• Bakin Ciki Hausa Novel's Part 2
    Bakin Ciki Hausa Novel's Part 2
  • BAKIN CIKI (TRUE LIFE STORY) 2 to 1
    Ta wuce inda aka aiketa kamar zata tashi sama sbda saurin ta dawo gida.Ta zube
    wa inna cefane,ko zama bata yi ba ta fara fadin "inna mama na cikin hankalinta kuwa? Tace,me tayi? "Kin san danliti ya dawo....""Danliti?" Waye shi? Dan gidan buzu mai shayi fa inna."Oho ,ina jin ki me yayi? Lokacin da aka yi bikin yaya Abdulrahman danliti yaga mama ya nuna yana son ta wlh a lokacin ko kallonsa bata yi amma ban san yadda aka yi ya shawo kanta ba,ynzun nan na gamu da ita Ta fito shagonsa leda cike da kayan sweet." Inna ta dafe kirji ido waje,mama fa kika ce? Wlh inna ni kaina mamaki ya kusa kashe ni.Danliti dan iska!"Inna tace,mun shiga uku ni saude wai! Ban ga ta zama ba dole in bincika na tabbata gidansu ba'a sa ni ba! Kai mama kamar mai hankali,me zai tsone mata ido a wajen yaron nan?Kai Allah ka shirya mana yara.Bari babanki ya shigo Insha Allahu yau din nan za ni gidan gara a yiwa tufkar hanci,kar ya kai mu ya baro!" Ya kamata inna,ni ina ganin ma kamar fada suka yi da Al-ameen don tun dawowar ta bata so ayi maganar sa."To ba sai ta fadi ba,ko yayyinta sun isa su kira shi su sasanta su balle ga iyayensa a gari."Ni ma dai hakan na gaya mata. Tace min babu ruwa na" "ita mama din ta fadi hakan? "Ko yanzu ta maimaita min kiris ya rage mu yi fada a titi,inna ta kuta,ta numfasa,kai jama'a yara halin su sai su,Ita fa ta kawo shi ba dole aka yi mata ba?Ta zabga tagumi bakin tana maimaita salatin Manzo,Da azahar mahaifin baraka ya shigo gida,inna saude ta maida masa halin da ake ciki.Nan da nan ya bata umarnin taje ta bincika,ai bata bata lokaci ba,cikin tsakar ranar nan ta kama hanya ta nufi gidan uban dawaki.Umma na daki tare da abban shi ma shigowarsa kenan gidan aka gabatar masa da abincin sa yana ci.-Inna ta shiga suka gaisa sannan suka koma dakin umman.Bayan sun gaisa da en hirarrakin zumunci kafin tace.magana ce tafe dani yaya amma ki duba ko alhaji ya gama cin abincinsa zan so in fade ta a gabansa."Nan take jikinta ya mutu,tace me ya faru saude?"To magana ce data shafi mama na rashin jindadi shiayasa nace ba zan bari ta kwana ba dole in zo in bincika,sai dai alhaji shi yafi dacewa ya sani,tunda nayi sa'a yana nan.Tayi dan tagumi......Subhanalillahi!Bari in yi masa magana.Ta mike jiki a salube ta shiga dakin abba ta iske ya kammala tace,wai magana ce tafe da saude idan ka gama ka taso muje,To muje gani nan".Ta gyara zama ta maida musu abinda baraka ta gaya mata umma ta shiga tafa hannu,abba kuwa sai daya mike."Kar dai ace shi ne yazo jiya da daddare?Lallai biri yayi kama da mutum,ina maman take? Umma ta dube shi ido taf da kwalla,tana daki. Kira min ita!Ta mike ta fita,har suka dawo tare babu wanda ya tanka sbda tsabar mutuwar jinin jikinta,a darare ta karaso dakin tana fadin,inna sannu da zuwa."Ta zuba mata ido,ke ma sannu."Ta gaishe da abba da umma na mata kallon mamaki,ta dube shi suka hada ido,tace abba ga-ni" yace,wanene yazo gun ki jiya? Ta sunkuyar da kai,tayi shiru,ya daka mata tsawa,ko baki ji ne?Nace waya zo gun ki jiya? Tana rawar lebe tace dan-liti?"Kin kuwa san ko waye danliti a garin nan? Tayi shiru,mama ni kike so ki mayar tsohon bnza,ki tozarta?jiya me na gaya miki? To ni ba hayaniya na kira ki mu yi ba domin a iya sani na ke mai hankali ce,kin san abinda ya dace,kin fi kowa sanin cewa saura 'yan watanni suka rage bikin ki.Sannan idan kika nutsu kika yi tunani ba mutuncin mu bane daga ke har mu ace an gan ki,kina karakaina a shagon wani ma,balle danliti sbda haka nake umurtar ki daga rana mai kamar ta yau,bana son in sake jin wani labari makamancin wannan!Ina fatan kin fahimce ni? Ta kara sunkuyar da kai yayin da idanuwanta suka fara tsiyayar ruwan hawaye,umma ta muskuta ta karbe "kin bani mamaki ba kadan ba mama,wai ma in tambaye ki,me kike nufi da bin sa har shagonsa? Shiru babu amasa,umma ta cigaba,wannan katon sakarci da me yayi kama?A zaton ki abin birgewa ne yadda 'yan mata ke tsayuwa kofar shagon samari suna amsar abin hannun su?Ban taba zaton hakan zai fito daga gareki ba mama kuma mun saurara miki ne kawai sbda wannan shine karo na farko da irin haka ta faru!" Inna tace,kin ga gidan nan da dukkan jama'ar gidan dake cikin sa ana ganin girma da mutuncin su musamman mahaifnki,don girman Allah kar ki bari wani ya rusa wannan ginin,ya hure miki
    kunne ya kai ki ya baro,kin ji mam? Ta goge
    kwalla bata ce uffan ba,abba yace,to mun ci mun
    rufe anan bana son ki sake aikata wani
    abinda zai sa ayi miki zama irin wannan,kin ji ni? Ta
    amsa da kai tana goge kwalla.umma tace
    tashi maza muje ki dauko min ledar kayan da
    aka ce ya baki,a iya sani na dai baki da yunwar su,maza
    tashi muje!Ta mike da kyar umma ta tasa
    ta suka je dakin ta dauko ledar.Umma ta
    fizge cikin zafi tace,Allah yasa in sake gani ko ji sai kin sha
    mamaki!" Ta fice ta bar dakin,ta bar
    mama cikin tashin hankalin da bata taba jin irinsa
    ba,har inna ta gama zamanta ta bar gidan mama na aikin
    kuka a daki domin dai tamkar sun kara
    debo soyayyar danliti ne sun kara antayawa
    cikin zuciyarta.Ita wannan ranar da suke kwakwazon
    an sanya mata ta jima da manta saurayin
    ma balle ranar,ba shi a idon ta ko birnin
    zuciyarta.Al'amarin ya daurewa iyayenta
    kai,shin wai me mama take nufi da kukan ta?
    Tambayar
    zukatan su kawai suke yi amma basu da
    tabbacin amsa.Karfe takwas da rabi cif!
    Lokaci ne
    da motar danliti ke fakin a kofar gidan uban
    dawaki,kai tsaya ya aiko yaro a kira masa
    mama,abba na nan a falo yana gadin
    zuwansa
    don haka yace da yaron yaje yace tana
    zuwa. Umma ta fito masa da kullin ledar kayan
    kwalamar da ya ba mama Abba ya karba
    ya bi
    bayan yaro kamar jiya,yau ma yana
    harde jikin
    motarsa yana kada mukullai sai dai yau kananan
    kaya ke jikinsa,gaba daya ya firgita kofar
    gidan
    da kamshin turare.Yana hango uban
    dawaki
    tilasa ya gyara tsayuwa yana 'yan kame kamen
    gulma ko kafin ya karaso ya tsugunna
    yana
    fadin,sannu alhaji,yace yauwa sannu,ya
    sake
    fadin ina wuni? Lafiya kalau,mike abin ka,magana
    zamu yi,ya mike a hankali yana sunkuyar
    da kai
    kamar muminin gaske.Abba yace
    magana guda
    daya ce nake so zan gaya maka danliti,'ya ta
    sakeena na riga nayi mata miji,tuni aka
    sa musu
    rana har ma lokacin ya kusan zuwa da
    yardar
    Allah sbda haka ina rokon ka da girman Allah
    kayi hakuri ka nemi wata,daga yau kar ka
    sake
    zuwa gun mama don tana da miji,ina
    fatan ka ji
    ni? Ya dan yi shiru jim kafin yace naji alhaji
    amma nima ina roqon arziki ka bar ni in
    rinka
    zuwa muna gaisawa,tnda ba'a daura
    ba.Wlh..."Abba ya katse shi,ba zai yiwu
    ba danliti domin koda babu alkawarin wani akan
    mama kai
    kanka ka sani zai yi wuya ka sami
    auranta,sanin
    kanka ne kaf garin nan babu wanda ya
    san tushenka,kaje kayi tunani mana.Ya saki
    baki
    yana kallon abba ran sa a bace,abba ya
    mika
    masa keda yace ungo nan,yasa hannu ya
    karba kafin ya cigaba da fadin,abubuwan daka
    bata ne
    dazu tunda ba auranka zata yi ba bai
    kamata ta
    amshi kayan ka ba.Don Allah kayi hakuri
    ka nemi daidai kai,sai da safe.Ya juya ya shige
    gida
    abinsa ya bar danliti a tsaye.
    )Ya kara harde kafafuwansa yana irin
    murmushin mugunta,sannan yace ko
    banzo ba ita zata zo wajena,koda kuwa kasheta
    zaku
    yi ta
    dawo.Dama ai zuwan nawa na hure
    kunne ne ba
    wai neman nake da gaske ba."Yayi er
    budurwar dariya ya bude motar sa ya shiga ya sake
    fadin,sai ni dan gidan buzu mai shayi
    taba ni
    kaga tsiya da bala'I!Ya ba mota wuta
    yaja ya bar
    harabar gidan hankalinsa kwance.Sabanin mama
    da take ji kamar ta saci jiki cikin daren
    nan taje
    wajen danliti shiyasa tayi ta leken
    falo,amma
    kash!Abba da umma sun ki tashi har dare yayi
    sosai suna tattauna zancenta.Daren nan
    bata yi
    barcin kirki ba sbda bakin cikin an hana
    ta fita
    ganin danliti.Gari ya waye ko alama umma ta ki
    sakar mata fuska,sam abin bai dameta
    ba Allah-
    Allah take yi kowa ya kama
    gabansa,itama ta
    samu ta sulale,ai kuwa abba na fita karfe goma
    umma ta gama abnda take yi,ta dare
    gado kamar
    yadda ta saba barcin safe,mama ta gama
    caba
    kwalliyarta ta sadada ta bar gidan.Ta kwarara
    sallama kofar shagon danliti,ya taso cike
    da
    fara'a yana amsawa kafin yace,a zatona
    ke ma
    zaki juya min baya ne,har na fara shiga damuwa,jiya
    sam ban yi barci ba.Ta dube
    shi
    cike da tausayi tace nima haka danliti ko
    gyangyadi ban runtsa ba,me zai sa na
    juya maka
    baya alhalin na san cewa nima zan cutu? Ya zura
    mata ido a marairece yace,abbanki ya
    nuna baya
    so na ban san yadda zanyi da rayuwata
    ba
    sakeena,kar ki bari ciwon zuciya ya kama ni.Kwalla
    suka taru cikin idanuwanta tace
    ka
    daina fadar wannan maganar don
    Allah,in ka ga
    na rabu da kai to sai dai su kashe ni in
    daina numfashi,zuciya ta kai take so kuma
    bana
    ra'ayin auran kowa face kai." Kwalla suka
    zubo bisa kuncinta.Da sauri ya
    tauko sabuwar tìshu kware ta ya yago ya
    miko mata,"share hawayenki, ki daina kuka.Na
    yarda
    dake sakeena,amma mece ce mafitar
    mu? Ta
    dan kada kai tace, "zanyi tunani,ka ban
    dan lokaci kadan,zan samo mana mafita.'ya
    daga
    kanta ya fito ya gyara zaman benci.Yace
    zauna
    kiji
    Ta zauna gefe shi ma ya zauna ya fuskanceta
    sosai yace,me zai hana ba zaki gaya
    musu ni
    kike so ynzu ba?Ta daga ido ta dube
    shi,jim,amma ba tace komai ba,yace "kar
    kiji tsoron komai kai tsaye ki gaya musu ke
    kin
    sauya ra'ayi ni kike so,za'a yi miki tilas
    ne?Dole
    a baki wanda kike so,don babu wanda zai
    zauna miki da shi,idan kuma kina son in rasa
    raina ne
    shikke nan........Ta kada kai tace,"nace ka
    daina
    fadar rasa rai danliti idan ka mutu nima
    mutuwar zan yi.Ka kwantar da hankalinka insha
    Allahu a
    yau zan gaya musu na sami sauyi wanda
    hankalina yafi kwanciya."Ya dafe kirji,ya
    lumshe
    ido yace,kin sa naji sanyi cikin raina sakeena.Ya
    bude ido ya bi ta da kallo ya cigaba,idan
    kika yi
    min haka kin gama min komai sarauniya
    ta,ba
    zan cika baki ba sai mun yi aure zaki ga tsantsar
    son da nake miki,bana jin akwai wata 'ya
    mace a
    fadin duniyar nana da zata sami irin
    gatan da zan
    nuna miki." Tayi dan murmushi tace,Allah ya
    nuna mana,yace amin.Ya dan gyara
    zama ya
    sake gadin,"wai sakeena kin san cewa
    kin fi
    kowa kyau a duniyar nan?Ta saki baki,ido waje
    tace,duk duniya? Wlh duk duniya babu
    mace mai
    kyau irin naki,ta kada kai tana murmushi
    tace,"ka
    daina fasa min kai danliti,ni na san ban kai ka
    ba,ya washe baki ya nuna kansa ya9e "ni
    kuma?
    A'a ni dai kike son ki fasawa kan,ina ni
    ina ke?
    kin gan ki kuwa?kin ga wannan dan bakin naki
    dagwas ba karamin kashe min jiki yake
    ba."Ta
    sunkuyar da kai tana 'yar dariya ya bita
    da kallo
    yana shafo habarsa."Mama!" Muryar kawai taji
    anyi mata wani gigitaccen kira,gaba
    dayan su
    suka kalli mai magana,ta bi shi da kallo
    babu
    tsoro ko wata fargaba tace,ah!yaya ali! saukar
    yaushe?"Ya kara tsuke fusk,yace me kike
    yi
    anan?"Tace me kuwa?Ba komai,taso
    muje
    gida,kaje ina zuwa,"ina wasa dake ne? nace ki
    taso mu wuce." "Ta dubi danliti suka
    hada ido
    yace,tashi ku tafi sai wani lokaci ko?Ta
    dan
    numfasa ta mike ta wuce,yaya alin dake tsaye,ya
    bi ta da sauri ya sameta,"mama,wai
    mafarki nake
    yi ko kuwa gaske ne?Ta yamutsa fuska
    "da aka
    yi me?" Zaune na gan ki kofar shago kina hira da
    wani...." 'Wani? Ba ka ma san danliti
    ba?"Shut up
    don Allah!waye danliti kike gaya min
    magana ba
    dadin ji?Hauka kika yi?Ina mutunci ga'ya mace
    tana hira da maza a kofar shago gaban
    jama'a?
    Ban san ki da wannan ba,yaushe kika
    canza
    mama? Ta ballo masa harara ta ja dogon tsaki ta
    kwahsi sauri ta wuce shi,shi ma ya biyo ta
    yana
    fadin,ban gane nufin ki ba?"Ta juyo ta
    dube shi
    tace,wai menene yaya ali?"Shi kike so?" 'Ai
    kaji,menene na sake tambaya?
    ya kara cika da mamaki,'Ban fa gane shi
    ki
    ke so ba mama.Ina Al-Ameen din?" Ido
    jajur! Ta dube shi,"kai ka san wannan sunan,don
    girman
    Allah ka kyale ni da tambayoyin nan." "Ba
    zan
    kyale ki ba Mama,hasali ma sai na gaya
    wasu Abba.Wannan ai zubar da mutunci ne da
    cin
    amana!Me ya tsone miki ido a wajen
    Dan-Liti?Ke
    ma kin shiga sahun 'yan matan da yake
    ruda da kyan sa ne?Kai na ya daure Mama.Allah
    yasa
    abinda na ke gani da ji ba gaskiya bane."
    Da
    gaske ne yaya Ali! Kuma ko baka gayawa
    su Abba ba,ni da kaina zan gaya musu."Ta
    zura da
    gudu ta bar shi tsaye, shakare da
    mamakinta.Kafin ya iso gida kansa,ya
    kusa
    fashewa sbd tunani da al'ajabi.Rokon Allah kawai
    yake yi Allah yasa mafarki yake yi. Kai
    tsaye
    sasan su Mama ya zarce.Suna tsakar falo
    umma
    ta tirke ta da tambaya,"Idan biki gaya min inda
    kika je ba sai na sumar dake yau a gidan
    nan!"Yayi sallama.Umma bata iya
    amsawa ba,sbd
    bacin ran da take tare dashi.Ya-ce,'yanzu
    na koro ta daga shagon Dan-Lati suna
    zaune bisa
    benci suna hira Umma.Yaushe Mama ta
    sauya
    haka? Tuni Umma ke sallallami,ta dafe
    kirji ta-ce "shagon Dan-Lati ki ka koma Mama?Mu
    kike so
    ki zubarwa mutunci a garin nan? Ai kuwa
    baki
    isa ba,ba ki isa ba Mama!'Ji ka ke tim! Ta
    rufe ta da duka ta ko'ina.kafin yaya Ali ya kawo
    mata
    dauki,ta sha dan banzan duka.Kukan ta
    ya watsu
    cikin sassa,matan gidan da kananan yara
    suka sheko don ganin meke faruwa?Al'amarin
    ya
    daure masu kai,ganin Mama na birgima
    tsakar
    falo tana ture hannayen Yaya Ali dake
    kokarin rarrashinta
    [11/01 19:21] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***2(TRUE LIFE STORY)
    Wa ya mutu Ali? "suka tambaya,yayin da
    umma
    ta fito daga daki dauke da wayar rediyo
    kafin su
    yi aune,ta fara tsula mata.Haba gaba daya
    matan suka cafke hannun Umma, 'Hajiya
    Halima!
    Lafiya wannan abu haka?Me ta yi da zafi
    irin
    wannan duka?" Umma na haki tace wai yarinyar
    nan ita ce zata siyar mana da mutunci?
    Ta rasa
    wanda zata tsaya da shi, sai Dan-Liti?
    "Dan-Liti?
    Waye Dan- Liti?"Dan gidan Buzu mai shayi mana!
    Yau kwana uku kenan muna fama da ita
    ta rabu
    da yaron nan,ta ki! Jiya yazo kofar gidan
    nan.Alhaji da kansa ya same shi ya gaya
    masa tana da rana a kanta.shine don dibar
    albarka ta
    bi shi shagon sa,yanzu Ali ya ganta ya
    koro ta!
    Wace irin tijara ce wannan sbd Allah!
    Tuni suke kallon juna suna tafa hannu,hajiya
    hajo tace "danliti kuma?Waye bai san
    tarihin su
    ba a garin nan?Yaron da tun tasowar sa
    garin
    nan basu da aiki sai bata 'ya'yan mutane koda
    baki da wayau sosai ai kin yi dan
    hankalin da
    zaki gane buzu mai shayi kasurgumin
    kwarto
    ne,shi kuwa danliti kananan yara sau nawa ana
    kama shi dasu?Ko kin mance ranar da
    dubu ta
    cika suka ci shegen duka.Danliti ya sha
    da kyar
    shi kuwa buzu ya shura barzahi?Me ya dawo da
    shi kike kwadayi da har idon ki ya rufe
    kika kasa
    duban kazantar dake tare dashi?Hajiya
    Gaje tace
    "duk ba ma wannan ba kina nufin zaki fasa auran
    Al-ameen ne?Umma tace,karya take yi
    sai dai
    bayan ran mu,bari kuma alhajin ya
    dawo,yau din
    nan zai maida ta minna tnda zaman naki anan
    abinda ya haifar kenan!Ta tashi da gudu
    ta fada
    dakinta har da danna sakata ta bar su
    nan suna
    maida yadda aka yi. Shi dai yaya ali tunda ya
    sunkuci jakar sa
    ya
    fada dakin mahaifiyarsa bai sake
    kyakkyawan
    motsi ba sai tsabar tunani.Muryar
    mahaifiyarsa yaji a kansa tana fadin,"kai kuma
    yaushe
    ka
    shigo garin?"Firgigi ya dube ta na'am!"Ta
    zura
    masa ido,nace yaushe kazo?Ya sauke
    gwauron numfashi yace,"zuwa na kenan
    inna".ciwon daya
    sami mama,ai ya same ni domin jinin mu
    daya......"Gafara can sakarai kai ka san
    wannan,da su ma sun san cewa jinin ku
    daya ba'a hana ka auranta ba ai sbda haka
    ban ga
    dalilin dogon tunanin da kake yi ba,don
    daga ita
    har iyayenta basu san ka na yi ba!Gara
    tun wuri ka halkantu ka gane cewar alhakinku ne
    ya
    kamasu!Idan ba haka ba,ina mama,ina
    danliti?
    Marasa asali da tushe ga tarin abin gori
    da na kunya a jikin sa?"Ya dafe goshi
    idanuwansa suka
    kara kadawa,yayi hucin zafi ya
    dubeta,"duk
    wannan maganar bata taso ba inna
    abinda nake so ki gane shine muddin mutuncin
    mama
    ya
    zube,to martabar gidan nan gaba daya ta
    fadi,ashe kuwa dole in damu tnda nima
    dan gidan
    nan ne,ga shi kuma mama ta dauko hanyar bada
    mana kasa a ido.
    Tace can dai zata badawa iyayenta masu
    kwadayi,ban sa aka ba balle ya dameni
    wahalar
    banza kake yi dama ruwa da abinci ka samu ka
    ci,daya fiye maka wannan sakarcin!Ya
    sake dafe
    goshi yana kada kai,me yasa innar sa
    baza ta
    gane ba?Takaici ya kara kama shi ya sunkuci
    jakarsa ya koma dakinsu.Haj Gaje ta
    shigo
    saboda gulma ta cigaba,sharri kala kala
    suka yi
    ta jifar uban dawaki da su.La'asar sakaliya abba
    ya dawo gida ya iske idanuwan umma
    sun jirkita
    jajur!Ga kumburi sun yi,ko bai tambaya
    ba ya
    tabbatar akwai abinda ke damun ta,don haka ya
    kasa cin abincin data kawo masa,ya zura
    mata
    ido yace kamar akwai abinda ke damunki
    sadiya?
    Tace akwai matsala alhaji amma ka ci abincin
    sai mu san abin yi."Fuska ki ta bayyana
    tashin
    hankali dake tare da ke ban jin abincin
    nan zai
    iya wuce min ba tare da naji damuwae ki ba.Gaya
    min uwargida,ni kadai gareki
    wanda zai
    saurari kukan ki."Ta dan yi murmushi
    karfin hali
    tace mama zata siyar da mutuncin mu a
    garin nan gara ka dauketa ka maida minna ko
    abj ta
    zauna can har zuwa lokacin
    bikinta."Gaban sa ya
    fadi yace,me tayi?Bata daina zuwa
    shagon yaron nan ba,yau ali da kan sa ya koro ta
    tana
    zaune
    bisa benci suna hira,benci fa a kofar
    shagon
    bakin titi?Kamar mama yadda muke a
    garin nan take zama tare da danliti?Ta goge
    kwalla,ina zan
    sa BAKIN CIKI Alh,anya kuwa mama ce
    ke aikata
    wannan abu?Hankalin alh yayi
    mummunan tashi ya fuskanci umma da kyau ya
    sanyaya
    murya
    yace,ki daina zubda mata hawaye halima
    ke
    mahaifyarta ce,sai abin ya kara wargaje
    mata......" "Ba yin kai na bane alhaji,hawayen ke
    tilasta
    wa kansa zubowa."Yace duk da haka ki
    rinka
    daurewa kina mata addu'a,insha Allahu
    gobe zan maidata minna ko ta ki ko ta so dole ta
    zauna.Ni
    abinda ban gane ba shine,tana nufin ta
    fasa
    auran Al-ameen ne?Idan wani abu yayi
    mata ai sai tayi bayani,ba wai ta nemi ta maida
    mutane
    sakarkaru ba!Ina take ne?"Tace tana
    daki a kulle
    tun safe daya koro ta,haushi yasa nayi
    mata duka har ynzu bata fito ba."Ya mike cikin
    fushi
    ya nufi dakin ya buga da karfi yana
    fadin,"tashi ki
    bude kofar nan!"Tana budewa ya cafko
    hannunta ya jawo ta zuwa falonsa,hakan ya sanya
    mama
    cigaba da tsiyayar hawaye,ya cillata
    tsakar dakin
    ta zube gefen ummanta.Ya zura mata ido
    yace,"ashe wani lokaci zai zo da zamu ce ki bar
    abu ki ki bari mama?Kin dai san
    maganara auren
    ki da al-ameen ko?To ynzu nake so ki
    gaya min
    manufarki ta bin danliti shagonsa.Gaya min inji
    tun kafin mu tara 'yan kallo!Tayi kasa da
    kai
    kukan ta ya karu.Abba ya daka mata
    tsawa,"kuka
    na tambaye ki? Ki gaya min dalilin bin sakaran
    yaron nan nace?Ta cigaba da share
    kwalla tana
    mutsu mutsun rashin gaskia,leben ta na
    makyarkyata tace,"shi....shi na
    ke......na..na...ke so ab...."Umma ce ra doke ta da
    bayan
    hannu
    tace rufe mana baki mara kunya!"Ta dubi
    abba
    dake tsaye sake da baki tace,"ka ji ko?Ni
    na san take-taken ta kenan!"Ya matso ya cafki
    kunnenta
    cikin tsawa yake magana."Idan barci kike
    yi to ki
    farka ki bude kunnuwanki da kyau ki
    saurare ni! Ni ba tsohon banza bane,in har kin ga ki
    auri
    yaron nan,tabbaci hakika ni uwaisu na
    mutu an
    binne ni cikin kabari na!
    Ya girgiza kunnen kamar zai tuge shi,kin ji ni!
