauki najasa ba.
    Nafila ya shiga yi da rokon allah yasa ummi ta so
    shi, ya kuma hada masa kansu. Koda zai tafi
    masallaci bai tashi ummi ba tunda yasan ba
    sallah zatayi ba. Bishira ta fito tasa kujera kofar
    daki ta zauna, saboda tashi bai bar ummi bacci
    ba, don haka ta tashi in tana al'ada yini take
    wanka gaba daya sai ta tah ktankyamin jikin ta.
    Ta fito da bokitai duk ta cika d ruwa, Bishira tana
    kallonta sai da ta wanke bayi tas, sannan tayi
    wanka. Sauri take tayi kwalliya don a cikin
    nasihohin da umma tayi mata a safiyar da za'a
    kawota gidan miji tace kada ta sake mijinta ya
    ganta cikin kazamin yanayi. Kuma kada ta bari ya
    shaki wari daga gareta, tayi shafe shafenta.
    Atamfa ta saka riga da siket mai ruwan hoda
    hoda da ruwan kwai. Daurin dan kwali ta kafa
    sannan ta feshe jikinta da turaruka masu kamshin
    gaske, sannan ta shiga gyaran dakin duk da ba
    datti yayi ba. kayan da abba ya cire ta ninke don
    da jallabiya yake zuwa masallaci, sannan ta dau
    kujera ta kishingida saida gari yayi haske sannan
    ya nufo gida. Tsaki bishira ta jamashi maimakon
    amsa sallamar ta kara da cewa an girma ba'a
    san an girma ba, an kwana da yar ciki abin
    kunya. Ai wallahi baka cika dan halas ba da ka
    auri yarinyar datayi sanadin kulleka kaci duka har
    aka ballaka ba. Ya kalleta dalilin kenan da ban
    cika dan halas ba? Tace eh baka cika ba, yace
    toh jeka naji ni shege ne, in don dai na auri ummi
    ne, tace munafuki dama can kana sonta. Ya sake
    wai wayoowa yace so kuwa mai tsanani. Takaici
    ya cikata ta daga murya allah ya isa munafuki.
    Ya nufi dakin ummi wadda ke sauraren duk
    abunda ake. A cikin ranta tace ina ma son da
    gaske ne? Tasan ya fada don kawai yaba
    matarsa haushi. Da sallama ya daga labulen,
    ummi ta amsa tare da tashi daga kishingida da
    tayi, ya zauna tare da lumshe ido. Lokacin daya
    kuma ya shaki kamshin turarukan data fesa. Ya
    kalli Fuskarta labbanta da yake matukar so sun
    sha jambaki ruwan hoda. Take abba ya manta da
    duk wata damuna koh kalma marar dadi da
    bishira ta fada masa. Daga inda take zaune ta
    dan rankwafa don girmamawa tace ya abba ina
    kwana? Lafia qalau ummin abba ya bakon wuri?
    Ta lumshe ido saboda jin dadi sunan daya fada
    mata. Alhmdllh ya sake karkatawa yana kallonta
    sosai yace to masha allah, yanxu kinsan minene?
    Ta tattara hankalinta gareshi tace a'a? Yace kiyi
    hnkr nasan a al'adar ta hausawa amarya ta Kan
    yi sati daya cir ba tare data yi ko cangal ba. Toh
    hnkr zakiyi kinga ke tun daga kawoki jiya kin
    soma da wanki toilet. Sannan yanxu ma ina son
    ki ciro rishonki a hada shi a sa kalanzir mu karya.
    Kin dai ga yanayin yanda matar gidan take
    gudanar da nata kishin. Ummi ta gyara zama ta
    tuna nasihar ummanta da tace in zaki yima
    mijinki magana kalaman ya zamana kin zabo su
    ne ba wai kin sakesu ba. Ta kalle shi, shima ita
    yake kallo, tace ya abba don wannan ne kake ban
    hnkr? Yayi murmushi tare da lumshe ido ya kuma
    budesu lokacin guda, a yaran soyayya yana nufin
    eh, itama ta fahimci yaren don haka taci gaba da
    cewa. Ya abba ni dama ba zama nazo ba, neman
    aljanna nazo kuma zanyi komai don na sameta.
    Don haka kadaina bani hnkr umurni kawai zaka
    bani. Tun daga tsakiyar Kan abba har zuwa
    babban yatsansa sai da ya motsa, don sanyin
    muryar da ummi tayi amfani da ita tare da
    kyawawan kalaman ta. A zuciyarshi yace tabbas
    ummi haihuwar ummanshi ce, duk rainon umma
    dole zai zama daban ciki ya'ya. Ya kalli ummi
    allah yayi maki albarka tace amin. Ta mike ya
    bita da kallo taje gurin da a ka shirga mata
    kayan aiki ta zakulo risho yace to muje kicin dinZURFIN CIKI book 4 part 4
    ZURFIN CIKI book 4 part 4
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:13
    Ta mike ya bita dkallo tje gurin da aka shirge mta
    kayan aiki ta zakulo risho yce to muje kicin din.
    Tkarya murya, ya Abba amin afuwa, bna son in
    shiga kicin din can kmin hakuri insa rishona
    akofar daki. Ykalleta, bazai tkura mta ba domin
    ysan duk wnda yzauna da umma dole zai zama
    me kyankyani, yce indai zai miki kiyi kawai , in na
    smu ynd da nke so dga baya sai ayi miki kicin a
    gurin, tce ngd. Shi kan da kanshi yfito darisho yn
    budewa ya hadashi, tafito da tukunya tanufi rijiya,
    ta dauraye sannan tazubo ruwa.Bishira kuwa
    dma tazo talabe duk tji maganganun dsu kayine,
    jin abba zai fito da risho sai ta gudu daki. Sintiri
    ta dinga yi tna magana ita kadai, wato abban
    walid nece mazai ce anga irin nawa kishin?
    Yarinyar dya ce bsonta yke ba dole akayi masa
    shine har ysoma kai mta gulmata. Har dawani shi
    mata albarka , tunda uwarta ta kitso mata ynda
    zata ce ai dole yashi mta albarka, to ni ya tsine
    min kawai. Ummi ta amshi galan din kalanzir din
    dga hannunshi tre da cewa ya abba kawo inzuba
    zai ce ta barshi kenan wayarshi ta soma ruri,
    yadaga. Anty ce, suka gaisa tce tna son yin
    magana da bishira ya mike ytafi kaimata ummi
    kam ci gbata yi dasa kalanzir dinta takunna
    rishon tdora ruwan zafinta takoma daki, shima
    yna bt wayar ydawo. Anty tce bishira dm na kira
    kine inji bakuwar dta kwana a gidan da safennan
    kin bta abin kari ko? Bishira tahade rai tamkar
    tana gabanta, anty tome mexan bta, ina ruwana
    ma da ita? Dazunnan fa suka gama gulmata wai
    har yna ce mta tye hakuri tdai ga irin mtar gidan.
    Anty tce hauka kike tyi shi ysa ai dole yce haka.
    Ynzun dai sai ki tashi kibsu abin kari, hka da rna.
    Karki sake yarinyar nan ta dora tukunya sai byan
    sati daya, kina jina ko? Bishira tace to bdan
    zancan ykai ranta ta amsa ba. Sai don tunanin
    kada zancan zuwa makkanta yafasu . Sunayin
    sallama ta aje wayar tre da cewa, koda uwarta
    tke ywo bzan dfa mta abinci ba. Sai da ummi ta
    wanke flas din shayin sannan tazuba ruwan, falon
    bishira yje ydauko kayan shayin dbiredi. Tace,
    itama kakai mta ruwan zafin. Yce ta dafa, ygama
    yashirya tsaf don zuwa gurin aiki, harbakin kofar
    daki tarakashi. Yce, ummi naroke ki koda bishira
    tna zaginki ne don Allah kda ki kulata, sambana
    ganin laifinta don nasan sboda sona tkeyi. Nan
    da wni lokaci komai zai daidaita. Ummi tce kada
    kadamu insha Allah ba abin dazai faru, allah ya
    tsare yace amin nagode. Dakin bishira yaleka ya
    amshi wayarshi, sannan yce mezakuyi drana?
    Tzabga mishi harara, ina ruwana dawani abinci.
    Ya aje mata dari hudu. Gashi kusai nama nasan
    akwai komai ko? Tsaki taja, gara maka dauki
    kudinka don bzan dafa ma munafukai suci suji
    dadin zagina. Yakalleta, Allah yganar dke. Tdg
    murya yganar dakai dai maci amana sainaga
    bayanku. Bki yataba kafin yafita, baice mata kala
    ba. Ummi ta kinkimi akwatinan kayan abba dya
    kawo mt tgyara msu mzauni, sannan takwashe
    'yan kofunan dasuka sha tea ta wanke. Sannan
    takoma dki tna jin wsu kawayen bishira sunzo
    sunata habaice dazage-zage, ummi bt fito ba
    bare ta tanka. **** **** Bashir abin duniya ya
    ishe shi, ykasa sukuni sbd son ummi, yzuga
    ummanshi sun kai suka gidan su sahabi don
    afasa auran anfasa kuma duk da hk ummin
    tzama btashiba. Jinshi yke tamkar ykashe abba
    don tsana, don hka koyaushe cikin zuga umma
    yke dan kawai tatsani Abb. Guraran sha biyu
    ummi bacci yasoma dibanta sai tji muryar
    umman bashi akofar dakinta tna cewa ina ummin
    tke munafauka, fitsararriya tadaga labulan kofar
    tarike. ummi takalle ta. Kin kalle mi mna 'yar
    makirai. Kin bar smun zman lfy a gidannan, kuma
    uwarki ko tn tsafi dbakin kare dbakin dodo sai
    kinbar gidan dana. Ke inzan tafi dazani daya
    mtsawar bokaye da 'yan bori suna nunfashi kin
    smun nutsuwa agidannan. Bishira tace, umma
    shima munafuki ne shida yce bai sonta amma
    dazun haryi dni sukayi. Umman bashir tce shi
    Abba kimasa uzuri, duk abinda ykeyi byin knshi
    bne, anriga an rikita shi, bakya ganin shi duk
    afirgice yke? 'yar bori tafada min komai, ynzun
    karya tambaya muke nema. Bishira tce duk dhaka
    ma ynso, ai ance asiri yan tarad dahali. Umman
    bashir tce hk ne, shi dinma ai ubansa zaici ba
    dagin kafa. Ummi datna zaune kai duke, sam
    zantukansu bsu dme tba, abu dya yagirgizata
    btun asiri. Bta son ashiga tsakaninta da mijinta
    tun kafin su fara son juna. Saidai kuma dta tuna
    da addu'o'inta da takeyi bta fsa yi ba. Ga Azkar
    safe dayamma, saitasamu ntsuwa tsan Allah
    yafisu.ovels / ZURFIN CIKI book 4 part 5
    ZURFIN CIKI book 4 part 5
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:33
    Umman bashir tagama jarabarta tafita, karfe daya
    drabi Abba ykira wayar dke hnnun ummi tdaga.
    Cikin girmmawa tce, snnu da aiki ya Abba, ina ftn
    kn cikin koshin lpy? Yyi murmushi cikin jindadi
    yce, lpy nke ummi, am...in... Dama zan cene kin
    ci abinci? Tce A'a, amma bna jin yunwa, dnaji
    yunwa zn sha tea ai, kda kdamu kai fa kci? Yyi
    dan tsaki, tsiyar bna cin abinci awaje ummi,
    abincin umma kdai ke min dadi, Allah ys zki gjeta.
    'yar driya ummi tayi, insha Allahu sai mna fita.
    Yce anya kuwa? Tce insha Allahu ai nace. Kin
    gma mgna yafadi tre dyin murmushi mai sauti,
    yawwa bari in kirata ta turo miki da abinci, tce to
    ngd. Yce, nima na gode, sai ndawo. Tce, to Ya
    Abba kdawo lpy, ka kula min dkanka. Tkashe
    wayar, yjima yna kallon wyar tre dmamakin ynda
    ummi ta iya zantuka masu kwantar dahankali, irin
    wdanda bishira da ta ba ta shekaru bta iya ba.
    Ykira lyin ummanshi suka gaisa, yce ummana don
    Allah kitura ma ummi abinci, umma tce, kan wani
    dlili Abba? Tci gba dacewa, tbdijam!, bza ayi hk
    dniba. Abba ymarairaice murya, don Allh ummana
    yunwa tke ji. Umma tce, ta tashi tdora mna?
    Abba tsaya kaji, dadai wta ce can kke aure ba
    ummi ba sai na aika mta, amma ynzun ga
    uwargidanka agidan shi kenan sai in aikamata da
    abinci? Wannan ba gsky bne, sannan zgin da ake
    min ai sai ya linku yfi nada, yce umma duk wnda
    yzageki rshin fhimta ne. Kuma fana baiwa bishira
    kudin cefane amma tki tdafa musu abinci, tce kila
    tgaji ne, shiyasa bta dfa ba. Ita ummi dba saita
    amsa tdafa musu ba? Yce, amma dai umma
    tsakani da Allah kowacce amary bsai ta kwana 7
    bsannan tke fara dfa abinci? Umma tce, ai ba
    addini bne al'ada ce, don takama girki ai ba laifi
    tyi ba, yce, shikenan umma tunda kin hna sai
    anjima, tce mujima dayawa. Shiru abba yyi yna
    tunanin mgangnun umma, ysan gsky tfada, amma
    dmuwarshi ummi dbta ci komai ba. Ykalli agogo,
    saura kusan awa 2 ytashi, wayarta yske kira,
    tdaga yce ummi kisha tea din umma bta da
    abinci kfin ndawo. Tce, to ya Abba, kkusa
    dwowane? Yce, sai nan da awa 2. Tce to Ya
    abba, sai ka iso. Bta wni sha tea bdon bta jin
    yunwa sam, tshi tayi tasake kakkabe dkinta don
    mutane suna tshigowa ganin dki yra dmanya. Tas
    tkakkabe ko ina tafito tshare tsakar gidan lungu
    dasako, bishira lokacin mbata gidan wsu yra
    dsuka shigo tbasu kasko suka smo mt rushi
    tzuba turaren wuta mai kyau dkamshi. Tnayi tn
    kallon agogo, saura minti ashirin yaya Abbanta
    ydwo ta wanke byi tsake wnka, sannan tdibar
    masa ruwan wanka shima ta aje akofarta. Trufe
    kafin ya iso, tshiga dki tna ta shafe-shafenta, sai
    lokacin bishira ta shigo gida. Tna rike da 'yarta
    akafada, ita kanta 'yar ba amata wanka ba bre
    uwar, tkwabe hijabi trataye, sannan tzauna akofar
    dakin tna kallon tsakar gidan. Duk da ita knta
    gurin ybta sha'awa, amma bki ta taba tre dcewa,
    wahalalliyar bnza. Ummi tayi mtukar kya cikin
    wando da riga nawani ydin dshi Abba ydinka mta
    a babbar sallar dta gbata. Tasaki gashinta sosai
    tyi wani daurin dankwalin da ita ce ta iyashi
    amma gshin nta duk yna wje. Tfesa turarukanta
    sannan tfada kan kujera, tkalli agogo minti goma
    takaru akan lokacin dya fada mta. Zuciyarta tdan
    dmu tkosa sosai ta gnshi bta ki yzauna agida tyi
    ta kallonshi tre da sauraron muryarshi ba. Sai
    dkusan minti 20 sannan Ya Abba yshigo, tsayawa
    yyi yna kallon tsakar gidan, yau kam farin cikine
    ya mye gurbin bakin cikin dyake ji aduk lokacin
    dya shigo gidan ykalli tsakar gidan. Kamshin irin
    turaren wutan da umma ke cika gidanta dashi ne
    yke shaka. Ysaki murmushi tre dyin sallama,
    bishira dke zaune dabas atsakar gidan maimakon
    ta amsa sallamar sai tsaki taje dogo tre da cewa.
    Aikin bnza. Kallonta kurum yayi ranshi ya baci.
    Bai cemata kala ba ynufi dkin ummi, tyi nisa cikin
    buga game. Sallamarshi ceta sata yin jifa da
    wayar akan kujera tamike tdaga labulan daidai
    lokacin dyke cewa inshigo? Ta amsa sallamar
    dwata murya wadda bta san ma tna da ita ba,
    suka kalli juna cikin ido, lokaci 1 suka ski
    murmushi tmika hannu kafadarsh rtaye da wta
    jaka wadda bda ita yfita ba. Ya salubo jkar ymika
    mt tre dcewa, kirike dakarfi, tce to, sannu
    ddawowa. Yshigo rike da leda ahannunshi yzauna
    tre dcewa. Yauwa, tnufi robar ruwa data dauraye
    jug din data tnda don shi kadai, tzubo ruwa tzo
    dakofi tadauraye kofin snnan tzuba ruwan tmika
    msa tre dsake cewa, sannu dkokari. Ydubeta,
    yauwa kema sannu dkokar, dud da byajin kishi
    dole ne ysha ruwan, ybude bki ysoma shan ruwa.
    Sai yaji ruwan yfi duk wani ruwa dyasha a tsayin
    rayuwarshi gardi dkuma dadi, ydubeta ido lumshe
    dama ruwan amare dadin shi dabanne?? ZURFIN CIKI book 4 part 6
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:37
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa,
    yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire
    takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan dan
    teburin da aka aje don dora abinci ko kofi. Tazo
    takwashe tkalman tkaisu kusa da kofar fita tyi
    musu ajiya mai kyau, sannan tadauko dan twul
    tshare kasar gurin. Ykalleta, yi hkuri nshigo miki
    dki datakalmi ko? Tce bkomai aranshi yce nsaba
    shiga dakin bishira da tkalmi. Yjanyo ledar dya
    shigo da ita tre dcewa ummana tki aiko miki da
    abinci ko? Tace, kyi mta mgnane? Ya ciro take
    away din yasiyo mata, zo kici, ai dole ta bmu na
    dare, zan jene in tsaya mata. Ummi tdubeshi,
    anty bishira fa ka bata nata ne? Yyi mta banza,
    tduba ledar tga guda daya gakuma wnda yciro
    mata. In kaima anti bishira? Ydaka mta tsawa tre
    dharararta, ke! Ban aike kiba, tatsaya tna
    kallonshi, meye ruwanki da mtata, kin fini snin
    meye kamata nayi kenan? Yja dogon tsaki tare
    djanyo jakar dta dora mishi akan gado, jikin ummi
    yyi sanyi. Ta tuna damaganar da umma acikin
    nasihar dta mta, kda kizama dga cikin mtan
    dsuke btawa mzajensu rai. Hakan yna sawa miji
    yatsani matarsa, kiyi tka tsantsan kinsan hlin
    abba yna dsaurin fushi. Dsauri ummi tasulalo dga
    kujera. Don Allah kyi hkuri ya abba, ban san
    zakaji haushi ba. Ydubeta fuska daure, hwaye
    ygni sun cika idonta yace, kda ki sake hawayen
    nansu zubo, tsa ytsunta tdanna idnunta, tshi ki
    zauna ki dauki abinci kici. Tzauna tarike abincin
    tkasa ci. Ykalleta suka hda ido cikin ido, tariga
    shi mgna kayi hkuri Yaya Abba, tausayinta
    ykamashi amma sai ydake. Bnason kisake mgna
    akan abinda yshafi mtata kinji ko? Da sauri tce,
    bzan kra ba. Yyi dan murmushi ci abincinki.
    Tasauke wta irin ajiyar zuciyar dhar ya klleta da
    ido ya tmbayeta lpy? Dabaki tfurta lpy lau, yce ci
    abincinki. Ummi tdauki abinci tn ci, jefi-jefi tna
    kallonshi, shi kuma yna ta kokarin kunna laptop,
    don ymantar da ita. Yce, kinsan menene wannan?
    Ta a'a yace computer ce, agurin aikinmu aka rba
    mna. Ummi tace, kyauta? Yce A'a za'aringa
    cirewa acikin albashinmu, mtso kigani. Tdan
    mtsa inda zta iya kallowa, ykunna yna nuna mta
    abubuwa, yce ai nsan ki zaki iya sarrafata, tce
    wai, bazan iya ba Yaya Abba. Yce, nima sai
    nshiga mkarnta akwai tnan cikin gri zan shiga nyi
    diploma, salis shi tuni yyi. Ummi tce amma gshi
    ynzun mkana sarrafata, yce ina dan hwa ta office
    dinmu ai tce tayi kyau Allah ysa albarka yce
    amin. Ykashe komai ydauki take away din ynaci.
    Sannan yce, bri infita. Tdube shi itakam bta son
    yfita don umma tce mta tzama mai tsare mijinta
    dga zaman majalisa koyawo. Indai ba mkarnta
    yke zuwa ba, yma ztayi thana shi fita tatambayi
    knta, tdube shi cikin tausasa murya. Ya Abba hka
    zka fito bkayi wnka ba? Tmike gruwa nan nadiba
    bari inkai mka, shima ymike. Sai anjima zanyi
    ummi, ynzun shago nke sn zuwa. Akwai wsu
    dinkuna da za a amsa yau ina son ingako yaran
    sun gama snnan inson in yanka wsu dunkunan
    ciki har dnaki, koda yke saina gwada ma tukunna.
    Tce, tokadan huta mana ynzun faka dawo, ygane
    bta son yfita ne, don hk yce kda kidamu dg shago
    ba inda zanje. Har bkin kofa tarako shi tarike
    labule, to sai kdawo, yce to, ynzun mbai kalli inda
    bishira tke ba, yyi wje. Datsaki traka shi tre
    dcewa, girma dai yfadi warwas, murmushi yyi mai
    sauti yfice abinshi. Ita kuwa sai thau zntuka,
    kinibibi a auran mka miji sannan a nuna anfi ka
    sonshi, yrinya lokaci nabaki. Ummi dai sai tkaro
    kofarta, koda dre abinci daidai cikinta bishira tyi
    taci tba 'yarta shiko Abba bai shigo gidan basai
    bayan sallar isha'i. Byan yje sun sha dirama da
    umma, tce itafa bta yi abinci dsuba, yce umma
    gskiya toki bmu na babanmu. Tyi driya, kasan
    abin dakake fada kuwa abba? Inbaku abincin
    mijina? Ai kuwa bkwaci ba. Tsohuwa tace, kai ina
    mtarka ita bazata dafa fa? Kodon tsoronta
    fakakeji ko? Abba yce eh bazata dafa ba ina
    ruwanki ke tsohuwa kin cika sa ido. Tce, nasa
    din, ai gskiyane kowa ysn uwargida ke yin girki
    harsati guda. Abba yce, to mu tsarinmu bhka bne,
    tkwashe da driya. Bwani tsarinku bhaka bne kila
    ma kinyin girkin tyi, yce oho dai bza kiji bdai, tce
    jeka intayi tsami mji. Umma dke tsheka driya tce,
    abbana zoka dauka gashi nan yce, yauwa
    ummana mungode, tce abba bka shiga gidan
    nanne? Yce wai gurin umman bashir? Tce eh, yce
    ina zuwa mna, tce todon Allah kadinga shiga, nan
    yyi musu sallama ytafi. Lokacin dya shigo gidan
    dindim! Sai daya tda injin, aranshi cewa yake yi
    lallai mta dakíshi, jimatar dko darana tada inji tke
    yi amma ynzun don kda wtan tga hske ko tji iskar
    fanka shine taki tadawa.I novels / ZURFIN CIKI book 4 part 7
    ZURFIN CIKI book 4 part 7
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:41
    Ya aje kular kofar dakin ummi yaleka dakin
    bishira, tana kwance kan gado, itafa bata jin cewa
    zata dazama dakishiya, dole cikin biyu ayi daya,
    kota tada ballin dazai saketa komuma tanemi duk
    wata hanyar daza akori wannan 'yar iskar
    yarinyar. Yashiga dakin, muhibba daketa wasa
    akan gadon da baya zaton tun da aka kafashi
    tasake kakkabe shi, yace hibba. Yarinyar ta
    waiwayo cikin murna tanufo ubanta da dan
    gwaranci, bishira tasa hannu tasuri 'yarta yace,
    bishira duk wannan abin daki keyi fabashine
    mafita agare kiba. Ki kwantar da hankalinki ki
    nutsu ki kama girmanki, yarinyar nan zata biki
    amma in kin zabi akasin haka kece zaki koko....