    Wannan itace magana ta karshe da zanyi
    akan
    danliti kuma gobe ki shirya kayanki zan
    maida ki
    minna!"Ya shirga mata dundu tare da fadin,"tashi
    ki bani wuri!Ai bata iya tashi ba nan ta
    baje ruf
    da ciki sbda tsananin zafin dundun da
    yayi mata
    abnda bata saba ba,sai ta ji shi har cikin kayan
    cikinta sun dau zafi ba kadan ba,Ta fasa
    kara
    mai shiga zuciya tace wayyo Allah na
    shiga uku!
    Na shiga uku!Yaya ali ya mike a firgice,gabansa
    ya yanke ya fadi ya fito da sauri yana
    tsinkayar
    kukan mama,ya nufi sasa.Umman ke
    fadin,'ba ki
    shiga uku ba mama sai nan gaba muddin baki
    dauki nashihar da muke yi miki
    ba!"Hannu biyu
    yaya ali yasa ya ciccibe ta ya mikar da
    ita,zafin
    duka da tsananin BAKIN CIKI dake dankare cikin
    ran ta yasa ta kwakume.Yaya ali bakin
    gado ya
    zaunar da ita ya dago fuskar ta hannu
    biyu yake
    share hawayenta,yayin da nasa kwallan ke
    neman sauka,yace "haba mama ki yiwa
    kan ki
    fada mana!"Murya na rawa tace,me nayi
    masu
    yaya ali!Sbda Allah me nayi?"Me kika yi? ynzu a
    wajen ki wannan ba laifi bane?Haba
    mama!Ba
    haka kike ba,kin sauya da yawa kar dadin
    bakin
    danliti yasa hankalin ki ya gushe,laifin me al-
    ameen yayi miki kike so ki yi masa
    wannan
    sakayyar?A zato na koda babu Al-ameen
    nine
    mutum na farko daya kamata ki fara kawowa ran
    ki don na dade ina yawo da ciwon son ki
    mama.Ki tausaya mana me zai sa ki
    canza
    kyawawan halayen ki?
    Ya Girgiza kunnen kamar zai tuge shi. Kin ji ni!
    Wannan itace maagana ta karshe
    da xanyi
    akan Dan-liti, kuma gobe ki shirya kayan
    ki, zan
    maida ki bani wuri. Ai bata iya tashi ba,
    nan ta baje ruf da ciki, saboda tsanannin xafin
    dundun
    da yayi mata. Abinda bata saba ba, sai
    taji shi
    cikin kayan cikinta sun dau xafi ba kadan
    ba. Ta fasa kara mai shiga xuciya. Tace wayyo
    Allah na
    shiga uku! Na shiga Uku! Yaya Ali ya
    mike a
    afirgice, gabansa ya yanke ya fadi, ya fito
    da sauri yana tsinkayar kukan mama, ya nufi
    sasan.
    Umma ke fadin baki shiga uku ba Mama,
    sai nan
    gaba muddin baki dauki nasihar da
    mukeyi ba miki ba! Hannu biyu Ya Ali ya sa ya
    ciccibeta ya
    mikar da ita, xafin duka da tsananin
    BAKIN CIKI
    da ke dankare cikin ranta ya sa ta
    kwakume Ya Ali. Bakin gado ya xaunar da ita ya
    dago
    fuskar
    ta hannu biyu yake share hawayen ta,
    yayin da
    nasa kwallan ke neman sauka. Yace,
    haba mama kiyi wa kanki fada mna! Murya na rawa
    tace, me
    nayi musu Ya Ali? Saboda Allah me na
    yi? Me
    kikayi? Yanxu a wajenki wannan ba laifi
    bane? Haba mama! Ba haka kike ba, kin sauya
    da yawa
    kar dadin bakin Danliti ysa hankalinki ya
    gushe.
    Laifin me Al-ameen yayi miki, kike son ki
    masa wannan sakayyar? A xato na koda babu
    a
    alameen, ni ne mutum na farko daya
    kamata ki
    fara dawowa ranki, don na dade ina yawo
    da ciwon sonki Mama, ki tausaya mana, zai
    sa ki
    canja halayenki? Ta xuba masa kwala-
    kwalan
    idanuwanta da suka kara fitowa waje
    jajur! Tace, Yaya Ali ina ganin girman ka, ka kyale ni
    da
    wadannan surutan, don ba xa suyi tasiri
    ba. Ni
    nace ina so Al-ameen, yanxun kuma
    bana son shi Danlilti nake so. Ra'aryi nane, ba sai a
    kyale ni
    ba, ko akwai wanda zai zauna min da
    shi? Ya
    bita da kallo, ta sa aya kafin yace, ki
    daina tunanin wannan ra'ayin na ki mai yuwuwa
    ne, kin
    dauko katon aikin da xai rushe martabar
    gidan
    nan a idon jama'a. Idan baki son Al-
    ameen, ki musanya da ni Mama, zai fi miki kyau a
    bisa
    shirmen da kie sonyi. Ta runtse ido tace,
    yaya Ali
    je ka kawai! Ba ki son gaskiyya? Ta
    kauda kai kwalla na tsiyaya. Ya sanya murya yace,
    xan bar
    ki ki kwanta kiyi tunani sosai, cikin kan ki.
    Ina
    rokon ki girma da Allah, ki manta da
    kudirin da kika dauko. Bata tanka ba, haka bata
    dube shi ba
    yace, A bakin tofa ya tsaya ya kare mata
    kallo
    kafin ya sake fadin, bana so ana taba
    jikin ki mama, tamkar ni ake tabawa nakeji. Pls
    ki sauya
    tunaninki. Haushi ya kara kuma ta, ta
    juya masa
    baya. Ya fice yana kara waigen ta. A
    daren nan daga ita har Yaya Ali babu wanda ya iya
    cin
    abincin balle barci. Tunanin Mama shine
    xata ga
    yadda za'ayi a raba ta da garin nan. Cikn
    xuciyar ta tasha alwashin ko sun maida ta, zata
    dawo,
    dole su gaji su kyale ta da wanda take
    so. Dalilin
    da yasa ke nan, yau kwata-kwata taki
    bude kofar ta, kowa yayi bugu, iyayinsa har
    kawunninta, sai
    dai kalaman bakin su suka kare. Amma
    mama
    taki bude kofarta. Duk wanda ka duba
    ransa bace yake, musamman Abba, fuska
    kamar gobara
    ya dubi Umma yace, dauko min tabarya!
    Ta mike
    a salube ta shiga kicin ta dauko masa
    tabarya, ta mika masa. Alh basiru yayi caraf! Ya
    karba. Yace
    karka balle kofar nan yaya, asara biyu
    xa'ayi.....
    Yace yarinyar nan dole ta bar garin nan,
    ba xata xauna tana jawo min xagi ba, ana kallo
    na tsahon
    banza, bansan abinda nake yi ba! Buge
    min kofar
    nan, ko ka ba ni da kaina, in sauketa!
    Kowa yayi cirko-cirko. Alh. Basiru ya kai wa kofa
    duka da
    tabarya, sai ga sallamar Yaya abdul-
    kareem.
    Basu gama amswa ba, yaci gaba da
    tambaya, lfya? Me ya faru da kofar? Abba yace,
    nayi farin
    cikin xuwanka, don ni ma a yau nayi
    niyyar tafiya
    gunka. Me ya faru abba? Umma ya naga
    kamar kina kuka? Yace, mama ce.... Me ya
    sameta? Ya
    kwashe kaf halin da suke ciki ya gaya
    masa. Kai!
    Bai gaskanta kunnuwansa ba, shi yasa
    yace, abba ban yarda da wannan maganar ba,
    ya
    kamata asake bincikawa. Abba ya xuba
    masa ido
    jajur! Yace, wannan maganar ni Uwaisu
    nake gaya maka ita. Abdul kareem kasan kuwa
    ba za
    ayiwa mama kage ba, domin ni na
    haifeta.
    Saboda haka gidan ka xata xauna can
    har xuwa lokacin bikinta! Yace, ya xama wajibi, don
    ganin
    nan da kuka yi min xuwa nayi in tafi da ita
    dama.
    Al'ameen ya damu kwarai har yana ganin
    kamar wani abu ne ya faru da ita ake boye
    masa. Wlh
    jiya ya turo mahaifiyarsa da yamma wai
    ta zo ta
    bincika masa lfiyar mama, shine nace shi
    kwantar da hankalinsu Insha Allah da kaina xanje
    in dawo da ita. Wannan al'amari ya daure
    min
    kai. Yaushe mama ta canza haka? Kawu
    Basiru
    yave xancan banza takeyi, tunda ita ta kawo
    Al'ameen har aka sanya musu rana, bata
    isa tace
    ta canza shi ba! Wannan karya take yi.
    Haushi ya
    kara kure yayanta, ya mike ya suer tabarya ya
    kaiwwa kofar duka sau biyu kofar ta
    balle, bata a
    dakin. Ya nufi kofar bayi ya murda can
    ma
    garkamen yake, bai tsaya wata-wata ba, ya maka
    mata tabarya. Bugu daya kofar ta
    wangem, sai
    ga mama jikin bango ta fita hayyacinta
    saboda
    tsabar kuka. Al'amarin tamakar mafarki yayana
    yake gani. Ya xura mata ido, yace hauka
    kikayi
    mama! Me Al-ameem yayi miki? Iye? Yayi
    miki
    laifi ne da ba zaki fada ba! Sannan ki rasa wanda
    zaki bi, sai dan liti!
    Kinji abinda nace? Kin yi karya ki xuabar
    mana
    da mutunci a garin nan! Zo mu wuce, ban
    son jin
    komai daga gareki! Ta sulale kasa hannaye biyu
    bisa kanta, ta kara fasa kuka mai
    tsananin
    gaske. Matan gidan suka kutso kai cikin
    bayain
    suka tarairayo ta, suka fito da ita dakin. Yaya
    yana fadin ko mutuwa zakiyi yau, sai na
    tafi dake
    mu je can idan Al-ameen ya kira waya, in
    tambayehsi a gabanki, muji abinda ya
    hadaku! Amma yaro na sonki yana tattalinki.
    Iyayeynsa
    na ririta ki, tashi guda kice ba kiyi da shi,
    aikin
    san wannan karya kikeyi. Ina kayan ta
    suke umma? Hada mata si don baxan bata
    lokaci ba!
    Gaba daya suka yanyame ta da fada
    kowa na
    fadin albarkacin bakinsa, su Umma na
    hada mata kaya. Su Hajiya Hajjo na rarrashi ta suna
    bata
    baki tare da gyara mata jiki da fuska.
    Yaya Ali
    kuwa yana xaune gefe rayuwa tayi masa
    bakikkirin! Ana janta, tana togewa suka saka ta
    gabn motar yayanta. Ya jefa jakar ta
    gidan baya,
    daga nan yayi sallama ransa bace, ya ja
    motar
    yayi gaba da mama. Dole ne ya saurar daidai
    shagon Danliti, domin akan mahada
    shagon yake.
    Tsayuwar su wajen, ya jawo hankalin
    Danliti
    xuwa garesu. Ya xuba wa Mama idanuwan sa
    suka sha kwalli rangadau! Haka ita take
    kallonsa
    kwalla fal! Suna neman sauka. Ya daga
    kanka ta
    fito kofar shagon, irin duban da yake mata ya
    bayyanar da damuwarsa karara bisa
    fuskarsa.
    Tausayinsa ya lullubeta, nan da nan
    hawayen
    suka fara bulbula. Yayanta bai kula ba, kokarin
    sa, duk motocin da suka kawo, suka wuce
    shima
    ya samu ya haura. Yawanci duk manyan
    motoci
    ne, kamar yadda akansan babban titi ne, wanda
    ya mike ya tafi har lagos. Suna
    tsagaitawa ya
    cilla tasa motar ba tare da ya fahimci
    Danliti da
    mama sun ruga sun gama magana da idanuwansu
    ba. Kawai ji yayi ta kara
    gocewa da
    kuka mai karfi. Ya dan dubeta, ya kada
    kai. Yace,
    Al'amarin ki na bani mamaki, look kina
    jina? Saurare ni muyi magana ta fahimta. In
    tambayeki
    xaki bani amsa? Hankalinta sam ba
    awajen sa
    yake ba, balle ta saurare shi. Fuskar
    Danliti take gani, irin yadda ya shifa damuwa yana
    neman
    xubar da hawayensa, shi ya kara dagula
    mata
    lissafinta. Yace, saboda Allah zaki gaya
    min Al- ameen yayi miki da zaki juya masa baya?
    Tayi
    shiru, danliti na cigaba da yawo a idonta.
    Yace,
    kin kuwa san tun ranar da kika dawo
    garin nan. Al-ameen ya rasa nutsuwarsa? Ban iya
    kirga
    yawon wayoyinsa ba, tunaninsa kina
    cikin wani
    matsanancin hali ne aka boye masa. Kar
    ki saki reshe ki kama ganye Mama, domin kowa
    yasan
    Danliti lalata rayuwar ki kawai zai yi, ya
    kai ki ya
    baro ki tashar danasani. Ki ga ya min
    idan Al- ameen yayi miki laifi ne, ni da kaina xan
    masa
    magana in ja masa kunne. Kinji? Bai yi
    aune ba
    yaga ta balle murfin motar ta dire waje.
    Ta mulmula cikin ciyayi. Cikn tashin hankali
    ya take
    birki.... Allah yasa ba babu mota a
    bayansa, yayi
    fakin gefen titi, ya fito. Can ya hange ta
    tana kokarin tashi, amma ta kasa, kafin ya
    gangara
    wajen 'yan tsirarrun jama'ar wajen sunyi
    caa!
    Kanta. Suka ciccibota, suna sallalami
    tare da mamakin yadda aka yi abin ya faru. Gaba
    daya
    gwiwowin ta sunyi mugun kurjewa ta
    xura da
    gudu amma bata je ko'ina ba mutane
    suka cafke masa ita. BAKIN CIKI yasa ya dauke da
    wani
    mahaukacin mari daya tilasta mata
    xubewa kasa.
    Wani dan dattijo cikinsu ya kama shi.
    Yace, haba malam yaya haka kuma? Baka ganin
    kaddarar da
    ta sameta? Da ta mutu fa? Ku rinka
    kulawa da
    murafen mota mana don gudun irin
    hakan! Idanuwan sa ajuye yake magana, kyaleni
    da
    yarinyar nan baba! Da kanta ta bude
    murfin ta
    fito! Iskanci ne kawai, dama kin mutu, mu
    huta da wannan BAKIN CIKIN da kike son jefa
    mu!
    Saboda haka xan koma in gayawa abba
    kin bude
    mota ki diro, ni kuma ba xan tafi dake ba,
    ki xauna kiyi duk abinda kika ga dama
    agarin nan,
    tunda lalacewa kika xaba. Allah ya shirye
    ki! Ya
    shura takalmansa ya koma mota ya tayar
    yayi kwana ya koma gida ya bar Mama anan
    tana
    faman kuka, jama'ar dake wajen suna
    mamakin
    wannan abu har sun kasa fassara shi.
    Dan dattijon nan shi ya riko ta hankali suna
    tafe tana
    bashi labarin wai auran dole ake son yi
    mata.
    Kwarai kansa ya daure jin cewar ita 'yar
    gidan Uban dawaki ce, don haka ya tasa ta har
    gidan.
    Amma me? Suna xuwa kofar shagon
    Danliti ta
    xarce can tayi xamanta bisa benci. Dan
    liti ya fito aguje da ayuba, mamaki ya rufe
    ayuba, shi
    kuwa dan gogan munafuncin ne yasa
    gaba, sai
    yazo ya narke a gabanta. Yace, saboda
    me sakina, kinaso ki rasa ranki ne? Tace
    gara in
    mutu da su raba ni da kai, ya dubi Ayuba
    a
    gigice. Yace, kawo min mukullin mota
    ayuba! Ya shige shagon da surinsa, shi kuma ya
    juyo gunta
    ya marairaice yake fadin, aure na Allah
    ne
    sakeena, ina so ki yarda da wannan. Duk
    iya son da muke juna idan Allah bai nufi auran
    mu ba,
    babu yadda xamuyi. Don me xaki nemi
    halaka
    kanki? Bata bashi amsa ba. Ayuba ya
    mika masa mukulan. Bai jira tace wani abu ba, ya
    kamo
    hanninta taso muje asibiti asa miki
    magani.
    Dattijon nan ya bisu da kallo, duk tausayi
    ya rufeshi. Rashin sani kenan, ya fi dare
    duhu,
    domin shi gani yake irin haka ke jefa yara
    yawon
    banza..
    [11/01 19:24] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***3 (TRUE LIFE STORY)
    Wasu iyayeyn na da ra'ayin rikau, idan kuma
    ka bibibya kwadayi ne, wata kila wancan yafi
    wannan kudi ne? Sai dai kuma ai uban dawaki
    mutumin kwarai ne, me xai sa ya aikata haka
    akan yarsa? Duk da cewar dan dattijon nan
    talaka ne, ya doshi gidan uban dawaki, don ya
    bashi shawara. Fuskar Umma a sharkaf da
    hawaye take muryar ta har rawa takeyi, bai
    kamata ka baro ta can ba abdul... Yaya xanyi
    umma? Kona cusata cikin, sake fitowa xatayi.
    Mama ba zata mutu a hannu na ba, umma ta tafi
    inda take son xuwa, kanta tayi mawa. Fatana
    kwai Allah ya yaye mata abinda ke damunta.
    Kuyi hkr ku kyaleta anan domin ina mai tabbatar
    muku xata xauna can ba dawowa xatayi ba.
    BAKIN CIKI ya hana abba magana, sai A. Adamu
    ya iya fadin, gaskiya, gara ta xauna a cigaba da
    yi mata nasiha watakila a dace. Kuyi hkr Yaya
    mu dauki wannan a matsayi kaddara. Kai abdul
    idan ka koma Al-ameen ya kira ka kwantar masa
    da hankali ka... In ce masa me kawu? Gaskiyya
    xan gaya masa shi ma ya hkr da ita tunda ba ita
    kadai bace 'ya mace. Allah xai bashi wata. Ko
    kuwa? Abba ya dube shi, sai yanxun ya iya cewa,
    karka gaya masa haka abdul, da yardar Allah sai
    inda karfina ya kare akan mama. Indai ni na
    haifeta kuma ni ne xan daura mata aure Insha
    Allahu shine xai aureta. Kawai ka bashi hkr kayi
    masa wannan bayanin da naga ya maka yanxun.
    Ya dafe goshi yayi huci zafi kafin ya dubi Umma.
    Yace ki share hawayenki, umma ki yi mata
    addu'a Allah ya shiryata. Ni xan koma sai yadda
    ta kama. Basu amsa ba, ya mike kawu Basir da
    Adamu suka yo masa rakiya kuma suna gaya
    masa kalaman da suka dace ya gayawa Al-
    ameen. Da dan dattijon nan sukayi kicibis yana
    sallam cikin xaure suka amsa nan take. Yace
    baka shaida ni ba ko yaro? Nine wanda yaga
    lokacin da yarinyar gidan nan ta bude murfin
    mota ta fito, tayi min bayani ita 'yar mai girma
    Uban dawaki ce, shine nace ai mai martaba yana
    da saukin kai xan xo in bashi shawara game da
    auran dole, yayan ya dube shi da kyau. Yace
    hakan ta gaya maka? Yace, kwarai hakan ta
    fada. Yace to tayi maka karya, kawu ka na iya yi
    masa bayani, don na tabbata abba baxai iya
    fitowa ba ahalin da yake ciki. Alh. Basiru yace
    yanxun ina take? Yace tana can ta tsaya wani
    shago har sun tafi, zai kaita asibiti. Suka dubi
    juna, yaya yace, kunji ko? Mama ta tafi, bata jin
    kira saidai addu'ar Allah ya shiryata. Ni na tafi.
    Ya fice ya barsu nan tsaye. Alh. Basiru ya dubi
    tsoho yace mun gode baba, amma kayi hkr,
    bazaka ji komai daga gareni ba, saboda ban sami
    izinin yin hakan ba. Maganata gaskiyya da nake
    so ka gane shine karya yarinyar ke maka, tare da
    shegantaka irin ta yaran yanxun. Mun gode da
    kulawarka. Tsoho yace, shikenan nima na gode,
    amma don girman Allah abi a hankali asamu a
    sulhunta. A. Basiru yace ba komi baba mun
    gode. Sukayi sallama ya shige gida. Tsho ya
    kama gabansa cike da wasi-wasi cikin ransa.
    Falon Uban dawaki A. Basiru ya koma ya
    xayyane masa labarin da tsho yaxo da shi, da
    kuma shawarwarin da ya bayar. Abba bai iya
    cewa komai ba saboda tsabar bacin rai. Sun jima
    suna tausar xuciyar Abba sannan suka koma
    sasan su, inda matan suke xaune dirshan suna
    xuba gulmace gulmace. Suna zagin mama da
    iyayenta. Basu hanasu ba, hasalima zama sukayi
    suka dora xancan babu dadin ji, ita kuwa baiwar
    Allah mama, tana tare da Danliti cikin mota,
    bayan fitowarsu asibiti, yana ta faman
    rarrashinta, don ta daina kuka ta kwantar da
    hankalinta, da kyar ya samu ta nutsu ta daina
    xubda hawayen. Yayi fakin kofar shagon sa ya
    juyo ya fuskance ta. Yanxun ya xamuyi mu
    fuskanci juna abba ya gane cewar idan ba mu
    auri juna ba, komai zai iya faruwa da mu? Tace,
    ai ga misali nan na fara nuna masu kuma ba xan
    fasa ba, ina nan akan baka na. Ya marairaice
    yace wannan misalin bana son irinsa sakeena,
    don bana son na rasaki. Gaba ki daya kin fita
    kamanninki kin kuwa ci abinci yau? Ta kada kai,
    abinci ba xai iya wuce min ba Dan liti ina cikin
    wannan masifar meye illar ka? Da abba xai ce
    samm baka dace dani ba?
    Ya lumshe ido, ya bude kafin yace,
    saboda suna ganin ni bako ne, bani da kowa
    agarin nan..... Ta katse shi, hakan shine xai nuna
    daga sama ka fado? Wannan ba hujja bace
    Danliti, son rai ne kawai irin na iyaye ni kuwa ba
    xan yarda ba, sai dai muyi ta ba juna wahala. Ya
    ja gwauron numfashi ya sauke, ya lalubo yatsun
    ta ya runtse su cikin nasa, ya xuba mata ido
    yace, nasan ki na sona sakeena, amma ki daina
    damuwa ko sun hana ki xuwa wajena, sannan ki
    daina wasa da rayuwarki, don tana da
    muhimmanci aguna. Abu da gaba, ki daina zama
    da yunwa, ita ma zata iya illata minke. Yaunxu
    abinda nake so dake, ki zo muje shago in hada
    miki tea ki sha, sannan kije gida ko sun zage ki,
    kar ki ce dasu komai, don kar su sami damar
    dukanki. Kinji bebi na? Ta amsa da ka. Tace,
    yauwa mai kyau, to dan kalle ni mana, ta dube
    shi suka yiwa juna xuru, jim kafin ta kauda kai,
    tana dan murmushi, shima murmushin yayi yana
    mata kllon kwadayi, ya ja yatsunta xuwa bakinsa
    ya sumbata. (kuji dan iska). Ta kwace da sauri
    ta kara sadda kai. Yace, bebi na kenan, sarkin
    kunya. To muje ko? Zaki iya sauka ko in zo in
    fito dake? Ta balle murfin batare da tace wani
    abu ba ta fito, shima yayo waje yana kallon
    yadda take dingisawa har cikon shagon sa. Ya ba
    za mata tabarma ta zauna. Ayuba na mata
    sannu. Akwai wani labule jikin wata kwana a
    shagon, sai alokacin ta gane daki ne. Cikinsa Dan
    liti ya shiga ya fito da filas da kofi da cokali ya
    aje gabanta. Yace ga ruwan zafi, ki daga idonki,
    ki duba duk irin madarar da kike so, ki zaba na
    dauko miki. Tana murmushi tace, kai wacce iri
    kake sha? Yace ai bana shan madara a tea,
    ganye kawai nake sha. Kinsan buzaye ai? Tayi
    dariya tace, ba'a raba su da jiko. Yace shayi dai.
    Ta ciga da dariya tana fadin, to shayi, wai
    menene sirrin shayin nan ne? Yace xan gaya miki
    amma da farko wacce madara kika zaba, in
    dauko miki? Na kowa ki sawa cikinki abinci.
    Tace, bani peak ta ruwa. Ya mike ya dauko hade
    da katon bread ya hada mata tea mai kauri,
    domin duka ya juye peak din. Tana sha, suna hira
    ya gaya mata ire-iren shayin su. Bayan ta
    kammala, ya matsa gareta yace, yanxun ya
    kamata ki koma gida kiyi barci, ki huta kinji?
    Karki damu ko an hana ki xuwa nan, wane tym
    zamu hadu. Ke dai kiyi addu'ar fatan samun
    nasara. Tace, Insha Allahu zanyi. Yana murmushi
    ya mika baki ya sumbaci kuncinta. Ta sunkuyar
    da kai tana murza yatsunta. Ya zura mata ido,
    gaba daya jikinsa yai la'asar, sannan ya dago
    habarta, suka dubi juna, yace I love U! Tace me
    too, yace, to ki tashi kije gidan, zaki iya ko? Tace
    xan iya. Ta yunkura ya taimaka mata mikewa
    suka fito tare ta sallami Ayuba, ya dan taka mata
    kadan ya dawo, yana zuwa ya kwashe da dariya,
    ya mikawa Ayuba hannu suka tafa. Ayuba yace,
    baka da kyau dan iska. Yace raina kama gayya!