    Kai malam! Ta katse shi, bafa wata sauran
    magana fanasan komai, ni yanzun saki kurum nafi
    muradi, ya ce sakin lafiya? Ni yanzun ma na
    soma sonki, tadaga mishi hannu tare da daga
    murya, nikuma nadaina sonka, karya ne makace
    kana sona kuma kanason waccan banzar. Dole
    acikinmu akwai wadda kafi so. Abba yace to ai
    kece, ke nafi son kuma ita tasan haka, kalmar
    tashi tadan sanyaya mata zuciya. Don haka bata
    sake magana ba, yace kina bukatar wani abu ne?
    Tace don Allah nidai ka fita kawai, yace to na
    fita. Ummi lokacin tana canza kaya zuwa riga
    dazani na leshi, sosai tayi kwalliya tamkar
    kasureta ka ruga don kyau. Fuskarta sake ta tari
    Abbanta dasannu dazuwa, ita ce tasa musu
    abinci kowa da plate dinshi, amma sai ya aje
    nashi yace suci nata. Dama taso yin hakan amma
    tana tsoron kada ya gwasaleta, sai da sukayi
    dam sannan yace bari yayi wanka tatashi takai
    masa ruwan wanka tadawo. Kafin ya fito ta sake
    gyara ko ina, jallabiya mai gajeran hannu yasaka
    mara nauyi ya wadata jikinshi da turaruka tana
    kallonshi cikin sha'awa. Taso taimaka mishi tun
    agurin shafa mai, amma tana tsoron kada yaga
    zakewarta, don haka tashare tare da cewa
    dasannu za azo gurin. Ysake cewa zai koma
    shago, tace haba yaya Abba yanzun kuma?
    Yadauko tape dinshi nagwada mutane, zo in
    gwadaki, har da kayanki zan yaka yanzun.
    Yarannan 'yan shiriritane, badon naje dazun ba
    dasun sani nasaba alkawari, dinkunan su kawai
    suka yi tayi suka aje wanda nabasu. Ummi
    tabata fuska, ya tausasa murya, come on zo in
    gwada ki, bazan jima bakinji ko? Tatashi taje
    gabanshi ta tsaya. Sai dai mamakinta duk
    dunkunan da Ya Abba ya sha yi mata abaya bai
    taba gwadata basai yanzun? Koya manta yanda
    yake mata ne? Tsawon siket din ta ya soma
    gwadawa, tana tunani sai taji ratsawar dan
    yatsansa tare da tape din a kwankwasonta, duk
    da cewa dariga ajikinta saida hakan yasa taji
    wani yanayi ajikinta. Har ma takalle shi, haka nan
    ya auna hips dinta da kirjinta, shi kanshi ya shiga
    wani yanayi alokacin, haka nan yakoma shagon
    cike dakewarta. Kayan bacci tasaka ta kwanta a
    gadon tana da yakinin bazai mata komai ba,
    tunda yasan bata sallah. Har kusan goma da rabi
    tana jiran shigo warshi shiru, waya tadauka ta
    rubuta mishi sako da cewa. Ya abba don Allah
    kadawo ni dai tsoro nake ji. Ya karanta yayi
    murmushi, azuciyarshi yace, don ita ya kwafe,
    yayi dunkunan yana son kudin don ya sai mata
    akwati da kayan shafa zuwa kayan ciki. Share ta
    yayi sai kusan sha daya darabi sannan yatashi
    tare da sallamar yaran, haka nan itama sai daya
    hado mata duguwa rigarta ta shadda wadda
    dama anriga anyi sirfani ajikinta. Dakin bishira
    yasoma lekawa, bacci yadauketa sosai agefen
    gadon take da alamun baccin yazo mata ba cikin
    shiri ba. Abba yayi murmushi tare da cewa, wa ya
    fada miki ana cin bashin bacci? Ina zaton matar
    nan jiya bata runtsa ba, yau gashi yazo ba shiri.
    Har ya gyara mata kwanciya itama 'yar ya gyara
    ta amma bishira bata farka ba, don haka yakashe
    mata wuta yafita. Yaso kashe injin amma garin
    da zafi gashi basu kawo wutar nepa ba, gidan
    yarufe yazo ya tura kofar ummi data rufe. Karar
    kofar ne ya farkar da ita amma bata motsa ba,
    tun daga kofar yatsaya yana kallonta, can
    tsakiyar gadon takwanta bata dora kanta saman
    filo ba. Amma tana manne da filo daya akirjinta
    fuskarta yake kallo, a jikinta taji kallonta yakeyi.
    Kusan minti 4 sannan ya aje ledar hannunshi.
    Shirin bacci yake amma yakasa daina kollonta,
    shikanshi yana mamakin wannar jarababben son
    dayake ma ummi, duk da dakewar dayake don
    kada yabada kanshi amma sai yadinga jin wani
    abu yana fisgarshi. Tamkar yafito mata da zallan
    sonshi gareta, tsoronshi inta gano kila tarainashi.
    Kadan-kadan takan bude ido ta saci kallonshi, sai
    daya gama komai a tunanin ta ya kwanta a
    gadon amma sai taga yadauki filo yakwanta a
    kan kujera. Haka suka rayu har tsawon sati daya,
    ranar yabar dakin ummi ranar kuma tasoma salla,
    ita ko bishira satin nan tayi shine tamkar
    mahaukaciya sabon kamu. Ranar kuma da abba
    yadawo dakinta bata runtsa ba shima bata barshi
    ya runtsa ba, daga bisani dole yabar dakin
    yakoma falonta yakwanta. Haka gidan yaci gaba
    da kasancewa, in Abba yafita ummi bata da
    sauran sakewa saboda zagi da habaicin bishira.
    Wani sa'in har da kawayenta, ko makota 'yan
    jam'iyarta su shigo suyi tayi, ummi bata kula su.qnovels / ZURFIN CIKI book 4 part 8
    ZURFIN CIKI book 4 part 8
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:50
    Duk abinda bishira zatayi kada takulata. To ita
    duk bawannan bne damuwarta ba, damuwarta
    ynda Abba sam yaki nuna sha'awarta gare shi,
    duk dayasan tana sallah, hka nan duk lokacin
    dakwananshi yajuyo kanta sai dai ya jefa filo
    akan kujera ya kwanta. Takasa gane ma'anar
    hakan, tun tanajin dadin ynda bai nemeta ba
    saboda tsoronsa da take harta dawo tasoma jin
    haushi. Ita ma fa mutum ce cikakka mai lafiya,
    sannan tana kwana daki daya da san kacecen
    abun sonta ya ya ba zata damu ba? Sai dai tayi
    wa kanta alkawarin a yau in zasu shekara ahaka
    ba za ta taba yi masa tallar kanta ba ma'ana
    baza takai masa kanta ba. Sai dai zatayi masa
    kyale- kyale taga karshen girman kai, ta kosa su
    hadu da fati don ta bata sakon kananan kaya
    tasiyo mata don ta bata labarin cewa ta kwashe
    su a wambai. Kwananta goma taso ma girka, duk
    tsawon kwanakin nan abincin siyarwa dana
    umma suke ci, domin bishira taki dafa abinci.
    Ranar da zata fara girki ta haukata gidan da
    kamshi, tuwon shinkafa miyar shuwaka, tasan
    Abba nason tuwon shinkafa. Tun kafin ya dawo
    yamata waya ta aika shagonshi, 'yan shago sun
    ci suna santi, haka nan ya gayyaci abokansa
    kofar gida ya shimfida musu tabarma suka ci tare
    da lemu, zobo da kunun aya. (reall ehem tazubo
    mun nawa na koma 1 site ina kimtsa cikina lolx)
    ga nama ya wadata a ciki, abba yaji dadin yanda
    abokanshi sukayi ta santi, safiyar ranar kuma
    kunun gyada ta musu da kosai. Duk wannan
    abincin da ummi keyi bishira ko a harshenta ta ki
    ci, cewa ma tayi ita fa kowa tayi girkinta don
    baza ta ci abincin ummi ba. Kuma ba shegiyar
    dazatai wa girki, hakan yayi wa ummi dadi don
    nata ganin ta bakin tsohuwa ce, da ta ce ko kwai
    bishira tadafa shine dai dai a cikin bawo to baza
    ta iya ci ba bare wani abinci. Sun zauna tsawon
    wata daya ahaka ummi bata taba leka ko kofar
    gida ba, tana kewar ummanta gara ma tsohuwa
    duk ranar juma'a in tadawo masallaci takan biyo
    gidan taga takwararta. Dakinta Abba yake
    yagama karyawa ya shirya zai tafi aiki, ummi ta
    kalle shi tana son tambayar zuwa gidan umma
    tna jin tsoro. Ya dubeta kamar kina son cewa
    wani abu ko? Ta ce am dama inaso inje gida in
    gaida su umma, yajuyo yadubeta suka hada ido.
    Gabanta yafadi, ta sunkuyar dakanta, yace a'a
    tadaga ido takalle shi, wani kunci taji aranta, ga
    matanshi nan yini take garari a layi bata ko
    tambaya amma ita ta tambaya shine ma zai
    hanata? Ya dauki jakar shi, ta mike ta rakashi
    har tsaka gida tare da yi masa addu'ar Allah
    yatsare, yini tayi da takaici dama haka mata suke
    ji in an hana su zuwa anguwa? Daran ranar zai
    koma ga bishira don haka bata san dawowarshi,
    tana kwance kan doguwar kujera tana karanta
    littafin hausa ( naleka muku kozanga sunan
    littafin amma bangano mukuba) kamshin turaren
    shi ne yasa tasan yashigo, don littafin yadauki
    hankalinta. Ta amsa sallamar daya sake yi tare
    da mikewa zaune, yana sanye da kananan kaya
    tamkar wani dan saurayi, yayi kyau a idonta
    kamar ta rungumeshi. Tace sannu dazuwa yace
    yawwa, dauko mayafinki muje tazura takalma
    bayan tagoge sannan ta ciro mayafi, yace a'a
    dauko hijabin. Ta maida ta dauko hijabi tafito
    sannan yakulle kofar, saida suka fita waje sannan
    yadubeta, hannu rabbana zakije musu? Tace yaya
    Abba toni bani da kudi ai. Sukabi ta wani super
    market suka sai sabulai da turare, akafa suke
    takawa sannu ahankali suka jero duk da cewa
    bawata hira suke ba, Abba ne yake amsa waya
    jifa-jifa na jama'a masu sonshi. Tun daga nesa
    suka hangi mahaifansu suna cin abinci a inda
    suka saba. Alhaji babba dakarami. Cikin zumudi
    ummi ta ce, yauwa gasu alh. Abba yaje haka
    zakije musu da rawar kanki ko? Cikin shagwaba
    tace, wanne rawar kai nayi toni yaya Abba? Yace,
    na gani kinayi kamar zaki kwasa da gudu, kafin
    tayi magana sun iso gurin dukkansu suka zube
    akan tabarmar daga gefe. Abba ne yasoma cewa,
    sannunku alh. Alh. Yace, a'a kune? Alh karami
    yace, uwata harda ke? Tace, eh ina yininku?
    Sukace lpy lau. Alh. Karami yace, uwata kunanan
    lpy ba wta matsala ko? Ta ce, ba komai alh..
    Yace to Allah yyi maku albarka, ya azurtaku da
    'ya'ya ma su albarka wadanda kuma zasu biku.
    Abba yace amin suka hada baki da Alhaji babba,
    alh babba yaci gaba da cewa, Abba ya hakurin
    shirmen ummi kuma? Ince dai bawata matsala?
    Abba yakalleta mun gode Allah alh, amma bwata
    matsala, ummi tamike dazumudi bari a karasa.
    Tun daga soro take kwala ma umma kira. Umma
    tce, A'a muryar wa nake ji haka? Ummi tashigo
    da gudu ta cakume umma, tsohuwa tafito tana
    fadin lale. Dakin tsohuwa tasoma shiga suka
    gaisa sannan tadawo dakin umma, sun gaisa
    umma tasake mata nasiha, ummi tace umma ni
    matsalata daya matarsa. Kullum saitayi min
    habaici tana zagina wata rana r harda kawayentaRFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 9 ZURFIN CIKI book 4 part 9 Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:54 Ita ko bishira gidan su umman bashir ta tafi dakuka wiwi, tace Abba yamata duka takan sun taka hakkinta sun fita ranar girkinta. Tayi magana ummi ta mata tsaki shi kuma yazo yazo yahauta da duka, umman bashir tace duka! Duka akan ummi? Tabdi, tashi muje gurin wadanda suka daure masu gindi. Umma na kokarin shiga daukin alhaji taji sallamarsu sama-sama, gabanta yafadi ta amsa tare da dawowa baya. Sahura tace to suwaiba, abinda kuka shiirya yasoma tasiri. Abba yayi wa bishira shegen duka saboda 'yarku, umma tace haba sahura, yaya ki ke irin wannan maganar? Mu ne zamu sa Abba ya cutar da iyalinsa? Sahura kiyi nazari. Alhaji yafito, me yafaru ne ni kejin hayaniya suwaiba? Umma tace, oho. Sahura tace, bishira fada musu. Nan bishira ta shaida masu yanda ta tsara ma umman bashir, alhaji yadaga waya yakira Abba, Abba yana dagawa alhaji cikin zafi yace Abba maza kazo yanzun duk in da kake. Abba yace to alhaji, ummi ta mike zan bika tsoro nake ji ni daya, cikin zafin rai yace abin daki ke tsoro ya cinye ki, ya fita fuuu. Cirko-cirko ya same su a tsakar gida, sai muryar sahura kake ji tana rashin mutunci. Alhaji karami yadawo gidan shi sai ya jiyo muryar sahura a can gidan, ya nufi gidan don haka kusan tare suka shiga gidan da Abba. Alhaji cikin bacin rai yafada Abba da fada, abba bai katse shi ba har sai daya kai ga tambayarshi cewa me yasa yayi mata duka? Yace, banyi mata duka ba alhaji marinta kawai nayi, umma ta ce mari kawai ne Abba? Alhaji karami yace, to kan wane dalili ma zaka mare ta? Abba ya koro musu komai, ya kara da cewa, wannan har zata ce an mata tsaki, zata yi duka ni wane irin zagi ne bata min ina hakura darajar iyayenta? Ya nuna ta, wallahi in kika kai ni bango zaki koma gidanku don bazan iya ba na gaji, nan kuma su alhaji suka shiga bashi hakuri. Ita kuma suka bata rashin gaskiya, sai dai duk da haka umma tai masa fadan kada ya sake daukan ummi ranar girkin bishira ya fita da ita, yace to. Umman bashir taja bishira zo muje ai dama nasan baza suga laifin 'yar su ba. To wllh marin da yamiki ki tabbata bashine. Ko nan da yaushe ne ki rama shi kan ummin, in ba haka ba duk da banice uwar data haife kiba sai na tsine miki. Alhaji karami yace, to katuwa mara lissafi, ke dai kinji haushin rayuwarki, to ki sani duk randa ta rama duka akan ummi ni kuma akan ki zan rama wa ummin inga ta tsiya. Alhaji babba yace, kada kai ma kazama su mana aminu. Tsohuwa tace, gskiya ne, in har tazama silar dukan ummi itama sai ya mata taji. Umma tace, a'a duk abin ba zai kai haka ba insha Allahu, kai dai abba kayi ta hakuri sannan kadaina sa hannu kana dukan mace. Yace, umma dukana fa tayi, sai kace wani soko zan tsaya mce tna dukana, umma tace, to ai tace ummi taje duka, yace ummin 'yarta ce? Alhaji yace, tafi gidan kahadasu kayi masu nasiha, Abba yace ai baza ta tsaya ba, wannan yarinyar fa sai dai addu'a ni in nagaji kawai hakura za ayi, umma tace bana son jin wannan zancan, alhaji karami yace ai gskiyarshi ne, shi yasan irin zaman dayake da ita. Alhaji babba yace, ai kuma darajar mahaifinta za aduba, da mutuncinsa, Abba yace ai dama alhaji ni banda mahaifinta da tuni nayar da kwallon mangwaro na huta da kuda. Umman tace je ka gida Allah ya kyauta. Nan dai ya musu sallama yanufi gida. Ummi da gske tsoro ne da ita, da rana in ba kowa bta damuwa, amma da dare tfi son tdinga jiyo motsin bishira koda habaicin dta sabayi mata. Soro taje ta tsaya tana yi tana leka waje, can ta hango bishira, don haka takoma daki ta kullo kofa aranta ta ce kada tazo tayi min duka. Ummi tna jiyota lokacin data shigo tana cewa wllh kan yarinya zan rama marina, wannan dole ne koba dade saina ramashi. Abba kan bai nufo gida ba, shagonsa ya wuce lokacin goma ta gota, yaran sunyi shirin tafiya, don haka ya amshi makullin ya shiga shagon saman teburin da suke yin yanka da guga ya hau ya zauna. Tagumi ya zuba hummu biyu tare da sauke wata ajiyar zuciya mai karfi, me yasa ummi ta furta kalmar data tuna mishi cewa bata sonshi? Sakankancewa dayanda ummin kenuna mishi yasa shi jin kamar sonsa take ashe dai shi yake shermenshi. Ya tuno wani labari yaya tabaji na wani mutum da aka ara masa mata wadda bata sonsa, tazo tazauna dashi tsawon shekaru kuma tayi masa biyayya matuka. Ga 'ya'ya sun haifa yaran sun yi girma sosai, suma sun zama magidanta, sai wata rana mutumin nan suna hira da matar, yace oh, wance dafa ba kya sona, yanzun gashi harmun tsufa kin manta dawata kiyayyah. Tadubeshi, inji wa yace maka na manta? Biyayya kurum nake maka amma har gobe bana sonka. Abba yajinjina kai, lallai dole ne ya nutso, yadaina tunanin ummi tana sonshi kokuma zata soshi, shidai da kaddarar sonta tafada mishi sai yayi ta addu'a Allah ya bashi hakurin jure zama da ita ahaka. Bai san adadin lokacin daya dauka awaje ba kuma baisan adadin tunanin dayayi ba. Daga karshe yarufe shagon yanufi gida. Ganin yanda garin yayi tsit shine yasa shi kallon agogon hannunshi, daya da minti shabakwai, lallai lokaci yatafi. ZURFIN CIKI book 4 part 10
    ZURFIN CIKI book 4 part 10
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:55
    Yanufi dakin bishira aranshi yce da wanda yake
    kinka gara mai sonka ko mahaukaci ne. Gdon
    yahau tagefe ya kwanta suka saka muhibba
    atsakiya, ummi kuwa duk tsawon lokacin nan
    tkasa bacci domin bata ga shigowarshi ba. Idonta
    biyu har sai daya shigo ta leka ta windo tana
    kalloshi har yashiga dakin bishira ya rufo kofa,
    sannan ta kwanta tare dayin ajiyar zuciya. A fili
    tace ina ga fa har dani alaifin nan, amma bari
    gari yawaye inba shi hakuri durkusa ma wada ai
    ba gajiyawa bane. Bishira tafarka cikin dare taga
    Abba kwance hannunsa na dama dore kan jikin
    'yarsu, ta tsura mishi idanu tana son mijinta
    sosai. Ban dahaka data kaishi koto ya bata
    takardarta koda mahaifinta xaimata baki
    sanadiyar haka, amma shi yanzun yadaina sonta.
    Takai hannu tadora a kumatunshi, ahankali
    yabude idanu, suka kura majuna ido yace bishira
    me yasa kike yin abinda zai samu mu samu
    sabani bayan kinsan sone ya hadamu?
    Idanuwanta suka kawo ruwa, Abba dane ka soni
    kaji dani har alokacin ina ganin ba Wata mace
    data kai ni dacen gwanin iya soyayya. Amma
    yanzun duk ka zuba ni a kwandon shara har kana
    marina saboda ummi. Ya ce, a'a ba sbd ummi na
    mare kiba, saboda kin dukeni ne amma kiyi
    hakuri. Banason kina zubar da kanki a gurinta,
    yawan fadanku zai sa raini ya shiga tsakaninku,
    ni kuma ba zan so ta rainaki ba. Kuma da kin
    kwantar da hankalin ki ummi fa ba wai tana sona
    bane, ita fa an matsa ma tane, kuma su umma da
    kike zagi na rantse miki masoyan kine. Ta ce
    tokai kana son ummi ne ? Ya dan yi jim, sannan
    ya ce ai dai kin san yanda auran namu da ita
    yakasance bagatatan bai dace ace kinma tsaya
    yin wannan tambayar ma. Tadan yi shiru, zancen
    nan ya shige ta bakamar yanda ta zata da farko
    ba, ko dadin baki zaimata? Sannan ta tuno da
    ranar da fati tazo. Ta labe taji koza suyi
    zancenta sai taji suna ta hirarsu, acikin harar fati
    ke cewa wai kuwa ya kuka kaya ne ummi? Nasan
    yanzun ai kin warke, kema kin goge. Ta ce
    damefa? Fati tace, a'a ki gane mana, batun
    kwanciya. Ummi tace, kin san cewa yaya Abba ko
    gadona bai taba kwana ba? Fati tace kai haba?
    Ummi tadinga yimata rantsuwa, tuno da wannan
    sai bishira ta yarda mijinta ma baya son ummi,
    don haka sai ta saki murmushi. Yace, tunanin me
    ki ke yi? Tace da ina ga kamar dadin baki kake
    min, amma dana tuno naji ummi tana fadama fati
    wai baka taba ko kwanciya a gadonta ba, bare ka
    hada jiki da ita sai na yarda. Abba ya zaro ido, a
    ina kika ji suna zancan? Ta ce, a'a tazo mata
    rakiyane naji suna maganar a soro. Abba ya
    girgiza kai. Bishira tace, kuma da gske hakane,
    yakai hannu yakama nata tafin hannun, wannan
    wani sirri ne tsakanina da ummin. Ynda ba zan
    fada mata komai tsakanina dake ba, haka itama
    zan sakaya nata sirrin, tadai fahimci hakane, don
    haka sai ranta yayi mata dadi har ma ta baiwa
    Abban kanta a daran. Ynda taga yna rawar jiki ya
    tabbatar ma ta ba wani angwanci da yayi, don
    haka zuciyarta fes ta wayi gari. Duk da cewa
    abba ya tashe ta cewa taje tayi wanka harda
    Allah yahadata amma tayi niyar baza tayi hakan
    ba sai gari yayi haske. Ummi ta fito don tanuna
    mata cewa Abba ya kwana da ita. Bishira an dafa
    ruwan tea an kai falo sai wannan rawan kai ake
    yi. Sai data lura ummi ta dauko tsintsiya tasoma
    sharar gidan kamar yanda tasaba, sannan tafito
    da buta aka nufi bandaki, kai ko dankwali babu
    aka yiwanka aka fito. Gashi yna ta digar ruwa,
    ummi ta fahimta kuma tagane cewa tayi hakan
    don ta nuna mata ne. Kuma taji zafi aranta
    kamar ynda bishiran taso, ta amma azuciyar ta
    sai tace na banza jiya nan yakora miki mari.
    Lokacin da abba ya shigo gidan tagama shara
    tana kwashewa, bai ko dubeta baya shige falon
    bishira, kan ummi yasake daurewa, me yake
    faruwane haka da zafi? Ta tambayi kanta. Data
    koma daki tagumi ta zabga tana tunani ita da
    suka yi kaca-kaca ma sun shirya bare ni? Kamar
    tabi shi har falon bishiran ta gaida shi, amma sai
    tafasa. Tazuba ido taga zai bar gidanne ba tare
    daya leko dakinta ba? Sun gama karin
    kumallonsu tsaf yayo wanka don tafiya gurin aiki,
    sai dai kayan dazai saka suna dakin ummi. Ya
    fito yanufi dakin. Ciki- ciki yayi sallama ita kam
    tsoro ne ya tsirga mata, tasake tambayar kanta
    mekuma yafaru? Ta amsa tare da gaida shi. Nan
    ma a ciki ya amsa, yadauki kayan sai dazai fita
    sannan yace ba kya bukatar komai ko? Tayi
    karfin halin cewa sugata ceta kare. Ya dube ta
    furka tsuke me yasa baki fada minba? Ta ce, na
    manta ne, yace to sai kije gurin bishira da dibar
    miki inzan dawo na siyo. Ba kya neman komai da
    rana ko? Tace a'a sai nama kawai ya daga
    murya, kullum ne ya zama dole a saka nama a
    abinci? Jikinta har bari yake don tsoro, ta ce a'a
    yaja tsaki ya fita. Ummi tasaka kanta cikin cinya
    tana furta 'inna lillahi wa inna ilaihir raji'un.'
    hawaye suka soma yi mata sintiri.KI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 11
    ZURFIN CIKI book 4 part 11
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:57
    Dadi tamkar yakashe bishira don tna labe tana
    jinsu afalon ya saka kya yashirya tsaf, sannan ya
    nufo dakinta don dauka jakar laptop dinshi. Jin
    sallamarshi tayi mza tashare hawaye sannan ta
    amsa, yshigo ya dauko dari biyu ya aje mata
    akan gdo, ga kudin maman nan kura, kada fati
    tzo kifada mata baki kudin nama kullum tunda
    har kin iya shaida mta cewa ban tba kwana
    agadonkiba. Kin kosa inkwanta dakene? Yadauki
    jakar yarataya sannan yayi mata wani kallo sama
    dakasa, to banga gurin kwana agadon naki ba.