    Gaskiyya ta gurzu, na tausaya mata wlh. Shegiya
    akwai taushin fata, baka ji ba kamar auduga, duk
    ta susuta ni. Ya zura masa ido yace, tunda kuka
    shiga, na karance ka, shi ya gaba na yayi ta
    faduwa, kar ka sata labulan nan. Yace, ko na
    sata ba zata hani ba, nake gaya maka kuma babu
    abinda zai faru dani. Kawai dai ban yi niyya bane
    yanxu, ni nasan abinda nake hari. Yace a dai rika
    tuna Allah Danliti, shagalinka yayi yawa kuma ina
    ma kwadayin cin ubanta nakeyi, ai har uanxun
    duniya bata fara zaginta ba. Kaga da sauran
    mutuncinta. Ya bishi da kallo, bai ce komai ba,
    yayi tsaki ya tashi ya koma shago abinsa. Tana
    tafe tana dingishi, ta iso gida, kanta tsaye bata
    fargabar komai ta fada zaure, kicibus suka yi da
    Ya Ali sabe da jakar sa zai bar garin. Ko kallon
    sa batayi ba ta wuce, ya biyota yana kiranta bata
    waigo ba, balle ta amsa, ta shiga sasan su har
    falo yana binta. Su abba na kallon ikon Allah,
    domin dai Mama bata saurara ba, cikin dakinta ta
    shige. Ya Ali na shigowa ya gansu, ya ja birki
    amma ransa na son ya shiga wajen mama, yayi
    magana da ita, abba ya dube shi. Yace, Ali ka
    daina wahalar da kanka abanza, mama bata
    bukatar komai sai addu'a. Saboda haka ka kama
    hanyarka ka koma bakin aikinka. To amma, kayi
    hkr Abba, don girman Allah karku daketa, kamar
    yadda kace nayi mata addu'a kuma kuyi mata
    addu'ar. Yace, na yarda da kai Ali, amma ban
    yarda auran kowa ba, sai wanda na aminta da
    shi. Zan gani idan ita zata daura wa kanta aure
    ko mune? Yace, haka ne Abba don Allah ina
    rokon 2mins in ishiga in dayi mata nasiha, koda
    bazata saurere ni. Ya suke numfashi yace, shiga
    Ali, Allah ya sa taji abinda zaka gaya mata. Ya
    aje jaka ya wuce cikin dakin. Tana kwance niyyar
    barci ma takeyi, kamar yadda Danliti ya
    umarceta. Yana shigowa ta runtse ido ta juya
    baya, ya tsya kanta yace, komai zakiyi, dole in
    gaya miki gaskiyya, tunda kunnuwanki naji.....
    Fadan hakan yasa tai sauri ta toshe kunnuwan
    nata da yatsunta. Yace aikin banza kike yi Mama,
    kuma rayuwar ki na cikin hatsari, muddin baki
    daina jefa su abba cikin BAKIN CIKI ba. Menene
    anfani abinda kika aikata yanxu? Ki kashe kanki
    a banza da wofi, ba asarar Danliti bane, don na
    tabbata duk tsananin son da yake mi, ba zai
    hallaka kansa ya biki ba. Ki nutsu kiyi tunani.
    Akwai abinda magabatan mu ke hangowa
    kan wannan ra'ayin naki. Ni zan koma kuma ina
    fatan zanji canji daga gareki? Ya juya ya fice
    bata re da ta daga kai ta dube shi ba. Wani
    dogon tsaki ta raka shi da shi, wanda ya tilasta
    masa juyowa ya dubeta ji, sannan ya karasa
    ficewa. Ya dauki jakarsa ya kara yiwa su Abba
    sallama, ya bar gidan ciki da Al'ajabin maras
    misaltuwa a zuciyarsa. Bayan tafiyarsa, su
    Umma suka shigo gunta ta tana kudundune ta
    dunkule wuri daya, ko 'ina jikinta ciwo. Umma ta
    zauna gefen gadon shi kuma Abba n atsaye
    kanta, yace Mama barazanar kashe kanki ba zai
    sauya abinda ke cikin raina ba, idan ma baki sani
    ba, ki sani gara ki mutu da mutunci na ya xube a
    idon duniya. Saboda haka fadowar ki a mota bata
    girgiza ni ba balle ta cire daidai da kwayar zarra
    na alkawarin da na daukarwa Al-ameen da
    iyayensa. Mu zuba ni dake, duk wani matakin
    rashin kunyar da kika hau, ni na fi ki hawa
    matakin karshe! Ya juya ya bar dakin. Umma ta
    kura mata ido, hawaye suka cika idanuwanta,
    tace Mama zaki iya tashi ki saurare ni? Ta shiru
    bata motsa ba, ta sake fadin, idan har ni na
    haifeki kuma na isa dake, to ki tashi zaune ki
    fuskance ni. Ta jima kafin ta yunkura ta tashi
    fuskar ta sharkaf da hawaye, kamanninta sun
    sauya, saboda fitinar da ta daukarwa kanta a
    tunanin iyayenta. Umma ta zura mata ido, kafin
    tace, nasiha xan miki, idan kiji ki dauka wahala ta
    kare miki, idan kuma kince ba haka ba to rayuwa
    zata cigaba da yi miki kunci, domin Allah ne ya
    wajabta miki yi mana biyayya, muddin ba mu sa
    ba masa. Ban jin akwai wani dalili ko hujja da
    xaki gayawa ubangiji da ace kin mutu sakamon
    bude murfin motar da kikayi, ki fado lasa.
    Wannan ya nuna muraran kin kashe kanki ne da
    gan-gan. Ma'ana kin mutu kafira. Me zai jawo
    miki wannan masifar da hankalinki da komai? Ko
    kuwa kina so ki nuna mana kin fi karfin mu cikin
    dan kankanin lokcine ne? Kina nufin mu sanya
    miki ido ki zubar da mutuncin ki da mu a garin
    nan? Ban taba tunanin Mama, ke din nan zaki
    zama kaza kici share baki a game da irin so da
    Kaunar da Al-ameen da iyayensa syka nuna miki.
    Haka kuma ban taba mafarkin ke din nan zaki iya
    hango wani da namiji ya rufe miki ido har kice
    kin fo sonsa akan Al-ameen. Kina nufin daman
    can yaudara sa kike yi ba tsakani da Allah kike
    sonsa ba? Har yanxun mafarki nakeyi Mama, don
    ba gaskanya abinda yake shirin fitowa daga
    gareki nake ba. Ki yiwa girman Allah kir ki bari
    wannan magana ta zama gaskiyya, ba ke kadai
    za'a zaga ba har damu iyayenki. Na mu ma zai fi
    yawa saboda mune muka isa dake. Yanxun
    abinda na rokonki shine, ki share hawayen ki ki
    gaya min, laifin me Al-ameen yayi miki kike son
    ki katse masa rayuwa? Gaya min daga ni sai ke
    ce a dakin nan kuma share hwayenki, muddin shi
    ne baida gaskiyya. Ta shre hawayneta wasu suka
    xubo mata, kalaman ummanta masu taushi ne
    dashiga xuciya, amma kash Danliti ya riga ya
    gama da ruhinta. Allah ya bashi sa'a ya kamata
    ahannu, idanuwanta ba sa ganin kowa sai shi,
    kunnuwanta ba sa sauraron kowa face kalaman
    yaudarsa da izgilanci. Dalilin da yasa kenan
    kalma daya bata tasiri a hrt dinta, a duk tsahon
    jawabin da Umma tayi, da ka dubi fuskarta, zaka
    gane bata yarda bane kawai. Murya cunkushe
    tace, ni babu abinda Al'ameen yayi min Umma,
    kawai raina yafi kwanciya da Danliti kuma shi
    nake so na aura. Haushi kamar ya kashe Umma
    ta mike tsaye. Tace, to baki isa ba! Mu dan Liti
    baiyi mana ba, idan kina da wasu iyayen da za
    su dauta miki auran to bismillah!
    Ya ci gaba da fadin, ai kuwa bata isa ba,
    ni zanje in dauko ta kuma dole ta auri wannan
    yaron tunda itace tace tana so tun farko! Yace,
    Yaya duk yadda kake tunanin al'amarin nan ya
    wuce nan, amma ka gwada ka gani, kilan kai tafi
    jin tsoronka, sai dai kafin nan xance Al-ameen
    din ya kira ka, kuyi magana, don ni gaskiyya ban
    san me xance masa ba. Yace ba wani abu xan
    rarrasheshi, ya kwantar da hankalinsa, kaima
    yaunxun nan ka kama hanya kaje ka yiwa
    Hajiyansa bayani, kace kar su damu ba wata
    matsala bace babba. Ya numfasa ya amsa da to
    kawai. Lallai babban yaya yana dau kara abin
    wasa ne. Suna aje waya Aunty amina ta nufo shi,
    me ya faru ne wai? Nan take ya labarta mata
    abinda ke faruwa. Tun kafin ya kare idanunwanta
    ke waje, wai kana nufin Mama ta fasa auran Dr?
    Yace gara da kikace wai, don bata ida ba. Ni xan
    je na dauko ta, cikin gidan nan zata zauna sai ya
    dawo. Ta kada kai cikin damuwa, tace amma
    mama ta ban mamaki, me Dr? Yayi mata? Babu
    abinda yayi mata, wani ta hango saboda rashin
    hankali irin naku na mata da butulci! Tace wlh na
    yadda sai dai matsalar banyi zaton haka ba daga
    wajen Mama ba ganin yadda take nunwa Dr. So
    mai tsanani, duk yaudara ce, kai gani kuma a
    zahiri ai ta nuna. Amma ai tayi kuskure ni zan
    gyara mata zama, don bata isa ta zubda mana
    mutunci ba! Tace gaskiyya ne. Allah yasa ta
    gane. Ya wuce tebur don cin abinci. Shi kuwa
    abdulkareem, bai sami zaman cin abincin ba
    gidansu Al-ameen ya nufa ba tare daya san wane
    irin bayani xai iya yi masu ba, don hankalinsu ya
    kwanta. A haka ya isa gidan. Nan da nan aka
    tarbe shi da girmamawa da abubuwan kusa da
    baka, marafa baya gari, saboda haka mami ce ke
    tare da shi, ina fatan dai kaci abinci? Yayi dan
    yake yace, Alhmdlh Hajiya, nagode. Tace amma
    dai ko Juice kasha ko? Haba, kamar wani bako?
    Yanata murmushin rashin nayi, yana kallo ta
    xuba masa ta mika masa, Ungo sha don Allah.
    Kuma maimakon kazo min da surukartwa, yau in
    riketa cikin gidan nan sai tayi min sati. Ya aje
    kofin lemo ya kara gyara zama, Yace Hajiya, hkr
    na zo in baki, domin ban sami dawowa da Mama
    ba,... Saboda me? Kodai maganar Al-ameen
    gaskiyya ce, sakeena na cikin wani hali? Bata da
    lfya ko? Ya karkada kai.... Tace karka bote min
    komai Baban ameer, duk tsananin da sakeena ke
    ciki, nasan yadda xan rarrashi Al-ameen don
    hankalinsa ya kwanta. Gaya min me ya faru da
    ita? Jikinsa ya kara sanyi, cikin taushin murya,
    yace Matsala ce babba Hajiya, wacce ni kaina
    ban da ita ba, sai da naje daxun. Ashe tun
    komawar ta gida, wani yaro ya hure mata kunne,
    shi ya hana ta dawowa. Su abba na ta fama da
    ita kuma suna kan kokarin su don ganin raba ta
    da shi. Na yi nayi ta biyo ni, taki hajiya, shine
    Abba yace in zo in baku hkr kafin yazo. Insha
    Allahu za'ayi maganin abin. Gaba daya hankulan
    mu atashe suke, al'amarin yana daure mana kai.
    Idanuwanta xuru akansa, hannunta bisa kunci.
    Tace, wyyo Allah! Wayyo Allah! Me xanji yau mai
    kama da almara? Ta goce da sallalami, yanxun
    baban ameera kana nufin sakeena tace amanar
    Al-ameen kenan? Idanuwanta suka cika da
    kwalla, yayi da yaya Abdul ya kara kasa da
    kansa. Yace, kiyi hkr Hajiya, a gaskiyya ban san
    yadda xan fassara wannan al'amarin ba, amma
    abinda nake so ki gane Abba ba xao rungume
    hannayensa ya sanya mata ido ba. Haka muma
    'yan uwanta. Muddin kuwa tana son albarka dole
    tabi umarnin mahaifinta. Shi yasa ya fara turo ni
    kafin ya zo da kansa ya ga alhaji. Haka kuma ku
    rarrashi Al-ameen ya kwnatar da hankalinsa
    komai zai daidaita cikin hukuncin Allah da
    yardarsa. Ta cire tagumi. Tace, a gaskiyya ba
    zan iya fuskantar Al-ameen da wannan maganar
    ba, in katsa masa karatu. Na san ya damu kwarai
    ya san halin da sakeena ke ciki, amma ba xan iya
    gaya masa wannan mummunan labarin ba, kuma
    na rokr ku don Allah ku kyaleshi kawai. Gara abar
    shi cikin duhun da agaya masa sakeena ta sauke
    alkawarin da ta daukara masa. Na tabbata komai
    nasa zai tsaya jarabawar su gab take da xuwa.
    Ni da kaina xan iya xuwa na roketa, ta tausaya
    wa Al-ameen karta kashe masa zuciya. Kwalla
    masu zafi suka xubo bisa kuncinta bata re da
    saninta ba. Hankalin Abdul ya kara tashi, BAKIN
    CIKI ya dada lulluba shi. Don girman Allah Hajia
    karki xubda hawayenki akan maganar nan. Da
    yardar Allah komai zai gyaru. Kamar yadda kika
    ce kar agaya masa ba, ba za'a gaya masa ba.
    Gara ace masa bata da lfiya ne, xuwa lokacin da
    xa'a shawo kanta. Ta goge kwallah, tace ina
    ganin hakan zai fi sauki iyaka dai yayi tunanin
    jikinta, mu kuma nan mu rinka gaya masa tana
    samun sauki. Yace, to shkienan, Allah yasa
    mudace. Don girman Allah hajiya kuyi hkr,
    sakarci ne kawai irin na yara. Tace, ya za muyi
    baban ameer? Dole mu rungumi kaddara. Ya mike
    babu isasshen laka a jikinsa, yayi mata sallama
    ya fice, batare da hajiyar ta kara ko motsi ba.
    Wucewar awa daya da rabi tana zaune xuciyarta
    cike da sake-sake iri-iri. Ji take kamar a mafarki
    abdul yaxo mata da wannan mummunan labari,
    wanda take ganin zai iya salwantar fa rayuwar
    dant tilon danta da takeji da shi. Duk fadin
    duniyar nan bata hada shi da kowa.
    Yaya marafa zaiji, idan wannan labari
    yake kunnen sa? Tabbas xai fita shga damuwa,
    domin yafi ta sanya Al-ameen ransa, ko alama
    baya son yaga ya nemi abu. Waya ta dau ruri a
    falon, ita ta katse tunaninta tare da haddasa
    mata faduwar gaba mai tsanani. Ta mika hannu
    ta dauka ba tare da tayi hasashen mai kiran ba.
    Tayi sallama cikin raunin murya. A raunane taji
    muryar Al-ameen ya amsa mata kafin yaci gaba
    da cewa, mami na, ashe sakeen ba ta da lfiya
    shine aka boye min? Ni ban ma yarda bata da
    lfiya bane Mami, kawai ku gaya min idan mutuwa
    tayi, xan hana Allah ikonsa ne? Ai nasan yafi ni
    sonta, kuma ta shi ce ban isa in hana shi amsat
    kayansa ba.... Tace saurareni Al-ameen, kar
    hankalinka ya gushe.idan baka yarda ba da
    maganar yayun sakeena ba, ai ni mahaifiyar
    kace, ba xan rufe maka komai ba, ka yarda ko
    baka yarda ba? Murya na rawa ya amsa, Na
    yarda mami, tace to sakeena bata mutu ba,
    rashin lfya ce ta sameta aka maida ta gida. Bana
    so ka damu da yawa, domin sosai take samun
    sauki, gobe ma xan sake xuwa in dubo ta, kaji?
    Ya numfasa yace, amma Mami me yasa za'a
    ajiyeta gida? Akaita asibiti mana, ko can xariya
    xanyi magana da abokina, na tabbata xai kula da
    ita tamkar ni. Pls mamy ki basu shawara idan
    kinje goben. Tace ba ciwon asibiti bane, shedanu
    ne suka tabata, kuma su iyayen nata suna tsye
    neman magani. Kai ma kasan xa su xauna ba. Ni
    dai rokona gareka shine ka nutsu ka kwantar da
    hankalinka, ka fuskanci jarabawar ki mai xuwa.
    Ka zama mai imani da Allah, shi xai sa ya karbi
    addu'ar ka idan kayi mata. Ka jini? Ya goge
    kwalla, yace naji mami don Allah idan kinje ki
    dafa kanta ki karanta mata ayatul kursiyu, falaki
    da nasi. Idan har gane ki ko da baxa ta iya miki
    magana ba, ki gaya mata Al-ameen dinta na
    gasheta, kuma xan ciga ba da yi mata addu'a har
    xuwa lokacin da xanji muryar ta a waya.
    Idanunwanta suka tara kwalla. Tace, Insha Allahu
    xan gaya mata, tare da dukkan abinda kace,
    muddin kayi min alkawarin zaka kwantar da
    hankalinka. Da sauri ya amsa, Allah nai miki
    alkawari mami, kinsan bani da wani buri daya
    wuce in faranta maku rai. Tace, Allah yasa dalilin
    alkawarin da kayi min Ubangiji ya yayewa
    sakeena abinda ya sameta! Yace, ameen Mami
    na! Dadina bai dawo ba ko? Bai dawo ba sai
    zuwa jibi. Yace Allah ya dawo da shi lfya. Ta
    amsa da ameen. Yace ki gayawa su iya su taya
    mu da addu'a, Allah ya taimake mu. Tace, xan
    gaya musu. Al-ameen, karka damu kaji? Murya
    raunane ya amsa, to mami sai kinsake jina. Bata
    iya kara komai ba ta aje wayar, domin muryarsa
    kawai ta isa jefa mutun cikin damuwa. Taci gaba
    da xama dauke da tagumi tunani na cin xuciyarta
    fiye da tunanin mai kallonta. Haka al-amarin yake
    wajen Al-ameen, domin dai rayuwa tayi masa
    tsauri kuma hasashen rashin lfiyar Mam yafi
    koma zama cikin ransa. Ba don yayi wa mamy
    alkawari ba, da babu makwa zai iya baro abinda
    yakeyi ya dawo ya ganewa idon sa Mama, tana
    cikin mummunan hali. Kafin kace kwabo, kowa
    ya fahimci samun sauyin sa, domin ya yamutse
    ya wayi garim duk kuzarin da nutsuwar sa basu
    jikinsa. Yana zaune addu'a yana tafe addu'a,
    haka acikin aji, hankalinsa yafi rinjayea ga
    addu'o'in da yakewa mama cikin ransa. 12pm
    washegari lokacin ne motar Mami ke fakin kofar
    gidan Uban dawaki. Yayin da mama ke kwance
    rankas ciwon jiki, sakamakon fadowar da tayi
    daga mota. Can da nan bata iya motsawa,
    Baraka ke tare da ita tana zazzaga mata
    nasihohi, duk da ta san bata sauraron ta, sai dai
    ya zama wajibi gareta, ta kara gaya mata
    gaskiyya. Mami tayo sallama falon ta shigo,
    gaban Umma ya yanke ya fadi. Ta amsa tana
    fitowa daga dakinta. Yake baki kawai takeyi,
    amma zuciyarta ta shake take da takaici tare da
    BAKIN CIKI mai tarin yawa. Ga wata kunya da ta
    yo wa idanuwanta dirar mikiya, mai alaka da
    ciwon dundumi. Sannu da xuwa Hajiya! Ta amsa
    mata da fara'ar karfin hali. Ta nuna mata kujera
    ta xauna, tana kara yi mata sannu da xuwa.
    Sannan ta debo mata abubuwan sanyi masu
    ruwa. Ruwan ta fara xuba mata, ta mika mata ta
    sha. Suka gaisa cikin girmama juna. Ta kara
    gyara xama, tace, sai kika ganni da rana tsaka
    ko? Fuska kunshe da tashin hankali. Tace ke dai
    bari, nasan kin sami sako maras dadin ji. Ta kada
    kai dauke da damuwa. Tace naji sakon da ya
    hani barci jiya, wanda ya sanya ni rama kafin
    safiya. Ina jajantawa shi kansa Al-ameen da ya
    sallama rayuwarsa kaf kan sakeena. Nayi kuka
    da wadannan idanuwan nawa, don na tabbatar da
    amsata ba alkhairi bace a gareni, domin komai
    zai iya faruwa ga tilon da na, farin ciki na kuma
    sanyi idona. Shi ya sa nace xama bai ganni ba,
    tilas inxo in rarrashi sakeena, ta tausaya min kar
    in rasa Al-ameen. Wadannan kalami sosai suka
    sanya hawayen Umma suka tsinke nan take, ta
    rasa me zata ce wa Mami ta sanyaya mata rai?
    Dole tayi kuma domin dai bata da kwakkwarar
    mafada, mama na nan akan bakanta babu sauyi.
    Da kunnunwata ta, taji lokacin da take gaywa
    Baraka tabbas zata iya kashe kanta, saboda
    Danliti. Mami ta cigaba da fadin ki daina kuka
    Hajiya, Baban ameer ya gaya min tashin hankalin
    da kuke ciki, kukan bashi da alfanu.......
    [11/01 19:35] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***4(TRUE LIFE STORY)
    umma ta hare kwalla ta katse ta Tabbas
    mama bata da lafia ciwon daya kamata mai
    tsanani ne maganin Allah, dole kuwa in yi kuka ,
    don mama ta dasa mana BAKIN CIKIN da ban
    taba tunani ko mafarkin irinsa ba daga ni har
    Abban ta mu na cikin rudu tare da mamakin
    yadda wannan alamari ya kasanze haka, hakuri
    zakuyi hajia sannan ku taya mu addua mama
    kam ko ta so ko taki doke ta auri Alamin, tunda
    zabin ta ne na farko bamu muka cusa mata shi
    ba. Hasali ma bamu san lokacin da suka hadu
    ba. tsabat rashin kunya ce irin t yayan zamani da
    rashin sanin mutuncin mutane. saboda. haja hajia
    karki damu kuma dabarar da kikayi wa alamin
    tayi daidai sai dai akwai sauran rina akaba domin
    fadar kalmar ciwon ma ba zai bar shi yayi sukuni
    ba. Tace zaifi sauki akan a gaya masa gaskiar
    magana ni na dauki dawainiyar kwantar masa da
    hankali kullun ya kira waya. Tace to shikenan
    Allah yasa mu dace ta ce ina sakinar take mu
    gaisa Ta mike tana fadin Taso muje in kaiki
    kwance ma take bata iya tashi. Ah me ya faru?
    ina fatan ba dukanta kukayi ba, ta ce Baban
    Amira bai gaya maki bude mota tayi ta diro kasa
    ba? ido waje ta dafe kirji ta diro daga mota? tace
    ya wuce wai! zo muje ki ganta ta tashi dauke da
    mamakin tana fadin naga abinda ya ishe ni ni
    yasu, sakina da gaske take bata son Alamin.
    suka cusa kai dakin, baraka dake zaune bakin
    gado ta mike tana gaishe su. umma ta nuna wa
    mami wurin zama a bakin gadon tace zauyna
    hajia kinga idanuwan maras kunya ta juya kan
    mama taci gaba ga hajia nan tazo da kanta
    inkinga dama ki bude ido
    ta kudundune kai cikin pilli mami ta dube su
    tace ku bamu wuri hajia ita baraka suka bar
    dakin mami ta karasa matsowa tasa hannu ta
    birkito ta kuka taga tanayi tasa hannu biyu ta
    tallafo kuncin ta ta sanyaya murya tace sakina
    dan dubeni kinji? ta dago idanuwa jajur ta dube
    ta hawaye suka wuce bisa kuncinta. mami ta
    kara goge su . ta ce na san ba'a siyan so mama
    da yau nayi cinikin sa ko nawa ne na siya wa
    alamin, koda zai kasance zani daya zai rage min
    a fadin duniya. amma kash hakan ba zai taba
    yuwuwa ba, sai nayi imanin ko dan yaya ne kin
    san mahimamcin rike alqawari me yasa kika
    dauki alqawarin da ba zaki iya cikawa ba? me
    yasa kika yaudari shi kika bari tsananin son ki ya
    zauna a zuciyarsa? kina so ki kashe shi ne
    sakina? ki tausaya min ana gaya masa sakon nan
    zuciyar sa zata iya bugawa ya mutu mama. shi
    kenan na rasa shi kuma ban da wani alamin na
    sonki mama sai dai ayi zancen dan adam
    ssaboda haka ki gaya mani abubuwan da yake
    miki wadanda baki so har suka sanya ki tunanin
    fasa aurensa. wallahi nayi maki alqawarin zan
    masa fada tare da lallashi in kuma. gargade shi
    kinji? gaya man matsalarki da alamin. hawaye
    suka ci gaba da ambaliya bisa fuskar mama
    domin ko sunan alamin bata son ana ambatowa
    tsawon lokaci bata tanka ba sai kwarara ruwan
    idonta kamar zai kare mami ta sake fadin da
    alama alamin dai bai maki komai ba sakina
    tsuntsun son sa ne kawai ya tashi daga kansa ya
    koma wa wani ko?
    ta kara aje ido kasa mami tai wawan ajiyar
    zuciya idanuwanta suka kawo kwalla baki man
    halacci ba sakina a iya tunani na mutuwa ce
    kawai zata raba ki da alamin shi yasa gaba
    dayan mu muka dora burin mu a kanki. bamu da
    wami buri face Allah ya nuna mana ranar da zki
    zama mata danmu sai gashi dare daya kin juya
    mana baya. A tunani ki kinyi daidai? baki gudun
    kar amana ta ci ki sakina? kiyi tinani cikin
    natsuwa duk wanda ya ha'inci wani Allah ba zai
    kyale shi ba. zan barki kiyi tunani kan magana ta.
    idan kin canza ra'ayi ki koma minna zuwa gobe
    Alamin yaji ki hankalinsa ya kwanta kinji? yace in
    gaishe ki kuma yace inyi maki addu'a. Ta
    taimaka mata ta kwanta a hankali idanuwanta
    rufe suke yayin da mami ta dafa kanta tayi mata
    addu'oi da alamin yace tayi sannan ta kirata ta
    bude ido. nizan koma sai najiki a minna karki bari
    shaidan ya rinjayeki ki bar mai tsananin sonki
    cikin kunan zuciya nakasa zaiyi kinji? ta lumshe
    idon a natse mami ta wuce ta bar dakin umma ta
    shiga tare da sallama ta nemi wuri ta zauna
    yayin da baraka ta fice. ta basu wuri ta
    saurareki? tace to! bata dai tanka ba sai kuka da
    zan fito. ma nayi mata addua' kallo na ta dinga
    yi. da alamun za'a dace tace kwarai da gaske
    bari in lallaba hajia zan shiga wajen gwaggo
    sannan mu wuce . to a gaishe ta da kyau Allah
    ya kiyaye hanya
    Suka wuce suna fadin"Amin"har kofar gida
    tayi mata rakiya,motarsu ta daga ita kuma ta
    dawo gida dakin mama a koma suka taru da
    baraka suka ci gaba da yi mata nasihohi tana
    kudundune bata tanka ba,balle su gane me take
    nufi,Awa guda bayan tafiya mami yaya. Abdul-
    kadeer ya iso gidan daidai lokacin kuwa Abba ya
    dawo gidan,yayan tare yake da dakarun sojoji
    guda uku,duk suka fito,suka toge suna sarawa
    abba,sannan suka gaishe shi tare da yayan suka
    rankayo yana ruwan masifa, maganar banza
    yarinyar nan take yi,mu makace ta kawo shi ko
    mu muka hadasu wannan ai iskanci ne yanzun
    nan zan wuce da ita shiya na dauko kuratan nan
    su yi min gadinta a mota na ga ta inda zata
    fito,Nonsense kawai"
    Abba yace kayi daidai domin ni mama ta ginsheni
    ko ganinta bana sonyi cikin gidan nan,saboda
    "BAKIN CIKI",abu kamar al'mara yana so ya
    zama gaske yarinya ta bamu kunya ta zubar
    mana da mutunci basu ma san sun shigo falon
    ba sai da umma tace maraba da babban yaya
    yace sannu umma bamuyi sallama ba ko?raina
    bace yake ina mama?tana daki ina fatan tafiya
    kazo yi da ita sosai kuwa umma akwai kurata
    uku nazo dasu wadanda zasu gyara mata zama
    muddin tayi yunkurin bata mana lokaci tace yayi
    kyau wallhi yanzu ma hajiyar al-amin ta bar
    gidan nan bakaga uwar kunyar da ta lullubeniba
    na rasa inda zansa kaina
    Abba yace tazo kikace"tana ma cikin garin
    nan bata wuce ba"Abba ya nemi waje ya zauna
    ya kama kai,shi kuwa yaya babba dakin ya nufa
    kina jina baza ki fito ba"umma tace da wace
    kafar zata fito bayan ta kusan kashe kanta,yace
    kadan ta gani amma yau sai kin bar garin nan ko
    za ki mutu!Useless girl!kina nufin ki zubar mana
    da mutunci ko,baki. Kai wannan matsayinba,I
    swear,kin ji na rantse"yasa hannu ya fisgo ta da
    karfin sa yana fadin"stand up my friend"ta
    tsandara kara mai garfin gaske saboda gaba
    gabobain ta suka amsa suka kaiwa kwakwalwar
    ta zuwa falon dole gabobin suka loma aiki ashe
    dama wuri suka samu.
    Ya dankwafar da ita bisa kujera tace wayyo
    na shiga uku yace"No lokacin bai zoba tukuna sai
    kin ci gaba da bijire wasu umma I'am telling you!
    yau abuja zamu wuce ki zauna can, sai lazy
    doktan ki ya dawo ai ke ki ka zabe shi tun farko
    so now you have no reason ki ce kin fasa bayan
    kun kusa aure ya dubi umma yaci gaba karki ji
    tausayinta ta umma ki fidda ta a ranki har sai
    tayi biyayya a gareku,
    Ta kada kai tace tuni mama ta fice min a rai
    balle tausayinta ko alama babashi cikin raina ka
    tafi da ita duk abinda ya dace kuyi mata don ta
    gane kuskuranta yace wannan dole ne Abba bari
    mu wuce umma ta fara magana bari in hado
    mata kaya yayin da abba da babban yaya kamar
    zasu cinye mama a falo kuka take tamkar za a
    zare mata rayuwa umma ta fito da jakar kayan ta
    wurga mata gyale bisa jiki,yaya soja ya mike
    tashi karki bata min lokaci taki mikewa yasa
    hannu ya maketa
    sannan ya cafko. ta yana fadin zan iya
    karya ki u know dat! gara ki shiga hankalinki bai
    sake taba har kofar gida ita kuwa umma cikin
    sasa ta shiga ta gayo masu za a wuce da mama
    don haka suka yo waje ganin yadda za a yi
    saboda suji dadin karaars wa. A gaban su ya
    cilla wa kuratan daya zo da su ya ce kusa min
    ita a mota! kan kace kwabo mama na cikin mota,
    suka sanya ta tsakiya yayanta na gaba sanda ya
    jefa jakarta a but yaya ya juya da sauri ya zauna
    matsayin driver babu bata lokaci ya murza
    mukulli mota ta tashi ya bar wajen, idanuwan
    baraka suka cika da kwalla nan da nan ta fasa
    kuka ta koma cikin gida da gudu. sauran matan
    na ta fadin Allah ya kiyaye hanya ubangiji yasa a
    dace. umma ta juya ta shiga gida su suka biyo
    bayanta . ganin hankalin umma yayi mummunan
    tashi yasa hajia gaje ta janye hajia hajo cikin
    gida ta mika hannu suka tafa sannan ta tallafe
    haba ido waje tace Ashe abin har ya girman
    haka? wanan sojoji kamar an zo kama gagararren
    barawo? ta ce ai kamar hakan ne tunda ta gagari
    iyayenta. zamuga ikon Allah yarinya na neman
    tayi wa iyayenta bakin cikin daula, sun ga samu
    zasu ga rashi ai kinga haj halima kamar ranta zai
    fita sai kace dole suka sake tafawa haj hajo tace
    Hakki ne nake gaya miki kadan ma suka gani
    badai danliti ta jajibo masu ba? Allah dai ya
    kiyaye lalacewa! ta tabe baki Nayaushe kuma?
    wai ance wa kuturu Allah ya laance ka!
    shagonsa fa take zuwa tsinancewa ai ba sai an
    tambaya ba! hajia hajo tace Allah shi kyauta haj
    gaje ta amsa na gaba domin dai wannan ya riga
    ya faru anyi abin kunya maga yadda za ayi! sun
    jima suna yada labaran banza da karairayi kai
    duniya ina zaki da mu? rayuwa kenan uban
    dawaki da umma suna kallon ikon Allah suna
    fama da BAKIN CIKI sai fatan Allah ya musanya
    masu alkhairi
    Mama kuwa tun isowarsu Abuja take kudundune
    cikin daki duk hargagin yaya soja baisa ta dauki
    lomar abinci tasa wa bakinta ba,al'amari ya
    daure wa anti amina kai ta zauna ta siga yayyafa
    mata nasihohi da rarrashi ko Allah yasa ta gane
    amma ina Alla bai nufa ba tukuna shi kuwa soja
    babu abinda ya dame shi cewa yayi zai fi kyau
    da zata bari yunwa ta kasheta a yau hakan kuma
    shi zai tabbatar masa ta cika mai kunnen
    kashi,yasa kai ya bar gidan amma kuratan
    sojojinsa na nan tsare da gidan bayan masu gadi
    mutun biyu ke nan yanzu sun zama su biyar,kafin
    yamma mama taci kukan daya fidda ta daga
    hayyacinta bama ta jin tarin yunwar da ke cikin
    ta saboda tsananin tashin hankalin da take ciki
    domin ita kanta ta san ta shigo kurkuku zai yi
    wuya ta kara ganin dan liti sai dai tunanin ta bai
    yanke ba duk tsananin da zata shiga baza ta
    taba auren wani ba dan liti ba.
    [12/01 17:26] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***5(TRUE LIFE STORY)
    Saboda haka taci gaba da zama cikin kunci da
    yunwa har bayan sallar isha'I yayanta ya shigo
    gida kamar shi alamin ke kira wayar sa ta hau
    bugawa falon kai tsaye kan wayar ya nufa ya
    dauka yayain da malami ya sheko da gudu don yi
    masa oyoyo.anti Amina ta biyo bayansa daga jin
    muryar al'ameen kasa yana cikin farin ciki da
    doki cike da zuciyarsa ina yini yaya,yace lazy
    dokta ya karatu?"Yana yar dariya ya amsa
    Alhamdulillahi ai na kira can minna don in
    tambayi jikin mutunniyar sai aka ce min ta sami
    sauki harma ka taho da ita, yace haka ne amma
    kasan yana yin rashin lafiyar sai a hankali cikin
    dan kankanin lokaci sai ta birkice bari in turo
    maka ita,koda kaji sauyi daga gare ta kar ka
    damu haka yanayinta ya sauya,jikin sa yayi
    mugun sanyi duk a lokaci guda gabansa ya ci
    gaba da faduwa murya dishe yace to yaya Allah
    dai ya bata lfy,ya amsa da amin ya aje kan wayar
    gefe ya amsa gaisuwar iyalinsa sannan ya haye
    sama ya fada dakin mama yana shiga ta kara
    kudundinewa cikin bargo yasa hannu ya kwashe
    bargon ya watsar gefr yace tashi zaune sai ga
    antin ta shigo ta matsa bisa shimfidar ta birkito
    ta tana fadin yi mata a hankali ke mama tashi
    kinji! Ta ciccibo ta ta tashi zaune kamar wacce
    ta shekara tana ciwo saboda tsabar fita hayyacin
    da tayi Tausayi ya lullube antyn a hankali tace
    kinaji na?
    Ga alamin cen ya kira waya don Allah ki fidda
    mu kunya ki tashi ki je ki saurare shi badon mu
    ba sai don girman Alkawarin da kika daukar masa
    kafin ya tafi tashi kije kudinsa na bin iska kinji?
    Tamkar antyn na magana da dutse don ko motsi
    batayi ba sai idanuwa ta ke ambaliyar ruwan
    hawaye . Haushi da takaici suka rufe yayanta ya
    daka mata tsawa mai tsanani sai ta zabura
    bazaki tashi ba? Alamarin ya kara kure su cikin
    mamaki sukaji wannan kalmar ta fito bakinta
    Nifa yaya ba zanyi magana da kowa ba Gaba
    daya suka ware ido baki sake sai dai shi
    soja baya tsayawa yana kallon raini don haka ya
    cira hannu ya tsnke ta da wawan marin da yayi
    sanadiyyar daukewar numfashinta karkaf,ta zube
    sumammiya ya nuna cikin zafi yace ni zakiyi wa
    rashin kunya ba na wasa da ke ni zan iya karya
    ki wallhy anti amina da tuni take kwasar salati
    tace ai maganar karyawa ta kare tafa suma
    yallabai yanzu me za a cewa Al'ameen din
    Yace ta mutu ni tayiwa rashin kunya bata isa ba
    wallahi!Mtsw"ya ja dogon tsaki ya bar dakin
    falon ya sauka ya dauki kan wayar ya kanga wa
    kunnensa hello al'ameen naji na ya amsa ina
    kinka yaya yace kayi hakuri da mama al'ameen
    ya katse shi me ya faru yaya ina take yace ta
    suma al'ameen kayi hakuri da ita domin mama ta
    riga ta sami matsala....". Ya sauke salati ya
    katse shi yaya bazan iya hakura da sakeena ba
    kowane irin hali ta shi ina son ta haka koda kuwa
    ciwon hauka ne ya kamata,Roko na gare ku shine
    ku taimake ni ku kai ta asibiti don Allah ko
    nawane zan kashe yaya please ku taimake ni ya
    goge hawayen dake zuba bisa kuncinsa yayin da
    jikin yaya soja yayi mugun la a sar cikin taushin
    murya yace kar ka damu al'ameen zamu kaita
    kar ka damu kaji sai da safe. Ko kamin ya gama
    amsawa ya kife kan wayar
    al'ameen sai da ya lalubi wuri don baya gani
    yadda ya kamata sauran abinda ke zuciyar sa
    kuwa biro na ba zai iya rubuce shi ba domin
    al'amarin gagarumi ne maras misaltuwa sai dai
    muce Allah ka kiyashemu sharrin masu sharri
    amin summa amin Anti amina keta faman neman
    ran mama shi
    kuwa yayanta bai sake komawa ta kanta ba
    dakin sa ya shige don yin abubuwan da yake
    ganin suna da muhimmanci a gare shi ita kuwa
    mama zafin. Mari da tsananin yunwa tare da
    tarin damuwa su suka taru suka jefa ta cikin
    doguwar suma awa daya da rabi ta kwashe babu
    motsin rai sannan ta dawo duniya,ta fasa kuka
    tana fadin wayyo Allah na zan mutu wayyo Allah!
    wayyo!" Nan da nan hawaye suka tsunkewa anti
    amina saboda tausayin da ya kamata murya na
    rawa ta tarairayo ta tana fadin mama ki tausaya
    wa kanki wannan mugun halin da kika jefa kanki
    kin kuwa ga yadda kamannin ki suka sauya wane
    irin masifar so ne wannan na bala'I. Akan da
    namiji kike wahalar da kanki a banza a
    wofi ki mutu ya nemi wata ya aura,wannan
    sakarci ne mama kiyi wa kanki fada tun dare bai
    miki ba sannan ki sani idan kika ci amanar
    al'ameen Allah ba zai kyale ki ba,ta fizge jikin ta
    ta sake faduwa bisa shimfida ta kara fasa kuka,
    malami ya budo kofa ya shigo cikin sanyin jiki ya
    karasa gun su yace mami uncle al'ameen ya
    bugo waya, kafin anti amina tace wani abu tuni
    mama tayi wuf ta tashi zaune cikin sababi take
    fadin ba za a zo ba kaje ka gaya masa bazan
    dauki wayar ba dole ne sai na aure shi nace. Ba
    zan aure shi ba duk ku taru ku kashe ni kowa ya
    huta ta sake komawa ta dase ciki anti amina da
    malami suka saki baki suna kallon ikon Allah.
    Jimawa kadan ta dube shi tace,Mu je falon."
    suka fice jiki babu kwari,musamman Malami da
    sababin ya bashi tsoro ba kadan ba.Anti Amina
    ta dauki wayar tayi sallama,suka gaisa kafin
    yace, Ya jikin sakeenar? Ta farfado kuwa? 'Ta
    farfado Al-Ameen, har ta samu barci. Ya sauke
    numfashi,'Allah ya kara mata lfy. To amin.yace
    Anti,don Allah ki taimaka ki tuna wa yaya tafiya
    asibitin.Ni ina ganin babu abinda zai gagari asibiti
    koda matsalar junnu din ne, akwai ta su irin
    gudumawar da zasu iya badawa. Please Anti a
    kai ta asibitin a gwada." Idanuwan ta suka kara
    tara kwalla,jin yadda muryar sa ke rawa,ta
    tabbata hawaye ne ke zuba bisa kuncin sa.Ta
    numfasa tace "karka damu Al-Ameen,duk wani
    iya kokari ana yinsa.inshaAllahu Allah zai dube
    mu ya yaye mata wannan lalura.ka kwantar da
    hankalinka kaji? Ya amsa,Hankalina ba zai
    kwanta ba Anti,har sai
    naji muryar sakeena da bakinta ta gaya min
    tabbacin samun saukin.Ban san halin da sakeena
    ke ciki ba Anti,kowa cewa yake tana samun
    sauki,amma ni ban ji alamun ba a jiki na.zuciya
    ta tana min sake-sake iri-iri akan sakeena kuma
    tana nuna min ita acikin mummunan hali.jin
    muryar ta ne kadai zata warware min rudun dana
    fada.....Anti Amina ta amshe,komai yayi zafi
    mgnin sa Allah Dokta.ka tsaya wa addu'a kawai
    ita ce kadai zata taimake mu.shi kenan
    Anti,ngd.Idan Allah ya kaimu gobe zan sake kira
    ko na dace jin muryar ta.Tace To Allah ya yasa
    a dace.ameen
    Sukayi sallama ta aje waya ta koma bisa kujera
    ta kama kai hannu biyu ta matse kwallan ta tace
    wannan masifa Allah ka yaye mana,muryar mai
    gidan taji yana fadin kema zai zauna kina bata
    lokacinki yau mu ma bazamu ci abinci ba ke nan
    Ta share fuska ta dube shi yallabai ba ka ki
    kalaman dokta bane su suka kara dafani wallahi
    ya ya zamuyi da yarinyar nan ne yace oho!ni kizo
    ki ban abinci ina jin yunwa ta mike ta nufi kicin
    shi kuma ya wuce ebur yana kiran malami ya
    sauko da gudu yana amsawa gani dadi kaima yau
    baza kaci abinci. Bane yace ai na ci dadi to
    koma daki kayi barci sai da safe,ya juya ya haye
    saman yayin da anti amina ta fito da jerin kayan
    abinci bisa tire ta jera bisa tebur sannan ta zuba
    masa taja kujera ita ma ta zauna yana ci tana
    maida masa kalaman al'ameen sai da ta kare ya
    kurbi ruwa ya dube ta, Yace ni kinga duk wannan
    shiriritar ina yi ne
    kawai saboda hajiyar sa ta roki a rufe masa
    amma ni ban ga dalilin yawo da hankali ba yanzu
    ina fa'idar yin shirun tunda hankalin sa da ake so
    ya kwanta bai kwanta ba?mama ko zata mutu
    shi
    zata aura to me ne ne abin jin tsoron gaya masa
    matsalar da ake ciki banda shiriritarku ta mata,ta
    ce ai ba haka bane yallabai kaga kuma shi kansa
    marafa ya goyi bayan hakan"shi ke nan sai ki yi
    ta rarrashinta kafin gobe idan ta amince yin
    maga da shi shi ke nan idan kuma taki kya nemi
    wata karyar ki shirya masa kinga sharo karya ya
    same mu ke nan sai abinda Allah yayi ina
    amfanin sa
    Ta numfasa tace al'amarin hakuri zamuyi tayi
    rokona gare ka don Allah ka daina dukanta
    wallahi taurin kai zai kara mata ido waje yake
    magana muddin tayi min rashin kunya zan
    tabbatar da na hukunta ta yadda ya kamata don
    ni ba sa'an ta bane,you know that so ba zan
    dauki iskanci ba kina iya hawa sama idan kin
    kare maganar,tace ran maza ya huce yallabai ba
    ina nufin wani abu bane yaci gaba da cin
    abincinsa bai tanka ba ta zura masa ido tana dan
    murmushi ta san halin yan kayan ta idan kayi
    magana kaji yayi shiru to kaima ka tsuke dan
    bakin ka ka kama kanka shi zai fi zama alkairi.
    Garin Allah ya waye,baya ga sallah babu abinda
    Mama ta aikata,ta yada kai bisa kafet tayi lamo
    kamar sumammiya.Gaba daya ta rame,fuskar ta
    ta tsuke duk ta bushe idanuwanta sun kode sun
    firfito waje, sbd tsabar kuka.Malami ya fito
    wanka ya tsugunna gabanta yace "ìna kwana
    Anti?Tayi banza dashi,ya zura mata ido,Baki da
    lafiya ne Anti? Tunda ku ka zo da Daddy baki min
    mgna ba. Ta ballo masa harara,sai na tsinka mka
    mari ka sake min magana! Ta ja tsaki,ta juya kan
    ta wani gefen.Haushi ya kama shi,ya tashi ya ci
    gaba da shirin sa. Wannan karon kam bai gane
    kan gadon Antinsa ba. Me ke faruwane? Karfe
    bakwai daidai Anti Amina ta shigo,tana shigowa
    Mama ta rintse ido. Anti Amina ta dauko bisa
    kanta,ta dan dafa ta na san ba barci kike yi ba,ki
    tashi don girman Allah ga Dokta can ya kira.
    Kamar yadda na gaya miki jiya so yake yaji
    muryar ki,hankalinsa ya kwanta ko da gaisuwar
    sa ki amsa,zai ji dadi Mama.
    [12/01 17:32] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***6(TRUE LIFE STORY)
    Ku da baku wurin in kun amsa.To Mama ta amsa.
    Haushi kamar ya kashe anti Amina.ta mike tsaye
    tace, kar ki tashi Mamaa,idan kin sake jin nayi
    mikí mgn akan Al-Ameen,duk abinda kika so kiyi
    min! Mts....... Ta ja tsaki ta wuce. Mama ta
    rakata da nata dogon tsakin anti amina ta waigo
    rike da kugu ta zubo mata ido,lallai mama,ni kike
    yiwa tsaki? Yayi miki kyau! Taja kofa ta fice.kan
    wayar ta duka rai bace. Tace, hello! Yace hello
    anti,ta tashi? Bata tashi ba dokta.(nace"dokto ka
    fiya nace dolene?) "ba matsala,ai barcin ma yana
    da amfani a gareta.zan sake kira,ngd antí. Cike
    da tausayinsa ta amsa,kar ka damu sai anjima.
    To suka aje waya. Ta haye sama shake da
    haushi,amma bata nuna wa yallabai ba,don ta
    san ita zai tsatstsage danya. Iyaka tace da shi
    bata tashi barci ba Wasa wasa mama fa har ta
    sake kai bayan
    la'asar batasa kwayar abinci a bakinta ba
    hankalin anti amina ya tashi kwarai da gaske
    mama kam bata cikin hayyacinta gaba daya ta
    galabaita yunwa na neman tayi mata illa koma in
    ce tayi matan,shiyasa tana jin waya na ta
    bugawa taki dagawa don tasab mai kiran kuma
    bata da abinda zata gaya masa a hakikanin
    gaskiya ma hankalinta yafi rinjaye akan mama
    dake ta zama da yunwa tun safiyar jiya
    Tayi fada tayi rarrashi duk a banza misalin karfe
    biyar ta hada tea ta shigo da shi dakin wai ko
    Allah ya bata sa'a ta dan kurba me zata gani
    mama ke ta madedewa tsakar daki wata irin
    farar kuffa na hauhawa bisa bakin ta,tasaki kofin
    tea ta tarairayo ta tana sallalami kinga irinta ko
    mama nayi nayi dake kice abinci kin ki kina so ki
    kashe kanki a banza a rude ta sake bazamowa
    falo ta dauki waya ta kira wayar ofishin yaya
    abdul kadeea ta shaida masa halin da mama ta
    shiga
    Amma yanzu za a fara wucewa da ita asibiti nan
    take ya bata izini yace zai same ta asibitin babu
    baa lokaci soja daya ya sakata mota anti amina
    na tare da ita a gidan baya tana shafa mata ruwa
    a fuska sojan na jan motar an bata gado ga ledar
    ruwa na aiki a jikinta, wucewa minti talatin yayan
    ya iso ya same su jugum jugum,suna kallon ta
    rai bace ya watsa hannaye aljihu yace dama
    haka take so ba kuma shi zai taimaketa ba
    muddin tana motsin rai al'ameen ne mijinta so
    idan ta farfado ki fara gaya mata kafin na dawo
    zan koma ofis muna da mitin,tace to adawo
    lafiya ya wuce cikin kuzarinsa kuratan sa na biye
    da shi har bakin mota suka koma sannan guda
    ya bude masa ya shiga direban yaja suka
    wuce,anti amina ta ci gaba da zama dauke da
    tagumi zuciyar ta na mata saka iri iri haka wayar
    al'ameen ke ci gaba da bugawa cikin gidan ba a
    dauka ba malami ya shigo gidan dawo war sa ke
    nan daga maka ranta,kicin ya wuce kai tsaye
    saboda yunwa ce ta koro shi ya debo abinci ya
    zauna ya fara ci waya ta sake daukar ruri ya
    mike da filet din a hannunsa yana kara lomar
    shinkafa da salad ya dauki waya baki cike da
    abinci ya ce hello hello malami al'ameen ne ba
    kowa ne a gidan yace eh nima yanzu na dawo
    school mai gadi ya gaya min sun tafi kai anti
    mama asibiti wai ta suma.
    Jikin al ameen Ya kara mutuwa ya ce gaskiya
    Uncle duk ta rame kamar ba ita ba bata magana
    sai kuka Tunda suka dawo da dadi ba ta ci komai
    ba ko ni bata. Yi min magana ba sai yau ta ce za
    ta mare ni idan na sake gaishe ta wane irin ciwo
    take yi uncle hawaye suka tsunke wa Al Ameen.