    Hakanan banga abin kwanciya ajikinki ba, yafice
    yabar ummi tsaye tazaro idanunta cikin matukar
    al'ajabi da kunya. Ina ya Abba yaji zancen nan?
    Kodai fati ceta fada masa? Wata zuciyar tace fati
    baza ta iyayi masa zancan nanba saidai in
    ummarsu tafada mawa ita kuma tafada masa.
    Inko hakane fati batayi mata adalci ba, ai hira ce
    irinta aminta tsakaninsu, gashi ta bata kunya har
    tasa ya Abba naganin tazaku. Tokuwa tasha
    alwashin nuna mishi bahaka take nufi ba, afili
    tace Allah yabamu rai da lpy. Sai kuma tasoma
    kuka. Bishira tafadi kan dadi ashe gara data fada
    masa zancen dataji suna yida fati, gashi yanzun
    yayi mata rana. Lallai labe yayi mata amfani sai
    kawai tasabi 'yarta tazari mayafi tafice makota,
    yau kan tana da labari mai dadi sai yawon raba
    shi take bata manta ko kalma daya. Sannan
    darana tazo tahau kici-kicin dora girki, lokacin
    ummi tafito don yin alwala, ita ko karyawa batayi
    ba don tawuni da takaici ya Abba. Tana kallon
    yanda bishira tazubu kayan miya tana jajjagawa
    batare data wanke ba hancin kawai ta cire. Ummi
    tayi alwala tashige daki, ranar har dare ummi
    bataci komai ba, duk da tanajin yunwa. Zantukan
    abba kawai kemata yawo a kwanya. Tayi kuka
    harta gaji fuska ta kumbura. Tun uku yadawo
    baiga ummi ba, bishira tagabatar masa da abinci
    dakyar yayi cokali uku. Dama yazo dafura, yasha
    sannan yanufi shago, yini yayi yana tunanin
    kamar bai kyauta ma ummi ba, amma yana
    mamakin yanda ummi ta iya cewa bai hau
    gadonta ba. Kenan inyahau din dakuma abinda
    yabiyo bayan hawa gadon duk zata ringa fesarwa
    ne? Kai yafaji haushin abu biyun nan dacewa
    bada sonta aka daura masu auran suba dakuma
    fada ma fati sirrinsu. Saidai duk dahaka zuciya
    da idanunshi suna matukar kewar ganin ummi,
    sai shida yadawo gidan. Ruwan wanka ya diba
    yanufi bandaki, man shafawarshi dasauran su
    suna dakin ummi, don haka yakalli bishira. Bari in
    dauko kayana can dakin ummi kozaki dauko min?
    Tace, bazan jeba kaje da kanka. Tana kwance
    kan doguwar kujera lokacin kanta yana matukar
    sarawa, don kuwa yanda yayi sallamar da kyar
    itama dinda kyar ta amsa. Saidai ita badon
    wulakanci tayiba, saidai don yanda take jin
    jikinta. Yashafa mai tare da feshe jikinsa da
    turaruka. Idanunshi suka sauka kan darinshi biyu
    daya aje mata. Yakalleta, ke ina abincin da kika
    dafa? Batare data dubeshiba tace, bandafa ba.
    Yace sbd me? Tace banjin yunwa, kaikuma naga
    ba anan kake ba, baki ya taba yasa kaya yafice.
    Har tayi sallar isha'i lokacin tasoma jin jiri, amma
    bata da niyar shan ko tea tanajin ya shigo ya aje
    mata ledar ta kusan minta 30 kafin tataso tazo
    tatura kofarta. Sannan taduba ledar, nama ne
    balango yaji albasa da tumatiri, sai sugar da
    madara, nan ta aje su tayi kwanciyarta afili tace
    natabbata kurar kenan indai naci maman nan.
    Bacci yadauketa can kusan ukun dare fa yunwa
    fatakai yunwa, kowa yasan yunwar dare yanda
    take jigata bawa, a gigice ummi ta tashi tahada
    tea tahau sha da gaggawa. Tagama kamar taci
    naman sai kuma tafasa ( tamiko min ninkuma
    nayi fuska nacinye au namanta madawani azumi
    lolx) ta kauda kayan ta koma ta kwanta, aikonan
    fa cikinta yahau hautsinawa. Dagudu tatashi
    tanufi fita tana bude kofa kafin takai bandaki
    tasoma sheka amai, tun bude kofarta abba
    yafarka dasauri yafito. Riketa yayi ganin yanda
    take sheka amai kamar zata amayar da hanjin
    cikinta, sai sannu yake mata. Data gama yajanyo
    ruwa ya wanke mata fuska ta kuskure baki.
    Yawanke gurin gurin tana gefe tsugunne, cikinta
    da kanta sai ciwo sukeyi tana mikewa sai jiri.
    Nan tafadi ragwaf, shine yadauketa tamkar ya
    dau jaririya don rashin nauyi yace duk kece kikayi
    makanki sanadin wannan matsalar. Don kina
    fushi saiki yiwa abinci yaji, ai gashi nan kema
    kina ji ajikinki, kan kujer yadorata ya cire mata
    siket din atamfar dake jikinta, don duk sun jike sai
    na ciki. Yajuyata zai zage mata zif din rigar tana
    son ta hana amma bata dawani karfin hanawa.
    Tanaji tana gani abba yacire mata riga, gashi ko
    best bata saka ba sai breziya. Takai hannuwanta
    tarufe kirjinta. Shikam ganinta ahaka yasa tsigar
    jikinsa tashi, tun daga karamin yatsansa har
    tsakiyan kansa ruf da ciki ta juya tayi, shi kuma
    ya kunna mata fanka yafita. Zaune ya samu
    bishira atsakiyar gado, ta kalle shi da tuhuma, me
    kaje yi dakinta? Yce amai naji tanayi shiyasa
    nafita, bta dlpy ne, tsaki taja sannan ta kwanta.
    Shi kam bai runtsa ba, kunnanshi da hankalinshi
    suna can, dga bisani madayaga baccin yaki sai
    yatashi yayi alwala yasomayin nafila. Dazai tafi
    masallaci yske lekawa yaga IKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 13
    ZURFIN CIKI book 4 part 13
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:05
    shikenan yanyun bata dawani aji agurin Abba
    ummi da tsoron allura sam taqi tsayawa jiya ma
    don agalabaice take Nurse din tace ke dai
    shagwaba ta miki yawa A ce allura ma kin kasa
    tsayawa kefa mace ce Wata rana ma haihuwa
    zakiyi ummi fa taki tsayawa nurse tazo tace ma
    Abba taki tsayawa abba yaleka dakin allura
    menene haka ummi tsoron alluran ki yayi yawa
    kitsaya mana Tadube shi fuska a shagwabe ya
    Abba dazafi nikam na hakura da allurar nan Abba
    ya shiga dakin ya kalli nurse din zo kimata ba
    zanyi asarar kudina ba Ummi bata ankara basai
    jinta tayi atsakiyar kirjin Abba shi kanshi sai jin
    wani abu yayi yataso daga tafin kafarshi zuwa
    tsakiyar kanshi Har yayi baya dasu tamkar zasu
    fadi to bare ummi wadda jikin nata ya dauki rawa
    Ya kalli nurse dinda idanuwanshi wadanda suka
    canza kala nan da nan zo kiyi mata Yadaga
    hajabinta tare dazame zanin daidai inda za ayi
    mata allurar shigar allurar ta saka ummi cewa
    wash tare da sake makalewa jikin Abba Don kuka
    tasaka wanda daga jinshi kasan shagwaba ce
    zalla ya lumshe ido lokaci daya ya kuma budesu
    nurse din tace kai ke kam kin cika shagwaba
    Abba ya dora yatsunshi guda adaidai gurin da
    akayi allurar yana murza mata tare da rada mata
    'sannu' akunnenta Rekicewa tayi sannan ta
    kwace jikinta daga gare shi wani yanayi ta tsinci
    kanta mai girgiza bawa Ya sauke ajiyar zuciya
    sannan yace mu tafi suna cikin mota dukkansu
    sunyi shiru Abba kasala ce da muradin matar shi
    yasa shizama hakan Ita ko ummi mamakinta ba
    yau Abba yasoma taba jikinta ba can baya yasha
    rike ta yazane ta, yasha rungumeta ayi mata
    allura, bata taba jin irin abinda taji yanzun ba Ta
    jingina da kujera tare da lumshe ido sai take ta
    tuno yanayin dataji lokacin daya mannata
    ajikinshi. Tsayawar motar ne ya sata bude
    idanunta, azatonta gida suka zo,sai taga ashe
    gurin kayan kwalama ne Ya kalleta, ina zuwa Ya
    fita ya nufi zuwa ciki jim kadan ya fito da ledoji,
    kaji ya siyo da madara mai tsafta, har da
    kankarar dayaji tana tambayar umma yasai
    musu. Tace, gama fa kankarar umma tasai mana.
    Bishira ta cika fam don takaici, kamal kaninsu
    Abba yaduba mata ko ummi tana gidan umma, ya
    fada mata bata nan. Ta tabbatar suna tare, ta
    cema umman bashir tunfa safe suka fita tare
    umma tace tun safe wane iri? Tace wai bta da
    lpy yaje kaita asibiti Umman bashir tace Allah ya
    tashe mu lpy Goben nan zan tafi kauye dama
    gobe ta ce indawo gaje 'yar bori, ina fada miki
    ummi dakanta zata bar gidan basai ance mata
    ba. Bishira tace dahaka zata faru zanfi kowa farin
    ciki, umman bashir tace kece aida shegen kyamar
    'yan kauye bakison mutane Matsalarki kenan da
    ace zaki jure muje tare kiyi kwana 2 'yar bori da
    bokan tsauni zasu cika miki aiki Bishira tace
    zanje umma. Biyan bukata ai yafi dogon buri
    umma tace taki turo minshi ince masa sha'ani
    zamu don kada yace zai hana, bishira tace to.
    Sun sameta agidan ummi tayi dakinta da ledar ta
    shikuma yashiga gurin bishira. Ranar daya dawo
    dakin ta kuwa tayi kyau cikin doguwar rigar
    shadda ruwan kunkumadi, tun yana kallon ummi
    asace harya kasa dauke idonsa Ummi talura ta
    birgeshi sosai don haka tazauna bakin gado tana
    fuskantarshi hira ce suke yi jifa- jifa itace ma
    tasoma sako zancen Ya Abba zance ma alhaji
    yasai min TV nagaji dazama shiru Abba yace a'a
    banason haka ina sane zansai miki, tace to
    Bishira dake labe ta girgiza kai aranta tace ashe
    za ayi bala'i duk randa yakawo TV ai itama ai
    iyayenta suka sai mata. Tace to yaya abba
    inason makaranta ya aje laptop din daya soma
    budewa yamaimaita kalmar makaranta? Ta ce eh,
    yace sai nayi tunani Ummi ta marairaice tunani
    ya Abba? Kai dakake son inyi karatu? Yace
    shikenan haka sukayi ta hira har lokacin
    kwanciya ummi tayi shafa'i da wuturi tayi shirin
    baccinta takwanta Abba yau yakasa nutsuwa
    tamkar yaje ga ummi, amma girman kai ya
    hanashi. Ranar sama-sama yayi bacci sau biyu
    yna fita yana watsa majikinshi ruwan sanyi kozai
    dan samu nutsuwa. Har lokacin daya tafi gurin
    aiki bashi da wani kuzari. Ranar fati tazo lokacin
    bishira ta tafi badadinta, ummi tahau fati
    damasifa tare da fada mata yanda sukayi da ya
    Abba. Fati ta rantse tamaya kan cewa ba wanda
    yasan zancen nan don bata fada ma kowa ba,
    sukayi ta tunanin ta ina ne zancan nan yafita?
    Fati tace to ko kiyi hankali koda Anty bishira tana
    miki labe? Ummi tayi shiru tna nazari, can tadubi
    fati Bazan zargeta ba, domin ban taba ganinta ba
    amma zansa ido fati tace gara kisa kam yanzun
    harzuwa yau baku sasanta ba? Ummi tace aini
    bana bukatar sasantawa dashi tunda yace baiga
    gurin kwanciya agadona ba Fati tasaka dariya ke
    dai kada kicika baki,ummi tace kedai mu bar
    wannan zancen inbaki kudin kayan don Allah?
    Tati tace kibani dan bnida matsala mijina she ne
    yakaini nasai nawa zance yakaini insai miki
    kinason wanduna Ummi tace kinjiki da siket zaki
    debo min Ai har gajerun wanduna ki kwaso min,
    wulakanci zanyi a gidan nan.vels / ZURFIN CIKI book 4 part 15
    ZURFIN CIKI book 4 part 15
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:12
    Saidatayi sallah sannan tazauna gaban madubi
    duk da shirin bacci take yi Saida tashafa manta
    da hoda sannan tadan goga jan baki. Tafesa
    turarenta ta isa gurin kayan baccinta dake cikin
    dirowar dora akwati, ta dauko duguwa tazira
    sannan takama karshen kitsonta tahada su guri
    daya ta tufke. Zata ha gado yace, ga nama kizo
    muci. Ta fada gado tare da jan filo ta dora kanta
    da kirjinta sannan tace nama saikace wata kura?
    Dazun fana danci amiyar danayi. Yace nida na
    siyo shine nazama kuran ko? Tace, a'a ya Abba
    kaine ranar nan naji kace kura. Kullum ake cin
    nama? Yayi murmushi aranshi yace, ok nan na
    rama ne kenan, sannan yace toshi kenan bari in
    ajiye miki naki. Nan tayi kwanciyarta. To 'yar
    gidan tsohuwa, yafada danufin zolaya, tace kai
    kuma dan gidan ummanka. Cigaba yayi dashiga
    yanar gizonsa, ita kam a gajiye take bacci
    yasoma fizgarta. Lokacin dayazo shima ya
    kwanta akan gado, ta bude ido lpy Yaya Abba?
    Ya dubeta tsakaninsu mutum daya zai iya
    kwanciya. Wace irin tambayace wannan mutum
    da dakin matarsa da gadonta atambaye shi lpy?
    Tatashi zaune, gani nayi ba guri agadona, yayi
    shiru, wato ummi bata barin bashi, ta tsura mishi
    ido tana jira jin mezaice. Yatashi zaune, idanunshi
    akan lebunanta, toni dai ga guri na samu, ta
    sulale itama takwanta rigingine tare dajan bargo
    tarufe rabin jikinta. Shima hakan yayi, ummi
    fargaba ce tasa tanemi bacci tarasa, shikam
    addu'ar bacci yakaranta sannan yashafa
    yalumshe idanu. Duk su biyun bacci sama- sama
    sukayi koda Abba baisamu nasarar kama kayan
    ummi ba amma aranshi yace wannan sharar fage
    ce. Dasannu za'a kai ga muradi, ko washegari
    daya kwana adakin dai bawani cigaba sai sake-
    sake Abban yayi tayi azuciyarshi, na cewa
    yakauda wata kunya ya fito mata amutum, amma
    yakasa hakan. Musamman yanda yaga ummin
    tana da shegen wayo, ba kamar yan yazata ba.
    Sannan gashi ta iya yin ado irin na tsokana.
    Hakan yasa duk ranakun girkinta Abba yana
    zumudi amma yakanyi kwanan rashin sukuni.
    Wata jumma'a tsohuwa ta riski ummi da irn
    wannan shiga tariga da gajeren wando, ta kawo
    mata ziyarar data saba inta dawo masallaci.
    Salati tasaka tare da cewa, yarinyar nan kece
    haka kinzamo sai kace arniya? Ummi ta tashi
    tsaye tayi juyi tare da cewa. Ynzun tsohuwa ban
    birge kiba? Ta ce kitson naki ne kurum yamin
    kyau, amma wannan shiga dame tai kama? Kuma
    shimai sunan malam yakasa hanaki koke ma
    yasoma tsoron nakine? Ummi ta tuntsure da
    dariya, ba tsorona yake jiba, shine ma yake son
    kayan don shine ma yasai minsu. Tsohuwa tace,
    oho! Eh lallai ta mike Allah ya taimaka, duk abin
    ku dai baza ki koma baturiya ba, ummi tace oho
    dai ke dai kuma baza ki iya wannan ba. Tace,
    Allah ya tsare nida wannan shiga, ummi ta dauko
    dari biyu ganin tsohuwa ta mike, nizan tafi in dan
    zazzaga in ziyarci jama'a. Ummi ta kama
    hannunta ta saka dari biyun, gana goron
    jumma'a, Allah ya hadamu aladan ziyarar. Suka
    fito tana cewa. Ke kullum nazo sai kin bani kudi
    ummi, to Allah ya shi muku albarka, Allah kuma
    yasa ki sauko lpy. Murmushi ummi tayi duk 'yan
    gidan su kallon mai cike suke mata. Duk hirar
    nan tasu bishira najinsu, ta cika tayi fam. Dama
    Abba yana kwana da ummi? Ashe shine yake sai
    mata kananan kaya? Ashe har tana da ciki shine
    yamata karyar cewa baya sonta? Tana dawowa
    raka tsohuwa, bishira ta kalleta, karamar yarinya
    ta iya karuwanci, dube ki. Ummi ta kalleta babba
    fa ya rike girmanshi inba haka ba inhau in taka,
    kuma niba karuwa bace, kema kalle ki. Ta taso
    zan zane kifa? Ummi ma tadaga murya. Sai kace
    wata 'yarki? Ba ki isa ba. Bishira tazo zata
    shakota, ummi ta daka tsalle taja baya. Karki
    sake ki taba ni. Nan fa gidan ya kacame, bishira
    sai ashar take zugama ummi, tana kiranta 'yar
    matsiyata. Ummi tace, banga kamannin masu
    arziki ba a jikinki, nan makota suka shigo yin
    rabo. Ummi ko tana fada mata take ramawa, abin
    da yafi yiwa ummi ciwo datace ummanki
    matsafiya, nasan komai saboda bakin asirinta ne
    sahabi yafasa aurenki aka mannawa mijina. Don
    shima ya fada min ba ya sonki, har yanzun bai
    taba kwanciya dake ba. Ummi tace, kazama mara
    sallah me labe, kina labe min akofan don bakin
    kishi, kuma insha Allahu sai Allah yasakawa
    ummata tunda kika ce tana asiri. Maman amir
    kawar bishira tuni taruga takira umman bashir,
    sai dai cikin sa'a tanazuwa Abba nayin parking.
    Ganin yanda mahaifiyarshi tashiga gidan cikin
    hanzari haka shima agurguje yafada gidan, ranshi
    yayi mugun baci yanda yaga gidan cike da
    jama'a. Ga bishira mutum biyu sun rike ta tana
    zambarmar asake ta ta lallasa ummi, ga ita kuma
    ummi tsaye akofarta kanta babu ko dan kwali ta
    sha gajeren wando ya dan gota gwuiwarta da 'yar
    riga tana maida martani. Yace ma matan dasuka
    rike bishira, ku saketa suka sake ta ya daka mata
    tsawa da karfi, duk ku fice min daga gida,
    magulmata tunda duk yawanku kun kasa sasanta
    su. Sum-sum suka wucesuna tabe baki, duk
    dahaka bishira bata daina magana ba.ZURFIN CIKI book 4 part 16
    ZURFIN CIKI book 4 part 16
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:14
    Haka umman bashar batasan yarda komai ya faru
    ba. Amman ta shiga zagi da tsine ma ummi har
    da ce mata karuwancin ne ya motsa, ai dama
    nasan tun kafin kixo gidan nan kinsan maza.
    Bishira ta ce umma wllhi ga babban mai laifin
    nan, muna funtata sukeyi duk ire ire wadannan
    kayan na jikinta shiya sai mata su, ni bai siyo
    min ba. Na gaji da hakuri ana cutata gwara
    yaban takarda ta. Umma tace daina fadin ya baki
    takarda insha allahu saidai ita ya bata, Abba
    yayima bishira wani kallo tare da cewa ki tafi
    mana sai me? Yarda kika gaji da ni nima Haka na
    gaji da ke, ya kalli ummi yace ke kuma mi nake
    fada maki kullum? Itama cikin fushi tayi magana
    toh shikenan saita ta zagina tana ma ummata
    sheri don ita kake so? Bishira ta cafke dama ai
    ya fadaman baya sonki. Ummi ta kalleshi ko zai
    kare kanshi, amman baya kokarin Haka saima
    kara zaro mata ido da yayi yana cewa. Ni kike ma
    ihu ummi? Zuciya tazo mata wuya nata ganin an
    daketa ne kuma an hanata kuka. Shi kanshi ya
    tozarta ta da ya fadama kishiyarta baya sonta.
    Duk da tasan da haka ta kalli bishira cikin daga
    murya tace, an fada maki na damune don baya
    sona bana son ya soni don nima bana son Shi....
    Mari Abba ya sakar ma ummi da bayan hannu,
    kalmar da ya tsana kenan, zafi yakeji a Zuciyarshi
    ko tunowa yayi da ummi bata sonshi. Daki ummi
    ta fada, ta fada kan gado tana kuka, ya kalli
    bishira kije gidan ku sai nazo, umman bashar
    tace ba inda zataje kuma in ka sake na samu
    labarin ta tafi saina debe maka albarka. Tasa kai
    fuuuu ta fice, tunda ka dauki hukunki mai kyau ka
    duki marar kunya ai naji dadi. Bishira ma taji
    dadin haka, Shi kuwa ba don su yayi ba zafin
    furta bata sonshi ne yasa ya daketa. Yana shiga
    dakin ummi lokacin ta mike tana kuka, ta dauko
    zane ta daura tana kuka sosai. Ta zari hijabi ta
    zura zata fita, yace ina zaki? Taki sauraronshi
    zata fita ya rikota, ina zaki nake? Tayi magana
    cikin daga murya cikin muryar kuka tace gidan
    ubana kai kuma ka zauna da warda kakeso,
    tunda ya mareta nan ya gane bai kyauta mata ba,
    don yasan ba dole bane ta fahimce Shi, sai ya
    samu kanshi da jawota ya rungume. Duk da suna
    cikin bacin rai Duk kansu saida sukaji wani irin
    yanayi. Yace kada kiyi yaji ummi kinsan dai koh
    kinje su umma fada zasu maki. Cikin sanyin
    murya yayi maganar, kan ummi ya sara, ta kwace
    daga jikinshi ta sake fadawa kan gado. Sabon
    kuka ta saki, ya zauna bakin gado ya kamo
    hannunta ta sarke ya tsunshi da nata ya dan
    matsa, ummi! Ummi!! Tashi kiji, cikin kuka tace
    mi zanji yaya Abba, kawai ka rabu dani, ni baka
    man adalci ba. Ya za'a yi kaje kana fada mata ni
    baka sona kasa tana man gori, umman bashar
    harda ceman wai ni nabi maza. Ya sake kwantar
    da murya yace ki yarda ni ban fadama bishira
    cewa bana sonki ba, kuma batun umma kisashi a
    gefe kawai don ni nafi kowa sanin halinki. Nafi
    kowa sanin tarbiyar umma na... Duk da haka ai
    baka kare kanka ba lokacin da take fada ba,
    ummi ta katse kiran da yake mata, yasan ummi
    sarai yanzu kam bazata saurari komai ba, koma
    ta saurara zata ta kalubatanshi ne, don haka sai
    yace to Tashi ki bani abinci. Kin Tashi tayi don
    kanta jinsa take kamar ya fado, mi kewa yayi ya
    fita, ya rasa sukuni, koda yaje shago kasa yin
    komai yayi, sai murza hannunsa da ya mari ummi
    yake. Ya ciro wayarsa ya kira ummin tayi ta
    ringing kusan sau 3 kafin ummi ta daga yace
    haba ummi, inata kira kayi banza dani? Shiru dai
    tayi bata tanka ba, ummi cikin disashiyar murya
    tace, dama haka ne, sai an kwance ma mutum
    zane kasuwa azo gida ace za'a daura masa. Sai
    ta kashe wayar. Daga nan gidan umma ya nufa,
    tace anya Abba lafiyarka kuwa? Naga Duk ka ya
    mutse. Ya zauna suka gaisa yace umma ina fa
    lafia, dazun bayan sallar jumma'a ina iso wa gida
    da yunwa sai kurum na samu gidan tam d
    jama'a. Ummi da bishira na tarar suna ta zage
    zage har aka samu wata shedaniya taje ta kira
    umman bashar. Umma tace subhanallah! To ya
    akayi yanzu? Yace tarwatsa taron nayi, nasan
    koda ban tsaya bin bahasi ba ummi ce mai
    gaskiya. Domin bata kula bishira, Duk yarda akayi
    ta kure ta ne. Tsohuwa daga can gefe tace, wai
    bayan zuwa na gidan sukayi fadan? Abba yace
    oho ni ban masan mafarin fadan ba. Umma tace
    kai wannan abu allah ya dai dai ta maka su.