    Bai san lokacin da ya kife kan wayar ba malami
    yabi ta hannunsa da kallo. Bai gane komai ba
    dan haka shima ya aje ya dauki abincinsa ya
    cigaba da ci yayi sallar magariba dadinsa ya
    shigo yayi masa sannu da zuwa ya amsa ya haye
    sama ya cire kaki yasa kana nan kaya jaket da
    wando ya sauko ya shiga kicin ya hada kayan
    abinci cikin dan matsakaicin kwando ya kira
    malami yace kai mota ya jirashi can su tafi
    asibitin,yace dadi yauwa uncle al'ameen ya kira
    waya dazun me kagaya masa na gaya masa anti
    ta sume kunje kai ta asibit to ke ka kirani a mota
    ya dauki kwando yayi waje jim kadan dadinsa ya
    fito suka tafi har zuwa lokacin mama bata gane
    kowa yayan ta ya zauna nan zuwa goman dare
    sannan suka koma gida da malami
    Anti amina ta kwana tare da ita kiran asubahin
    farko ta dawo hayyacinta ido ta zurawa anti
    amina kafin ta fasa kuka anti amina ta matsa
    gare ta ta dafa ta saman goshinta tace me yasa
    kike wahalar da kanki bayan ki na sane da cewa
    aure tsakaninki da al'ameen babu fashi,ta goge
    hawaye wallahi wallahi anti bazan. Taba cin
    abinci ba har sai yaya ya maida ni inda ya dauko
    ni kinji kuma na rantse bazan kaffara ba,baki
    sake take kallonta tama rasa ta cewa mama ke
    ci gaba da fadin na gwammace na mutu da a
    raba ni da dan liti sabo da haka mu zuba nida
    yaya idan jan idonsa zai sa in daina son dan'liti
    anti amina tace gadkiya ne kuma yanzu kika
    tabbatar min kinyi nisa ka kya jin kira
    To abinda zan gaya miki shine ki guji bacin ran
    iyaye rayuwa ki ba zatayi kyau ba muddin kika
    bar mahaifanki da BAKIN CIKI sannan dole ki
    fuskanci kalubale tunda kika ci amanar dokta
    bazan rufe miki ba mama koda nan gaba in ta
    Allah ta kasance zaki tuna dani kice na gaya miki
    a asibitin nan wallahi yadda kika sanya al'ameen
    kuka da radadin zuciya kema sai dan liti ya
    dandana miki fiye da hakan
    Da namiji ne fa ki bari ya gama shanye romon da
    yake hange a jikin ki kisha mamaki daidaiku ke
    da rikon amana su ajiye ki ke kadai suna
    girmamaki a matsayin matar sunna mai tsananin
    kamanta gaskiya shi ne zai ce kik zai kara aur
    amma sauran shagalinsu suke sha a waje su
    barki hoto a gida balle wannan Dan'liti daya sami
    shaidar banza don haka kibi a hankali mama so
    ba hauka bane tace na ji kin fada amman yarda
    ba dole bane ko ashe kin gane domin ni duk
    abinda mutun zai fadi akan Dan'liti ina daukar sa
    a matsayin hassada ina abin hassadar ga Dan'liti
    koda ban san shiba labarinsa ya gamsar dani
    kuma na tsane shi idan kin tsane shi ki daina
    maganar sa don zai sanima in tsane ki
    Ta ware ido sosai tana kallon ta ban yi mamakin
    jin kalamanki ba tunda kika iya shafawa
    idanuwanki toka ba kya ganin mahaifanki ki balle
    ki saurari nasihohinsu gareki kin ban kunya
    mama ban taba zaton wata rana mai kamar
    wannan zata zoba in sha Allahu zan rarrashin
    dadin malami ya kyale ki duniya ta koya miki
    hankali,ido cikin ido ta bata amsa zaifi kyau idan
    kika yimin wannan kokarin haushi yasa anti
    amina ta mikie ta fito babban falon asibitin tayi
    zaune har aka kira asalatu tayi alwala tayi sallah
    ta je ro addu'o'I tare da rokon Allah ya sanya wa
    al'ameen dangana idan har ya rasa mama
    Cikin shigar kakinsa tsaf ya shigo asibitin tare da
    malami shi ma sanye da kayan makaranta
    kuratan sojoji biyu na take masa baya dauke da
    kwandon kayan karin kumallon safe a babban
    falo ya same ta zaune bisa dardumar
    sallah,malami ya fara isa gun ta ya gaisheta ta
    amsa sojojin dake biye suka kwashi gaishuwa
    yayin da ta miki ta tarbi yallabai amma fuskarta
    babu walwala sannu da zuwa tace dashi ya amsa
    yauwa ya dai jikin na ta, tana ciki shiga ka ganta
    ai ta farfado tun asuba,ko?suka jera zuwa dakin
    tana gaishe shi jin muryarsa yasa mama ta
    runtse ido ya tsaya kanta yace ki daina matsr ido
    nasan kina ji na ina fatan amina ta gaya miki
    sako na saboda haka ina son ki gane wannan
    sakarcin bazai firgitani ba abinda na sani kawai
    al'ameen ya dawo a daura maku aure middin kina
    numfashi sauran shawara ta rage gare ki,
    Anti amina dake ta kallon ledar ruwa tasa
    hannu ta dago igiyar tabbas abinda take zato
    shine din. Ruwan ba a jikin mama yake ba cirewa
    kikayi mama, ta juya kan yallabai tayi masa kuri
    ka gani ko ta cire ruwan yaya ya kawo iya wuya
    kamar ya nannausheta yake. Ji cikin fushi ya
    juya ya fita anti amina tace da kanki ki ka kama
    drip din ki ka tuge,sau dubu aka samin sau dubu
    zan cire me ruwanku dani tunda baku kauna ta
    tana rufe baki yayan na shigowa da wasu nosis
    biyu amma abin karin haushin mama taki yarda
    su mai da mata ledar ruwan nan basu san
    lokacin da yayanta ya cire hannu ya tsinka mata
    mari ba,sai da bakinta ya tsatso jini saboda
    haushi da takaici kafin ayi haka ya bar dakin anti
    amina ta biyo bayan sa ta bar nosis na rarrashin
    mama yana shiga mota ita ma ta fada ciki tace
    kayi wa girman Allah yallabai karkayi fushi ka
    tsaya ka saurareni kar ki min magana akan
    wannan wawayar yarinya," I have finish with her,
    dama munyi waya da abdul-kareem sun ce za su
    zo harda abdul-rahman so suna zuwa zasu wuce
    da ita daga can su bata kudin mota ta wuce
    fandogari zan iya kashe yarinyar nan idan ina
    ganinta,
    tace wallahi ni ma shawarar dana ke son in ba
    ka ke nan idan kaji maganganun da mama ke
    fadi zaka tabbatar da tayi nisa bata jin kira sai
    addu'a kawai zamu zauna ne tana bamu wahala
    koda yaushe mu ma asibiti a aikin banza?ba zai
    yuwu ba a irin take taken ta tana gab da fara
    sufa mana zagi ku kyale ta da dan-litin shi ne zai
    koya mata hankali,yace ai an gama dokta zuwa
    kice ya sallame ku kawai zan sake kiran abdul-
    kareem din in ce su dame mi gida ta numfasa
    don murna kafin tace,"!58,naji dadi yallabai Allah
    shi taimake ka ita kuma ya shiryar da ita amin
    ga break fast can kije kici ki kyale ta bari mu kai
    malami school gada can zan shiga ofis to a dawo
    lafiya amin,ta fito sannan sojojin suka taso daga.
    Inda suke tsaye tare da malami suna jiran su
    babu bata lokaci suka bar harabar asibitin anti
    amina ta koma ciki tace wa nosis su kyale ta su
    tafi abinsu guda tace oga zaiyi fada madam idan
    ya shigo.
    ni nace ku tafi kawai abin ku ba mu muka
    kawota ba,kuma mu zamu biya bill ku wuce kwai
    ba wani abu"nosis suka wuce da mamaki anti
    amina ta hada abin kari ta hau ci bata sake
    komawa ta kan mama ba har likita ya shigo
    misalin takwas da rabi na safiya anti amina ta
    maida masa bayanini yallabai likita yace a'a baza
    ayi haka ba nan ya ja kujera yayi ta rarrashin
    mama,tayi shiru kamar da gaske sauraronsa
    takeyi da kansa ya nemo jijiya ya maida mata
    ruwan amman me yana gamawa bai ko bar dakin
    ba ta sa hannu ta zare ta aje masa robobin sa
    haushi ya shake likita ya jima yana kallon ta
    sannan ya dauki (file)din ta yayi rubutu,ya dubi
    anti amina yace kuna iya tafiya gida madam da
    alama ba zamu shirya da sakeena ba tace ai
    dama na gaya maka kayi hakuri dokta kan ta tayi
    mawa tace ba wani abu shawa ta kawai ia ce ku
    kyale ta ta auri wanda ta zaba may be rabon
    wahala ke kiranta,tace sosai kuwa dokta mun
    gode ji suka yi mama taja wani shegen tsaki duk
    suka bita da kallo likita yace I'am sorry for yau,a
    tunaninki kinyi abu
    Mai kyau ke-nan? NO,ba hk rayuwa take ba.
    Ya kamata ki rinka kulaw. Ya sa kai ya
    fice.Nosis din sa suka take masa baya,kowanne
    su babu wanda bai shakì taikacin Mama ba. Tana
    hada kaya direba na shigowa, yaya ya turo
    shi,idan anyi sallamar ya kaisu gida. Shi ke nan
    kaya sun tsunke karkashin kaba. Ya kwashe
    kaya,ta dubi Mama tace, ki na iya tasowa muje
    gida,idan kin so.Ta yunkura ta tashi,Anti Amina
    bata saurareta ba ta wuce abin ta. Da kyar ta
    sauko daga gadon,wani mugun jiri yayi tafiyar
    ruwa da ita,ta koma dabas! Ta zauna.(maganin
    mara jin magana,yarinyar nan tana ban haushì!
    Mts!) Tafi minti uku dafe da kai,sannan ta sake
    mikewa ta daddafa bango ta fito tana layi. Kowa
    kallon ta yakeyi,musamman Noisis din da komai
    ya faru a gaban su,ai nan take aka shiga maida
    labari. A mota ta same su. Anti Amina na gidan
    baya,duk ta kulle sakatun kofofin biyu,saboda
    haka dole Mama ta bude murfin gaba ta zauna
    tare da direba. Ko a cikin gidan ma,babu mai
    kula wani,hasalima Anti Amina kwanciyar ta tayi
    tasha barci,bayan ta yi wanka ta sauya kaya.Ita
    kuwa Mama taci gaba da sanya tsananin kunci
    cikin ranta,ji take kamar ana hura wa zuciya ta
    wuta.Tsananin son ganin Dan-Lati da kewarsa
    suka hana ta sukuni. A yadda jiri ke dibar ta,sau
    uku tana fitowa waje ta tsaya wai ko zata ga
    lakwa-lakwa ta sulale ta gudu.Amma ina,ko
    fuska babu a wajen kuratan nan,balle ta sami
    hanyar fita.Don haka ta kifa ciki tsakar falo,tayi
    ta sharara kuka har azahar,bata san lokacin da
    barcin wuya ya sace ta ba.
    Anti Amina ta sauko tayi girki ta gama bata
    farka ba.Dawowar Malami ya kwarara
    sallama',shi ya tashe ta,tayi doguwar mika tare
    da hamma mai kunshi da yunwa da wahalar
    duniya. Ta tashi zaune taja jikin ta,ta zauna ta
    jingina da kujera,wucewar 'yan mintoci.sannan
    idanuwan ta suka kwalli agogo.karfe daya hard a
    rabi. Da kyar ta yunkura ta tashi ta haye sama a
    wahale,tana shiga dakin ta zube a kasa,sbd babu
    karfi a jikinta.Malami da ke cire kayan
    makaranta,ya zubo mata ido.yana so ya gaisheta
    yana jin tsoran mari. Ya sauya kaya,ya fice daga
    dakin,wajen Momin sa ya shiga idanuwan sa cike
    da damuwa. Ya zauna kusa da ita,tana kallon
    yadda ran sa ke bace,don hk ta rungumo
    kafadun sa tace, "Yaya dai,yunwa akeji? Ya kada
    kai yace, Momi Anti fa zaa mutu,ku maida ta
    asibiti.Allah bata warke ba. Ta zura masa
    ido,tace,Ba laifin mu bane Malami,a gaban ka ai
    kana kallo taki yarda asa mata Drip. To ya take
    so muyi?" Yace, kawai ku kira mata abba yayi
    mata fada. Wlh bana son Antí ta mutu. Ina son ta
    Momì,me yasa take ta wannan ciwon ne? Ta
    kara rungume shi tace, kowa ma nason Antin ka
    Malami,kuma babu mai son mutuwar ta,Matsalar
    taki cin abinci ne,shi yasa ka ganta haka. To sbd
    me? Tace kaga ka yi shiru da bakin ka,kai yaro
    ne ba ruwanka da maganar manya.kai daì idan
    ka yi sallah ka roki Allah ya bata lafiya. Yace, To
    Momi,tace. Maza kicin ka zuba abincin ka.'ya
    fice tana kallon sa.
    Zuwa karfe biyar Mama ta sake fadawa cikin
    mummunan hali,bata gane kowa. Anti Amina ta
    rasa inda zata sa ranta,domin ta rasa yadda zata
    yi da Mama don ta ceto ran ta. Ta sauko falo da
    nufin kiran wayar ofishin yallabai. Shigowar mota
    harabar gidan,shi ya dauki hnklnta ta zage
    labulan taga ta daga.Motar Abdulkareem ke fakin
    a harabar aje motoci,ta dawo da sauri ta nufi
    kofa cike da farin ciki da baya misaltuwa. Ta
    bude kofar tayi waje,farin cikin ta ya karu,ganin
    har da Abba acikin su. Sannun ku da zuwa! Ta
    isa wajen tana fadi. Duk suka amsa,sannan suka
    rankayo cikin gida. Malami ya rugo ya rungume
    Abba. Bayan gaishe gaishe suka tambayi Mama.
    Tace,tana daki babu kyan gani,nama fito ne,in
    kira dadin Malami ko za mu sake komawa
    asibitin ne,sai gaku. Wlhy Abba taki cin komai
    tunda suka zo garin. Ban jin tasa ruwa a
    bakinta,wannan masifa dame tayi kama? Duk
    suka yi shiru sbd takaici,babu wanda ya tanka
    har Anti Amina ta mike ta kawo musu abincin da
    ababen sha. Ruwa kawai suka sha Abba. Ya-ce,
    muje mu ganta. Duk suka rankaya saman.
    Yanayin da suka riski Mama,ba karamin daga
    hankulan su yayi ba. Abba ya zura mata ido,idan
    da zai hadu da ita a hanya,ba zai shaida ta
    ba,sbd sauya kamannin da tayi,sbd tsananin son
    cikawa al-ameen alkawari ko alama bai barì
    tausayinta ya rinjaye shi ba. Don hk ya dubi
    sauran yace,wannan ba shi zaisa mutuncin mu
    ya zube a idon duniya ba.sbd hk zamu koma da
    ita asibiti,ta farfado.sannan mu wuce da ita
    fandogari. Farin ciki na Mama ta mutu a dakin
    nauran al-ameen wanan shne kwanciyar hnkli na.
    Ku dauko ta mu tafi.
    [12/01 18:20] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***7
    .Yayay abdul-kareem yace gaskiya ne abba shi
    kuwa yaya abdul-rahman abin ne ya zame masa
    banbarakwai don bai taba zaton labarin da yakeji
    abin ya kai haka ba duk da yana jin zafin abinda
    mama tayi ,halin da idanuwansa suka gane masa
    mama a halin yanzu kwarai tausayinta ya kwanta
    a zuciyar sa shi ne ya fara kai hannu ya ciccubo
    ta suka taimaka suka sauko da ita kasa kamat
    matacciya,da kyar likita ya karbe ta sai da yan
    uwanta suka yita rarrshinsa sannan ya bata gado
    yayi mata duk abinda ya dace. Acan yaya abdul-
    kadeer ya same su bayan sallar magariba kafin
    ayi issha'I suka rankaya gida akabar anti amina
    tare da ita,kusan kwana sukayi shawarwari akan
    al'amarin,kwana daya da wuni mama na kwance
    magashiyan ledar ruwa goma sha tara ta
    shanye,ana shirin daura mata na ashirin sannan
    idanuwanta suka fara washewa ta gane inda take
    hada ido da abba tare da karkaf yan'uwanta bai
    haifar mata da wata nadama ba illa kuka da ta
    fasa wai don su tausaya mata babu wanda ya
    tanka mata wannan itace shawarar da suka
    yanke babu wanda zai sake bata bakinsa don yi
    mata fada amma zata sha mamaki ranar da Allah
    ya yasa al'ameen ya dawo kasar nan,babu wanda
    yace cikanki har ta gaji da shashekar kukanta. A
    zaton ta shirun na su alamma ce ta saduda
    ma'ana sun rasa yadda zasuyi da ita dole suu sa
    mata ido anti amina ta fara bata ruwan lipton
    tana kurba da kyar take iya hadiye shi gaba daya
    Makogwaronta ya farfashe kafin gari ya sake
    wayewa mama ta samo kanta misalin goma da
    rabi kawai ganin su tayi sun shigo suna gaya wa
    anti amina an sallame ta zasu wuce yanzu bata
    yi mamakin jin haka ba don haka ta amsa da
    to,Allah kara lafiya ita kuwa yar gigalar murna ce
    fal cikin ta jin za a wuce da ita fandogari nan da
    nan suka kwashe kaya,yaya abdul-kadeer ya
    dauki matarsa,mama kuma tabi ayarin komawa
    gida a minna suka yada zango suka ci abinci tare
    da yin sallolin azahar da la'asr in banda su
    ameera babu wanda mama tayi magana dashi
    domin anti rabi ma ta sauya fuska al'ameen
    dintama bai sami kulawa ba suna idar da la'asar
    yaya abdul-rahman ya jawo matarsa daga inda
    ya aje ta aka maida jakar mama ciki ita ma ta
    fito ta shige gidan baya abba na tare da karamin
    yaya a gaba
    Shi ya jasu a hankali xuwa fandagori. tun
    daga kan kwana hankalin mama ya soma
    kwantawa, domin dai idanuwan ta sun hango
    wanda take son gani. yana zaune bisa benci a
    kofar shagonsa, yayi murmushi itama ta sakar
    masa nata. har motar ta wuce, ba su daina leken
    juna ba. sai da ta daina hangensa, sannan ta
    zauna sosai kirjibta nata bugawa, ji take kamar
    ta balle murfin motar ta fice taje gunsa. ya
    mikawa ayuba hannu suka tafa. yace baka da
    kyau! Yace karya kak don ubanka, kalle ni sama
    da kasa! ba kyawun sura ba, ina nufin.... ya kai
    masa naushi a kafada, shi ya katse shi. zan
    ci..... kai! ka kiyaye ni fa wlh! me na gaya maka?
    yadda suka dauke ya ahaka za su dawo min da
    ita. wahalar banza sukeyi sakeena mallaka tace.
    yace ranar da Allah kuma zai kama. ayuba baya
    wajen, duk ka gama iskancin ka. ya ballo masa
    harara yace, to ko ka na wajen me zakyi? kai ma
    ka ji da naka, don ubanka. Menayi? ni nakai ka
    iskanci a garin nan? dama wane kai, amma
    sannu a habkali xzaka biyo ni mujera hanya
    watakila ma ka xarta ni. ya tabe baki yace Allah
    ya sawwake, kai din ma so nake na janyo ka
    baya. ka auri yarinyara nan, ka manta da
    kudinrinka na wulakantata. ya dafa shi yace ka
    dan kula da shagon, bari na je nemo gasasshiyar
    kaza. kasan dole anjima ta zo£ ya xuba masa
    ido kawai, bai ce masa komai ba. yayi dan
    saurayin murmushin. ya mike ya fada motar sa
    yayi birnin gwarin tsinke. kai tsaye mama dakinta
    ta shige. umma bata gasganta idonta ba, irin
    yanayin da taga mama saboda haka tatashi tabi
    bayanta.
    Kallo daya tayi mata taji kanta ya ci gaba
    da sarawa, wani kululu ya daure xuciyarta,
    idanuwanta suka tara kwalla, saboda tsabar
    BAKIN CIKI. Ta jima kafin tace, Mama kina da
    hankali da tunani kuwa? Ji tayi an dafata ta biyu,
    muryar Yaya abdul rahma ke fadin, baki da lfya
    Umma, karki daga hankalinki, abba yace ki fito ki
    kyale ta. Ya kamo ta suka fito, jiri na dibarta, shi
    ya sa tace yawuce da ita dakinta. Abba ya taso
    ya biyo su, yayin da take kwanciya a gado.
    Gefen gadon ya xauna yace, bai kamata ki bar
    ciwon ki ya tashi ba halima, kin ji dai abinda Dr.
    Ya fada, jininki ne ke hawa saboda damuwar da
    kika sanya a ranki. Ki hrk kawai. Tace, ba
    alamun yin nadama a wajen Mama, ni kaina,
    nasan haka,amma shawarar da mu ka yanke da
    'yan uwanta shine mu sanya mata ido tayi
    shirmen ta, sai ranar da Al-ameen ya dawo xata
    gane mu ma ba muyi nadama ba. Abdul yace
    saboda haka ki kwantar da hankalinki, ISA sai dai
    mama ta mutu a dakin Al-ameen, ba zamu ji
    kunya ba. Su Yaya babba da Iyalnsu duk sunce
    gaishe ki, sai sun xo. Tace ina amsawa, Allah ya
    taimake mu, suka amsa ameen. Abba ya dube
    shi ya cigaba, kai ma ya kamata ka hanxarta
    wucewa yamma tayi sosai. Umma ta amshe, ba
    xai bari xuwa gobe ba? Yace, akwai aiki Umma,
    yanxun nake so na lallaba. Ta dan kada kai.
    Tace, to Allah ya Tsare agaida min safiyya da
    kyau. Zata ji, ki daina damuwa Umma, komai xai
    wuce da yardar Allah. Ta amsa da kai, tana fadin
    shikenan abdul, Allah yayi maka albarka. Yace
    amin. Ya wuce cikin hanzari. A tsakar gida ya
    hadu da su Haj.Hajjo. Ashe da gaske ne kun
    dawo? Yara ke fada mana yanxun. Yace eh, nima
    xan wuce kd kenan. Gaba daya suke to Allah ya
    tsare! Ya amsa yayi gaba abinda, su kuwa ciki
    suka kutsa kai dakin mama. Kwakwazon surutun
    su ya sa Abba ya ta so fito. Sannuku da dawowa
    Yaya. Yace yauwa, ga haliman can a dakin ta.
    Haj. Hajjo tace, muna nan mun ganin ikon Allah.
    Mama ta dawo kashi ba rai? Yace haka take so,
    ai ku daina bata bakinku, kowa ya sa mata ido.
    Haj. Gaje tace, lallai kam wannan al'amarin sai
    ido. Allah ya kyauta. Ameen. Suka fice tare suka
    koma dakin Umma, suka isheta da surutu. Duk
    iya kokarin mama na son fita a wannan daren
    abin ya faskara, domin dai Abba ya kasa ya tsare
    a falo har goman dare ya garkame kofar ya shige
    dakinsa barcinsa. Allah da ikon sa, abba bai xare
    mukulin ba, domin bai taba tunanin Mama xata
    iya aikata wani abu a wannan tym din ba lallai
    abba bai san Mama ta wuce tunaninsa ba. Yana
    bada baya, taji motsin rufe kofarsa ta yi wuf ta
    mike, takalmanta a hannu tare da mayafinta.
    Tayo sanda ta fito jim, tsakar falon bata ji mtsin
    kowa ba, sannan ta karasa kofar ta bude ta cikin
    nutsuwa ta sulale ta fice. Can ma kofar sassan
    hka ta bude ta, ta wuce zaurukan gidan, ta zare
    sakatun ta bude ta fita ta maida kofar ta sakaya.
    In bakayi bani wuri! Ta callah da gudu bata ko jin
    rashin karfin jikinta, sai da tayi rabin tafiya,
    sannan ta tsaya ta sa takalmanta ta yafa gyalen
    tana ta xuba haki, ta dau hanya babu jama'a
    sosai. Gata nan ga ta nan har kofar shagon dan
    gogan. Ya tare da dije a kofar shagon bisa banci,
    ta cukuikuye shi kamar na goye fadi yake, wai
    dan Ubanki dole ne? Kin fa matsa min da yawa,
    xan ci ubanki a daren nan, in ga mai kwatar ki!
    Kawai ganin mama yayi akan su. Ya banbare dije
    ya ture gefe, bai bata lokacin ya daga kanta ya
    shige, shagon yana jan tsaki. Mama ta daga
    itama ta bishi. Dije kuwa mikewa tayi ta kakkabe
    jikinta ta wuce tana kwafa. Ya hade rai a kujera,
    bai ko kalle ta ba. Ta matsa gare shi murya
    sanyaye tace, fushi kayi danliti? Ni ban yi fushi
    ba sai kai? Ina can naki ci na ki sha saboda kai.
    Ashe ka na nan ka tare da wata? Dubi yadda na
    rame na sauya kamanni, saboda tunanin ka
    Danliti. Bai kamata ka yi min haka ba. Ya dago
    idanuwansa farare sol! Sunji kwalli ya dubeta, ko
    mai nai miki ai kekika jawo, kinbi 'yan uwanki ki
    manta da ni, ba dole in sami wata ba! Tun
    yaushe kuka shigo garin nan? Nayi ta xuba ido,
    amma ban ganki ba, me kike tunanin xan dauka?
    Kafin tace wani abu ya fizgo hannunta xuwa
    daki, yana kara fadin, idan karya nake yi, xo muje
    ki gani! Ayuba dake kwance bisa katifa yayi
    firgigi ya tashi yana kallon ikon Allah. Ledar kaji
    ya janyo ya xaxxage su. Yace me kika gani nan?
    Saboda ke na tafi har birnin gwari na siyo miki
    gashin xamani kajin turawa.
    Dubi nan juice ne kala-kala har sanyi su ya
    fita, baki xo ba. Ba dole in yi fushi ba, in saurari
    mai so na! Ta sauke numfashi, idanuwan ta taf!
    Da kwallah, ba laifina bane Danliti, baka san irin
    bakar wahalar da na sha ba, don kawai su dawo
    da ni. Sau biyu ina kwanciya a ascibiti, dube ni
    da kyau, kai kanka kasan ba haka nake ba.
    Amma kayi hkr, tunda kana ganin kamar da
    gangan nayi, ka hkr? Ya xura mata ido jim,
    sannan yayi dan murmushi ya ware hannayensa
    yace, to oyoyo! Ta sa hannaeyanta ta rufe fuska.
    Yace kunya? Ashe baki so na, lallai na yarda ni
    kadai nake haukan sonki. Yana rufe baki ta
    matso da sauri ta rungunme shi. Ayuba, yayi
    gyaran murya. Mama tayi wuf ta rabu da jikinsa.
    Ya dubi Ayuba, yace malam ka fita ka bamu
    wuri! Yace, ai ku ya kamata ku koma daga waje
    anan nake so mu xauna, fita ka bamu wuri don
    Allah, shago fah abude yake, ya yankura ya tashi
    yana fadin, gaskiyya kuyi sauri ku gamacin
    kazaraku, barci nakeji. Ba ruwanka wannan. Ya
    fice yana waigen Danliti yana masa ishara da
    idanuwansa dauke da gargadu, wanda shi kansa
    ya gane nufinsa, shi yasa yake wani irin
    mur0ushin na iya shege. Yana fita ya dubi Mama
    suka hada ido dukkan su sukayi murmushi,
    sannan ya kamo kafadunta yace, gashi dare yayi,
    amma dole ki xauna ki cinye kajin nan, domin
    saboda ke na siyo su. Ba tace komai bam ya
    xaunar da ita gefen katifa, ya jawo kayan
    kwalama, ya baje mata kajin, yana bata abaki,
    tun tana jin kunya har ta saki jikinta, tana amssa
    sosai tana ci, suka ci suka sha suna hirar bayan
    rabuwa. Bayan sun kare. Danliti ya dubi
    agogonsa ya ce shadaya da kwata yanxu, ya
    kamata kije gida ko? Sai gobe, ina fatan xaki rika
    cin abinci don ki gyagije kyanki ya dawo kamar
    da. Kinji ni? Tace, naji kuma xan kiyaye, amma
    don Allah ka daina bari 'yan mata na xuwa
    gunka, watarana xamuyi dambe da su wlh, kaji
    na rantse. Ya kyalkyale da dariya son ransa kafin
    yace, xaki kuwa sha duka, don dai nasan sunfi
    karfinki. Wannan jikin naki rugu-rugu babu kwari.