    Amman kyanshi kana zuwa ummin ya kamata
    kayi wa fada, koma ka zane ta, don itace karama.
    Abba har suna hada baki da Tsohuwa gurin fadin
    "Haba dai". Abba yace umma in itace da gaskiya
    kuma ai na zalinceta, yanzun da haka fushi take,
    Duk na tsorata bana son fushinta, sai taki cin
    abinci. Don allah umma bari in kira maki ita ki
    bata hnkr, umma tace ba zan bata hnkr ba, abinci
    kuwa kada allah yasa taci. Sai dai ayi tunanin
    abinda ke cikin ta, Tsohuwa tace, wannan
    sakaryar matar taka dama na lura fada takeji.
    Sanda nayi sallama tana zaune amman amsawa
    ta gagareta, don haka ma ko gaisheta banyi ba
    na wuce. Ita kuma takwara ka hanata saka
    wadannan kayan na arna. Abba yace, su ake yayi
    Tsohuwa, Tsohuwa tace, tafdi lallai yayi ya zama
    banza. Abba yake cewa Don allah umma ga nmbr
    bari in saka maki a waya, ya dauki wayar umma
    ya saka mata lambar wayar da ke hannun
    ummin, yace umma na roke ki lallasheta ba wai
    fada zaki mata ZURFIN CIKI book 4 part 17
    ZURFIN CIKI book 4 part 17
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:17
    Duk jumma'a abba yana dawowa gida
    musamman in ranar girkin ummi ne don cin
    abinci na musamman. Jumma'a biyu kenan bata
    fado kanta ba sai wannan, don haka tun alhamis
    taje ta yarfo kitsonta, ta biyo ta gidan su gurin
    tsohuwa tazo. Don haka suna gaisawa da umma
    tace gurin tsohuwa nazo. Suka shige daki tace da
    tsohuwa nazo ne indan samu dan wani sirrin.
    Tsohuwa tace, name ummi? Ta ce na gyaran jiki
    mana. Fati tace min kwanaki kin fada mata wasu
    abubuwa. Tsohuwa ta ce, ja'ira, kinga uwar bari?
    Dama nace zaki same ni ina kyakkyawan zamana,
    bada ina fada miki kina sharewa ba? Ummi tace
    haba tsohuwa banaso aji mu yanzun dai ki bani
    shawara sannan ki fada min abinda zanyi inja
    hankalin mijina. Ta ce, toda farko ki dinga kula da
    jikinki ta hanyar rufe shi ruf, kada kibar kofar
    iska. Banda tafiya ba takalmi, iska tana shiga
    tanan kuma mace narage ni'ima banda zama ba
    dankwali inso samu ne hatta tsarki ki daina yi da
    ruwan sanyi, ki dinga yida ruwan dumi. Sannan ki
    amshi bagaruwa gurin ummarki ki dinga shiga
    inkin tafasa da alif dakuma saiwar mata, sannan
    inkinyi al'ada kin gama kinyi wanka toki dinga
    matsa farin miski a ehem dinki. Sannan ki samu
    saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,
    mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari
    dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi
    biyu safe da yamma. Sannan ki aya garinta,
    kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,
    sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar
    ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai
    ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,
    citta, lemun tsami, ki markada su kisha. In anan
    maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum
    daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta
    musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban
    da dukkan sauran mata. Ki hada da biyayya
    tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi. Ummi
    tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin
    nan? Tace, bari zanba matar ado dake yawan
    zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu. Amma
    su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya
    siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin
    ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.
    Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje
    gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi
    tasan duk wadannan hadin matan? Tun ranar
    alhamis din ta soma aiwatar da darussan da ta
    debo daga tsohuwa, safiyar jumma'a ranar zai
    bar dakin bishira. Ya fito tana sharar tsakar gida
    ta gaidashi, ya amsa da fara'a, tare dawani kallo
    mai fassarar in ba keba. Cikin muryar data adana
    don shi kadai tace, ya abba ina son in je ayi min
    zanen fulawa. Yace jiya kin fita yau kam a'a.
    amma ki aika akira mai zanen tazo ta miki. Ta
    marairaice, towa zan aika yaya abba? Yace aike
    ni, ina ne gidan? Tace layin su umma ne yace to
    za'azo ai miki. Bishira tafito daga daki tazabga
    ma ummi harara, Tare dacewa kisisina. Abba
    yakalleta, kema sai tayi miki. Tace bana bukata,
    aikin banza, shikam yafice. Ummi kuwa tace gaba
    da aikinta, ita ko sai tasa kujera tazauna tana
    sakin zantuka, eh don kwalliyar tabanzanta tunda
    ba a iya biyawa miji bukata. Allah dai yasa ya
    fada min komai, to ni me zai dame ni don 'yar
    aiki kawai na dauki yarinya. Tashare min gida,
    tayi wa mijina abinci, daga nan fa? Saita saki
    shewa, ummi ta ce aranta yau zan bambance
    miki. Birabiskon shinkafa tayi da miya, ta wadata
    birabiskon da kayan lambu, miyar ta dauki nama
    da bushasshen kifi. Sannan ta hada musu kunun
    aya yaji dabino da madara, ta aikawa ummanta
    lokacin da kamal yazo daukar na ummarsu.
    Tasheka wanka taci doguwar rigar shadda koriya
    mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau ne daurin
    aurensu. Ga fulawar da yaje ya biya akazo aka
    zana mata. Tanajin rigimar muhibba tafito tazuba
    mata adan kwano tazaunar da ita akofar falon
    mamanta. bishira tafito kicin baki tasaki tana
    kallon ummi da tazo wucewa harda bangazar
    ummi, nan ko kamshi ya bude ta na turarukan da
    ummi ta fesa. Abba yana yin sallama ummi tafito
    da sauri, oyoyo yayana, bishira tana daga kicin
    dinta tana kallon su. Ummi ta rungume shi,
    sannu dazuwa sahibina. Ta amshi ledar
    hannunshi dajakar, yace yauwa sannu babyna
    tace inazan kai ledar? Yace akwai ta bishira aciki
    ki ciro. Ta mika mishi ledar ta wuce dajakar
    dakinta. Ya mika wa bishira lemo da abarba da
    yayo musu tsaraba sannan ya wuce danasu,
    awulakance ta aje. Yana shiga ummi tadan karo
    kofar yanda bishiran zata iya lekensu sosai ta
    gefen kofan. Ta cire masa hula ta aje akan
    madubi sannan ta kunna fanka. Ta shirya masa
    abinci, yauni zan baka har ka qoshi. Haka suka
    yita baiwa juna abaki har suka qoshi. Yakamo
    hannunta mai qunshi yana ta sumbata, wai kamar
    kada su goge. Kumatun shi ta shafa nima yau
    kamin kyau, koda yake dama kai me kyaune, ina
    sonka ya abba sosai. Cikin jin dadi ya mannota a
    jikinshi, nima ina sonki, ina manta kowa da komai
    in muna tare, tace ina tsoron kada wata rana ka
    juya min baya. Ya saqalo hunnuwansa cikin nata
    ina fata in mutu kafin lokacin. Ummi tasomayi
    masa wasu irin darussa wadanda tasan yana
    saurin tada sha'awarshi nanda nan kuwa tasa shi
    fita hayyacinsa yakama surutai. Ummi ta tabbata
    bishira tana wurin ta labe, don haka tai murmushi
    ta bishi suka tafi duniyar ma'aurata. Bishira
    tamkar tayi hauka sai kawai ta fado dakin tana
    fadin, maciya amana, har yanzun ba afita daga
    lokacin girkina ba munafiki. Abba ya tashi sannan
    yaja riga yasaka, ok dama kina labewa ne kiji
    sirrinmu? Da taga ya sauko da zafin rai saita
    gudu dakinta. Yabita yamata tatas, kuma ya fada
    mata cewa tazo ta shiga dakin ta zauna ba labe
    ba, yanzun zai komane yaci gaba daga inda ya
    tsaya. Tayi ta kuka gashi ba damar zuwa gurin
    umman bashir dole ta tafi gidansu. Shi kam abba
    shareta ya yi kosu umma bai fadawa ba. Sabuwar
    soyayya ma ya balle agidan, su ci abinci tare,
    wanka tare, su fita yawonsu a qafa ko amota. In
    yana gurin aiki bini- bini ya kira waya, ita kuma
    ko yaushe cikin kirkirar girki da kwalliya tare da
    dadadan kalaman dazata fada masa take.ZURFIN CIKI book 4 part 18
    ZURFIN CIKI book 4 part 18
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:19
    Ummi tayi alalar gwangwani ta sauke kenan sai
    ga aunty farida da yake tunda akayi auren ummi
    batazo gidan ba. Har daki ummi ta shiga suka
    gaisa tayi masu addu'a zama lafia, tayi mata
    nasihar zama da miji. Umman taji dadi tare da
    kwadayin ina ma bishira take da halin yayarta, ta
    zuba alala ta kaima aunty falon bishira. Ta isko
    su tana mata fadan kaxanta, cikin murna aunty
    ta anshi alalar taci bishira ta cika fam. Tun tana
    jurewa har tace aunty ai kin zubar min da kima,
    ya ya za'a yi ki anshi abun kishiya kici. Aunty ta
    kalli bishira fuska daure tace ke da ita akwai
    bambamci ne? Bishira tace aunty bambamci ma
    nifa jininki ce ita fa? Aunty tace a musulunci fa?
    Bishira ta hade rai tana kallon aunty, taci gaba
    da cewa, A musulunci tama fiki don tana sallah,
    Haka nima ina sallah, kefa kin faru? In kin soma
    sallar to kin shigo cikin mu ni da ita. Domin
    addinin mu ya nuna muna dukkan musulmi dan
    uwan musulmi ne. Inji mai tsira da aminci. Haka
    zan iya cin abincinta banci naki ba don bakida
    tsafta. Ta daka mata tsawa tashi don allah
    malama kije kiyi wanka, ki wanke duk jirwayen
    nan naki kafin In daukeki da motata. Da zasu tafi
    har kudi aunty farida taba ummi, ummi kam
    godiya ta dinga yi. Haka nan da abba ya shigo ta
    nuna masa tace ai abba ya ciri tuta a zuri'arsu,
    halin mahaifinsu ne da ita. Wata rana aunty ta
    bugo ma abba waya cewa aisharsu ta haihu don
    allah ya fadama bishira koda ya iso gida ya fada
    mata nan ta shiga murna. Washe gari tace zata
    gida tama mahaifiyarsu barka. Sannan taji randa
    zasu abuja wurin aisha. Yace ta shirya ya
    sauketa, ta samu aunty tazo nan dai sukeyi wa
    juna barka, mahaifiyarsu tace dubi yar uwarki sai
    yanxu ta haihu gwanin shawa. Amman kinje kin
    gwarje miji ma yayi maki kishiya, dubeki kamar ba
    yar gidan nan ba. Aunty tace mummy ai ita taso
    ta zama Haka, tunda kaxanta ce sana'arta.
    Hajiya zainu tace ni wani lokacin bana ganin
    laifinta a kaxanta, don a gida bata saba aiki ba.
    Laifinta daya a gurina wannan abba data nace ta
    aura, data tsaya ta gama karatunta ta auri wanda
    zai dobo mata yan aiki komai saidai ayi mata
    tana daga zaune, amman ta likema talakan tela
    wanda bashida ko sisi. Aunty ta katse mamarsu
    da cewa In tana da yan aiki shine har wanka
    zasuyi? Ta cire dan kwalin dake kan bishira kalli
    fa mummy har kanta zasu wanke mata. Mummy
    tace aiki gida ya mata yawa, yaushe har ta gyara
    jikinta? Aunty tace kawai mummy kina goyon
    bayanta ne. Bishira tace aunty mummy ta
    fahimta kece baki fahimta ba saboda kina da yan
    aiki. Mummy tace duk ba kece kika yima kanki ba,
    ga kishiya an maki, bishira ta tabe baki nima duk
    nadama ta isheni. Kuma shi da matar duk bana
    raga masu. Don ban damu ya sakeni ba, yaji ne
    dai nace na daina, daddy ko nazo cin mutuncina
    yake gabansu. Mummy tace kin man dai dai.
    Haka yake bishira kullum cikin tsokanan hayaniya
    da ita da miji ko kishiya. Amman ummi yamxun
    bata kulata Domin umma ta gargadeta. Bishira
    bata bar gidan ba saida mummy ta zugata
    Sannan tace mata jibi kizo za a kai su innarku
    yin barka abuja kije ki dan huta kafin suna.
    Bishira tace daman ban taba zuwa ba, ko anyi
    suna sai na huta. Aunty tace kada ku yanke
    hukunci ba tare da sanin mijinki ba kije kiji ta
    bakinsa. Bishira ta ce ina ruwana da yardarsa
    aunty. Haka kuwa data dawo ta shiga tattaro
    kayan ta dake jibge a gefen gadonta, don ita zane
    ko yau a aka dinka shi In tasa ta cire duk In da
    tayar kafin ta dauke shi yaji jiki. Wani ma saita
    goge ruwa ne, kamu ne, duk kyan zani saita goge
    tsakar daki dashi. Ranar dama abba dakinta
    yake, tace mashi jibi zamu abuja Inji mummy.
    Taso ya dan sai mata zani sabo wanda zata
    danci suna ya dinka mata. Yace akwai wani leshi
    dan sai maku yana shago, Tun wancan satin
    naso In zauna In dinkashi da kaina don mai tsada
    ne. Tace nawa ka siyeshi, yace dubu biyar ko
    wane daya, bishira ta tabe baki. Na zaci zakace
    sha biyar wai dubu biyar, yace matsalata da ke
    rainuwa yace bari zansa a dinka maku gobe ashe
    sunan har yazo? Tace a'a jiya pha ta haihu, ya
    sake kallonta jiya? Shine zaku tafi jibi? Tace eh
    mummy ce tace mu tafi jibi. Yace a'a kibari sai
    ana gobe suna kije. Kafin lokacin ma na samu
    wasu kudi da nike sa rai. Sai na sai maki kayan
    barka zanen maman da kayan baby. Bishira ta ce
    gaskia gobe zamu tafi, In ka sayi kayan barkar ka
    aika dasu can wurin mummy yan tafiya Ranar
    suna su kai mata. Abba yace nifa ban amince da
    tafiyar nan gobe ba. Ban yarda ba. Bishira ta ce
    ba wai ina neman yardarka bane, ina fada maka
    umurnin da mummy ta bani ne, ko ka mance
    mahaifiyata ce? Mamakinta ya cika abba, yace
    mahaifiyarki ita zata baki izinin tafiya ko ni?
    Umurnina da nata yanzu wanene...? Bishira ta
    katseshi kada kayi ganganci hada kanka da
    mahaifiyata, ita ta haifeni ta raineni har ka ganni
    kace kana sona Sannan ka dinga kokarin
    kwatanta kanka da ita? An fada maka kowa
    baisan darajar mahaifiyarsa ba irinka? Abba ya
    mike ni ne bansan darajar mahaifiyata ba? Tayi
    shiru yace nagode Kuma suna na hanashi ma
    gaba daya. Zan gani Kuma Bishira ta ce zako ka
    gani.ls / ZURFIN CIKI book 4 part 19
    ZURFIN CIKI book 4 part 19
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:14
    Duk ummi tana jiyo su amman bata fito ba, tana
    ta mamakin yarda bishira batasan darajar
    aurenta ba, bare tasan girman miji. Ranar da
    zasu tafi kuwa ko a jikinta ta dibi tsummanta ta
    nufi gidan su, Duk ta fadama mummy yarda
    sukayi. Mummy tace kinman dai dai talakan
    banza shine zai hada kanshi dani, tafiya zakiyi in
    yaso in kika dawo ya ce baya auren. Abba ya
    dawo ya samu dakinta a rufe, ummi na daka
    sakwara a kofar dakinta yace ina bishira? Ummi
    tace ina ga ta fita, don ina daki bansan fitarta ba.
    Ya daga waya ya kira aunty yace bishira tazo?
    Aunty tace bata fada maka zasu tafi abuja bane,
    Abba yace ta fadaman amman nace a'a sai ana
    gobe suna zataje, ya kwashe komai ya fadama
    aunty. Aunty tace kayi hnkr don allah idan ta
    dawo da kaina zan hadata da daddyn mu, Abba
    yace kiyi hnkr aunty na gaji da halin bishira inga
    wannan karo gwara kowa ya huta ni da ita. Aunty
    tace kayi hnkr Abba yace sai anjima ya kashe
    wayarsa. Zama yayi kan kujera dakin ummi yace
    gaskia wannan karo bazai fadawa kowa ba ya
    gama auren bishira. In bai nuna mata kurenta ba
    nan gaba zata masa abunda yafi wannan don
    Haka yabar komai sai ta dawo. Ummi kam
    batason ya rabu da matarsa, amman kam saida
    taga tarairaya cikin kwanu kan nan matsalarsu
    daya, Abba yace ummi kodai asibiti zamuje ne,
    ummi tace muce masu mi? Yace muyi masu
    bayani mana, ummi tace a'a. Yace to muje mu
    fadawa umma, ummi ta zare ido yanxu sai kama
    umma wannan zancen? Yayi murmushi. Ai da zan
    iya mata wannan maganar da tuni na mata,
    asibiti ma abunda yasa banson zuwa sai likita ya
    bukaci ganin wurin. Ni kuma ina kishin wani
    namiji ya kallan mi al'aurarki, ummi tace nima ai
    shine, ya sake janyota jikinshi. Yanzun Haka
    zamu zauna? Shine nakeson in fada maka naji
    kana ka gaji da aunty bishira kila zaka saketa ne.
    Toh don allah ka rabu da ita tunda ko ka saketa
    sai ka auri wata. Tunda nasan zama Haka bazai
    yiwu ba. Ta soma hawaye ya shiga lallashinta
    yace Allah zai yaye masu. Haka sukaci gaba da
    rayuwa cikin kwanakin da bishira bata nan, ummi
    tanason kalolin wasanin da Abba ke mata,
    amman da yaso kwatantawa ko allah ya amshi
    addu'a su ta warke saita kwace jikinta ya hau
    bari tayi ta kuka. Don Haka sai ya hnkr da
    bukatarsa amman ya takura sosai, kuma yana
    ganin dole yabar batun bishira yanxu don Haka
    ya jaye batun saki amman sai dole ya nuna mata
    kurenta. Ranar data dawo kwananta takwas
    Ranar ma bata da niyar dawowa sai da aunty ta
    kira mahaifinsu ta sanar dashi, ya kirasu a waya
    ya zagesu tas gaban mahaifiyarsu harda mai
    jego. Tace bishira ta dawo shine ya kira Abba da
    waya ya bashi hnkr yace Duk irin wannan ta faru
    ya kirashi ya sanar dashi. Abba ya shigo da T. V
    guda 2 daya ya kai dakin ummi, daya ya kai falon
    bishira wanda ya yanke kwadon. Ummi tayi ta
    murna bishira kuma ta daki Duk rashin kunyarta
    gabanta sai faduwa yake, batasan ya zasu
    kwashe ba. Sai da taga baiko kalleta ba daga ita
    har yar sannan ta dan saki jikinta, tasan ba zai
    tsaya a fushi ne in taci sa'a. An dauki sati guda
    Abba baya ko kallon inda bishira ta ke ko Ranar
    girkinta sai dai yayi kwanciyarsa a falonta. Duk
    da yana bukatarta Haka kuma ya janye yan
    wasanin da yake da ummi don wahalce yake
    bacci, ita kuma sai ta damu don ya saba mata
    sai tayi tunanin ko laifin tayi masa ne. Ita kam
    bishira ganin zura ido ba zai kaita ba, don Haka
    ta sauke zafin kai ta iske Abba a falonta wani
    dare harda kukanta take bashi hnkr. Wai sherin
    shedan ne ba zata sake ba, Abba ya dubeta mi
    kikayi? Tace nidai ka yafeman, yace ashe kinsan
    kinyi ba dai dai ba? Ai inda ke ce saikin kara,
    amman bari kiji na rantse maki duk kika kara
    zuwa wani wurin bada izinina ba wllhi sai kinsha
    mamaki. Tace na yarda, abun mata da miji nan
    dai suka sasanta, hakan nan dakin ta ya kwana,
    suna shiri cikin satin don bishira ta fahimci mijnta
    ita kadai a matarsa, yarda yake rawar jiki lokacin
    kwanciyarsu. ***ummi na zaune idonta kan tv
    Abba take kallo yarda yake watso turanci cikin
    kwarewa. Kullum kara sonshi take, ta kwantar da
    kanta a hannun kujera, kusan sati guda kenan
    tana lura da Abba. Baya son ko taba hannunta
    sannan ga wani shiri da yake da matarsa, sai dai
    yazo yaci abinci ya dauki laptop dinsa ya raba
    dare. Inko yazo kwanciya saidai ya juya mata
    baya sabanin kwanaki da yake mata makwanci da
    hakarkarinsa, lokacin tasan babu inda keda dadin
    kwanciya ga matar aure irin hakarkarin mijinta,
    sam bata iya bacci sai tunanin abunda tayi masa,
    amman yau din nan zata tmbysa ko laifi tayi
    masa, Bayan yaci abinci yayi wanka ta dauko mai
    zata shafa masa ya amsa da murmushi yace
    barshi kawai nagode, ta dawo ta zauna, zaya fita
    tace ina zaka ya Abba, yace aski zani, ko zaki
    rakkani tace eh yace taso muje. Suna tafe suna
    hirar aikin shi, yace An koma kirkirar wani filin
    kuma An saka shi ciki, yanxu abubuwa zasu kara
    mashi yawa. Sun isa babu layi An suma mashi ya
    mika mata wayoyinsa guda biyu tana danne
    danne kira ya shigo. Nan take ta hade rai ganin
    sunan dake jiki zainab dina, ya tmbyta da ido
    waya kira ta sake hade rai, sannan ta mika masa.
    Ya kalli sunan zainab sannan ya daga cike da son
    ya zolayi ummi yace zainabuna. Can bangaren
    Duk da kallaman Sun mata dadi tace da ba
    amman yanxu ta wani ce. Yaya salis ya kawo
    maka katin aurena? Yace eh yabani tace ya
    amarya? Yace gata bari in bata ku gaisa, ummi ta
    kauda kai tare da jan tsaki, yayi dan murmushi
    yanason yanda ummi ke nuna kishinsa, salon da
    take wurin kishinta daban ne. Yace zainab Wai
    tana gaisheki, zainab tace to ina amsawa. Ka
    gaida umma sannan ka sai masu anko kalla biyu
    ne. Abba ya naji ko kalla goma ne zan saya tace
    to gobe kazo gidan mu nan ake sai dawa. Ya kalli
    ummi yasan kadan ya rage ya kaita bango. Ya
    danne dariyar da ta taso masa yace gobe kikeso
    nazo gidanku zainab? Tace eh don gobe za'a
    kawo wasu kayan, yace to zanzo, ummi ta zaro
    ido ta mika tsaye dai dai lokacin da aka gama
    askin. Yayi sallama da zainab din sannan ya
    shiga karkabe jikinsa. Ummi kam tuni ta kai bakin
    kofa. Ya sallami mai askin ya isketa Sun jera
    yanxu ba kamar daxun da suke fira ba. Sun kusa
    layinsu yace muje mu gaida su umma tace ni
    bacci nakeji baice komai ba, Sun iso hijabi kawai
    ta cire ta kwanta, yace Wai lafia don zainab ta
    kirani tun dazun kin kasa sukuni?URFIN CIKI book 4 part 20
    ZURFIN CIKI book 4 part 20
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:17
    Ummi ta taba baki, Allah yakawo ta lpy. Ya ce ni
    ban soba gsky. Sbd ke ummi tadafa kirji, sbd ni?