    Ya fadi yana mammatsa hannayenta da
    kafafuwanta. Ta yankura ta tashi tana cewa,
    haka kake gani, ka maida abin wasa, zaka sha
    mamaki. Shima ya mike ya kamo yatsunta, yace
    karki damu, ke kadai nake so, ko da damben ya
    kama kuyi, xan shigar miki balle ma banda
    lokacinsu. Ke me xai dameki? Tayi murmushi,
    tace, to shikenan sai da safe. Ya sumbaceta
    yace, muje na rakaki. Suka fito yana rike da
    hannunta, tayi wa ayuba sallama suka wuce. A
    kofar gida suka fuskanci juna, tallafo kuncinta ya
    xura mata ido, yace karfa ki damu da ganin Dije
    tare da ni, wlh ba sonta nake ba, kawai ta matsa
    min ne dole muyi soyayya, amma xan dauki
    mataki akanta, tinda ta fara bata miki rai. Tayi
    murmushi, tace, nayarda da kai, ina fatam Allah
    ya yarda mana, ya bamu nasara abinda muka sa
    gaba. Da sauri ya amsa amin sakeena. To sai da
    safe nagode, wannan karon abin ya cigaba akan
    labbanta ya sumbace ta. Ta juya da sauri, ta
    tura gida ta shige ta maida sakatu. Danliti ya
    runtse ido ya jinjina hannayensa, shege ni! Ya
    juya yana takawa dda+dai kamar wani
    kasaitaccen basarake. Mama kuwa sanda takeyi,
    kamar barauniya ta turo kofar fa'aar dshigo ta
    mayar d hankali ta kuleta, ta fada gado. Tana jan
    mayafi, taji a; ttay bude kofa, tayi tsaye jim,
    sannan ya mayar ya rufe. Muryar umma taji tana
    fadin, menene alh.? Yace kamar motsin naji ana
    taba mukulli.. Tace Innalillahi an shi ne? Yace
    amma ban ga kowa ba. Ya dubi agogo, karfe sha
    biyu saura kwata, dare ma bai yi ba sosai, to
    Allah yai mana tsari da sharrin masu sharri. Yace
    amin, je ki kwanta. Cikin fargaba suka bar falon.
    Mama ta gyara kwanciya tana gyatsar naman
    kaxa. Dan kanta tace kwanta naman kaza. Tayi
    tunani Danliti har barci ya kwashe ta, shi take
    marfi yana sa mata naman kaza abaki. Da safe
    tayi wanka, duk 'yan ciwukan da suka rage ba su
    warke ba, ta goga musu mai, ta shafa hoda ta sa
    atamfah riga da xani, nan da nan ta dan yi fasali,
    duk da cewa akwai rama sosai a jikinta. Yau kam
    tayi dan kyan gani, ta fito falo wajen Umma cikin
    kicin inda take aikace aikacenta, tace sannu
    Umma ina kwna? Ta juyo da sauri ta dubeta
    sama da kasa, tace kalau na kwana. Ta kara
    matsowa tace, bari in gaida Abba, sai in xo in
    tayaki aikin. Bata amsa ba ta fice, ta bita da
    kallo sannan ta kada kai tace, Allah ya shirya.
    Dakin Abban tayi sallama, ya amsa ya bita da
    kallo, ta karaso gunsa ta tsugunna, ina kwana
    Abba?
    Yace Kalau, ta dan dube shi, amma bata
    kara komai ba, ta mike tayi waje ta koma kicin:
    Umma me xan tayaki? Tace ban so, koma dakinki
    kawai. Saboda me Umma? Ai ban isa na fadi ko
    saboda mene ba, tunda kin xama shafaffiya da
    mai. Je ki kawai ki sha xamanki. Kai tsaye kuwa
    ta wuce daki abinta. Tana fadi cikin ranta, kya
    gama girkawa, mu zo mu jajja (hmmm mama tayi
    nisa walle). Kan Umma ya sara ganin yadda
    mama ta wuce ko ajikinta, bata damu ba.
    Mamaki bai gama kashe Umma ba sai da ta
    hange ta kicin din tana diban abinda take son ci.
    Tana kallo ta koma dakinta ta cinye, ta maida
    kayan kitchen ta fito. Haushi ya kume Umma
    bata san tym din da tace, Uban wa kika ajewa
    kayan ya wanke miki? Tabbatacciya! Ta dan bata
    rai ta juya ta kwaso kayna ta wanke. Karfe 9
    abba ya fita harkokinsa. 9:30 mama figi gyale
    tayi waje, Umma nace na wanka. Ta sha hirarta
    wajen Danliti har 12pm sannan ta tsallaka ta
    gangara wajen Baraka. Sosai taga sauyin fuska
    wajen Inna saude. Sam abin be dame ta ba.
    Suna kebewa da Baraka tace. Kawata ban gane
    ba, sai da nayi miki kallon kurulla. Yanxun
    saboda Allah dawowa kikayi? Tace ga ni kuma
    kina ganina. Matsala tace, babu ruwan kowa.
    Mutane masharanta ne kawai, saboda Allah yayi
    wa Danliti kyau da farin jini, ga shi ya Rufa masa
    asiri, shi ya sa ake masa hassada.... Ta katse ta,
    idan hassada ce, ai kuwa kem kinyi masa da.
    Menen baki fada ba akansa? Tace, Rashin sani
    ne, duk surutan da akeyi wai dan Iska ne dan
    guguwa. Dan wata tsiyace, ni har yanxun Danliti
    bai taba furta min maganar banxa ba balle ya
    nemi aikata wani shashanci. Rashin fahimta ne
    kawai yasa ake masa zargi, kisan mutum mai
    farin jinin 'yammata (Kuji fa wai bai taba mata
    komai ba?) baki ganin ko mace ce ta fiye samari
    sai arinka mata wani irin kallo? Baraka ta sauke
    fuska, tayi guntun tsaki, baki jin kira Mama. Allah
    ya shirye ki. Ameen, ni bari in koma gida, dama
    lekowa nayi mu gaisa kisan na dawo. Tabita da
    kallo, ki na san kin dawo wajenki xano? Menene
    anfani kawancen mu? Bayan ko na gaya miki
    gaskiyya bakyaji. Allah ko? To Allah ya bamu
    alkhairi ki gaida mohd dinki, in yazo. Yaushe
    xasu kawo gaisuwane? Ko bai shirya aure bane?
    Wlh ban masa zargin komai ba, amma sonsa bai
    rufe min ido ba, ina bukatar in gama sanin ko shi
    waye tunda ba gari daya muke ba. Ta tabe baki,
    Baraka ke nan, Miss kakale! Ba kakale bane,
    gaskiyya ce kawai, daga kinta sai bata. Shi ya sa
    nake nuna mikita, don banson ki bata. Ta mike
    hannu daya kame da kugu, tace, nagode, ni nayi
    gida, kar Umma ta neme ni. Tasa kai tafice.
    Baraka ta biyota, ta sallami Inna ta rako ta iya
    zaure ta juya. Ta shige gida, tabar mama dauke
    da mamaki. Tai kwafa tace, kiyi da gwana
    yarinya. Ta kama hanya ta koma wajen Danliti,
    wasa-wasa sai da ta bata mini talatin anan,
    sannan ta karasa gida. Umma na zaune tskar
    falo ta sha tagumi, ta gaji Mama ta shigo babu
    ko tsoro ko fargaba tace, sannu da gida Umma.
    Inna saude na gaisheki. Ta zura mata ido ba tare
    da cire tagumin ba, jima kafin tace, da izinin wa
    ki ka bar gidan nan Mama? Ta mimmike kafa
    sosai akujera. Tace ai kinshifa wanka ne Umma
    shi yasa banyi miki magana ba. Umma ta
    numfasa, tayi hucin BAKIN CIKi tace, lallai kin
    isa mama, duk son danliti ne yasa kika zama
    maras kunya? To kibi a hankali, duniya zata koya
    miki hankali, muddin kika dauke ta kika goya. Ta
    figi gyalenta, ta mike cikin sauri tana fadin,
    Uhm.....! Ta wuce ta fada dakinta, tayi
    kwanciyarta. Umma ta kada kai, kwallah suka
    xubo mata, ta share tace, Allah kana kallo, munyi
    iya yinmu, amma shiriya na wajenka, kayi mana
    gaji Ya Allah. Nan Umma taci gaba da zama tana
    shan BAKIN CIKI tare da takaici mai tarin yawa
    har aka kira azhar, ta tashi tayi sallah. Abba ya
    dawo ta labarta masa, hannaye biyi ya kama kai,
    takaici kamar ya kashe shi, bai niyyara kara yiwa
    Mama wata magana ba akan Danliti, amma dole
    tasa ya kira tazo dakinsa ta xauna. Yayi mata
    kaca-kaca, sannan ya sa mata dokar fita ko'ina,
    duk da yasan ba dole bane tabi umarninsa.
    Tabbas hakan ne, yadda Mama ta fito dakin bakin
    nan nata ya kai wani gari wai shi ZUNTU. Shi
    kasna ya san rashin kunyta Mama ta kai wani
    mataki na kololuwa kwatance, ta xauna bakin
    gadon ta tana fadin a fili, wannan shine bature
    ke kira Impossible! Tunda kuka hana shi xuwa
    guna, dole inje gunsa mu ga juna. Ta saki wani
    lafiyayyen tsaki, ta yada kai bisa filo.........
    Maganar mama dutse. 7days
    kenan babu abinda ta fasa, muna iya cewa
    al'amarin kara haukata yayi. Domin a halin
    yanxun Mama bata shayi, agaban Umma zata
    dauki mayafinta, ta fice. Umma na kira, tana
    fadin tana xuwa yanxu xata dawo. Sau uku
    Umma na xuwa da kanta kofar shagon Danlinti,
    tana taso keyarta. Jama'a na kallon su, gwanin
    ban kunya. Sai da Abba ya hanata xuwa. Yace
    tasa mata ido, tunda ta zama gagararriya.
    Wannan abin kunya ya zama abin yayatawa
    awajen su hajjo, duk inda suka xauna xancan
    kenan. Babu abinda bai dawowa kunnen Umma
    ba, sai dai tayi kuka ta share hawayenta ta
    barwa Allah komai. Mama fa ta gagari kowa,
    suna ji suna gani mummunan labari na ta
    yaduwa har gidan Gwaggo Hausi. Daga can
    labarin ya mika gidan Marafa. Nana take mami
    ta tsani auran mama da Al-ameen. Shi kuwa
    Marafa nuna mata yake su daina kama jita-jita.
    Aure dai nufi ne na Allah, idan sakeena matar Al-
    ameen ce, bbu makawa xai aureta, idan kuwa ba
    matar sa bace si barwa Allah yayi masa zabin
    alkhairi. Duk da haka al'amarin yana jefa Mamai
    cikin tunani ba kadan ba, kuma da Al-ameen zai
    ji shawarar ta, da ta umarace shi daya hakura da
    sakeena, tunda shasahnci tasa gaba. Sallar
    la'asar ta kammala, amma bata bar sallayar ba,
    saboda gabatar da lazimi takeyi. Wata tasi tayi
    fakin kofar gidan, direban ya fito ya bude but,
    yana fido jakar kaya. Yana rufe but din, idanuwa
    na suka nuna min Al-ameen a tsaye ya cusa
    hannu gaban riga ya zaro kudi ya mikawa
    direban, yace, ka rike chanji. Ya sunkuci jakarsa
    ya wuce. Direba na xuba gdoiya. Ya tura karamin
    gate ya shiga, bakin mai gida har kunne ya taso
    da gudu ya amshi jakar yana fadin Maraba da
    oga! Fuskarsa babu walwala sosai, yace ya
    kuke? Lafiya lau oga. Ya shige masa da kaya
    falo. Al-ameen yayi sallama, muryar sa ta dauki
    hankalin duk wanda ke cikin gidan. Iya ta riga
    kowa fitowa, wa nakehi kamar dan Iya? Ya nufo
    ta fuska sake, ni ne iya, surprise ko? Ya dan
    rungumo tana fadin, ai kaki koya min turancin
    nan, da yanxun na gane nufinka. Yana murmushi
    ya rabu da jikinta, ya dubi Ladi, Hajiya Ladi ina
    fatan kunje kun duba min jikin sakeena ta? Tace
    muna dai shirin tafiya da hada tsaraba. Ya ce,
    baku da tsraaba? Gaskiyya kunyi min babban
    laifi. Tace, mun san hakan amma tuba muke. Ta
    ya kuke? Ta amsa lfya lau ya hanya? Yace,
    Alhmdlh. Yana juyo wa sukayi ido hudu da mami
    tana masa kallon mamaki. Ya nufe ta da sauri ya
    rungumeta, Mami na! Idanuwanta suka tara
    kwalla, ta kasa cewa komai har ya dago ya
    dubeta, yayi dan murmushi. Yace, nayi muku laifi
    Mami, kuyi min hkr na kasa daurewa ne. Tace
    nagode Allah da ya kawo ka lfya. Amma banji
    dadin xuwanka ba Al-ameen. Yace, na tuba
    Mami, ki duba halin da nake ciki, kiyi min uzuri.
    Ta dan kada kai. Tace, muje ciki ka sha ruwa ka
    yi sallah. Suka wuce yana tambayar Dadinda.
    Tace, xai dawo anjima daga kd. Yana xama Ladi
    ta shigo masa da ababen sha masu sanyi. Bayan
    ya jika makoshi, ya dubi Mami yace, ya jikin
    sakeena? Na daina kiran waya, don kunnuwa na
    ba za su jure jin mummunan labari ba, koda
    yaushe. Dalilin da yasa kenan, nace ya xama
    wajibi in xo inga halin da take ciki da idanuwa
    na. Dan hutu muka samu na sati daya, shine na
    yi anfani da wannan damar. Yaya yanayin jikin
    nata yake? Ta numfasa sosai kafin tace, jikin ta
    har yanxun a rikice yake, xan so ace Allah ya
    saka maka hkr, da dangana akan sakeena, domin
    kwakwalwarta ta jirkita Al-ameen..... Hauka
    Mami? Kina nufin sakeena ta haukace? Inna-
    lillahi wa Inna-illaihiri Raji-un! Idanuwansa suka
    tara kwalla, ba xan iya hkr da ita ba Mami, ko ba
    zata taba warkewa ba, sai na aureya. Alkawari
    ne wannan Insha Allahu ba xan karya wa sakeena
    ba. Tana ina ne yanxu? Ita ma nata idanuwan
    suka kawo kwalla. Ta ce, tana Fandagori, kuma
    ni ma xan so hakan Al-ameen, domin duk abinda
    kake so, nima shi xuciyata take matukat so da
    kauna. Amma al-amarin ya sauya salo, ka dauki
    kaddara kayi hkr da ita, hankalina zaifi kwanciya
    Al-ameen. Da gudu hawayen sa suka wuce bisa
    kyakkyawar fuskarsa, ya matso ta a hankali, ya
    dauko hannayenta biyu ya matse, ya dubeta ido
    cikin ido. Yace, har abada bana fatan in saba
    umarnin ku mama, amma ina rokon alfarma ki
    ban izini in cikawa sakeena alkawarin da daukar
    mata. Zan tafi samun nutsuwa, idan ina kallonta
    a matsayin mata ta kowane irin yanayin take. Ina
    rokon ki Mami ki taimaka min. Ya jingina
    goshinsa bisa kafadar ta, ya matse hawayensa
    tare da ajiyar zuciya mai karfin gaske. Haka
    maminsa ke cikin irin wannan yanain. Ta jima
    shiru tana tunanin zuci, tana son gaya masa
    gaskiyya, amma bakinta ba xai iya furtawa ba,
    saboda tausayin dan tilon dan ta. Ta yi ajiyar
    zuciya. Tace, nayi maka Umarni akan duk abinda
    yafi xama alkhairi Al-ameen. Mike ka je kayi
    sallah kaci abinci. Ya dubeta yana share kwalla.
    Yace, nagode Mami. Ta danyi murmushin dole.
    Jeka yi sallah. Ya tashi da sauri ya dauki jakarsa,
    ya fice. Mami ta raka shi da kallo, hannunta a
    kunci. Ta nunfasa kafin tace, Allah gamu gareka.
    Yana shiga, bangarensa ya isa ya yar da jakar
    hannunsa ya xauna gefen gado
    Ya kama kai hannayensa 2 yana yiwa
    Allah tasbihi. Jim kdan ya tura hannu aljihunsa,
    ya xao wallet dinsa ya bude ya xurawa dan
    karamin hoton Mama ido, nan da nan hwaye suka
    goce masa, bai ma san tsaninin kukan da yake
    ba har da shassheka, kamar xuciyarsa zata tsago
    kirjinsa. Allah da ikonsa, tamkar mami na da
    masaniya ta taso ta biyo shi dakin, don ganin a
    wane yanayin yake? Da sauri ta karaso ta zauna
    kusa ta shi ta rungumo abinta, idanuwan na tara
    kwalla. Komai ya sami bawa daga Allah ne Al-
    ameen, bai kamata ka xauna ka rinka kuka ba!
    Jin muryarta yasa hankalinsa ya dawo jikinsa,
    sannu-sannu hawayensa ya tsane. Ya dago ido
    jajur! Ya dubi Mami, yace mami ki amince min
    inje in dubo sakeena Yanxun. Ta goge masa
    guntun kwallan dake bisa kuncinsa. Tace, na
    baka izini Al-ameen, fargaba na kawai dare.
    Yace, kar ki damu Mami. Allah xai tsare.
    Shikenan, Ubangiji Allah ya sa ganinka ya xama
    waraka gareta, hankalin kowa yakwanta. Yace,
    Ameen Mami. Tace , To kayi sallah Maza-maza,
    don Allah kar ka zauna dogon tunani. Yanxun xan
    fito Insha Allahu. Ta mike ta bar dakin. Al-ameen
    Ya sauke numfashi, shima ya mike ya fada bayi,
    nan da nan ya watso ruwa ya dauro alwala ya
    fito. Bayan yayi sallah ya kimtsa, ya fito Mama
    ta matsa yaci wani abu, amma bai iya zama ba,
    gaba daya hankalimsa ya koma Fandogari. Sai
    dai ya sha Mamaki daya ga Mami ta nace dole
    ya tafi da direbanya, bai yi musu ba. Kai tsaye ya
    shiga mota direba ya ja shi suka dauki hanya
    suka bar Mami cike da damuwa tare da tunanin
    yaya al'amarin zai kasance idan Mama ta juya
    wa Al-ameen Baya?
    [12/01 18:24] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2*** 8
    Ba su ido Fandogari ba, sai
    karfe 8pm, babu bata tym gidan Uban dawaki
    suka dosa. Ya shige sassan sa tare da sallama.
    Umma ta amsa ba tare da ankara da mai muryar
    ba. Sannu Umma. Ta dube shi da kyau, gaban ta
    yayi mugun faduwa, ta mike tsaye tana fadin, Al-
    ameen! Saukar yaushe? Yace, yau din nan
    Umma. Ikon Allah. Sannu da xuwa! Zauna mana,
    ya zauna yana amsawa. Kafin yace, ina yini
    Umma? Ta amsa, lfya lau ya karatu? Mun gode
    Allah, ya jikin sakeena? Tayi dan shiru, kafin tace
    wani abu. Abba yayi sallama ya shigo, duk suka
    amsa amsa Abba! Yace, ah! Al-ameen! Saukan
    yaushe? Yace daxun da la'asar Abba. Ya xauna
    suka gaisa, sannan ya sake tambayar jikin
    mama. Abba yace ciwo na nan Al-ameen. Halima
    kawo masa abinci ya ci, kafin muyi magana.
    Abba bana jin yunwa, domin na riga na saba da
    ita, tun tym din na sami labarin tashin hankalin
    da kuke ciki. Abin daya hana ni jurewa kenan,
    nace dole in xo inga halin da Mama take ciki.
    Abba yace, gaskiyya ne. Mama na nan cikin
    lularar da ta sameta sai dai al'amuran zai ba ka
    mamaki idan na gaya maka alabari ya sha
    bambam Al-ameen, nasan an boye maka komai
    coz of karatunka, amma yanxun dole ka sani,
    tunda ka zo. Jikinsa ya kara sanyi, yayi xuru
    yana sauraron abba, al-ameen rayuwa ta
    sauyawa mama, wanda muke ganin sa tamkar a
    mafarki, daga ni har 'yan uwanta kaf! Babu
    wanda ba shi ckin alhinin wannan abu. Balle
    kuma kai da soyayyah ta hada ka Mama, kuma
    ita da kanta takwo mana kai cikin gidan nan. Shi
    yasa nayi rantsuwa, idan mama xata mutu, sai
    dai ta mutu a dakin ka tunda tun farko ita ta
    kawo ka. Ashe kuwa babu wani dalili ko uzuuri
    da xata kawo mana mu saurare ta. Nasan har
    yanxun kana jina a hagunce ne, baka gane inda
    na dosa ba. To bari na fito maka a mutum kada
    ka wahalar da kanka, Magana daya ce, mama ta
    gano wani kuma idanuwanta sun rufe ta manta
    cewar tayi xafin farko kuma na karshe a
    swajena. Ka fahimce ni? Gaba daya kansa ya
    kunce, daga yadda yayi kuri idanuwan sa kafe
    yana kallon Abba, suka gane bai fahimci su ba.
    Saboda haka yace, dole ka shiga rudu fiye da
    wanda ka shuga a baya, amma ina so ka sani,
    mu muna tare da kai, ba mu san kowa ba face
    kai, ba don komai ba sai don tun farko kai tafara
    kawo mana. Abinda nake son ka gane shi ne,
    xuwanka ya sanya ni farin ciki. Domin kai kadai
    nake jira in tabbatar wa Mama cewa lallai ni ba
    tsohon banxa bane, kuma bana magana 2.
    Ina mai tabbatar maka ba xaka koma ba
    sai na daura auranka da sakeena da yardan
    Allah. Na gama magana ta, ka tashi hankalinka
    kwance, kashiga wajenta tana nan cikin dakinta.
    Ya mike ya bar falon. Umma ta dube shi tace,
    Al-ameen! Murya dishe ya amsa, na'am Umma
    tace kayi hkr, ka kwantar da hankalinka. Mama
    bata isa ta xubar mana da mtunci ba. Kai zata
    aura da yardar Allah, domin da kai ne akayi mata
    baiko. Tashi ka shiga wajenta ku fahimci juna. Ta
    mike tabashi guri, don yaji dadin tashi......... Me
    kunnuwan Al-ameen ke ji yau? Ya runtse ido
    tamau! Ya girgiza kai wai ko barci yakeyi ne?
    Abba ya xo masa a mafarki. Ya bude idanuwan
    ya ware su sosai, tabbas zaune yake cikin falon
    su Mama. Kenan dagaske ne maganganun da
    Abba ya gaya masa? Kirjinsa ya soma bugawa ji
    yake kiris! Yarage ya zare masa rai, saboda wani
    gagarumin ciwo da yaji cikin xuciyarsa, nan take
    ya kama shi. Motsin kirki ya kasa yi har Umma
    ta sake fitowa da nufin dauko wa Abba
    abincinsa. Ta danyi jim, tana masa kallon tausayi,
    sannan ta matso tayi kiransa, ya dubeta firgigi
    idanuwa sun juye jajur! Tace, ka na xaune, baka
    shiga ba? Tashi ka shiga mana, ka kwantar da
    hankalinka, komai xai wuce Insha Allah, ya mike
    a kasale, ya nufi dakin ba tare da yasan me xai
    je yayi ba. Tana zaune tsakar daki ba ta hade kai
    da guiwa, tsiyayar hawaye kawai takeyi, domin
    tana jin duk kalaman da Abba ke fadi. Daf! Da ita
    ya tsugnna, bai san lokacin da yasa hannu ya
    dago fuskarta ba. Sukayi wa juna xuru tsawon
    lokaci kafin yace, kin ganeni sakeena? Al-ameen
    ne, kin gane ni? Ta kau da kai abinta. Da sauri ya
    kara juyo da ita, kiyi min magana sakeena ko na
    sami nutsuwa saboda ke na dawo kasar nan, don
    na duba jikin ki. Ina can tunani da xulimmi sun
    addabe ni, idan kin gane ni, ki amsa min, ya jikin
    ki? Ta watso masa harara, hawaye na kwarara.
    Tace waya gaya maka banda lfya? Yace, haka
    kowa ke gaya min tun tym din da na daina jin
    muryarki a waya, komai nawa ya tsaya sakeena,
    radadin ciwon daya sameki, ya hanani sukuni. Ina
    fatan gani na ya zama sanadin samun saukin ki.
    Ta goge kwalla. Tace duk wanda ya gaya maka
    banda lfya, ya maka karya, kalau nake, gani kuma
    kana kallo na xaune, sai dai na tabbata dawowar
    ka zata iya zame min cuta! Ya kara xura mata
    ido , kina nufin abinda Abba ya gaya min yanxun
    gaskiyya ne? Tace ka daina kokwanto. Ya
    langwabe kai gwanin ban tausayi. Yace dole nai
    kokwanto sakeena, don nasan akwai alkawarin a
    tsakanin mu, kuma bana tunanin zaki yaudare ni,
    wannan ya tabbatar min da tsantsan son da kike
    min. Ban taba kallonki da xuciya 2 ba sakeena.
    Shiyasa har halin yanxun da nake magana dake
    ban yarda kin karya alkawarin mu ba. Ta kalle
    shi a dage, ta watsar tace, ya kamata ka amince,
    tunda gashi da bakina ina gaya maka, tsutsun
    soyayyarka yayi fiffike yayi dogon tashi. Ya dafe
    kirjinsa a natse idanuwansa tam! Da wahaye,
    yace, bai tashi ba sakeena, nayi rantsuwa kina so
    na. Akwai miskhila dai a wani wuri, ki gaya min
    laifin da nayi miki. Wlh da kaina xan hukunta
    kaina, koda da jinin jikina ne xuba, idan har zai
    zama fansar tarin laifin da nayi miki. Gaya min
    da sauri inji. Ta ya mutsa fuska, hawayen ta ya
    bushe tace, Al-ameen ka farka daga barcin da
    kakeyi ka saurareni, ni sakeena na gaya maka a
    da naso ka, amma yanxun ban son ka, ba kuma
    zan aure ka ba, idan sama da kasa za su hade!
    Kaji ni ko? Sai na maimaita? Ya matse ido,
    kwalla
    masu zafi suka yo waje da gudu, ya dan kada kai
    murya shke yace, kin xuba min dafi, kin xuba min
    dafi sakeena. Baki tunanin amana? Yasa hannu
    ya kamo yatsunta, ya kura wa zobensa ido, ya
    ciga, baki kallon zoben alkawarin mu? Me yasa
    kika mance da dimbin kalaman da kika sha gaya
    min? Wadanda suka jaddada imani na akan son
    da kike min? Ta kwace yatsunta a hankali ta zare
    xoben, ta jefa masa, ga tsiyarka nan, idan shi
    kake kallo a matsayin alkawari, ni ma cire min
    nawa ka bani. Yaci gaba da kallonta, kafin ya
    dauko zoben yace, kiyiwa Girman Allah ki maida
    zoben nan sakeena.... Bazan karba ba! Idan ma
    ka aje shi, zan jefa shi masai! Kuma nima dole
    ka ban nawa! Yace sai dai ki kashe ni, sannan ki
    zare shi, wannan din ma zan ciga da boye shi,
    har xuwa tym din zaki sami nutsuwa dakin
    auranmu. Ta kwada masa harara, sannan tayi
    wani dan murmushi na kaico, ta kauda fuska, y
    mika hannu ya kamo habarta, ta sa nata da karfi
    ta doke nasa, kafin tace, karka sake tabani, idan
    ba haka ba kuma sai na kurma maka ihun dan
    iska! Ta mike da sauri ta bar wajen, kai tsaye
    bayi ta shige, ta maida mukulli ta kulle.
    Yayin da Al-ameen ke cigaba da kiranta.
    Ya tashi ya tsaya kofar bayin yana fadin, ki fito ki
    saurare ni sakeena, ya kamata mu fuskanci juna,
    mu gane inda matsalar mu take. A zatona har
    duniya ta nade ba zaki taba juya min baya ba!
    Tana daga ciki ta amsa, bazan fito ba. Daman
    kasan inda dare yayi maka, yace ki tuna alkawari
    sakeena, don Allah karki bari ayi min dariya. Idan
    na rasaki zan iya rasa komai nawa, ki tausaya
    min sakeena, kar damuwa ta kasheni. Tace, kan
    ka akeji! Ni na gama magana da kai. Ko za'a
    kashe ni ba xan sauya ba, dama ka kama
    gabanka zai fiye maka alkhairi. Ya tsaya jim,
    shiru goshin sa jingine da kofar ya rasa inda zai
    tsoma ransa yaji dadi. A hankali ya soma
    karannto Innalillahi Wa inna ilaihir Rajiu'un. Ya fi
    10mins tsaye. Sannan ya juyo da sauri ya fito
    yana share fuska da hankaci. Kawai arba yayi da
    su Abba zaune falon. Ya rage sauri ya nufi gunsu
    ya tsugunna, abba zan koma. Gab dayan su ido
    suka xuba masa, jim Abba yace, amma dai ba
    minna zaka nufa ba yanxu ko? Ya dan kada yace,
    kuma ka kwantar da hankalinka Insha Allahu
    Mama matar kace. Kar ma ka bata tym din
    wajen xuwa goben, kai tsaye ka wuce gida, ka
    gayawa Marafa ina tafe da kaina, muyi magana.
    Yace to, Abba na barku lfya. Ya mike ya fice
    suka raka shi da kallo. Ummma kam bata sami
    cewa komai ba, saboda tsabar tausayinsa. Yana
    fitowa Gambo direba ya balle murfin mota ya fito,
    ya tarbe shi ganin ogansa na ta share fuska,
    yaya jikin nata? Ya dube shi ido jajur yace ba
    sauki Gambo. Mu shiga mota, ka maidani gida.
    Yace yallabai ai dare yayi sosai, nayi zaton gidan
    gwaggo xamu kwana. Ya miko hannu yace bani
    keys, kai ka wuce gidan Gwaggon ka kwana! Ya
    dan sunkuyar da kai, yace yi hkr yallabai Allah ya
    sauke mu lfya. Shi tuni ya bude gidan gaba ya
    fada. Gambo ya xauna mazauninsa da sunan
    Allah ya murza mukulli yaja suka wuce, a tym din
    agogon motar yana nuna 09:45pm. A daren nan
    nake son ganin Dady na. Gambo yace Allah ya
    yarda mana, ita kuma Allah ya bata lfya. Ya
    kama kai ya runtse ido, ya jingina sosai da kujera
    yana fadin amin Gambo. Direba na ta tsula gudu
    cikin dare. Shi kuwa Al-ameen kurwarsa na can
    cikin tunanin baya. Itin tsantsan son da Mama ke
    masa, shi yake gani cikin idanuwansa, har xuwa
    ranar da ya xo sallama da ita a sch, kawai
    gambo ji yayi Al-ameen na sambatu, sosai kikace
    kina sona sakeena, dama yaudara ce? Me yasa
    sakeena? Me yasa? Hnkalin Gambo ya koma
    gunsa yayi kiransa sau uku, kafin yaji kiran. Ya
    xuba masa ido yayi da direba ke fadin, kayi hkr
    yallabai, yace sakeena ta yaudareni Gambo, ta
    xuba min dafin da xai wuya na sami maganinsa.
    Xan iya mutuwa Gambo, domin gaba daya na
    sallama kaina gareta. Ko kasan inda nake da
    mishkila ka gaya min in gyara? Gaba daya
    tausayin sa ya lullube gambo, ya kada kai da
    sauri, yace babu inda kake da mishkila Yallabai,
    sai dai ko ajizanci na dan adam. Ni kaina ban
    yarda sakeena bata sonka ba, watakila ciwo ne
    rudata yace, kai ma ka yarda bata da lfya ko?
    Amma kowa yace kalau take, ni nasan sakeena
    bazata ki ni haka kawai ba, zuciya na wasi-wasi.
    Gambo yace , kar ka damu Yallabai, Allah zai
    warware komai, sakeena zata zama matarka. Ya
    sauke numfashi mai karfi yace, wannan shine
    babban burina a duniya, komai Allah ya bani na
    gode masa, saura wannan burin ya rage min.
    Shima zaka sameshi Insha Allahu. Yayi dan shiru,
    sannan ya kada kai yace, laifi nane, rashin
    kasancewa ta kusa da sakeena, shi ya jawo
    shaidani ya shiga tsakanin mu. Lallai mata na da
    rauni Gambo, ba taba tunanin sakeena zata iya
    hango wani har ya rikita ta amince dukkan
    amanar da muka damka ma juna. Al'amarin na
    daure min kai, na rasa yadda xan fassara shi.
    Yace, haka ne yallabai, amma idan ka barwa
    Allah komi na tabbata xai maka zabin alkhairi. Ka
    sani ko wata jarabawa ce Ubangiji yake yi ma
    don ya gwada imanin ka. Kar ka damu Yallabai,
    Allah ba zai hana ka sakeena ba, idan har kayi
    imani shine mai hanawa da badawa. Ya sake
    jingina da kujera, ya runtse ido ka fadi gaskiyya
    Gambo, na gode. Bai sake tankaea ba haka kuma
    bai daina tunanin xuci ba, ma'ana sakeena bata
    daina xuwa cikin idanuwan sa dauke da lallausan
    murmushinta mai sanyaya masa rai, tana tura
    hularasa gaban goshi bakinta na fadin, so much!
    Shi ya sa baya aikin komai face ajiya xuciya.
    Gambo na jinsa tausayinsa nakara zama cikin
    ransa. Karfe daya dai-dai na dare motarsu na
    tsayuwa kofar gate din gidansu. Gambo yayi hon,
    nan da nan Mai gadi ya shaida hon din motar
    mami ne, ya taso a guje ya bude kofar, motar ta
    shige kai tsaye kofar shiga ya tsaya. Al-ameen
    ya fito, sannan ya wuce ma'ajiya motaci. Tun
    kafin ya kwankwasa, yaji ana kokarin budewa,
    don haka ya dakata hannayensa biyu cikin aljihu.
    Marafa ne da kansa ya bude kofar, suka zuba
    juna ido, daga bisani ne mami ta bayyana wajen
    har ta riga marafa magana, Al-ameen .
    Idanuwansa suka yi tam da kwalla, ta yi azama
    ta jawo shi ciki, daddynsa ya maida kofar ya
    rufe. Don me ka iyo daren nan Al-ameen? Sai
    kace babu inda zaka raba ka kwana! Ya zauna
    dabas! Ya kama hannaye biyu, Marafa ya xauna
    kusa shi.
    Ya rungumo kafadunsa, yace baka kyauta
    min ba Al-ameen, da ka dauko hanya cikin daren
    nan dan kuskure kadan za'asamu, shikenan ka
    ajwo mana tashin hankali, karfa ka manta, kai ke
    nan guda daya muke kallo zukatan mu na
    wankewa daga radadin rashin da. Ya dube shi ido
    jajur! Yayin da Mami itama ta xauna daya gefen
    suka sanya shi tsakiya. Yace, na kosa in ganka
    Dady, sakon Abba xan gaya maka, yace gobe
    yana nan tafe maganar aure na sakeena, kafin in
    koma yake so a daura shi. Mami tace, kun
    daidaita da sakeenar ne? Ya dan kada kai yace,
    sakeena ba warke ba Mami, hasalima bata gane
    ni ba, shiyasa tun farko nace a kaita asibiti, kowa
    yaki amincea da ni, ga shi nan kwakwalwarta ta
    tabu. Sakeena ta kasa ganeni Mami, ni kuma
    bazan fasa auran ta ba, domin shine babban buri
    na a duniya. Su abba sun goya min baya, kuma
    ku taimaka min buri na ya cika don girman Allah.
    Gaba daya ya kara daga musu hankali babu
    kamar Marafa da ko alama baya kaunar yaga
    dansa na kukan neman wani abu, shi yasa nan
    take ya ji ko ana ba maza ha mata, sai Al-ameen
    ya auri mama. Amma ita Mami bata an ta dosa
    ba, don haka tace. Al-ameen bania ron hankalin
    kanan, na ga alama baka yarda Sakeena lfy lau
    take ba.... Ku kuka gaya min ai Mami... Yanxun
    kuma ni na gaya maka lfya, kawai cin amanar ka
    tayi, tunda kaje bata saurare ka ba, kai ma ka
    manta da ita kawai, ka roki Allah ya musanya
    maka da mafi alkahiri. Bafa sakeena kadai ce ta
    yalwatu da dukkan abubuwan da kake so ba.
    Saboda haka ka kama kanka, ka nutsu ka gane
    cewa ko an daura auran, ba zaku zauna lfya ba,
    tunda idon ta ya bude, tana takamar tana da
    kyau, kowa na kallonta, kajini? Ya girgiza kai,
    idonsa xuru yana kallonta, tace au baka ji ni ba?
    Menene nufinka? Marafa ya amshe don Allah,
    don Annabi ki kyale shi, ba yace Uban dawaki na
    taf ba? Allah ya kaimu goben lfya, shi aure ai
    nufi ne na Allah. Yanun kaje ka kwanta mu
    saurari goben, kaji? Yace naji dady, don Allah ku
    tayni da addu'a sakeena kadai nake so. Yace na
    sani, addua kuwa kullum munayi, kayi alwala ka
    sami koda raka'a 2 ne kafin ka kwanta, na
    tabbata zaka sami nutsuwa ok? Ya amsa da kai
    ya dan bubbuga kafadarsa yace, yau dan Dady,
    Allah ya bamu alkhairi. Bai dai tanka ba, ya mike
    ya bar falon. Mami ta cire tagumi tace, sai Allah
    yayi wa yaron nan sakayya! Yadda tai masa haka
    Allah zai mata. In banda idon Al-ameen ya rufe a
    kanta, me zaici da ita? Yarinyar da gwaggo tace
    shagon saurayi take su raba dare suna.... Marafa
    ya katse ta, don son Annabi, ki bar wannan
    magana haba. Ki yi masa fatan alkkhairi kawai.
    Cikin bacin rai ta mike ta koma daki. BAKIN CIKI
    kamar ya kasheta. Shi kuwa Al-ameen yana can
    yana nafilfili kamar yadda dadinsa ya umarce shi.
    Da safe ya fito gaba daya ya zabge, kallo daya
    za kai masa ka tabbatar da hakan. Gaban mami
    ya fadi ta kwala wa Ladi kira ta zo a gigice.
    Tace, to hajiya. Ta juya da sauri ta fice. Mami ta
    dube shi tace, matso nan kusa da ni. Ya kara
    matsowa yace, ina kwana? Ta amsa tana shafar
    kansa. Ina dadina, bai tashi bane? Tace, kwana
    yayi baiyi barci ba, sai bayan sallahr asuba
    barcin ya sace shi. Tana rufe baki ladi na
    sallama da tiran abinci ta dire gabansu. Tace ga
    shi hajiya dr, Iya tace in gaida ka, yanxun xata
    shigo. Yace ina amsawa. Ta fita ta bar dakin.
    Mami ta jawo tiren ta hada masu shayi ta mika
    masa, ungo nan dan iya. Daute ka sha kaji karfin
    jikinka. Ya sanya kofi a baki ya kurba kadan. Wlh
    daci mami ba xan iya sha ba. Tace don me? Ka
    cigaba da sha za kaji bakin ya washe. Ga kuma
    farfesun, bude bakin in xuba maka. Ya bude 'yar
    kular ta debo a cokali ta mika masa, karbi ka
    gani mana. Ya bude bakin ta xuba masa tace,
    yauwa ko kai fah? Yanxun idan Abba ya zo
    maganar auranta kankama, haka za'a ga ango a
    rame? Dadi ya lullubeshi yayi wani lallausan
    murmushi yace, mami na rame ko? Kai baka ji
    ajikin ka ba? Bana so kayi angwanci a rame, don
    haka ma za ka kama abinci ka ci. Nan da nan ta
    ga ya gyara zama ya hau shan farfesu yana
    kurban shayi, kinsan wani abu Mami? Sai ka fadi,
    shayin nan ya daian min daci. To yi sauri ka
    shannye. Ya kuraba ya sake kallonta, yanxu
    Mami idan aka daura auran anan xan barta? Eh
    mana, ko ba xan iya kula da ita bane? Yayi dan
    murmushi, a'a mami na, amma ni na fison mu tafi
    tare can, kin ga kafin mu dawo ta mance da
    sakaran Yaron da ya hure mata kunne. Ko ma
    muyi xaman mu can tana karatunta ina aiki na,
    ko kuwa? Ta dafa kafadarsa, gaskiyya ne, ina
    goyan bayanka, sai dai in ta haihu ka kawo min
    maigida ko kishiya. Ya kyalkyale da dariya, kwalla
    suka cika idanuwan mami ta bisi da kallo tana
    gyada kai. Yayi gyatsa kafin yace, ina son twins
    mami, ko? Sai dai an mai son su baya samun
    su?
    Da sauki ya katse ta, no duk canfi ne Mami, ni
    dai ina so kuma Allah xai bani ameer da ameera.
    Tayi 'yar dariya tace, duk naji, idan ma 'yan hudu
    ne Allah ya kawo masu albarka, yanxun tunda ka
    koshi, kaje ka yi wanka kafin dadin ka ya tashi.
    Xai ji dadi idan ya ga ango shar! Yace haka ne
    mamina. Ina xuwa, ya tashi da sauri ya fice.
    Mami ta ta tallafe kunci ta ce nikam tawa....
    Nikam tawa ta sameni, ni Ya su, Allah ka
    duba mana. A bakin kofa suka hadu da iya suka
    gaisa. Sannan ya wuce bangarens, ya fada bayi
    ya sheko wanka, ya kimtsa jikinsa da wani
    lafiyayyen farin boyel mai taushin gaske. Ya fesa
    turare, ya dawo dakin Mami, ita ma wanka yi ta
    sauya kaya. Ta dube shi tana fara'a tace, haba
    yanxu na ga daidai. Ina ganin ma dai daga yau
    aka angwancin nan. Ya xauna kusa da ita yana
    dariya. Tsokanata kike sonyi Mami, me kika gani
    yanxun? Sai ma ranar kenan. Ki gane Mamina,
    ranar ba zaki shaida ni ba. Ta ware ido tana 'yar
    dariya zai hana? Sai dai ko amarya ta kasa
    shaida kai, amma ina mami zata mance da dan
    tilon dan ta. Dadi ya kara lullube shi, ya rungumo
    ta yana fadin Allah sarki mamina, Allah ya bar
    min ke tare da Dady na. Dadin ne kansa ya
    amsa, amin amin. Ya kara sa shigowa suna
    masuayar fara'a. Dadyna ya tashi lfya? Na tashi
    lfy Doktna. Suka gaishe shi cikin annushuwa, duk
    da bai san sirrin ba, xuciyarsa tayi masa dadi.
    Don haka ya xauna aka kawo masa abincinsa su
    ka fara ci tare suna kara kwantar masa da
    hankalin. Sosai kuwa hankalinsa ya kwanta, yana
    ganin tamkar an daura auransa da mama, tunda
    yana da magoya baya ta kowanne bangare
    [12/01 18:24] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***9
    Abba bai ga ta zama ba, 7:30 suka
    kama hanyar minna shida Alh. Adamu tare da
    Umma, domin ita tana bukatar ganin likita.
    Saboda ha ane aka tafi da Inna saude don ta
    rinka taimaka mata. Basu iske abdulkareem a
    gida ba, ya riga ya fita aiki. Hankalin Aunty Rabi
    ya dugunxuma nan da nan ta dauki waya ta kita
    wayar ofis dince, Yaya abdul yaji kamar zai mutu,
    saboda tsabar bacin rai, amma ba yadda zaiyi ya
    fito saboda tsarin aiki irin na banki. Daga nana
    aunty amina ta kira, itama ta shaida mata, kafin
    ayi haka labari ya gauraye ko'ina. Asibiti suka
    fara aje Umma tare da inna saude. Aunty Rabi
    itace jagora domin asibitin da banki ke da reg da
    su ne. Daga can da Abba da alh. Adamu suka
    dumfari gidan marafa. Da ganin su, gaban Mami
    ya fadi, fara'ar karfin hali kawai takeyi. Bayan su
    natsu a falo. Abba ya tambayi marafa? Tace, ai
    kuwa yayi sammako ya tafi Lafai, don shaidawa
    mutannan gida maganar daurin auren, shi kuwa
    ango na san ya ma kai zariya yanxun Insha
    Allahu. Kasan a can yawancin abokansa suke
    saboda can yayi krt. Ina fatan lfya? Ya sauke
    numfashi idanuwan sa suka kara juyewa yace,
    babu lfya Hjya, Ki Innalillahi Wa inna ilaihir
    raji'un! Alh. Adamu ya gaya mata. Ya gayara
    xama, yace hajiya wannnan al'amari babu dadin
    ji, a takaice dai sakeena ta gudu tun jiya har
    yanxu ba mu san inda take ba. Tsaye ta mike
    dafe da kirji, ta yi me? Ta kame a hakan bata iya
    kara komai ba. Abba yace, nayi iya yina Hajiya,
    amma mama ta nuna min ta karfina, hanyar da
    zabarwa kanta ta wuce da sani nan. Kuyi hkr
    hajiya, ni ban ma san da kalmar da xan gaya
    maku ba. Ta koma a hankali ta zauna cikin
    kasala tace, ai shikenan, duk abinda Allah yayi
    daidai ne, mu mun hkr, Allah ya musanya wa Al-
    ameen da mafi alkhairi, sukayi ji. Shiru kafin
    Abba yace mu na nan garin nasan har Alhji ya
    dawo. Itama hajiya tana nan na kawo ta asibiti
    tun jiya ciwon ta ya tashi abin sai yadda Allah
    yayi. Ta maida tagumi tace, dole Umma tayi
    ciwo, ubangiji Allah ya bata sauki ya kuma shirya
    mana zuri'a, suka amsa amin. Suka mike sukayi
    mata sallama suka tafi. Hawaye suka kubcewa
    mami, hannunta a kunci tace, ta faru ta kare
    kowa sai ya hkr! Tab, wannan yarinya ta daure
    min kai. Allah kayiwa Al-ameen sakayya! Iya da
    ladi suka jiyo hajiya na sambatu, suka fito suka
    taushi xuciyarta, babu bata tym ta sa driver ya
    kaita Lafai. Gado aka ba Umma, saboda yanayin
    jikin nata, yana bukatar kulawar likita sosai domin
    jininta ya hau, har ya haye yadda ko alama ba 'a
    so. Anan su abba suka ci gaba da zama har
    karfe 4. Yaya abdulkrm ya samu ya baro ofis. Kai
    tsayr asibitin ya nufa a sukwane. Da ka dube shi,
    kasan ransa a nbace yake, yana ganin Umma
    kuma al'amarin ya kara gigita shi. Ya dubi Abba
    ido jajur! Yace, yanxun wane mataki aka dauka?
    Abba yace, ni na sallama mama, tunda ta iya
    toazarta ni haka. Na kuma je gidan su Al-ameen,
    matslar kawai ban same su bam duk sun tafi
    raba goron gayyata, sai hajiya na samu shaida
    mata. Alh. Adamu yace amma ni ina ganin zai fi
    kyau abada cigiyar a gidajen Radio da Tv. Abba
    ya amshe, da kudin wa? Saceta akayi? Ba xan
    kara asara ba, yadda ta sa kafa ta bar gidana, ta
    tozarta ni, ta wulaknata ni, ta nuna min ban isa
    da ita ba. Wlh ni ma na hkr da ita. Ba xan yi
    mata baki ba, dan ko bance wani abu, tabbas ita
    da kanta ta kai kanta mkrntar koyo hankali. Za
    ku ce na gaya maku. Taje duniya cem ta ishi
    kowa riga da wando har da mayafin yafawa. Ya
    abdulkrm ya numfasa, yace ta yiwa knata, Allah
    ya shiryar da ita, yasa ta gane, suka amsa da
    amin. Jimawa kadan ya ba Aunty Rabi mukullin
    mota ta wuce dauko su Ameera daga sch. Kai
    tsaye ta wuce da su gida. Ta kama hidimar
    shirya abinci. Tana gamawa ta kwashe gaba
    daya da yaran suka koma asibiti. Ta iske kofar
    dkin da Umma take dankam! Da Jam'a, ashe
    bayan tafiyarta kadan su ya Abdul kadir da
    abdulrhmn suka iso. Can kuma sai ga dady da
    mami. Al-ameen ne kadai bai dawo ba. Duk
    tabisu ta gaida su. Dady kam yama rasa yadda
    xai fassara al'amarin Allah ya sa bai riga ya
    yayyada xancen ba ko 'ina, iyakar sa cikin
    babban gidansu. Allah ya kawo Mami tayi masa
    birki. Shi kansa yadda yakeji a tym din, idan xa'a
    gwada jininsa dole ace ya hau, amma daya iso
    ya dubi halin da iyayen Mama ke ciki sai yaga
    ashe shi nafila ne, tashin hankali na inda yake.
    Shi yasa ya nutsu sukayi magana ta fahimta da
    abba......
    Ya Dubi halin da Iyayen Mama ke ciki
    sai ya ga ashe shi nafila ne, tashin hankali na
    inda yake. Shi yasa ya nutsu sukayi magana ta
    fahimta da Abba. Suka dauki komai suka barwa
    Allah tare da rokon Abba daya amince ya bawa
    mama wanda ta sake xaba. Abba bai ce komai
    ba anan. Don baya jin zai iya ba Danliti 'yarsa su
    hada zuri'a da mutuncin sa da komai a gari.
    Yanxun tunaninsu dan gogan. Yaya al'amarain
    zai
    kasance? Bayan abba ya kauda masa duk wani
    shakku, ya bashi tabbacin babu wani face shi, shi
    ya kara karfafa masa gwiuwa har ya sami kafar
    tafiya gayyato abokan taya shi murnar angwanci?
    Wannan amsa sai wanda ya gani da idanuwansa.
    Gab! Da kiran sallah magriba duk suka bar
    asibitin, aka bar Inna saude ita kadai tare da
    Umman, wacce har yanxun barci takeyi, domin
    allurar da akayi mata mai karfi ce sosai, saboda
    ana son ta samu hutu kwarai da gaske. Su dady
    na isa gida, kamar tare suke da Al-ameen. Bai
    fhimci komai a fuskokinsu ba, don basu yarda
    yaga sauyi ba ya baje a kujera yace, wsh! Ai fah
    an fara kenanm kinji yadda naga ji Mami? Ta
    danyi murmushi tace, dan Iya kena, to abinda ya
    kamata ka hanzarta yin wanke ne, don gab ake
    da kiran magriba. Haka za'ayi Mami na, dadi ya
    aka baro mutanan Lafai? Ina fatan zaka jaddada
    musu su taso da wuri? Wannan ai dole ne, kama
    san kawunka ba shi da wasa. Yana ta far'a
    gaskiyya ne ni ma frnds dina ne ce masu kai
    tsaye su wuce Fandagori, ai gidan Uban dawaki
    ba boyayye bane, suna tambaya za'a nunna
    masu. Dadi yace, kayi daidai, yanxun tashi ka
    shiga wankan nnima shi xanyi aga wanda xai riga
    fitowa cin abinci. Ya mike xumbur! Yana dariya ni
    ne xan riga Dadi, to shikenan, mami ki na ji ko?
    Idan kuma na riga shi bulala tara, tace ni kuma
    xan cikashe dayar, su zama goma. Na yada. Bai
    jira komai ba ya kwasa da gudu, ya shige
    bangarensa. Mami ta bishi da kallo. Dadi ya sa
    hannu ya cire mata tagumi yace, ke ma tashi ki
    daina damuwa. Ta sauke numfashi, amma ba
    tace komai ba, ta yunkura ya taimaka mata ta
    tashi suka wuce. Kowa ya shige dakinsa. Al-
    ameen ya fara fitowa falon, ya nufi gefen tebur
    inda ya hangi ladi na jera abinci. Ya isa wajen
    yana fadin, angaida Maman abinci. Tayi dan
    murmushi. Tace ni ma na gaida dr. Yace na kusa
    dina cin abincinki Ladi, ina ganin daga yau nai
    masa bye bye. Tayi 'yar dariya, to aci gaba ne
    dr.
    Amma ina ganin akwai gobe kafin amaryar ta iso
    ko? Ya gyada kai, yana dan murmushi, wa ya
    gaya miki xan dawo ni kadai? Tana 'yar dariya ta
    amsa, au can xaka zauna? Kafata, kafarta, zata
    sake magana, ya dakatar da ita, shisshhh... Tayi
    tsit! Tana kallon sa yana boyewa bayan kujeru.
    Dadi ya fito mami na biye dashi, madalla, kinga
    bulala ta hau kan danki, kira shi na tsatstsala
    masa. Tace, yanxunn nan ma xaka ganshi a
    sukwane, kwai ganin sa sukayi yana gyara xaman
    kujera xai xauna. Gaba daya suka kwashe da
    dariya. Ladi na tasya su sannan ta bar wajen.