    Ni ya abba, kada kasa duniya ta zage ni, Tare fa
    nasameku? Yace to ni dai kada kiga kamar da
    son raina, tace don Allah ya Abba kabar zancen
    nan. Kaje kagyar mata dakunanta don su kamal
    bazasu iya ba, yanufi gurinsu ganin kamar ya
    damu yasa itama taje tasa musu hannu don dai
    ya saki ranshi, sun gyara tsaf ummi ta goge
    sannan ta rufe dakin. Har magriba bishira bata ji
    an ce za'a maida taba, sai ta dauki wayar
    kanwarta ta kira shi wai yazo don Allah
    yadauketa. Tsakanin mata da miji sai Allah, nan
    ya tausaya mata yace zaizo, kafin ya isa sai daya
    sai mata waya irin dai ta hannun ummi. Har cikin
    gidan ya shiga suka gaisa da babanta, yayi
    murna sosai yayi tawa Abba godiya, tare da ba
    shi hakuri yace yasan yanda ta horu zai gata
    canza da yardar Allah. Yasa aka turo ta yayi
    mata nasiha, sannan ya gargadeta da cewa inhar
    ta bari mijinta yakawa kararta zatayi mamakin
    abinda zai mata. Tace, insha Allahu baza ta kara
    ba, yakawo kudi yaba Abba, da kyar ya amsa ita
    kuma ya bata wasu zannuwa acikin leda, yace su
    raba da abokiya zamanta. Taje tayi wa hajiya
    zainu sallama suka tafi, tamkar baquwa haka ta
    koma, sai kace basu taba zaman aure da Abba
    ba, nauyinsa take ji. Suna tafe ya ciro waya ya
    miqa mata, tasa hannu ta amsa yace taki ce, tayi
    ta godiya yace ba komai. Sallamarsu tasa gaban
    ummi faduwa, ta dake ta fito ta amsa, wani kishi
    ya tasho mata amma saita danne. Ta kalli bishira
    tare dayi mata sannu dazuwa, ta amsa tana
    kallon ummi tayi kyau tagoge daga ka ganta
    kaga wayayya 'yar gatan miji. Ta dauko makullin
    dakin ta ba bishira, abba kuma ya nufi dakin
    ummi. Bishira ta dinga kallon yanda abba ya
    gyara gidan yaja gini ta gefen ummi yayi mata
    falo da kicin, sannan tsakar gidan an gyare shi da
    tiles. Haka bandakin su yagyara shi, nan dai
    bishira ta shiga dakinta ta zauna bakin gado tana
    yi wa allah godiya tare dayi wa kanta alkawarin
    har abada bazata ta kara yin yaji ko ta janyo
    abinda zaisa mijinta ya sake ta ba. Ummi tana
    kan gado tana karanta wani littafi yazo ya zauna
    bakin gadon bata ko kalle shi ba don haushi take
    ji. Sai take ganin kamar rawar kai yake yi da
    dawowar bishiran, kuma tuntuni yana zuwa gurin
    ta ya boye mata. Yace madam ina son in yi
    magana da ku ne ke da bishira, ummi tace ina jin
    ka, yace can zaki zo muje. Tace, gsky nagaji, kayi
    maganar da safe. Yagama gano kishi ne ke
    damunta, don haka yayi murmushi yace yanda
    kikace hakan za'ayi. Ya fita kamar minti 30
    yasake shigowa ya aje mata leda tare da cewa
    saida safe aciki tace Allah yabamu alheri. Yana
    tafiya taje ta banko kofarta, yau kam bacci ya qi
    idanun ummi sbd tayi sabon bacci a haqarqarin
    Abba. Dukkan filolinta ta rasa wanda zai maye
    mata madadin haqarqarin mijinta, ynzun yancan
    da wata tasan yanda yake wannan rawar jikin
    ynzun ya manta da batunta. Tarasa me yake
    mata dadi, littafin datake karantawa kuwa sam
    bata fahimtar abinda ke ciki. Hka ta dinga zubda
    hawaye har nisan dare, ganin bata da wata
    mafita, tashi tayi ta bude kofa lokacin 2 saura
    taje tayo alwala tazo ta kama nafila. Abba jin
    bude kofarta ne yasa shi leqowa ta window
    aranshi yaji tausayinta don yasan bata iya bacci
    sai ajikinshi, ita bata san ya leqo ba don ko
    hanyar dakin bata ishe ta kallo ba. Yakalli bishira
    wadda bacci yayi gaba da ita ya tausaya mata
    sosai yanda tayi tarawar jiki alokacin
    auratayyarsu dazun. Yadauko wayarshi yarubuta
    ma ummi sako. KI KWANTA KIYI BACCI BABY,
    TARE DA QISIMA CEWA KINA LAFE
    AMAKWANCINKI (WATO JIKINA) INA CIKE DA
    KEWAR LEBUNANKI Tana sallah taji shigowar
    saqo amma bata yi ko marmarin dubawa ba, haka
    tai sallah har zuwa lokacin da bacci yasoma
    fizgarta. Tayi adduo'o'i sannan ta kwanta, saida
    asubahi ne datayi sallah sannan ta karanta, dan
    tsaki taja tare da cewa, Karya kawai, kishi yasa
    ta fadin haka don tasan Abba sosai baya boye
    mata komai ynzun. Sai dai abinda yasake qular
    da ita da asubahin nan yanda tana fita shi kuma
    ya fito wanka, duk da tasan dole wani abu yafaru
    tsakaninshi damatarsa, amma sai taga tamkar da
    gayya ya tsaya don tafito taganshi. Tna idar da
    sallah ta dora ruwa akicin dinta, tadafa ruwan tea
    taje kicin din bishira tadauko flask tazo ta wanke
    ta zuba musu ruwan zafi taje kofar bishira tayi
    sallama bishiran ce ta bude ummi tamiqa mata
    tare da cewa an tashi lpy? Cikin sakin fuska tace,
    lpy lau, nagode. Ummi ta ce ba komai takoma
    dakinta ta kulle kofarta don yau bata da darasin
    safe. Abba ma yau bada wuri zai fita ba, don
    haka yadan samu baccin safe sai 8 yayi wanka
    ya karya, sannan yanufi dakin ummi. Kofarta tana
    rufe, ya kwankwasa ta share sai can dai dataji
    yaqi tafiya sannan tazo tabude. Takalle shiya yi
    kyau cikin kananan kaya, ta kauda kai tare da
    cewa, an tashi lpy? Yace lpy lau, kin karya? Tace,
    um'um sai anjima, zata rufe kofar yace,
    makaranta fa? Tace sai karfe 2 nake da darasi.
    Ta maida kofar ta rufe, yayi dan murmushin
    takaici sannan yafita. Kwananshi 2 dakin bishira
    yayi niyyar dawowa dakin ummi, don ya kosa
    yadawo ya lallasheta bazai iya daukar wannan
    shariyar da take mishiba. Tsakaninta da bishira
    lpy lau amma shi sai tana wani share shi. Ya
    shigo da zumudi zai nufi dakinta, tamiqe cikin
    fara'a daga wanke-wanken da take yi ta amshi
    ledar hannunsa da jakar laptop ta nufi dakin
    bishira. Shida bishira suka bita da kallo, ganin
    zata shiga bishira tace ummi yau ai dakinki yake.
    Ummi tace injiwa? Anty bishara ai kullum ke ce
    dashi har sai kin rama duk kwanakin da kika
    dauka agida. Kinga kenan kusan wata goma sha
    daya kenan. Abba cikin sauri yace ke
    mahaukaciya ce? Ina ki kasamo wannan fatawar?
    Ta kalle shi, sannan tashiga dakin ta ajiye ta fito
    taqara kallonshi gurin malamai, yace to ban
    yarda ba, don haka zanci gaba dayi muku kwana
    bibbiyunku, ummi tace to ni na yafe mata nawa
    kwanakin bishira tace nagode ummi. Haushi ya
    cika Abba, amma shi bazai dauki wannan horon
    da ummi take shirin yi masa ba. Yadawo dakin
    bishira a fili yafurta kema saina baki haushi zakiyi
    dakin sanin wannan furucin. Sharewa yayi yaci
    gaba da kwana dakin bishira tare da nuna kulawa
    ga bishiran. Ummi ta jure duk da duk daren Allah
    sai taci kuka ta gode Allah, sannan tashiga zargin
    cewa shi ma ya Abban dama can yana son
    tarewa dakin bishira, inba haka bame zaisa yayi
    saurin yarda kuma yayi ta nuna mata soyayya?
    Ganin ummi tana yi tamkar bata damu ba yasa
    shi qa rajin haushi, yadawo da yamma suna
    zaune kowa A qofarshi. Ummi tayi kwalliya cikin
    qananan kaya, bishira kuma tana sanye da leshi,
    karatun littafi bishiran keyi ita kuma ummi tana
    yin gyaran qumbunanta. Bawai suna wata hira
    bane amma suna kula juna sosai musamman
    bishira tana son su saba da ummi. Ummin ce.
    bata cika son fitowa ba, bishira ta tashi ta masa
    sannu dazuwa tare da amsar kayan hannunsa
    don yanzun tana koyi da ummi gurin kyautatawa,
    ummi ta kalle shi sannu dazuwa, ya amsa da
    yauwa baby. Yakalli bishira sweety zanyi wanka,
    tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai
    tazo tace masa takai nan k sweety zanyi wanka,
    tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai
    tazo tace masa takai nan kuma yajanyo bishira
    jikinshi. Ba wai yana da bukata bane, amma don
    ya shaqar da ummi sai ya banko kofar, qaran
    kofar ne yasa ummi kallon gurin dakin. Ta duqar
    dakai taci gaba da abinda take yi, kusan minti
    arba'in suka fito, Abba ya matsawa bishira wai
    suyi wanka tare, tace ni bazan iya ba akwai ummi
    dama da dare ne inajin kunya. Kuma kada taga
    kamar cin fuska ne, yace kenan don kada ki bata
    mata rai ni mijinki bazaki faranta min ba ko? Dole
    ta bishi suka shiga bayi. Baqin ciki yasa ummi
    tashi tashige daki, kuka sosai tayi daga nan bata
    fito ba sai magriba, tanayin alwala tarufo kofa,
    washegari ma qin bude qofar tayi daga alwalar
    asubahi. Abba yayi ta raba ido ya ganta amma
    bata fito ba, yasan fushi take, ya kira wayarta
    taqi dagowa yayi mata saqo cewa in zata
    makaranta tafito inkuma sai darana ta bude ta
    amshi kudin mota. Tana gama karantawa tayi
    wuri da wayar ba tare data bashi amsa ba, haka
    ya tafi. Bishira ta qwanqwasa ma ummi ta bude
    suka gaisa, tace naga baki fito bane ina fata lpy?
    Tace lpy lau bacci ne, tace yau baza kije
    makaranta bane? Ummi tace, zanje sai sha biyu.
    Bishira tace kinji dadinki ni gashi nan ina tayi
    masa zancen karatun amma ya share ni, ummi
    tace inkin matsa zai yarda, tace ko za ki dan sa
    min baki? Ummi ta riqe baki, ni a wa? Ke da yake
    hannunki ai ke ce zai saurara, ni kin zo ne ma ki
    zage ni. Bishira tace wane irin zagi? Ni dama ki
    amshi mijinki ummi don gangar jikinshi ce kawai
    agurina, amma ruhinsa yana gurinki. Ummi ta ce,
    ngd da zagi, bishira ta ce zancan gsky ne ba
    wani zagi. Haka suka yi ta rayuwa cikin kwanakin
    ummi kam har rama tayi shima Abba ya rage
    walwala don wanda yasan kan kula da shi
    kamarta. Yayi missing din abincinta. Amma ya
    gaji bazai jure ba. Ya tuna bishira tace masa zata
    ta yini gidan ummanshi. Don haka yana gama
    muhimman abubuwan da zai yi agurin aikin
    yanufi gida. Ummi tana shirin tafiya makaranta ta
    dauko jakarta sai kurum taga mutum kamar an
    jeho shi. Ta daure fuska tamkar bata taba dariya
    ba, yace ummi nagaji kin ji ko, na gaji da wannan
    horon naki. Laifin me nayi miki? In don na dawo
    da bishira ne sai in saketa, duk ba kece kika
    takura min sai na dawo da ita ba? Ummi tace, ni
    karka doran jakar tsaba kasa kaji su bini, ka saki
    matarka sbd ni? Ba ruwana. Yace, to ki dawo
    yanda kike, kuma ki janye batunki na wai kin
    haqura dani, niban haqura ba. Ke ma kuma nasan
    dole ki kasa kanki, ummi ta ce ni ban damu ba,
    ya ce qarya ne gashi nan duk kin rame? Ya
    canza daga fada zuwa lallashi, ummi don Allah
    na roqeki mu koma kamar da, haba bebyna. Ya
    lalubo hannunta ta qwace, don Allah ka tafi kada
    bishira ta dawo ta same ka anan ta zargi wani
    abu. Haushi yakamashi sosai, ya daga murya da
    qarfi, kin san Allah ummi zan hadaki da umma, ta
    nufi hanya fita, nikaga kada kasa ni yi latti don
    lokaci yayi nisa. Ya ficiko ta ta dawo ba zaki
    makarantar ba, ke an ma daina karatun tunda yafi
    ni. Ta zubar da jakar da hijabi ta nufi gado shi
    kuma ya fita cikin zafin rai, gidan su umma yaje.
    Bishira tana dakin umma tana sallah yabi umma
    kicin, umma gurinki nazo, ta dube shi lafiya
    Abba? Ya turo baki, alamun ranshi bace baki,
    yace umma ki sallami bishira, tace kamar yaya?
    Yace taje can gidan ko muyi maganar agabanta?
    Tace, kyale ta muje dakin babanku. Abba ya fada
    ma umma komai da ummi ke masa, tun dawowar
    bishira ran umma ya baci tace ka barni da ita.
    Banda shashancin ta da ita kadai take son
    azauna? Baga bishirar nan ba gidan nan ta gane
    kuskurenta ko yau yarinyar nan sai da tace in
    yafe ta nace ni dama ban riqe ta da wani abu ba.
    Shine ita zata qirqiro fitina? Yace, umma ai ba da
    bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane
    kurenta da dare kuzo kai da ita. Umma ce ta kira
    ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu
    don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar
    isha'i taje gidan. Can tasamu abba, nan ko umma
    ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo
    umma tafada mata komai sai ta shiga fada. Wai
    ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko
    ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya. Abba
    yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun
    in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma
    ni abin ya qare akaina? Nan fa umma tayi mata
    tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka
    kira shi awaya ya fita. Umma ta samu dama
    taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki
    yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice
    kinyi fushi da ita kin barwa kishiya? To kada in
    sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke
    ganinki da ita. Ta jima tana bata shawara kafin
    Abba yadawo suka nufi gida. Ya shiga gurin
    Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai
    kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,
    tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa
    s / ZURFIN CIKI book 4 part 21
    ZURFIN CIKI book 4 part 21
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:19
    Kwanci tashi asarar mai rai, shekara ta zagayo
    lokacin bishira da tsohon ciki, Abba nason yara
    don muhibba taqi dawowa tafi son umma dole
    suka haqura suka bar mata. Ta haifi 'yarta
    budurwa tubarkalla ranar suna ta ci sunan sahura
    inda suka sa mata walida. Ummi nason yara, don
    haka in tana gida to tana manne da walida, Abba
    yana damuwa da rashin samun cikin ummi,
    wanda ita ummin ta barma Allah komai. Shekaru
    uku sun sake biyo baya, lokacin Bishira ta sake
    haihuwar habiba takwara Abba yayi wa ummi.
    Tsohuwa an qara tsufa, 'yan rigingimu sun qaru
    tace ita Abba yama takwara amma bata son ya
    duke ta irin yanda yayi wa ummi. Abba kullum
    qara son ummi yake, umma ta matsa masa sai
    da yayi qoqari ya sai fili rabin filoti tace kuma a
    rage ciye ciyen dadin nan agina shì. Haka kuwa
    ya gina flat mai daki hudu, daya ummi daya
    bishira, sai nashi sannan na yara. Yayi qoqari
    gurin gyaran falon ita kuma ummi ya canza mata
    kayan daki don bishira an canza mata daza su
    tashi agidan su. Yace tabishi bashi in ya samu
    zai bata kudi amadadin kayan daya saima ummi,
    tace ta yafe. Ummi dake karantar (BUSSINESS)
    har ta hada (H.N.D) dinta kuma tayi bautar qasa.
    Abba dai yace baza'ayi aiki ba amma ya yarda
    tayi kasuwanci, Alhaji babba ne ya bata jari inda
    take saro kaya zannuwa, lesuna, takalma zuwa
    jakunkuna. Abin ya amsheta don har kayan aure
    tana hadawa, tana yin saqo irin su kwatano da
    chaina, india, pakistan ko dubai, ta hanyar wani
    wan kawarta. Haka kawai ummi ta samu kanta
    da zaban abinci, yawan bacci kasala da dai
    sauransu, sam bata san takamaiman lokacin
    al'adarta ba. Don bata wani lissafi in yazo shi
    kenan in bai zo ba bata damu ba tama cire ranta
    daga batun ciki. Abba ya kalli nonuwanta, baby
    kwanan nan kirjinki ya cika sosai, gashi kinyi
    haske ko kin canza mai ne? Tace yaya yaushe
    kazama likita? Yace, ummi kin fa canza shirya
    muje asibiti, ta ce ya Abba don Allah ka bar ni
    nagaji dazuwa asibiti. Yace, to ni zan je inya
    tambaya game da yanda ki ka canza. Cikin jin
    haushi tace sai ka dawo. Ga yara atsakar gida
    sun ishe mu, yace ni naki nake qawar in gani
    nasan addu'ar da nike yi bazata fadi kara banza
    ba, sannan ga qoqarin danake yi, shiru ta masa.
    Dagaske yake yi yaje yayi wa likita bayani, yace
    yadai kawo fitsarinta. Sai da suka yi tsiya da qyar
    bishira ta lallasheta ta yarda ta bada fitsarinURFIN CIKI book 4 part 23
    ZURFIN CIKI book 4 part 23
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:22
    Sam bishira bata damu da barin mijinta da zatayi
    gurin ummi ba, tunda ta jima da sanin cewa
    ummi bata da wani ammafni. Wannan ne ma
    yasa tasha alwashin in taje zatayi addu'a Allah
    yakara toshe ummin kada ta warke sam, tunda
    umma Bashir ta fada mata duk addu'ar da tayo
    kafin ta dawo an karba mata. Ta kuma kara bata
    shawara ta roko musu rigima suyi tayi har su
    rabu, Bishira tace duk zata roko. Ko ranar da
    zasu tafi sai da ta yi wa ummi habaici, kawyenta
    sun shigo wato makotansu a tsakar gida take
    fada musu cewa mijinta kurum take tunani. Wai
    zai sha wahala kafin ta dawo. Wata cikin su tace,
    wahalar me ga shi da amarya? Ta ce amaryar da
    ta ke a toshe, ai bata da ammfani. Ummi duk
    tana ji, takaicin duniya ya isheta sai dai ita zata
    so ace bishiran take ta roko ma kanta shiriya ko
    Allah zai sa ta dawo ta kama sallah. Dayar tace,
    to Bishira ki roko mata sauki mana, cikin zolaya
    tayi zancen, Bishira tace ba abinda zai kaini
    makka in roko ma kishiya abin arziki. Ummi ta
    fito ta ce Anty Bishira zai fi kyau ki roko ma
    kanki shirya ko in kin dawo kya fara sallah da
    tsafta. To ban san ma yanda zaki kwashe da
    ibadar ba ko za a karba tunda ba yin sallah ki ke
    ba. Ta taso fuuu, kawayen suka reketa suka ce
    kyaleta bakin ciki ne. Abba ya fito wanka yana
    cewa, Ok, za kuyi na bankwana ko? Yana da kyau
    hakan. Ummi ta koma dakinta. Tun bayan tafiyar
    Bishira Abba ya shiga takura musamman irin
    wannan lkc na sanyi. Ya dawo da yiwa ummi 'yan
    wasanni da ya daina, sai hakan yakara sa shi
    damuwa don haka ya shiga lallashin ummi ta
    fadawa umma....... Kuyi hkr da typing din banda
    lafia sstr dita nake sawa tana maku.els / ZURFIN CIKI book 4 part 24
    ZURFIN CIKI book 4 part 24
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:24
    Tace ita kam ba zata iya ba ranar wata juma'a
    suka tafi da nufun su fadama umma matsalarsu,
    sai dai har zuwa bayan isha'i da abban yazo don
    su tafi sun kssa sanar da umman komai, har
    sunyi sallama abba yayi kunar bakin wake yace
    umma ta fada maki matsalarta? Umma tace wa?
    Yace ummi tace a'a suka koma suka zauna. Abba
    kanshi na kasa Yace umma dama bata da lafiya
    ne? Umma tace mike damunta kuma? Yace ummi
    fada mata. Ummi ta sunne kai cikin cinya tare da
    cewa shiya fada. Cikin sa'a aka kira wayarshi,
    nan yayi waje ya barsu, umma tasa ummi saita
    fada. Ummi ta rasa ta inda zata dauki zancen,
    umma ta soma yi mata fada har tsohuwa ta leko
    tambaya take lafiya ba sunyi sallama dama basu
    tafi bane? Umma tace wai bata da lafiya ne,
    kuma ita da abban sun kasa fadaman shi yayi
    waje, ita kuma ta kunshe kai cikin cinya wai injira
    ya dawo ya fadaman. Tsohuwa taja hannun
    ummi zuwa dakinta, suka zauna bakin gado ta
    riko hannunta. Takwara fadaman abunda ke
    damunki. Ummi ta sunkuyar da kai ta kasa
    magana. Tsohuwa tace inda baki fadaman ba
    akwai wanda zai taimaka maki ne? Tunda naga
    duk yarda mijinki yake da umman ku ya kasa
    fadamata to abun mai girma ne. Ummi ta daure
    tace "Gabana ne fa a toshe....." tsohuwa ta rafka
    salati, sannan tace yannan badai angurya ba?
    Cikin tsoro ummi Tace, ni ma ban sani ba ko
    shine. Salati tsohuwa ne ta jawo hankalin umma
    tazo dakin da sauri. Tsohuwa Tace ina ga
    yarinyar nan angurya ne a gabanta. Umma Tace
    shine don wauta daga ke har abban kukayi shiru,
    dubi tsawon watanin da kuka dauka, tsohuwa
    Tace yanzun yaya za'ayi umma tace ni ina nasan
    yanda za'ayi, ai ni na zata yanzun babu masu irin
    wannan ciwon. Rabon da inji labarinshi tun muna
    yan mata. Tsohuwa Tace kai nima na jima banji
    ba, amman kinsan dama wanzamai ke aikin.
    Alhaji ya dawo daga sallar isha'i yaga abba tsaye
    a waje, Yace a'a babana dama baku tafi ba, Abba
    yace eh yanzun zamu wuce, ya biyo bayan Alhaji
    suka shigo suka riski zancen dasu dasu umma
    keyi. Alhaji Yace lafiya? Umma Tace yaran nan
    ashe zaune suka da lalura, tame inji Alhaji, umma
    Tace angurya ce ashe ta fito ma Ummi wai suka
    zaune. Alhaji yace meye kuma angurya Tace wani
    abu ne dake toshe mace. Nan fa suka shiga
    tattauna yanda za'a shawo kan abin, tsohuwa
    Tace wanzami za a kira ya yanka mata. Alhaji
    yace to gobe zai kira wanzami. ZURFIN CIKI book 4 part 25
    ZURFIN CIKI book 4 part 25
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:26
    Abba da jin haka sai ya fito, kishi fal da
    zuciyarshi, ya ce umma wanzami kuma? Ta ce
    eh, aikin sune. Yace gsky umma ba za a kai ta
    gurin wani wanzami ba , bagara muje asibiti ba.
    Tsohuwa ta ce, kaci gdanku da asibiti komai ku
    ce asibiti to wannan ba aikinsu ba ne. Abba ya
    ce, Nifa gsky ba xa a kai min mata gurin wani
    wanzami ba, umma asibiti zamu. Yanzu kai ya
    waye wanzamai ba duka suke dafa kayan aikinsu
    ba, haka kawai taje ta hadu da wata cutar? Alhaji
    yayi murmushi yasan kishi ne ke damun Abba, ya
    ce Babana kada ka damu, goben sai kuje asibitin,
    in sun ce ba su san shi ba to sai a zo a yi na
    wanzam ko ? Kunya ta kama Abba, Sam ya
    manta Alhaji yana gurin ya ce to Tsohuwa ta ce
    kuje in kun je ma dawowa za Ku yi dan me taurin
    kan tsiya. Abba ya ce naji kin ji ummi taso muje
    gda Tsohuwa ta ce oho dai, kuyi ta tafiya in dai
    akayi mata aikin ai dole ka barta ta warke . Alhaji
    da umma dai dariya sukayi ta yi musu, shi kuma
    yayi musu sallama, ummi kam kasa magana tayi
    don duk ta tsorata. Suna fita ta rike hannun Abba
    gam tana cewa. Don Allah ya Abba kada kabari
    wanzam yayi mini aikin nan, zan ji zafi. Ya
    rungumota, Ba zan amince ba wani ya ganmin
    al'aurar mata, likita ma mace zan nema ko nawa
    zan kashe . Ummi ta ce, to zan ji zafi ya Abba?
    Ya ce, made ki damu, in asibiti ne kila suyi miki
    allurar kashe zafi amma in wanzami ne ina za ya
    ga wata allura yayi mini. Ummi sarkin tsoro ranar
    kwana tayi cikin damuwa, washegari kuwa tun
    bakwai suna asibiti. Babban asibiti suka je sun
    yanki kati likita me kula da fannin mata aka tura
    su. Mata dayawa suna ta kallon su ummi
    musamman yanda Abba ke nan-nan da ita,
    sannan wasu sungane shi kasan cewar shi dan
    jarida mai farin mini. Wasu mazan kuwa sai zuwa
    suke suna gaida shi. An kirata dakin ganin likitan,
    ta mike zata Shiga Abba shima ya mike, wata
    Nurse ta ce, malam jira mana, ya ce ai duk Mu
    biyu ne bamu da lfy, ya shige likitan namiji ne ba
    yanda ya iya dole ya yi masa bayani likitan yayi
    ma ummi tambayoyi in da duk ta bashi amsa/ ZURFIN CIKI book 4 part 26
    ZURFIN CIKI book 4 part 26
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:27
    Sannan ya bukaci ta kwanta kan gado ya saka
    safar hannu, juya kai abba yayi don gaskia ranshi
    ya baci, lallai ya kamata mata musulmai su dage
    suyi karatun likitanci don su taimaki yan uwansu
    mata. Sai da likita ya gama dubata sannan ya iya
    dubansa, likita yayi wani rubutu ya mika abba
    tare da cewa, an baku gado zayi mata aiki gobe
    ko jibi. Abba yace likita zan iya sanin wane ciwo
    ne wannan? Likita yace tsirone dake fitoma mata
    dai daiku. Sam abba bai fahimta ba don haka yayi
    mashi sallama. Umma ce a wurin ummi tana
    shan magani kafin ranar aiki inda abba
    hankalinshi ya rabu biyu rabi gurin aiki rabi garin
    ummi. Don ma umma ta koreshi da so yayi ya
    rika kwana, addu'a kam yana yinta. Ranar da
    za'ayi aiki abba hankalinshi duk tashe. Yana
    zaune bakin gadon da take kwance ita kuma tana
    can ana aikin. Wayar umma ce a hannunshi yana
    ta danne danne, ba don nishadi ba don kawai ya
    rasa me zaiyi. Dript ya shiga yana ta bin abinda
    ke ciki, mamaki ya cikashi lokacin da yaga irin
    text din da ummi tasha rubuta mashi don ta tura
    ma abba, sai kuma ta fasa. Tamkar cikin mafarki
    abba ya rika karanta sakwanin dama ummi tana
    sonshi zurfin ciki ne tayi? Ya sake bude wani
    rubutu cewa, Ya Abba ina sonka, ina kaunarka
    duk wani motsi na numfashina kara sonka nake,
    ka tausaya mun sonka zai zama ajalina, duk
    ciwon da nakeyi na sonka ne. Ko na rantse ba
    zanyi kaffara ba, in kaji haushin kalamaina ka
    yafeni, nasan ni ba ajinka bace, amman ka daure
    kace kana sona koda bada gaske bane. Gama
    karanta sakon yayi dai dai da dawowa da ummi
    dakin, da sauri suka nufeta idonta biyu saidai
    daga gani tasha azaba. Tayi wujiga wujiga. Abba
    ya kama hannunta cikin matsanancin sonta da
    tausayi. Sannu suka dinga yimata, nurse tabasu
    magungunan da za'a rika bata, umma kuma ta
    dauki wayarta don sanar da alhaji an gama aikin.
    Abba yasa bakinshi dai dai kunnenta yace ina
    sonki ummi, ina matukar sonki. Duk da tana cikin
    wani hali taji kalaman nasa har a tafin kafarta.
    Ta bude jajayen idonta ta dubeshi, ya sakale
    hannunshi cikin tafin hannunta ya hade su. Ta
    girgiza kai dai dai lokacin da nurse din ta sake
    shigowa tace ga kayanta, ya amsa zaninta ne da
    siket da sauransu. Tace ka barta tayi bacci kafin
    ta tashi zafin gurin ya ragu, kila zuwa dare a
    sallame ku. Umma tace to mungode. Nurse tace
    yarinyarki nada dauriya, anyi mata allurar kashe
    zafi bata kama jikinta ba amman bata yimuna ihu
    ba. Likita ma ya yabata da kokarie ta, Abba ya
    kalli ummi cikin tausayi. Sai gurin karfe ukku ta
    farka wurin kam ya dan lafa da radadin, abba ne
    yaje gida ya dafo masu abinci sannan ya nufi
    wurin aikin shi. Don ranar bada wuri zashi ba.
    Tunda ummi ta farka take ta kokarie tunowa shin
    kalaman da taji cikin mafarki ne ko kuwa ido biyu
    ne? Bakwai na dare likita ya shigo ya kara duba
    ummi sannan yace suna iya tafia gida. Ya basu
    maganin sha sannan yace ta rika shiga ruwan
    zafi da dettol. Umma ta kira abba ta fada masu
    batun sallama. Yace su jirashi yana zuwa. Ummi
    tace da ummansu su alhaji pha? Tace sunxo kina
    bacci harda ummanku sahura.els / ZURFIN CIKI book 4 part 28
    ZURFIN CIKI book 4 part 28
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:30
    Bansan lokacin dana dauka ina rigimniya da sonki
    danqare a zuciyata.Ummi da ban sameki ba da
    tuni bana garin Kano domin lokacin yanke
    shawara nayi in nemi canjin aiki zuwa wata jihar
    har yau ban daina yiwa Salisu addua ba wanda
    shine mutum na farko da ya soma tsegunta min
    kin zama mata gareni So, Ummi baya raina
    abinda yake so da nayi zaton zubar da kima ne in
    furta maki kalmar so musammam in na tuna ke
    baki soma, zurfin a so bashida wani amfani don
    na sha wahala.Ba zan Qara boye dimbin son da
    nike maki ba Ummi ko gaban wa zan nuna kina
    jina matsala? Ummi wadda ke zaton mafarki take
    sai taji bakinta yana furta wayyo dadi Ya Allah
    kada ka farkar dani in har bacci nike Abba yace
    ciji yatsanki zakiji zafi Ummi nine Abban ki mai
    sonki wanda ya reneki tun kina zanen gobe.
    Hawaye suka soma zubo mata cikin muryar kuka
    tace Ya Abba da gaske kana sona? Nafi zaton
    tausayina yasa ka furta haka, Amma koba gaske
    ba ne na gode kuma naji dadi Amma ka sani Ya
    Abba ina sonka mai tsanani sai tasa kuka. Yace
    ummi yi shiru, in kukan takaici ne kukan ya kare.
    Nima na jima ina sonki jiya naga sakonki a wayar
    umma da kike rubutawa mai dauke da nuna sonki
    gareni. Sai zurfin ciki ya hanaki, don allah ummi
    kada ki koma zurfin ciki a sona, ki zazzage min
    duk irin sonki gareni. Ummi tace yau kam ji nake
    kamar a mafarki. Sun nutsa a cikin hirar so suna
    ta baiwa juna labarin halin da suke shiga a baya,
    a lokacin daya ganta da wani namiji yace
    hankalinsa yayi mugun tashi. Sai lokacin daya
    fuskanci bashir na sonta, ita kuma Tace ta tsani
    koh mace ta kira layin shi, zainab kuwa data
    samu labarin ta kamar ta mutu. Tace ko bishira
    bata kishi kamar yarda take kishin zainab, sunyi
    nisa basu san sun kwana zance ba, sai da ummi
    taji kiran sallah. Tace ya abba kaji abunda naji,
    yace sallah ake kira naji, kin sani kwana zance.
    Ban gaji dajin muryarki ba amarya tah. Ummi
    tace gari yayi saurin wayewa kaje kayi muna
    godia ga allah ta hanyar nafita, yace to matata.
    Hamdala ta rikayi har bacci ya dauketa, muryar
    umma taji tana cewa ummi ki tashi kiyi wanka ki
    gasa jikinki. Tana zaune cikin baho wanda umma
    ta zuba ruwan dimi da dettol, tsohuwa ta shigo
    cikin bandakin. Ummi tace don allah tsohuwa fita,
    tace don allah ja can anki a fita din, ta saka
    hannu cikin ruwan wankan ummi dake gefe a
    bokiti. Tace ina suwaiba? Ai karo mata ruwan
    zafi, wannan ruwa yaushe zata gasa jikinta, idan
    da dan tawul dauko in danna mata jikin. Ummi
    tace nidai tsohuwa ki barshi don allah, sai kace
    wata mai jego? Tsohuwa tace tafi can kuda baku
    san darajar jikinku ba. Wannan rawar kan da mai
    sunan malam keyi idan ba'a gyara kiba saiki ba
    sai zance ya dawo baya, idan anyi magana ku
    yan zamani kuce bamu waye ba. Alhali ku
    wayewarku itace kwalliya amman jiki ba'a san a
    gyara ba, umma tazo ta kara mata ruwan zafi a
    cikin bokiti. Tsohuwa tace yau a sawo bagaruwa
    a tafasa ruwan shigar tata da ita don tayi saurin
    warkewa. Kuma ko ina zai hade, in kin koma
    gidanki kin kwana biyu ki dinga hada bagaruwa
    da alim kina tafasa su kina shiga.IKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 29
    ZURFIN CIKI book 4 part 29
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:31
    Umma Tace xa'asiyo tafita tabar su ummi
    nacewa to tsohowa kije mana tace bantafiya sai
    naga yanda xakiyi ganin ummi tabata lokaci nan
    tsohuwa ta dauki tawul din tashiga nadar ruwa
    tana dannama Ummi, Ummi tanacewa itadai
    abata tayi da kanta. Tsohuwa tace gaddamace
    daku ya'yan yau kinga duk macce dake rufe
    jikinta tafita daban damasu tallar jiki. Ita macce
    anfison a sameta ko yaushe da dumi a jikinta,
    yawo babu takalmi ko a tsakargidane yana
    ragewa mace dumi sbd sanyinda ke ratsa tafin
    kafarta har ni'ima yana ragemata. Sannan zama
    atantagaryar suminti shima yana rage mace, da a
    ace zaku gane kunga masu saka hijabinnan da
    safa? bakaramin wayo suke yimukuba. Inda za'a
    banbance za a samu sunfiku ni'ima da kyau fata,
    don haka sai kin dage Ummi dai tayi shiru, amma
    aranta cewa take wannan tsohowa ko ina tasan
    wannan duk bayanin? Filo aka ajewa Ummi ta
    zauna tana karin kumallo, duk takosa taga
    abbanta, koda ta tsinkayi sallamarsa tamkar
    tamike ta taroshi. Amma dole yaje yagaida su
    alhaji, tsohuwa tace aefa mu kuma bana munga
    takanmu don nan zaka dinga likemana. Yace
    dadin abundai nima nan gidan ubanane, da
    uwata. Umma tana kicin tanamasu dariya. Tunda
    ya zama idanunsu sunsarke da juna sun kasa ko
    magana Ummi ce tayi karfin halin lumshe ido
    sannan tabude tace sannu daxuwa. Tasowa yayi
    ya tsugunna kusa da 'its, yajikin babyna?sunan
    yamata dadi, naji sauki bari in kawomaka abun
    karinka. yamika mata tafin hannunsa tasaka nata
    yahadasu ya yasarke, murya kasa kasa yace
    barshi na' amso. Ta kula abba mutum ne maison
    wasa da tafin hannu. Ita kanta tanason hakan da
    akwai wani sako da tafin hannu ke isarwa acikin
    duniyar ma'abota so, kila wannan dalilin ne yasa
    abba ke kashema tafin hannusa kudi da mayukan
    da ke saka laushin hannu har ita mah ya
    saimata. Koda umma ta shigo Ummi tayi kokarie
    amshe hannunta amman abba yaki saki, kuma a
    hakan ya karya. Umma kasa zaman dakin tayi
    domin a baki abba yake ba Ummi abinci, umma
    nafita taceels / ZURFIN CIKI book 4 part 30
    ZURFIN CIKI book 4 part 30
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:33
    Daren ranar duk suna kan kujera doguwa a dakin
    umma ya bude mata laptop wai yana koya mata
    kanta kwance a cinyarsa, umma ta shigo dakin
    tsohuwa tace tsohuwa zaifi kyau mu sallami
    yaran nan na gaji da ganin wannan aiki nasu ai
    tasamu sauki. Tsohuwa tace suwaiba ina laifin ta
    kwan goma ma, umma tace anya zasu kwan
    goma nan? Gobe bakwai guda ta koma dakin ta,
    tsohuwa tace shine nan. Abba yace Ummi kinfa
    samu sauki ba zakizo mu koma gidan mu ba?
    Tace su umma ne zasu maidani ai nima ya abba
    inason in koma yace yau nan zan kwana in sunga
    haka sun kuramu, Ummi tace ya abba kayi hnkr
    kada ka kwana, shine yace kin yarda goma inxo
    mutafi ko ba sanin su umma? Tasa dariya tace
    taf inajin kunya bazan iya binka ba yace to kuwa
    zan kwana a nan. Suna cikin haka umma ta leko
    tace abba bazakaje gida ba yanxo fa sha biyu
    saura, yace umma nima nan zan kwana. Ta rike
    haba nan din lafia? Yace to umma nima ba gidan
    mu bane? Ummi tace dama yafi umma kada yaje
    wani abu ya rudashi, umma tace a'a abba tashi
    ka tafi insha allah gobe Ummi zata koma yayi
    murmushi tare da cewa nagode umma.nan dai ya
    tattara yanashi yanashi ya tafi gida cike da
    kewar matarshi, itama Ummi lamo tayi a gado.
    Bayan umma ta gama yimata fada ta bari ta
    warke taki ko, sai cewa tayi umma ni fa na
    warke. Umma ta kalli Ummi cike da mamaki tace
    yaran yazo saidai a barsu. Shiyasa akace idan
    macce ta isa aure ayi mata a huta. Ita kam Ummi
    tana ganin a barta tabi mijinta ta faranta mashi
    shine abinda yafi dacewa don yanxu ba inda ya
    kai mata dakinta dadi bacci. Duk da kashedin da
    tsohuwa tasa abba dakinta tayi mashi na cewa
    ya bar Ummi sai ta kara sati kafin yace zai
    kulata da sunan auratayya, bai sa abba jin zai iya
    ba. Don haka koda ta fada mashi cewa yayi kadai
    da huruminki da wanda ba naki ba duk sai kin
    shiga? To nidai ki lafa man haka. Ya fice a dakin.
    Ita kuma tana ta fadanta tana cewa "Na shiga din
    dan neman yaro, da kyar ya barta ta kara kwana
    biyu ya afka mata don shi hkr sa ya kare, ta
    nuna mashi ita fa tsoro take ji kada ta wahala, ya
    lallasheta yace ba wani wahala. Ummi tana son
    faranta ran mijinta. Don haka ta jure duk da
    yarda yazo mata ba sauki, sai dai tasha albarka
    kuma ta kara samun wani matsayi na
    musammam a gunsa. Cikin satin ta zama yar
    lelenshin kafin sati biyu ta hardace duk wani
    darasi da abba yake koya mata, abba jinsa yake
    kamar wannan lokacin ne ya fara rayuwar
    angoncinsa. Sam ya manta yana da wata mata
    uwa duniya saida Aunty ta kirashi tace lafia baya
    kiran matarsa sai ga abba da girman shi ya girba
    karya. Wai ya kira ya kasa samunsu Aunty ta
    yanda tunda farkon tafiyarsu yana kiransu sun
    gaisa da bishira tana tmbyrshi ina hibbarta? Sai
    lokacin ya tuna kwana biyu bai ganta don tana
    gidansu umman bashir, amman sai yace tana
    lafia in yaje zai kirata taji gwarancin yar tata.
    La'asar sur suka jero ita da abba don su dan
    zaga kurum. Sun shigo gidan ahmad da muktar
    duk basu rabu ba saida sukaji sun saba da ummi.
    Don ita haka take yana da wuya kayi zaman awa
    guda da ita bakaji ta kwanta maka a rai ba. Abba
    yaji dadi yarda Ummi ta nuna kauna ga matan
    abokanin nasa, yasan bada jimawa ba matansu
    zasu zama kawaye kamar yarda yaso da bishira
    amman taki. Daga can suka nufi layin su gidan
    su umman bashir Ummi tace su fara shiga su
    dauki muhibba abba yace bazata yarda dake ba.
    Ummi tace zata yarda muje a ran abba tsoro
    yake gada umman bashir ta gwasaleta Ummi, sun
    sameta tana shara da sauri Ummi ta amsa ta
    soma sharewa hakan ya faranta ran abba sai dai
    da ya kalli umman bashir yaga tana hararar
    Ummi, saida ta gama taxo ta zauna suka gaisa
    abba na rike da hibba tayi kaca kaca da kunu
    gashi duk ya dunkule dama ko lokacin da bishira
    tana nan haka zakaga yar duk kazanta. Ummi ta
    bude post dinta ta cire dari biyu guda biyu ta
    mikawa umman bashir gashi umma kin sai goro
    saida ta tabe baki ta amsa babu ko godia, sai dai
    abba cikin jin dadi yace angode, da hibba taki
    binsu Ummi tace kamal xo ka siyo wa hibba
    alawa, kinga baba kamal baya nan xo muje in
    sayo maki. Cikin sa'a sai taxo zasu fita sai ga
    bashir dauke kai yayi tare da jan tsaki daya shiga
    gidan sai ya hau umma da fada Wai ta daina
    barin Ummi da wannan abba suna zuwa in ba
    haka ba zasu kawo mata wani asiri. Umman
    bashir tace suta zuwa ma indan ta nine mi jiya
    tayi bare yau, ka gansu dari hudu yanxu ta bani
    don haka bazan hana zuwa ba amma fa ina nan
    yarda nake bazan canza ba, suna shiga gidan su
    umma kicin ta wuce ruwan zafi ta zubu ta cude
    muhibba tas, ta wanke mata kai ta chajeshi ta
    shafeta da mai nan ma basu jima ba suka nufi
    gida zanen umma ta ansa ta goye muhibba, shine
    ya bude dakin bishira duk kayan yarinyar sun rine
    da datti, Ummi dai ta zazzaba yace .ba maidata
    za'ayi ba, Ummi tace ta dan kwana biyu mana.
    Yace tana fitsari fa. Ummi tace kasawo muna
    pampers Yace shikenan duk da ya nuna bayaso
    yarinyar ta zauna gurinsu amman yaji dadi sai
    lokacin bacci daya shigo ya shigo da pampers din
    ta saka mata Sannan ta kwantar da ita can gefe
    ta azama mata pillo guda haba guda baya, su
    kuma suka kwanta a nasu makwancin suka
    cigaba da soyewa. novels / ZURFIN CIKI book 4 part 31
    ZURFIN CIKI book 4 part 31
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:36
    Ummi tana son yara don haka hibba ta dinga
    samun gata, satinta guda umman bashir ta dinga
    jaraba sai an dawo da ita. Wai kwadayi ne don in
    bishira tadawo ta bata tsaraba, amma koda ta
    tafi da hibban yarinyar sai taqi sai kuka har dasu
    amai. Dole aka dawo da ita, don alhaji karami
    cewa yayi atattara mata kayanta duka inyasake
    samun an maido da ita sai ya saba ma umman
    bashir. Hakan da babbar sallah abba yakashe
    musu kudi ita da hibba, sai dai duk abinda yasai
    ma ummi to ya aje ma bishira nata. Ita kam tana
    can duk addu'arta akan ummi ne, kafin ta dawo
    ummi tafita, don haka data dawo da kwarin
    gwuiwarta ce wa bazata samu ummi agidan ba.
    La'asar sakaliya, direban gidansu ya iso da ita
    gidan kamar yanda mahaifinsu ya umarce shi
    cewa in ya dauko su kada yaso dasunan, ya dire
    kowa agidanta. Kasancewar unguwa uku suka
    soma zuwa sai anty ta taya bishira diban kaya
    su shiga. Daidai kofar dakin bishiran abba na
    kwance rigingine, 'yar T-shirt ajikinshi fara kar.
    Dawandon jeans gajere iyaka gwuiwa. Ummi
    kuma dogon wando ne irin mai kama jikin nan
    dariga mai kamar singileti kanta yasha kana nan
    kitso, tayi filo da kirjinshi yana bata labarin wata
    mota da yake son yabada tashi yayi ciko. Ita
    kuma tana ce masa ya dai je ya shawarci umma,
    muhibba kuwa tana ta faman wasa da sabbin
    kayan wasanta da ummi tasai mata. Ita ma cikin
    'yar shimi mai kyau, kanta kuwa ummi tayi mata
    kitson (3 in 1). Sororo bishira ta tsaya tana
    kallonsu, sam bata tsammaci a irin addu'ar
    datayi zata dawo ta samu ummi agidan ba. Basu
    ganta ba saida anty tayi sallama tare da cewa, ya
    naga kin tsaya? da sauri suka waiwayo duk suka
    mike. Gaban ummi yayi wata muguwar faduwa,
    amma duk dahaka cikin fara'a ta nufe su, bishira
    ta hade rai matuqa sannan taqi ko kallon ummi
    ta nufi 'yarta. Anty kam cikin fara'a suka gaisa da
    ummi harta zage jakarta dake kafadarta tabawa
    ummi wani dan agogo mai kyau. Nan dai ummi
    tayi ta godiya shima abba ya mata godiya. Abban
    ne ya shigar mata da kayan daki, ummi tana
    cewa anty kin mana dawowar bazata, dakin fada
    da an share miki dakin. Nan ma bata tanka ba,
    ummi dai data gaji dayi mata sannu bata amsa
    ba sai kurum ta nufi dakinta, zuciyarta babu dadi,
    tasan yanzun ya Abba zai raba jin da yake da ita
    zuwa su biyu. Bishira tayi kyam tana ta qamshi
    don anty baza su barta tazauna masu da qazanta
    ba, ga haqorin makka an sako ana ta qwambo.
    Ranar dakinta Abba yakwana, yanda bata ga
    wata rawar jiki daga gare shi ba tayi zargin ummi
    tasamu lafiya. Hakan ya qara dagula mata lissafi,
    tayi rabon tsarabarta daga kawayenta sai
    maqota, don ko umman bashir daga zam-zam
    bata qara mata komai ba. Dama tana cike da
    haushin umman data bari ummi ta daukar mata
    'ya gashi nan muhibba ta liqe ma ummi. Hakan
    ya shaqar da umman bashir har tace amaida
    mata zam-zam dinta ita bata sha. Wato don taje
    makka shine zato zo ta canza hali? Ita kuma
    bishira ta amsa tare da cewa, ai ba ita ta aike ni
    makkan bada har sai tazabi abinda zan bata.
    Ummi ko zam zam din ba abata ba, kuma ko
    ajikinta. Abba kam shita kawo masa dogayen
    riguna da T-shirt masu kyau, amma su anty ne
    suka matsa mata sai ta saya. Ranar daya dawo
    daga dakin bishira ummi tana fashin sallah gashi
    yanuna yana dalarura alokacin. Sai tace ta yafe
    masa yau dagobe yaje gurin anty bishira, yace
    A'a tace ba haramun bane nina amince, yace
    nasani. Shiba yason sai yatafi tafara damuwa ko
    tazo tana jin haushinsa, tace ba komai saida
    yatafin kuwa har kuka tayi don kishi. Amma
    tabawa zuciyarta hakuri tasan wata rana wannan
    jarumtar datayi zata zame mata alkhairi. Ita ko
    bishira koda yazo mata sam bata damu ta
    bincika ba, tunda taga ba girkinta ba, saima ta
    hau murna yayo satar kwana ya bata musamman
    dataga dayayi wanka yakoma dakin ummi, haka
    washegari. Don haka sai tashiga daga hanci har
    da 'yan habaice habaice, kafin tadawo tun da
    dama da namiji dan uwansa yake kwana. Tana
    nufin ummi bata ba tayi masa amfanin komai
    wannan yasa ummi ta daura aniyar cusa mata
    takaici, aranta tace tunda cinikinki labe nikuma
    zansa miki hawan jini. Kamal yazo daukar abincin
    da ummi ta saba sawa yau har da kunun gyada
    tayi. Bishira ta kalle shi, wai kai wannan abincin
    na waye kullum kake zuwa dauka? Yace na
    ummarmu ne. Ta taba baki, ummar nan taku
    kwadayinta yayi yawa, ko kuwa itama asirin ya
    kamata ne? Kamal kuwa yaje yafada sai ga
    umman bashir agidan suna zage zage da bishira,
    tana ce ma bishira dadin abin gidan dana nazo
    kwadayin ba gidan ubanki ba. Marowaciyar bnza
    ai dama ina da cikinki, lokacin da Abba yasai
    maku TV, yace ki bani naki sai ki kace gara kiyar.
    Bishira tace, Eh na hana TV aiba wani shegen ya
    sai minba, ubana yasai min, kuma nace mai
    kwadayin yarinyar daki kace uwarta mai asiri,
    menene na amsar abincinta kici banda kwadayi?
    Shiyasa kika bata 'yata ashe don asami abinci
    ne, umman tasa kuka ni ke ke zagi? Yau ko abba
    zai zo gidan nan zai zaba ko ni ko ke. Ummi dai
    tana daki tana jinsu. (aranta tace dadi na da
    gobe saurin zuwa). Bishira tace dama ya darajaki
    ne shine za kice haka, yazo din nace mai kwadayi
    harda rainawa na baki zam zam butulu duk
    abinda na miki kin manta kece kika aikeni
    makkan? Umman tace, zuwa makkan naki dashi
    gara babu, don nasan da kyar ne in za akarbi
    wannan aikin nani ke da bakya sallah arniyar
    banza qazama. Ummi harda riqe ciki don dariya,
    haka dai suka yi tayi wajuna gori har dai 'yan
    kallon da suka taru suka soma bda haquri,
    umman bashir tayi gida cikin kuka. Tagayawa
    'ya'yanta komai su bashir dasunce sai sunje sun
    zaneta umman bashir din tace barta ku barta
    kawai bari abban yadawo. Da dare ta ritsa shi
    agidan yasha mamakin wai yau mahaifiyarshi da
    bishira ne suke fada yace hakane dama duk
    zamantakewar da ba'a kafata don Allha ba wata
    rana sai ta rushe. Nan yayi tawa bishira fada da
    cewa uwarshi sa'arta ce dazata tsaya ta dinga
    gaya mata magana? Nan fa aka sake kacamewa
    har abba. Yakai ga kwasa wa bishira mari,
    sakamakon irin rashin kunyar data rike qugu take
    tsulawa umman bashir din. Ummi ganin abin yana
    tsawo ta fita taja umman bashir tana bata haquri
    ta zaci zata hantare ta amma sai taji tana cewa
    ba komai ummi sakayya ce tunda na nuna ina
    sonta dole tamin haka. Abba yace ummi tasa
    mayafi taraka umma gida, hakan ya qara qona
    ran bishira gashi yanda taga Abba ya bata rai zai
    iya yin komai, dole ta koma daki tana cizon yatsa
    tare da tunanin mafita. Ummi kuwa ahanya sai
    lallashin umman take tare dayi mata alqawarin
    cewa duk abinda take so ta tambayeta zata mata
    shi tarakata har gida sannan tadawo. Sabon kuka
    umman bashir tazauna tanayi, takaicinta yanda
    bishira ta zage ta taci mata mutunci agaban
    ummi, tashare ido tare dayin ajiyar zuciya a fili
    tace dani take magana. Ynzun ummi tasan kishi
    fiye da baya, don ta hau turbar ma'aurata kuma
    tasan muhimmancin abinda ake yiwa kishi, don
    haka zatayi komai na jan hankali don ganin taja
    mijinta gareta. Kuma inta lura cewa bishira ta
    maqale mata aqofar daki sai tayi ta jan abba da
    wasanni, don ta quntata ma me labe. Amma
    hakan baisa ta daina ba, don haka ta daura
    aniyai saita mata abinda zata tona kanta ha abba
    yasani. Duk jumma'a abba yana dawowa gida
    musamman in ranar girkin ummi ne don cin
    abinci na musamman. Jumma'a biyu kenan bata
    fado kanta ba sai wannan, don haka tun alhamis
    taje ta yarfo kitsonta, ta biyo ta gidan su gurin
    tsohuwa tazo. Don haka suna gaisawa da umma
    tace gurin tsohuwa nazo. Suka shige daki tace da
    tsohuwa nazo ne indan samu dan wani sirrin.
    Tsohuwa tace, name ummi? Ta ce na gyaran jiki
    mana. Fati tace min kwanaki kin fada mata wasu
    abubuwa. Tsohuwa ta ce, ja'ira, kinga uwar bari?
    Dama nace zaki same ni ina kyakkyawan zamana,
    bada ina fada miki kina sharewa ba? Ummi tace
    haba tsohuwa banaso aji mu yanzun dai ki bani
    shawara sannan ki fada min abinda zanyi inja
    hankalin mijina. Ta ce, toda farko ki dinga kula da
    jikinki ta hanyar rufe shi ruf, kada kibar kofar
    iska. Banda tafiya ba takalmi, iska tana shiga
    tanan kuma mace narage ni'ima banda zama ba
    dankwali inso samu ne hatta tsarki ki daina yi da
    ruwan sanyi, ki dinga yida ruwan dumi. Sannan ki
    amshi bagaruwa gurin ummarki ki dinga shiga
    inkin tafasa da alif dakuma saiwar mata, sannan
    inkinyi al'ada kin gama kinyi wanka toki dinga
    matsa farin miski a ehem dinki. Sannan ki samu
    saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,
    mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari
    dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi
    biyu safe da yamma. Sannan ki aya garinta,
    kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,
    sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar
    ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai
    ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,
    citta, lemun tsami, ki markada su kisha. In anan
    maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum
    daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta
    musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban
    da dukkan sauran mata. Ki hada da biyayya
    tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi. Ummi
    tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin
    nan? Tace, bari zanba matar ado dake yawan
    zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu. Amma
    su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya
    siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin
    ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.
    Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje
    gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi
    tasan duk wadannan hadin matan? Amma data
    tuna cewa 'yar katsina ce sai tace ba mamaki.
    Tun ranar alhamis din ta soma aiwatar da
    darussan da ta debo daga tsohuwa, safiyar
    jumma'a ranar zai bar dakin bishira. Ya fito tana
    sharar tsakar gida ta gaidashi, ya amsa da fara'a,
    tare dawani kallo mai fassarar in ba keba. Cikin
    muryar data adana don shi kadai tace, ya abba
    ina son in je ayi min zanen fulawa. Yace jiya kin
    fita yau kam a'a. amma ki aika akira mai zanen
    tazo ta miki. Ta marairaice, towa zan aika yaya
    abba? Yace aike ni, ina ne gidan? Tace layin su
    umma ne yace to za'azo ai miki. Bishira tafito
    daga daki tazabga ma ummi harara, Tare dacewa
    kisisina. Abba yakalleta, kema sai tayi miki. Tace
    bana bukata, aikin banza, shikam yafice. Ummi
    kuwa tace gaba da aikinta, ita ko sai tasa kujera
    tazauna tana sakin zantuka, eh don kwalliyar
    tabanzanta tunda ba a iya biyawa miji bukata.
    Allah dai yasa ya fada min komai, to ni me zai
    dame ni don 'yar aiki kawai na dauki yarinya.
    Tashare min gida, tayi wa mijina abinci, daga nan
    fa? Saita saki shewa, ummi ta ce aranta yau zan
    bambance miki. Birabiskon shinkafa tayi da miya,
    ta wadata birabiskon da kayan lambu, miyar ta
    dauki nama da bushasshen kifi. Sannan ta hada
    musu kunun aya yaji dabino da madara, ta
    aikawa ummanta lokacin da kamal yazo daukar
    na ummarsu. Tasheka wanka taci doguwar rigar
    shadda koriya mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau
    ne daurin aurensu. Ga fulawar da yaje ya biya
    akazo aka zana mata. Tanajin rigimar muhibba
    tafito tazuba mata adan kwano tazaunar da ita
    akofar falon mamanta.bishira tafito kicin baki
    tasaki tana kallon ummi da tazo wucewa harda
    bangazar ummi, nan ko kamshi ya bude ta na
    turarukan da ummi ta fesa. Abba yana yin
    sallama ummi tafito da sauri, oyoyo yayana,
    bishira tana daga kicin dinta tana kallon su.
    Ummi ta rungume shi, sannu dazuwa sahibina.
    Ta amshi ledar hannunshi dajakar, yace yauwa
    sannu babyna tace inazan kai ledar? Yace akwai
    ta bishira aciki ki ciro. Ta mika mishi ledar ta
    wuce dajakar dakinta. Ya mika wa bishira lemo
    da abarba da yayo musu tsaraba sannan ya wuce
    danasu, awulakance ta aje. Yana shiga ummi
    tadan karo kofar yanda bishiran zata iya lekensu
    sosai ta gefen kofan. Ta cire masa hula ta aje
    akan madubi sannan ta kunna fanka. Ta shirya
    masa abinci, yauni zan baka har ka qoshi. Haka
    suka yita baiwa juna abaki har suka qoshi.
    Yakamo hannunta mai qunshi yana ta sumbata,
    wai kamar kada su goge. Kumatun shi ta shafa
    nima yau kamin kyau, koda yake dama kai me
    kyaune, ina sonka ya abba sosai. Cikin jin dadi
    ya mannota a jikinshi, nima ina sonki, ina manta
    kowa da komai in muna tare, tace ina tsoron kada
    wata rana ka juya min baya. Ya saqalo
    hunnuwansa cikin nata ina fata in mutu kafin
    lokacin. Ummi tasomayi masa wasu irin darussa
    wadanda tasan yana saurin tada sha'awarshi
    nanda nan kuwa tasa shi fita hayyacinsa yakama
    surutai. Ummi ta tabbata bishira tana wurin ta
    labe, don haka tai murmushi ta bishi suka tafi
    duniyar ma'aurata. Bishira tamkar tayi hauka sai
    kawai ta fado dakin tana fadin, maciya amana,
    har yanzun ba afita daga lokacin girkina ba
    munafiki. Abba ya tashi sannan yaja riga yasaka,
    ok dama kina labewa ne kiji sirrinmu? Da taga ya
    sauko da zafin rai saita gudu dakinta. Yabita
    yamata tatas, kuma ya fada mata cewa tazo ta
    shiga dakin ta zauna ba labe ba, yanzun zai
    komane yaci gaba daga inda ya tsaya. Tayi ta
    kuka gashi ba damar zuwa gurin umman bashir
    dole ta tafi gidansu. Shi kam abba shareta ya yi
    kosu umma bai fadawa ba. Sabuwar soyayya ma
    ya balle agidan, su ci abinci tare, wanka tare, su
    fita yawonsu a qafa ko amota. In yana gurin aiki
    bini- bini ya kira waya, ita kuma ko yaushe cikin
    kirkirar girki da kwalliya tare da dadadan kalaman
    dazata fada masa take. Duk lokacin datayi masa
    zancen bishira sai ya ce, don Allah ta bar ta ta
    huta, ummanshi kuwa 'yar bin qwaqqwafi sai da
    tabi ta gano bishira bata nan. Don haka koda ya
    shiga gaisheta sai tace kada ya yarda yaje yama
    bata takardarta. Ita ko tana can uwarta tace ma
    mahaifinta abba sakinta yayi, shi kuma yace to
    sai tazauna tunda zaman gidan take so. Amma
    su sani daga abinci sai ruwan gidanshi ya amince
    tayi amfani dasu sai ko gurin kwana, amma bnda
    wannan ko makilin dinshi ta taba bai yafe mata
    ba, wannan hukunci yayi musu tsauri. Ko wata
    bata rufa ba taji gidan ya isheta don hajiya zainu
    taso maidata makaranta amma yace tagama
    boko. Bishira na zaune ta zuba tagumi hajiya
    zainu ta shigo dakiki tace tagumin menene kuma?
    Tace, su sumayyah ne wai nace suyi ma muhibba
    wanka sukace Allah yakiyaye. Wai tunda nazo
    dakinsu ya lalace da kazanta, hajiya zainu tace
    aiba karya suka yiba, don haka ma maida
    yarinyar nan za ayi ke kuma ki koma gidan
    antynku ko ki tafi abuja gidan aisha. Tace
    baxanje gidan aisha ba, don itama bama shiri,
    gara gidan antyn amma gsky ni abarmin 'yata
    kuma fakinsan bai sakeni ba. Tace, inda ubanki
    yasan ba saki bne da tuni bai kora kiba? Don
    haka mubarshi haka amma batun 'ya nice zan
    maidata. Ranar da ummi takira ummansu tafada
    mata cewa bishirafa tuntuni tayi yaji amma Abba
    yaqi zuwa, umma ta kira shi tace inya dawo gurin
    aiki tana son ganinshi. To kafin yadawo ma saiga
    hajiya zainu da direba tazo gidan su umma tadire
    musu 'yar, sannan tashiga gidan umman bashir
    tace, in kin haifi danki na halas ne ba shege ba to
    kisa shi ya aiko wa 'yata saki. Umman tace zoko
    kiga dan halas ne in yaso kuje ku nemi arne mara
    sallah dan uwanta kazami kubashi. Nan fa zage-
    zage ya tashi har su umma dasauran makota
    suka shigo. Dakyar aka tura hajiya ta tafi, tace
    kuma saita kira 'yan sanda anzo antafi da umman
    bashir. Alhji qarami ma cewa yayi maza abba
    Abba yarubuta takarda ya aika ma bishira.ZURFIN CIKI book 4 part 32
    ZURFIN CIKI book 4 part 32
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:37
    Shiko alhji babba da umma suka ce a'a abari
    qura ta lafa sannan aje. Koda aka kwana 2 abba
    kin bin alhaji yayi sai wani abokinshi alhaji
    yasamu suka tafi tare. Mahaifin bishira yaji
    mamaki cewa ba sakinta abba yayi ba. Kuma bai
    san sun maida 'ya ba, tadai ce mishi kunzo kun
    amshi 'yarku, to yanzun tunda haka ne kunga
    kenan bishira da uwarta basa son takoma gidan
    mijinta ko? Su alhaji suka ce eh, yace to ku sa
    shi ya rubuto takardarta ku kawo min, su alhaji
    sukace ba za'ayi haka ba. Yace, to kuje ku barta
    zata gane gidan ubanta bananne yadace tazauna
    ba. Sukai godiya suka tafi. Harta koma gidan
    anty farida mahaifinsu yace tadawo nan gidanshi
    badashi take takama ba? Wato ta kashe auranta
    zata je ta kashe na yarta dole ta dawo, tsohuwar
    dake musu aiki yace ta koma gida tahuta amma
    duk wata tazo ta amshi albashinta. Sannan yace
    bishira itace zata dinga wannan aikin duka ita
    kadai, lamarin yayi wa bishira tsauri da yawa,
    gashi ba fita duk ta rame ta lalace ga tunanin
    'yarta. Muhibba kuwa tana gurin umma, ummi
    ma takan daukota sannan ummi tasamu nasarar
    rufe bakin umman bashir, ta hanyar yi mata
    kyautuka ko me sukace sai ta aika mata. Tasa
    Abba ya canja mata gado don nata ya lallace,
    sannan da fati ta haihu tasa Abba ya sai mata
    garar abinci, ita kuma tasa zani da rigunan yara.
    Nan fa sai ga sahura babu ko kunya tana shima
    ummi albarka, ko bashir ne yakawo gulmarsu
    ummi sai tace ai ita bata yo halin uwarta ba.
    Tafi-tafi ma in ya kawo sai tace ai su umma da
    ummi sun gane kuransu. Haba sahura kodai ki
    gane kuranki? Abba yasoma damun ummi da
    batun ciki, wai shifa yana tsoro kada su gaji su
    umma, ummi tace su dai yi addu'a sunje asibiti
    ba wata matsala, likita yace in rabonsu yazo zasu
    haihu. Da kyar ummi ta shawo kan Abba ya
    amince ta zana (JAMB) don ci gaba da karatu,
    sannan ta shiga islamiya. Abba yayi kyau yayi
    kiba ya kara gogewa, haka nan ummi duk wanda
    yaganta saita birge shi, daka ganta kaga wayayya
    wadda mijinta yasan da ita. Taci nasarar samun
    (POLY) saboda bata samu abinda take so don
    zuwa (UNIVERSITY) ba, sai dai ba tasha dokoki
    kafin ta fara zuwa. Bayason kawaye baya son
    abokai, irin wanda wasu matan keyi sannan
    yadinka mata manyan hijabai, kuma banda hawa
    acaba, inya samu sarari zai dinga zuwa da kansa
    yana daukarta. Sai kuma gargadi na karshe kuma
    da babbar murya, in har ya daina samun kular
    datake bashi ta kowane fanni wai saboda karatu,
    to kuwa za adaina karatun gaba daya. Tace,
    insha Allah sai abinda yai gaba. Ya canja mota,
    umma tayi ta fada wai tafi son yasai fili yayi dan
    gidanshi irin na zamani yace za'azo gurin
    ahankali kada ki damu umma. Bishira ta sulale ta
    tafi na'ibawa gidan anty da kukanta wiwi don
    Allah ta taimaka mata taba Abba hakuri ya maida
    ta, wlh tagane kuskurenta. Anty tace, nifa bazan
    iya kiran Abba ba don kin riga kin bmu kunya, sai
    dai in ke ce zaki kira shi ga waya can. Ta dauko
    ta kira, shikuma ganin kiran anty sai yayi parking
    yadauko ummi daga makaranta, ya daga sai yaji
    muryar bishira. Cikin kuka tana cewa, don Allah
    abba nice, kayi hakuri indawo dakina, wallh zan
    canza, yace ok baki riga kin canza din ba, to bari
    inkin canza din sai muyi magana. Yakashe haka
    tayi ta kuka tagama anty tabata wasu kayan
    sawanta sannan ta tafi. In lokacin labarai yayi
    haka take zuwa ta tasa TV tayi ta kallonshi tana
    kuka, kullum kara sonshi take gashi yayi kyau
    idanunshi sun qara haske. Wata ranar jumma'a
    wuraran karfe sha daya ta saci jiki tanufi gurin
    aikin Abba, yana fitowa dakin daukar labarai
    akace wata tana nemanshi. Baiji wani mamaki ba
    don mata kanzo neman shi wasu suce suna
    sonshi wasu suce ganinshi kurum zasuyi don
    yana birge su. Yana zuwa sai yaga bishira, nan
    take ya daure fuska tamkar bai taba dariya ba,
    duk da cewa acan kasan zuciyarshi yatausaya
    mata. Ta tsugunna gwuiwa 2 tana rokonsa, yace
    ke tashi kada ki janyo min mutane, jeki zanzo.
    Koda ta tafi cikin murna shi ko harkokinsa
    yakama. Shiru-shiru tana saka rai bashi ba
    alamarsa. Nan kuma tashiga daukar waya
    kannanta tana kiranshi, harma yadaina dagawa.
    Wataran taje tasamu ahmad tana kuka, ahmad
    yace taje zai ganshi. Rannan kuwa har gida
    ahmad yiyi sallama da abba yashiga rokon Abba
    ya maidota. Abba yace taje taroqi mahaifiyarsa
    dasu umma insun yarda shikenan. Har gida
    ahmad yaje ya fada mata, bata yi sanyi ba tanufi
    gurin umman bashir. Umman tana zaune da
    'ya'yanta suna shan farfesun kifin da ummi ta
    aiko musu dashi, tana ganin bishira ta hade rai.
    Tace, lapiya? Bishira tace lpy lau umma zuwa
    nayi in roqi gafararki. Tace nime kika min? Tace
    don Allah dai ki yafe ni, ina son indawo dakina
    Abba yace sai kin hakura, tace oho, yanzun kin
    yarda ina da kima agurinsa? To bari kiji bazaki
    dawo ba, mai baqar rowa kince nimai kwadayi ke
    kuma mai rowa ko? To kin gani wannan ummi ce
    ta dafo mana ta nuna mata kular kifi, sanda
    kinanan bana cin komai bansan dana yana samu
    ko baya samu ba. Yanzun abin arziki iri-iri
    kidawo ki toshemana kofar samu? Tace, wlh
    bazan toshe ba, umman bashir tace dukda haka
    dai bazaki dawo ba. Tayi takuka sannan tafita,
    har zata wuce gidan su ummanshi sai ta tuna
    kada suyi mata dariya sai tace baridai ta shiga.
    Kyakkyawar karba umma tayi mata suka gaisa,
    tazauna umma ta kawo mata ruwa ta amsa
    tasha. Muhibba tana ta tsalle tsallenta kan kujera
    zuwa jikin umma, umma tace ji hibba ki gaida
    mamanki, ga mamakin bishira sai yarinyar ta
    kalleta tace. Umma niba wannan bace ba
    momina, momina sun tafi da babana zaya kaita
    makaranta. Umma tace, wannan ma ummarki ce
    yarinyar taruga dakin tsohuwa tana cewa, ita ba
    ummarta bace. Bishira ta bita dakallo, yarinyar
    tayi bulbul gata cikin shiga mai kyau da tsafta
    kanta yaji kitso da 'yan duwatsu. Saita soma
    kuka tana fadin mahaifiyata ta cuce ni, umma
    tace a'a kece kika cuci kanki, inbaki dauki
    damuwarki kin kai mata ba yaushe zatasan anyi?
    To ynzun dai dubi 'yarki tana gudunki sbd bata
    sanki ba, ina amfanin wannan? Tsohuwa tace
    kukan wanikeji ta shigo tana kallon bishira cikin
    mamaki tace. 'yar nan kece haka? Ciwo kikayi ko
    ko duniya ce ta juya miki baya? Kai jama'a dubi
    yanda kika kare kikayi bikinkirin. Ita da tadukar
    dakai tare da cewa bnyi ciwo ba nidai nazo ku
    yafe ni, sannan ku roqa min abba ya yafe min in
    dawo dakina. Yace, bazan dawo ba har sai kun
    yafe min, amma naje gurin umman bashir ta kore
    ni tace bazata bari in dawo ba. Kuma gidanmu
    wuya nake sha, kusan rabin aikin gidan nikeyi ga
    qannaina duk sun raina ni. Umma tace, yi shiru
    share hawayenki bari zaki koma. Tsohuwa tace,
    ke dai kin cika sa kai a uku suwaiba, gashi abin
    kirki bai karbe kiba. Kina yi ana zaginki ana zagin
    'yarki, bishira ta ce wlh duk na daina, yanzu na
    gane kune masu sona, umma tace ba komai.
    Tadaga waya ta kira alhaji ta fada masa komai
    yace to yana zuwa donshi ya qosa asulhunta
    yarinyar ta koma dakinta saboda darajar
    tsohonta. Yana zuwa yaji komai nan ya daga
    waya yakira Abba, yace yana zuwa yana hanya
    ne yace to ya same su gida. Abba yana shigowa
    ganin bishira yahade rai ya zauna nan dai alhaji
    ya hada su yayi musu fada da nasiha, sannan
    yace baya son abba yace komai komai kuma ko
    sun koma gida banda tashin tashina. Bishira tayi
    ta godiya alhaji babba yace su tashi ashiga gurin
    umman bashir din tana ganinsu tahau cewa alhaji
    dakanka? Maimakon ace in zo? Umma tace, a'a
    keda zamu zo baki hakuri ai mu ya dace mu
    shigo. Nai dai alhaji yayi bata hakuri tace taci
    albarkacinta na hakura, amma da sharadi inta
    sake maimaita halin da tayi abaya ko taje ta
    takurawa ummi tofa saita tabar gidan. Bishira
    cikin kuka tace ta daina insha Allahu, nan itama
    umman bashir din tace dasu umma su yafe mata
    sharrin shaidan ne da qaryar barayin imani wato
    bokaye da 'yan tsibbu suka ce ba komai. Nan
    alhaji yace da abba yakai bishira gida, ba don son
    ranshi ba yadauke tazuwa gida, sam bata damu
    da daure fuskarshi ba, dadi da murna fal ranta.
    Yana sauke tazai wuce tace, don Allah ka yafe
    min sannan ka gaida min ummi, yace zataji. Tace
    to yaushe zan dawo? Yace, duk lokacin dasu
    alhaji suka zo gurin dadynku. Nan yatafi, ita
    kuma ta shiga gida, hajiya zainu ta tsareta wai
    sai ta fadi inda taje, tunda ta kira anty tace, bata
    can. Bishira tace naje ba mijina da surukaina
    hakuri ne, hajiya zainu tace ni dazai maida ki ai
    sai nafi kowa murna. Na gaji da zamanki da
    qazantarki, tunda babanku yaqi ki koma
    makaranta yakashe miki kudi ki goge ko kya
    samu mai kudin dazai aure ki, to gara kin koma
    can kin qarata. Abba kam shi tunaninshi ta ina
    zai soma sanar da ummi dawowar bishira? Don
    baya son ko kusa hankalinta yatashi, baya son
    wani abu yayi musu katsalandan a cikin
    daddadan zamansu, don haka ya share bai fada
    mata ba. Da dare alhaji da umma suka je, an
    sasanta sannan suka taho da alkawarin cewa
    gobe zata dawo dakinta. Washegari umma ta kira
    Abba tace ya share ma bishira daki yau zata
    dawo, yace umma nifa gsky dabata hankalina yafi
    kwanciya. Sannan ina ta tunanin yanda zan
    tunkari ummi da wannan zancen, umma ta riqe
    baki tare da rafka salati, yace ynzun tsoron
    ummin ka koma ne? Yace, a'a umma kin gata
    sakankance ynzun hankalinta yakwanta sai kuma
    taji nazo mata da zance dawowar bishira? Tace,
    shi kenan nina fada mata. Awaya ta kira ummi
    tafada mata cewa bishira zata dawo, duk datasan
    cewa matar mijinta ce dama, amma sai da
    gabanta yafadi. Umma taja mata kunne da cewa
    kada taji kada tagani, abba ranar sai kusan sha
    biyu zaije gurin aiki. Don haka yace kannanshi
    suje su soma fito da kayan kafin yazo sunzo sun
    fada ma ummi, ita ce ta bude musu dakunan don
    abba ya canza makulli bayan tafiyar bishira. Abba
    ya shigo tana zaune kan kujera sai tunani take yi
    na irin zaman dazasu yi in bishira tadawo.
    Yazauna tare dariko hannunta, tunanin me ki ke
    yi? Takalle shi, halin rayuwa nake tunani, yace
    yanzun umma ta kira ni jiya sun je gidan su
    bishira wai yau zata dawo. Ummi ta taba baki,
    Allah yakawo ta lpy. Ya ce ni ban soba gsky. Sbd
    ke ummi tadafa kirji, sbd ni? Ni ya abba, kada
    kasa duniya ta zage ni, Tare fa nasameku? Yace
    to ni dai kada kiga kamar da son raina, tace don
    Allah ya Abba kabar zancen nan. Kaje kagyar
    mata dakunanta don su kamal bazasu iya ba,
    yanufi gurinsu ganin kamar ya damu yasa itama
    taje tasa musu hannu don dai ya saki ranshi, sun
    gyara tsaf ummi ta goge sannan ta rufe dakin.
    Har magriba bishira bata ji an ce za'a maida
    taba, sai ta dauki wayar kanwarta ta kira shi wai
    yazo don Allah yadauketa. Tsakanin mata da miji
    sai Allah, nan ya tausaya mata yace zaizo, kafin
    ya isa sai daya sai mata waya irin dai ta hannun
    ummi. Har cikin gidan ya shiga suka gaisa da
    babanta, yayi murna sosai yayi tawa Abba
    godiya, tare da ba shi hakuri yace yasan yanda ta
    horu zai gata canza da yardar Allah. Yasa aka
    turo ta yayi mata nasiha, sannan ya gargadeta da
    cewa inhar ta bari mijinta yakawa kararta zatayi
    mamakin abinda zai mata. Tace, insha Allahu
    baza ta kara ba, yakawo kudi yaba Abba, da kyar
    ya amsa ita kuma ya bata wasu zannuwa acikin
    leda, yace su raba da abokiya zamanta. Taje tayi
    wa hajiya zainu sallama suka tafi, tamkar
    baquwa haka ta koma, sai kace basu taba zaman
    aure da Abba ba, nauyinsa take ji. Suna tafe ya
    ciro waya ya miqa mata, tasa hannu ta amsa
    yace taki ce, tayi ta godiya yace ba komai.
    Sallamarsu tasa gaban ummi faduwa, ta dake ta
    fito ta amsa, wani kishi ya tasho mata amma
    saita danne. Ta kalli bishira tare dayi mata sannu
    dazuwa, ta amsa tana kallon ummi tayi kyau
    tagoge daga ka ganta kaga wayayya 'yar gatan
    miji. Ta dauko makullin dakin ta ba bishira, abba
    kuma ya nufi dakin ummi. Bishira ta dinga kallon
    yanda abba ya gyara gidan yaja gini ta gefen
    ummi yayi mata falo da kicin, sannan tsakar
    gidan an gyare shi da tiles. Haka bandakin su
    yagyara shi, nan dai bishira ta shiga dakinta ta
    zauna bakin gado tana yi wa allah godiya tare
    dayi wa kanta alkawarin har abada bazata ta
    kara yin yaji ko ta janyo abinda zaisa mijinta ya
    sake ta ba. Ummi tana kan gado tana karanta
    wani littafi yazo ya zauna bakin gadon bata ko
    kalle shi ba don haushi take ji. Sai take ganin
    kamar rawar kai yake yi da dawowar bishiran,
    kuma tuntuni yana zuwa gurin ta ya boye mata.
    Yace madam ina son in yi magana da ku ne ke da
    bishira, ummi tace ina jin ka, yace can zaki zo
    muje. Tace, gsky nagaji, kayi maganar da safe.
    Yagama gano kishi ne ke damunta, don haka yayi
    murmushi yace yanda kikace hakan za'ayi. Ya
    fita kamar minti 30 yasake shigowa ya aje mata
    leda tare da cewa saida safe aciki tace Allah
    yabamu alheri. Yana tafiya taje ta banko kofarta,
    yau kam bacci ya qi idanun ummi sbd tayi sabon
    bacci a haqarqarin Abba. Dukkan filolinta ta rasa
    wanda zai maye mata madadin haqarqarin
    mijinta, ynzun yancan da wata tasan yanda yake
    wannan rawar jikin ynzun ya manta da batunta.
    Tarasa me yake mata dadi, littafin datake
    karantawa kuwa sam bata fahimtar abinda ke
    ciki. Hka ta dinga zubda hawaye har nisan dare,
    ganin bata da wata mafita, tashi tayi ta bude kofa
    lokacin 2 saura taje tayo alwala tazo ta kama
    nafila. Abba jin bude kofarta ne yasa shi leqowa
    ta window aranshi yaji tausayinta don yasan bata
    iya bacci sai ajikinshi, ita bata san ya leqo ba
    don ko hanyar dakin bata ishe ta kallo ba. Yakalli
    bishira wadda bacci yayi gaba da ita ya tausaya
    mata sosai yanda tayi tarawar jiki alokacin
    auratayyarsu dazun. Yadauko wayarshi yarubuta
    ma ummi sako. KI KWANTA KIYI BACCI BABY,
    TARE DA QISIMA CEWA KINA LAFE
    AMAKWANCINKI (WATO JIKINA) INA CIKE DA
    KEWAR LEBUNANKI. Tana sallah taji shigowar
    saqo amma bata yi ko marmarin dubawa ba, haka
    tai sallah har zuwa lokacin da bacci yasoma
    fizgarta. Tayi adduo'o'i sannan ta kwanta, saida
    asubahi ne datayi sallah sannan ta karanta, dan
    tsaki taja tare da cewa, Karya kawai, kishi yasa
    ta fadin haka don tasan Abba sosai baya boye
    mata komai ynzun. Sai dai abinda yasake qular
    da ita da asubahin nan yanda tana fita shi kuma
    ya fito wanka, duk da tasan dole wani abu yafaru
    tsakaninshi damatarsa, amma sai taga tamkar da
    gayya ya tsaya don tafito taganshi. Tna idar da
    sallah ta dora ruwa akicin dinta, tadafa ruwan tea
    taje kicin din bishira tadauko flask tazo ta wanke
    ta zuba musu ruwan zafi taje kofar bishira tayi
    sallama bishiran ce ta bude ummi tamiqa mata
    tare da cewa an tashi lpy? Cikin sakin fuska tace,
    lpy lau, nagode. Ummi ta ce ba komai takoma
    dakinta ta kulle kofarta don yau bata da darasin
    safe. Abba ma yau bada wuri zai fita ba, don
    haka yadan samu baccin safe sai 8 yayi wanka
    ya karya, sannan yanufi dakin ummi. Kofarta tana
    rufe, ya kwankwasa ta share sai can dai dataji
    yaqi tafiya sannan tazo tabude. Takalle shiya yi
    kyau cikin kananan kaya, ta kauda kai tare da
    cewa, an tashi lpy? Yace lpy lau, kin karya? Tace,
    um'um sai anjima, zata rufe kofar yace,
    makaranta fa? Tace sai karfe 2 nake da darasi.
    Ta maida kofar ta rufe, yayi dan murmushin
    takaici sannan yafita. Kwananshi 2 dakin bishira
    yayi niyyar dawowa dakin ummi, don ya kosa
    yadawo ya lallasheta bazai iya daukar wannan
    shariyar da take mishiba. Tsakaninta da bishira
    lpy lau amma shi sai tana wani share shi. part 33 the end
    Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:45
    Ya shigo da zumudi zai nufi dakinta, tamiqe cikin
    fara'a daga wanke-wanken da take yi ta amshi
    ledar hannunsa da jakar laptop ta nufi dakin
    bishira. Shida bishira suka bita da kallo, ganin
    zata shiga bishira tace ummi yau ai dakinki yake.
    Ummi tace injiwa? Anty bishara ai kullum ke ce
    dashi har sai kin rama duk kwanakin da kika
    dauka agida. Kinga kenan kusan wata goma sha
    daya kenan. Abba cikin sauri yace ke
    mahaukaciya ce? Ina ki kasamo wannan fatawar?
    Ta kalle shi, sannan tashiga dakin ta ajiye ta fito
    taqara kallonshi gurin malamai, yace to ban
    yarda ba, don haka zanci gaba dayi muku kwana
    bibbiyunku, ummi tace to ni na yafe mata nawa
    kwanakin bishira tace nagode ummi. Haushi ya
    cika Abba, amma shi bazai dauki wannan horon
    da ummi take shirin yi masa ba. Yadawo dakin
    bishira a fili yafurta kema saina baki haushi zakiyi
    dakin sanin wannan furucin. Sharewa yayi yaci
    gaba da kwana dakin bishira tare da nuna kulawa
    ga bishiran. Ummi ta jure duk da duk daren Allah
    sai taci kuka ta gode Allah, sannan tashiga zargin
    cewa shi ma ya Abban dama can yana son
    tarewa dakin bishira, inba haka bame zaisa yayi
    saurin yarda kuma yayi ta nuna mata soyayya?
    Ganin ummi tana yi tamkar bata damu ba yasa
    shi qa rajin haushi, yadawo da yamma suna
    zaune kowa A qofarshi. Ummi tayi kwalliya cikin
    qananan kaya, bishira kuma tana sanye da leshi,
    karatun littafi bishiran keyi ita kuma ummi tana
    yin gyaran qumbunanta. Bawai suna wata hira
    bane amma suna kula juna sosai musamman
    bishira tana son su saba da ummi. Ummin ce
    bata cika son fitowa ba, bishira ta tashi ta masa
    sannu dazuwa tare da amsar kayan hannunsa
    don yanzun tana koyi da ummi gurin kyautatawa,
    ummi ta kalle shi sannu dazuwa, ya amsa da
    yauwa baby. Yakalli bishira sweety zanyi wanka,
    tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai
    tazo tace masa takai nan kuma yajanyo bishira
    jikinshi. Ba wai yana da bukata bane, amma don
    ya shaqar da ummi sai ya banko kofar, qaran
    kofar ne yasa ummi kallon gurin dakin. Ta duqar
    dakai taci gaba da abinda take yi, kusan minti
    arba'in suka fito, Abba ya matsawa bishira wai
    suyi wanka tare, tace ni bazan iya ba akwai ummi
    dama da dare ne inajin kunya. Kuma kada taga
    kamar cin fuska ne, yace kenan don kada ki bata
    mata rai ni mijinki bazaki faranta min ba ko? Dole
    ta bishi suka shiga bayi. Baqin ciki yasa ummi
    tashi tashige daki, kuka sosai tayi daga nan bata
    fito ba sai magriba, tanayin alwala tarufo kofa,
    washegari ma qin bude qofar tayi daga alwalar
    asubahi. Abba yayi ta raba ido ya ganta amma
    bata fito ba, yasan fushi take, ya kira wayarta
    taqi dagowa yayi mata saqo cewa in zata
    makaranta tafito inkuma sai darana ta bude ta
    amshi kudin mota. Tana gama karantawa tayi
    wuri da wayar ba tare data bashi amsa ba, haka
    ya tafi. Bishira ta qwanqwasa ma ummi ta bude
    suka gaisa, tace naga baki fito bane ina fata lpy?
    Tace lpy lau bacci ne, tace yau baza kije
    makaranta bane? Ummi tace, zanje sai sha biyu.
    Bishira tace kinji dadinki ni gashi nan ina tayi
    masa zancen karatun amma ya share ni, ummi
    tace inkin matsa zai yarda, tace ko za ki dan sa
    min baki? Ummi ta riqe baki, ni a wa? Ke da yake
    hannunki ai ke ce zai saurara, ni kin zo ne ma ki
    zage ni. Bishira tace wane irin zagi? Ni dama ki
    amshi mijinki ummi don gangar jikinshi ce kawai
    agurina, amma ruhinsa yana gurinki. Ummi ta ce,
    ngd da zagi, bishira ta ce zancan gsky ne ba
    wani zagi. Haka suka yi ta rayuwa cikin kwanakin
    ummi kam har rama tayi shima Abba ya rage
    walwala don wanda yasan kan kula da shi
    kamarta. Yayi missing din abincinta. Amma ya
    gaji bazai jure ba. Ya tuna bishira tace masa zata
    ta yini gidan ummanshi. Don haka yana gama
    muhimman abubuwan da zai yi agurin aikin
    yanufi gida. Ummi tana shirin tafiya makaranta ta
    dauko jakarta sai kurum taga mutum kamar an
    jeho shi. Ta daure fuska tamkar bata taba dariya
    ba, yace ummi nagaji kin ji ko, na gaji da wannan
    horon naki. Laifin me nayi miki? In don na dawo
    da bishira ne sai in saketa, duk ba kece kika
    takura min sai na dawo da ita ba? Ummi tace, ni
    karka doran jakar tsaba kasa kaji su bini, ka saki
    matarka sbd ni? Ba ruwana. Yace, to ki dawo
    yanda kike, kuma ki janye batunki na wai kin
    haqura dani, niban haqura ba. Ke ma kuma nasan
    dole ki kasa kanki, ummi ta ce ni ban damu ba,
    ya ce qarya ne gashi nan duk kin rame? Ya
    canza daga fada zuwa lallashi, ummi don Allah
    na roqeki mu koma kamar da, haba bebyna. Ya
    lalubo hannunta ta qwace, don Allah ka tafi kada
    bishira ta dawo ta same ka anan ta zargi wani
    abu. Haushi yakamashi sosai, ya daga murya da
    qarfi, kin san Allah ummi zan hadaki da umma, ta
    nufi hanya fita, nikaga kada kasa ni yi latti don
    lokaci yayi nisa. Ya ficiko ta ta dawo ba zaki
    makarantar ba, ke an ma daina karatun tunda yafi
    ni. Ta zubar da jakar da hijabi ta nufi gado shi
    kuma ya fita cikin zafin rai, gidan su umma yaje.
    Bishira tana dakin umma tana sallah yabi umma
    kicin, umma gurinki nazo, ta dube shi lafiya
    Abba? Ya turo baki, alamun ranshi bace baki,
    yace umma ki sallami bishira, tace kamar yaya?
    Yace taje can gidan ko muyi maganar agabanta?
    Tace, kyale ta muje dakin babanku. Abba ya fada
    ma umma komai da ummi ke masa, tun dawowar
    bishira ran umma ya baci tace ka barni da ita.
    Banda shashancin ta da ita kadai take son
    azauna? Baga bishirar nan ba gidan nan ta gane
    kuskurenta ko yau yarinyar nan sai da tace in
    yafe ta nace ni dama ban riqe ta da wani abu ba.
    Shine ita zata qirqiro fitina? Yace, umma ai ba da
    bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane
    kurenta da dare kuzo kai da ita. Umma ce ta kira
    ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu
    don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar
    isha'i taje gidan. Can tasamu abba, nan ko umma
    ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo
    umma tafada mata komai sai ta shiga fada. Wai
    ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko
    ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya. Abba
    yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun
    in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma
    ni abin ya qare akaina? Nan fa umma tayi mata
    tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka
    kira shi awaya ya fita. Umma ta samu dama
    taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki
    yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice
    kinyi fushi da ita kin barwa kishiya? To kada in
    sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke
    ganinki da ita. Ta jima tana bata shawara kafin
    Abba yadawo suka nufi gida. Ya shiga gurin
    Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai
    kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,
    tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa
    aranar. ** ** ** ** Kwanci tashi asarar mai rai,
    shekara ta zagayo lokacin bishira da tsohon ciki,
    Abba nason yara don muhibba taqi dawowa tafi
    son umma dole suka haqura suka bar mata. Ta
    haifi 'yarta budurwa tubarkalla ranar suna ta ci
    sunan sahura inda suka sa mata walida. Ummi
    nason yara, don haka in tana gida to tana manne
    da walida, Abba yana damuwa da rashin samun
    cikin ummi, wanda ita ummin ta barma Allah
    komai. Shekaru uku sun sake biyo baya, lokacin
    Bishira ta sake haihuwar habiba takwara Abba
    yayi wa ummi. Tsohuwa an qara tsufa, 'yan
    rigingimu sun qaru tace ita Abba yama takwara
    amma bata son ya duke ta irin yanda yayi wa
    ummi. Abba kullum qara son ummi yake, umma
    ta matsa masa sai da yayi qoqari ya sai fili rabin
    filoti tace kuma a rage ciye ciyen dadin nan agina
    shì. Haka kuwa ya gina flat mai daki hudu, daya
    ummi daya bishira, sai nashi sannan na yara.
    Yayi qoqari gurin gyaran falon ita kuma ummi ya
    canza mata kayan daki don bishira an canza
    mata daza su tashi agidan su. Yace tabishi bashi
    in ya samu zai bata kudi amadadin kayan daya
    saima ummi, tace ta yafe. Ummi dake karantar
    (BUSSINESS) har ta hada (H.N.D) dinta kuma
    tayi bautar qasa. Abba dai yace baza'ayi aiki ba
    amma ya yarda tayi kasuwanci, Alhaji babba ne
    ya bata jari inda take saro kaya zannuwa, lesuna,
    takalma zuwa jakunkuna. Abin ya amsheta don
    har kayan aure tana hadawa, tana yin saqo irin
    su kwatano da chaina, india, pakistan ko dubai,
    ta hanyar wani wan kawarta. Haka kawai ummi
    ta samu kanta da zaban abinci, yawan bacci
    kasala da dai sauransu, sam bata san
    takamaiman lokacin al'adarta ba. Don bata wani
    lissafi in yazo shi kenan in bai zo ba bata damu
    ba tama cire ranta daga batun ciki. Abba ya kalli
    nonuwanta, baby kwanan nan kirjinki ya cika
    sosai, gashi kinyi haske ko kin canza mai ne?
    Tace yaya yaushe kazama likita? Yace, ummi kin
    fa canza shirya muje asibiti, ta ce ya Abba don
    Allah ka bar ni nagaji dazuwa asibiti. Yace, to ni
    zan je inya tambaya game da yanda ki ka canza.
    Cikin jin haushi tace sai ka dawo. Ga yara
    atsakar gida sun ishe mu, yace ni naki nake
    qawar in gani nasan addu'ar da nike yi bazata
    fadi kara banza ba, sannan ga qoqarin danake yi,
    shiru ta masa. Dagaske yake yi yaje yayi wa likita
    bayani, yace yadai kawo fitsarinta. Sai da suka yi
    tsiya da qyar bishira ta lallasheta ta yarda ta
    bada fitsarin. Rungume likitan yaya lokacin da
    yake fada masa ciki ne in dai har fitsarinta ne.
    Afalo gaban bishira da yara abba ya rungume
    ummi yana murna, ji tayi tamkar tsokana amma
    ganin ya zauna yana ta buga waya yanata
    yadawa ta amince cewa gske ne. Don haka ta
    tashi ta shiga dakinta tayi alwala tazo tayi nafila
    raka'a 2 cikin kuku take godewa Allah tare da
    addu'ar ya raba lpy. Ya bata mai albarka.
    Tsohuwa ma kuka ta saka lokacin da labarin ya
    riske su. Ummi taga gata musamman daya
    kasance cikin yazo da kumburi tayi sumtum. Duk
    kowa ya tsorata sbd tunanin ko hawan jininta ne
    ya tashi. ALLAH cikin Ikonshi data tashi haihuwa
    saita santalo danta cikin gajeriyar nakuda, sak da
    abba kwabo da kwabo. Rungume ummi abba yayi
    don murna, sunan alhaji babba ya sake maida wa
    kuma walid din dai suke kiranshi. Watan yaron
    bakwai ummi ta sake rasa kanta, kuka wiwi ta
    dinga yi shiko abba murna kamar yayi rawa.
    Tasake samun da namiji inda yaci sunan alhaji
    karami suka sa masa hibban. Haka suka ci gaba
    da rayuwa cikin haquri da juna, tsakanin bishira
    da ummi, bama irin bishira saboda abba baya iya
    boye son ummi. Kan 'ya'yansu ahade ba kya
    gane bambanci, bishira ta gane umma uwa ce
    guda har da rabi, don haka hatta shawara saitaje
    gurin umma kuma ko sabani suka samu da abba
    gurin umma take zuwa. Ita kuma umma ta dauke
    ta babu bambanci da ummi, don bata taba fada
    ma ummi sirrin bishira ba. Sahura yanzun ta
    yarda umma da alhaji sune rufin asirinsu, kuma
    gatan Abba, bashi ma da yayi aure gidan dasu
    ummi suka tashi nan ya zauna. Dangin bishira
    yanzun sunga bishira ta samu natsuwa sun
    sulhunta. Abba agurin aikinshi yana ta samun ci
    gaba, lamuran sai godiya. Ummi tashafa addu'ar
    da takeyi sannan tamiqe tana linke dardumar tace
    kallon me ka ishe ni dashi ne ya Abba, yace ina
    kallo ne na kusan samun da na uku wannan
    karon takwara zan ma kaina. Ummi ta jefa masa
    dardumar hannunta, daina min fata ni, yace ban
    karanci likitanci ba amma ni likitanki ne. Ta fada
    kanshi, ya rike fuskarta yana kallonta cikin ido,
    ummi lokuta da yawa ina zama inta tuna da,
    musamman in na kalli 'yan yaranmu wadanda
    suke matuqar kama dani, tace me kafi tunawa a
    baya? Yace, yanda kikayi ta kirana awaya kina
    tsara ni suhaylan kaduna. Suka sa dariya. Ni kam
    nafi tuna yanda ni da kai muka yi ta 'ZURFIN
    CIKI' dason juna. Yace Allah yabarni da ke har
    abada matata. Ta kwantar da kanta
    amakwancinta ''Amin mijina''. Muma Allah ya bar
    mu da masoyanmu har gidan aljanna, ya bamu
    lafiya dazama lafiya. Ya zaunar mana da 'yan
    uwanmu lafiya, Amin ya rabbi. ** ** ** ** Bayan
    shekara goma naje nasamu yaya Abba nace
    inason muhibba yace badamuwa yabani kyautar
    gida da mota. Ummi kuma ta hada mun kayan
    lefe saboda namijin kokarin danayi na rubuto
    maku wannan littafin aka daura mana aure da
    muhibbata muka tare muka cigaba da soyayya
    fiye dasu ummi ma.
    @BABA MONO HAXOR




    No comments:

    Post a Comment


Pages