    Dady yace, gaskiyya ba haka ake yi ba, ai dai sai
    ya bari mu fito tare ko mami? Dariyar Al-ameen
    ta karu, yayin da Mami ke fadun, kaji wayau! Ta
    xuba wa kowa abinci yaci, suka kashi suna ta
    biye masa, suna labarin biki. Bukatarsu ya cika
    cikinsa, kuma ya ci sosai. Bayan su kammala
    Dady ne ya fara barin tebur din Al-ameen ya byi
    shi xasu yi wata magana, nan da nan ya mike ya
    bi bayansa. Mami ta kwala wa Ladi kira tace ta
    gyara kan tebur din, ita ma kai tsaye ta wuce, ta
    iske su xaune bisa kafet. Dayan gefen ta xauna,
    suka sanya shi tsakiya. Dadi yayi gyarn murya
    yace, wasu 'yan tamnbayoyi xan yi maka Al-
    ameen, ina fatan xaka nutsu ka bani amsa
    shakikiya. Da farko dai shin Al-ameen wa yake
    badawa, wa yake hanawa? Yace, Allah. To idan
    ya baka, sannan ya dawo ya karba, me yakamata
    kayi? Ya amsa, nayi masa gdya, watakila ya
    musanya min da alkhairi, ko Mami? Tace,
    Gaskiyya ne! Dadi yace, Madalla, abinda nake ka
    sanya wa ranka kenan. Idan har ka tabbata
    tsakanin ka da Allah ka amsa min tambayoyi na.
    Ka kuma san imani shine cikar dan musulmi, ko
    ba haka ba? A salube yace, sosai dady. Yauwa,
    to kayi hkr maganar da xan gaya maka. Nasan ka
    na son sakeena, sannan kayi imani Allah ne ya
    hadu ku ya sanya maka sonta, a da mu na ganin
    kamar itama tana sonka, kamar yarda kake
    sonta. Amma yanxun ta nuna yaudara ce kawai,
    saboda haka ka hkr da ita. Kamar yadda kace
    Allah xai musanya maka alkhairi. Ya dubi Mami,
    ya juya ya dube shi, Dady ban fahimce ka ba, ai
    sakeena na so na, xuga ce kawai kuma na
    tabbata da xarar aka daura auranmu, ni masan
    yadda xan da hankalinta gareni. Dady ya ka kada
    kai, maganar ka dawo da hankalinta gareka duk
    ya kau. Al-ameen sakeena ta gudu tun jiya babu
    wanda yasan inda take saboda haka nake
    rokonka arziki da ka kwantar da hankalinka, kayi
    imani da furucin da kayi daxu, Allah ba xai bari
    kasha wuya ba.
    Ya Dubi Mami fuska kunshe da tashin
    hakali yace mami ban fahimci ta gudu ba? Me
    dady yake nufi? Tace iyakar kiyayya sakeena ta
    nuna maka, tunda ta xabi ta dauki akwatinta ta
    bar gidan iyayen ta ada ace ta aure ka. Ta xabi
    ta ci mutuncin mahaifanta akan auranka.
    Wulakanci ya kai makura Al-ameen, ya kamata
    ka nuna mana ka haihu dan halas, kace kai ma
    ka hkr da sakeena. Ya xura mata ido, du sun
    kadu, mami kina nufin an fasa daura auran gobe?
    Tace abinda Abbanta yayi sammakon xuwa
    shaida mana kenan, ia ske ba ku nan kun riga
    kun tafi gayyata, ni na bi dadynka Lafai na
    dakatar da shi. Kai ma ina so ka dauki waya ka
    kira abokin ka dr. Lawal ka gaya masa an fasa,
    don ya gaya wa saura kar su yi wahala. Ya kada
    kai yace, baxan iya ba mami, na rantse da Allah
    sakeena na so na, ina xata gudu taje? Ban yarda
    ba mami sace min ita kayi, don a raba mu....
    Rufe min baki! Mami ta daka masa tasawa mai
    karfi, daga nan ta balle da masifa, kar ka yarda
    Al-ameen, amma ina son ka sani, babu maganar
    auranka gobe da sakeena! Idan kuma ka sake tak
    a wurin nan sai na tsinka mata mari, don ka gane
    ba wasa muke yi da kai ba! Yaya ana rarrashinka
    ana numaka gaskiyyar magana ka naso ka akrya
    ta mu? Sakeenar banxa sakeenan wofi? Ita
    kadaice mace a duniya? In sake jin xancen ta
    abakin ka sai na saba maka! Ku ma ka sani,
    daga daren yau ka fara shiri gobe xuwa jibi xaka
    koma sch! Kaji ko baka ji ni ba? Ya aje kai kasa.
    Dadi yasa hannu ya dago fuskarsa. Tuni hawaye
    suka wanke masa kunci, shi ya fara fadin, me
    yasa zata gudu ta barni Dady? Ko baxan hkr da
    ita ba, ai bai kamata ta gudu ba, hatsari ne
    babba ga diya mace, wa ya san hannu da take
    yanxun? Mami tayi caraf? Ta cafke, tana hannun
    wanda take so. Dama ka daina bata hawayenka
    a banxa. Sannan kama kunnunwanka da kyau ka
    ji ni, tun daga ranar da ka daina jin muryar
    sakeena awaya ta daina sonka, ta mance da kai,
    ta share ka a rayuwarta. Saboda kin da ta ke
    ma. Sakeena ta diro daga mota, da abin ya zo da
    karar kwana da yanxun an kusa mata sadakar
    arba'in. Sakeena tayi kwana da kwanaki tana
    yajin cin abinci, tayi ta suma ana mata karin
    ruwa a asibiti. Kai saboda kiyayyar ka, gabada
    dabi'iun sakeena suka sauya, bata gannin kowa
    da daraja, nballe ta saurari fada, da iayeynta da
    'yanuwanta ke mata ba dare ba rana. A karshe
    sakeena ta aikata abinda yafi komi muni akan
    diya mace. Duk saboda bata sonka, ashe ya
    kamata ka hankalta kasan halin da kake ciki, don
    kai ba yaro bane, kuma ba alfahari ba, ilimi
    muhammadiya da boko sai dai a yiwa wani gori
    ba dai kai ba Al-ameen, duk kuma wanda yayi
    imani da kaddara, baya tabewa Al-ameen. Ka
    maida al-amarin ka wajen Allah shi xai maka
    magani. Ya dube su daidai tamkar karamin yaro,
    murya na rawa yace, gaskiyya ne Mami, duk
    abinda ki ka fadi na yarda, kuma na hkr da
    sakeena, sai dai son ta ba xan iya cire shi cikin
    raina ba, saboda ba ni na aje shi ba, kuyi hkr, ku
    yafe ni, idan furuncin danayi ya muku xafi,
    sannan ina rokon ku don Allah da son Manxonsa,
    kar ku kullaci sakeena cikin xukatan ku akan
    wannan maganar. Wlh har yanxu ina ji ajikna
    sakeenna tawace. Dady ya rungumo kafadunsa
    yace, shikenan,ya Isa, munji rokonka mun amsa.
    Zamu cigaba da taya ka addu'. Yanxun abinda
    nake sonka da shi shine, ka kira Dr. Lawal ka
    gaya masa, don su sani. Sai dai in baka lambobin
    ka kira shi dady, bakina ba xai iya furta
    mummunan labarin nan ba. Ya mike ya jao
    durowar dadi ya dauki biro da paper ya rubuta ya
    bashi, ya mike xai fice, ya kusan kaiwa kofa
    mamy ta kira shi, ya juyo tace kayi nafilfilu cikn
    dare. Allah zai saurareka, ya nisa kafin yace
    xanyi mami. Ya sa kai ya fice. Mami ta dubi
    dady ta hadiye hawayenta, tace gobe in Allah ya
    kaimu xan koma Lafai wajen baba liman in samo
    masa ruwan addu'a ya sha ya sami sanyi cikin
    ransa. Yace hakan ma yayi, Allah ya sa mu
    dace. Tace amin. Ta jawo wa dady kan waya ya
    nemi Dr. Lawal, ya sanar masa. Yace an fasa?
    Subhanallahi? Wannan abu baiyi dadi ba. Don
    girman Allah dady a samu a daidaita, wlh Al-
    ameen yana son yarinyar nan ba kadan ba. Ya ce
    ba sai ka rantse ba Lawal, ni kaina nasan hakan,
    amma fadan da ya fi karfinka dole ka maida shi
    wasa. Mu nan muna ta addu'a Allah ya zaba
    mafi alkhairi. Ya numfasa, yace amin. Ina Dr.
    Yake? Ai sai da ka neme shi xuwa gobe, yanxun
    kam babu sukuni yana dakinsa. Yayi dan jim,
    kafin yace Allah shi kyauta, amma ayi kokari Dadi
    idan xai yuwu a sasanta. Ba komai mun gode a
    gaida Iyali. Zasuji, ya aje wayar tare da tsananin
    mamakin wannan abu? Me ya faru haka da xafi?
    Haka ya kwana da tambayar kansa, don babu
    alamar wata mishkila a tattare da soyayyar
    abokinsa da sakeena, ko daya zo sanar da
    xancen auran ma babu alamat akwai matsala
    babba. Labarin barci dai babu shi a wajen Al-
    ameen kuma xuciyarsa bata daina karyata masa
    xancan ba. Ko alama ta ki amsar sakon, saboda
    tsabar shakkun da yake ciki, wai sakeena taci
    amanarsa? Har 8am yana kan sallaya, ba don wai
    yana sallah ba, a'a kasala ce ta hana masa tashi.
    Mami tayi sallama ta shigo da tiran kayan karin
    safe. Ya xubo mata ido.
    Mami tayi sallama ta shigo da tiran
    abinci, ya xubo mata ido, ta aje a agbnsa, ta
    xauna gefe, sannan yace, ina kwana mami? Lfya
    lau, ina fatan ba ka tsananta wa kan tunani ba?
    Ya kada kai, ya xanyi mami? Kin san ba yin kaina
    bane? Ta dafa shi a sanyaye, kllm ina kara gaya
    maka Al-ameen, kai kadai ne garemu, kuma ka
    zama tamkar dubu, ba gare mu kadai ba,
    gabadaya al'umma za su so rayuwarka ta daure
    cikin fciki da walwala, saboda muhimmancinta,
    ina so ka san wani abu yau. Wlh na yi maka
    rantsuwar da ba kaffara da rayuwarka ta
    salwanta, gara ni in mutu, don na..... Ya rufe
    bakinta, a hankali, idanuwansa taf, da hawaye
    yace, kiyi shiru mamina! Da ni dake zamu rayu da
    yardar Allah cikin farinciki da kwanciyar hankali.
    Har ga Allah na hkra da sakeena mami, kawai
    ciwon fitar son ta ke azabtar da ni. Ka kwantar
    da hankalinki mamina, a hankali zaki gan ni
    yadda kike so. Tayi dan murmushi tace, Allah
    yayi ma albarka! Da sauri ya kwanta a kafadarta
    yana fadin amin mamina. Zauna da kyau na hada
    maka brkfst. Kaga masa na sa iya ta shirya
    maka da sassafe, na san kana so kuma kana
    kewarta, don ba'a samu a Rasha. Ya bita da kallo
    dauke da tausayi. Yace nagode mamina, amma
    tare xamu ci ko? Ta jawo fileta tana fadi ah! Me
    zai hana? Bari ka gani. Ta loda waina a plate
    tana xuba miya ya ware ido, yace mami kin cika
    abincin nan! Ita ma ta ware idon tace injiwa? Ni
    da kaine fa? Sa hannu ka gani ko asa man
    shanu? Ya kada kai, a'a kinsa banso kayan karni.
    Ka bar dadi yaro. Yayi 'yar dariya yace Allah ko?
    Ta tura masa a baki tace, haba ai ba sai na fadi
    ba. Dady yai sallama dakin ya karaso da sauri
    yana cewa iye! Masa kuke ci kuka nuna min 'yan
    ubanci? Gaskiya ba ha akeyi ba, ai sai ku kira ni
    ko? Ya tambaya yana kallon al-ameen cikin ido.
    Ya gayara masa wwuri, yace laifin mami ne,
    xauna abinka Dadyna. Ya xauna yasa hannu ciki,
    yace ai mami akwai rowa, Allah dai ya tsaga da
    rabona. Suna dariya ta bashi amsa, ka san kuwa
    da na kawai, na aka yi ma. Kaji ko? Tafi son ka
    akaina. Yayi wuf ya rike hannu da yake kokarin
    kai loma yace, ba xaka ci ba sai ka fadi! Gaya
    min, mami ta hau dariya shima ita yake yi. Dady
    na ga dai da ta rikice kanka. Tace babu wani sai
    kai, sannan aka sameni, ko ba haka bane mami?
    Tace ni xaka tambaya? Dady ya karbe yanki
    wainar daga hannunsa ya tura masa baki, yace
    cinye dana, ka bani amsa daidai. Bai gama
    cinyewa ba ya dauko cinyar kaza ya tura msa, ka
    ra da wannan kayi brush! Duk suka sa dariya,
    ganin al-ameen na neman kwarewa, kan kace
    kwabo sun yaudari Al-ameen ya cinye wainar da
    mami ta zo da ita, domin dai shi suka yi ta
    turawa da wasa da dariya ya take cikinsa. Bayan
    sun kare, mami ta dube shi tace yanxun ka tashi
    ka shiga wanka ka kimtsa, muje asibiti ka gaida
    Umma.... Umma? Me ya sameta? Tashin hankali
    ya sa ta sami hawan jini tuntuni, maganar jiya
    kuma ta kara birkita ta jininta yayi mugun hawa.
    Tana nan asibitin sun bata gado. Jiyan abba ya
    taho da ita. Ya marairaice yace, Umma na asibiti
    tun jiya baku gaya min ba? Ban dadin hakan ba,
    dady yace kayi hrk, ganin kai ma baka da sukuni
    ya sa muka kyaleka, kaji da guda 1. Ya mike
    yace ba sai nayi wanka ba, yanxun xan tafi, idan
    na dawo nayi, bai saurara ba ya wuce ya jawo
    dirowa ya dauko key ya fice. Mami ta biyo shi
    tace Al-ameen, ya tsaya cak! yana dubanta, ta
    matsi sosai ta dafa shi, ka tafi a hankali, idan
    kaje kace ina gaishe ta, ni ma xan biyo in na
    dawo daga Lafai, ya dan lumshi ido, ya bude
    yace xan kula mami, amma me xaki je yi Lafai?
    Tace uzurina xai kaini. Allah ya kiyaye hanya, ta
    amsa amin. Ya daga kai dubi dady dake tsaye
    yace, sai na dawo dady, to ina jin ma xan
    sameka asibitin. Yace shikenan sai kazo. Ya juya
    yayi waje, su iya na kokarin fitowa su gaisa.
    Amma ina saurin da yakeyi, ya hana su su same
    shi falon, tuni ya kai ma'ajiyar motocin, ya murza
    ya bar gidan. Umma na xaune an jera mata filo,
    ruwan lipton kawai ta iya kurba, ya xuna cikinta.
    Likitan ne yace ta dan jingina kadan ta huta. Duk
    'ya'yan sun kewayeta, abba na xaune gabanta
    bisa kujera. Gaba daya tausar xuciyarta suke yi
    don ta fidda abin a aranta. Sallamar al-ameen
    cikin dakin ita ta dauki hankalin kowa, suka amsa
    kona masa duban tausayi, ganin yadda ya xabge
    kamar mai ciwo, wai don ma su mami na yin iya
    kokarinsa akansa. Ya bisu daidai sukayi
    musabaha, sannan ya tsugguna gaban Abba suka
    gaisa. Tuni ganinsa ya sa hawayen Umma suka
    tsinke, yayi shiru a tsugunne. Abba ya dafa shi,
    yace sai ka dawo ka sami labari maras dadi? To
    ina so ka kwantar da hankalinka kayi imani da
    kaddara, ka sani yau da ace mama na da 'yar
    uwa xan baka ita, don in nuna maka iya kaunar
    da muke maka. Mama ta zabi ta wulakanta mu,
    shi yasa na ke son kowa ya cireta a ransa, mu
    manta da ita mu kyaleta duniya ta hora ta. Kayi
    hkr kaji? Ya goge kwalla yace naji abba, kuma
    nagode akan iya kokarin da kukayi min, amma
    abba ina rokon ka, don girman Allah ku ya fe
    mata, sannan ku sanya mata albarka, a auran da
    xatayi. Duk sukayi shiru, kowa ya xuba masa ido.
    Tausayin sa na ratsa su, umma ta goge kwalla.
    Tace Mama ba abar tausayi bace Al-
    ameen, don haka ka daina rokon ayi mata afuwa
    laifin data aikata. Ya kata matsowa gaban gadon
    yace, ba haka bane Umma, ki san sharrin
    shaidan, sannan xuciya bata da kashi, ba 'a son
    ran mama zata aikiata wannan abin ba, xuciya ce
    ta saka mata, na tabbata duk ranar da ta nutsu
    tayi tunani xata gane lallai bata kyauta ba. Don
    Allah Umma ko ina nan ko ba nan, idan Mama ta
    dawo ku amshe ta hannu 2, ku samata albarka.
    Insha Allahu shaidanin daya rinjaye xuciyarta, xai
    kyaleta, ta dawo diya ta gari kamar yadda take
    da. Abba ya kara dafa shi, yace idonka ya riga ya
    rufe a son mama, shi ya sa baka kallon girman
    laifin da ta aikata. Ya juya ya dube shi, ba haka
    bane Abba nasan ina son mama kuma har na
    mutu ba xan daina son ta ba, amma ku yafe
    mata, don rayuwar ta, tayi kyau nan gaba, ba
    farin cikin mu bane ace mama ta lalace tabi
    duniya, tunda gaba dayan mu nan, muna son ta.
    Kun yafe mata ko Umma? Tace kayi hkr Al-
    ameen ba xan iya cewa komai ba tukunna, ya
    abdulqadeer yace, ko mu bamu goyi bayan su
    Umma suyi afuwa gareta ba, har sai ta sauya
    zabin da tayi da. Tunda tace ba kai ba, to ka
    kawo wani dan mutunci tamkar kai, amma ba
    Dan liti ba. Wanna itace shawarar da muka
    yanke. Yana rufe baki dadi ya turo kofar ya shigo
    tare da gaishe-gaishe. Ya dubi al-ameen yace, dr
    na jiranka. Da mamai ya dube shi, dr. Lawal?
    Yaushe ya zo? Bai dade ba, muna shirin fitowa,
    sai gashi shine nace ya xauna xan biyo na gaya
    maka. Ya mike yayi sallama da su ya bar
    asibitin. Bai sami mami ba, don itama driver ya
    wuce da ita lfya. Dr. Lawal na babban falon
    gidansu, ladi sun adana shi da kayan kusa da
    baka, amma da ka dube shu kasan baya cikin
    sukuni. Yana shigowa ya mike da sauri ya tarbe
    shi suka kama juna. Dr. Lafai! Yace banyi xanton
    xaka xo ba. Dole na xo, wannnan mummanan
    labari ya hanani barci jiya. Yayi dan yake, kai dai
    bari, mu xauna aboki na. Suka zauna kujera daya,
    dr lawal yace, me yayi zafi likita? Idanuwansa
    suka kada yace, bansan me ke faruwa ba dr
    sama da sati 4 ina can na daina jin wayar
    sakeena, aka ce min bata da lfya ne, dalilin da
    yasa na dawo kenan don hankalina yaki kwanciya
    ita kawai nake son gani. Ina xuwa na iske labari
    ya sha bambam, wai sakeena ta sami wani ya
    hure mata kunne, har ta mance da manyan
    alkawuran da ta daukat min. Kowa yayi iya
    kokarinsa wajen nuna mata gaskiyya, amma sam
    tace ba san wannan ba. Abban ta kuwa ya sha
    alwashin ni da ta fara kawowa akayi mana baiko,
    ya sani ba xai daura mata aure da kowa ba, face
    ni don haka yace ba xan koma sai an daura
    auran. So da kaunar da nakewa sakeena yasa
    bana tunanin komai Illa xumudin a daura mana
    auran, shi yasa koda naje jiya bana nuna maka
    komai ba.a xato na bai kamata in tona kwanne
    sirri na sakeena ba, do kar a zage ta matsayin
    maci amana, ina ganin kamar idan muka kebe
    matsayin miji da mata, xan iya rinjayar ta. Son da
    take take min ya sake dawowa xuciyarta. Ashe
    duk abin da nake zato ya wuce nan dr.lawal
    kawai na dawo jiyan su dady ke gaya min
    sakeena ta gudu cikin dare ba a san inda take
    ba. Al-ameen ya jingina da kujera ya runtse ido
    sai hawaye shar... Na malala, hankalin dr. Lawal
    ya kara tashim ya xura masa ido jim sannan ya
    sauke numfashi ya dafa shi, yace, kana cikin
    tashin hankali aboki na amma Allah yace duk
    inda tsanani yakem to tabbas da akwai sauki. Pls
    ka zama jarumi a cikin jarabawar nan, ka bari hkr
    ya xama sanadin samun saukin tashin hankalin
    nan. Ya bude ido taf da kwalla, yace inason
    sakeena Dr. Kai kasan hakan, yace kwarai da na
    sani kuma xato na itama tana tsananin sonka. Ya
    matso shi sosai yace haka ne, wlh sakeena tana
    sona, to me yasa ta kini tym 1? Yace mata
    kenan Dr. Lafai. Balle sakeenna na da kyau da
    xata iya wasa da hankalin kowane da namiji.
    Watakila kuma wancan yafi ka duk abubuwan da
    take bukta. Dan wani minister ne a abja? Yace
    ban nemi sani ba, a yau ne nake jin sunansa
    bakin yaanta wai shi Danliti, danliti? Daga jin
    sunan kasan ba wani bane. Da sauri ya amsa ai
    kuwa wani ne.... (Hahaha Allah sarki lazy Dr.)
    tunda ya sace min sakeena. Ko da kuwa kwara
    masai yake yi. Inda ace xan gan shi xan iya
    durkuwa gwiuwa 2 in roke shi, ya bar min
    sakeena ta. Wlh itace rayuwata dr. Ya kada kai
    yace, ka daina fadar haka Dr. Lafao kar fa ka
    mance wani hani ga Allah baiwa ne, xa iya
    kasancewa sakeena kyan dan miciji gareta.... Ya
    dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu....
    Yace gaya min kowace kalma dr. Amma kar ka
    aibata min sakeena, ba xan taba ganin farinka ba.
    Ya xura masa ido, kunshe da mamaki, kafin yace,
    ba nufi nake nan ba aboki na, ina so ka gane
    cewar bakomai da kake bane yake kasancewa
    alkhairi a gareka, shi ya sa kullum ake son bawa
    ya roki alkhairi wajen Allah. Yace sakeen alkhairi
    ce gareni, tuni mafarkai na suke nuna min hakan,
    har xuwa yanxun kuma jiki na yana bani sakeena
    tawa ce, mishkila aka samu wani wurin, bana so
    musu da su Dady ne kawai, shi ya sa nake nuna
    musu na hkr da ita. Yace to idan baka hkr ba,
    yaya xakayi yi? Tunda batayi da kai? Babu
    abinda
    [12/01 18:24] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***10
    Amma nan da iya shkrun da xanyia
    duniya ba xan daina son ta ba har na koma
    Ubangiji. Ya xura masa ido, yace Al-ameen kar
    ka manta akwai gagaruminn aiki gabanka wanda
    kowa ya xura ido don ganin rawar da xaka taka,
    kasancewar kai kadai ake tunanin xaka iya taka
    ta kuma mutanenan arewa suna jiran daya
    tamakar dubu ya dawo masu da abin alafahrin a
    duniya baki daya. Ina ka sami nutsiwa ka
    fuskanci abinda ke gabanka ka tare da jadda
    imani a cikin ranka, lallai Allah xai iya baka wata.
    Ina fatan xuwa na ba xai xama abnxa ba ba,
    kuma addu'ar duk masoyanka a zariya ba zata
    fadi kasa banxa ba. Kowa yace Allah ya
    musanya maka da lakhairi, na tabbata Allah xai
    duba ya kawo sauyi na fadi daidai? Ya numfasa
    yace ka fadi daidai abokina na, na gode ma kowa
    bisa addu'ar da suka yi min. Xan koma rasha da
    yardar Allah cikin yardarsa xan dage na fidda
    kowa kunya. Sai dai abinda nake so ka sani har
    in mutu ina son sakeena. Yace tuni na sani,
    sannan ina da ilimin xuciya daya gareka, duk
    abinda Allah ya xuba cikin ta, babu me iya dauke
    shi. Ya koma ya jingina da kujrea, rungume da
    hannayensa, ya dan numfasa ya kada kai, dr.
    Lawal ya bubbuga kafadarsa ya sake fadin, ka
    manta kawai abokina, ya wuce, ya bishi da kallo
    kawai baice komai ba su dade tare. Dr. Lawal na
    kara kwantar masa da hanakili tare da nuna
    masa mahimmancinsa ga al-aumma. Bayan
    azahar suke asibiti ya gaida Umma, daga can ya
    wuce zariya, shi kuwa Al-ameen gida ya dawo,
    don shima ba ya son yana ganin Umma kwance
    tausayinta yana kara karya masa xuciya. Ya rinka
    jin kamar su abba ba xa su yafe wa sakeena ba.
    Wannan shine babban tashin hankalin sa. La'asar
    ta kawo jiki yana xaune shi kadai bisa gadonsa,
    tym-tym ya kan dauki hoton da ke bisa kirjinsa
    ya duba. Hotonsu ne shi da mama wanda sukayi
    a dakin Mami, xuwan ta farko gidan. Karo
    barkatai kenan daya daga hoton ya xura masa
    ido tsawon lokaci, sannan ya mike ya sake kife
    shi. Ya laluba aljihunsa ya dauko xoben da Mama
    da dawo masa dashi, ya xare na hannunsa ya
    hada su waje daya, ya xura masa ido. Sannan
    ahankali yake wasa da su, ya rike kowanne yana
    hada su karo. Cikin idanuwansa yake ganin ita ke
    rike da wanda ya bata, suke karawa juna.
    Wannan karon da karfinsa ya kara mata, na
    hannunta ya karye nan da nan ta shagwabe,
    gaskiya ba hake ake yi ba! Ba haka ake ba Dr.
    Al-
    ameen! Al-ameen tsananin kiran ya dawo da shi
    tunaninsa duniya. A firgice ya dubi Mami dake
    gabansa xaune. Ba xai iya cewa ga tym da ta
    shigo ba, don haka yake mata kallon mamaki,
    haka itama ta xura masa ido mai dauke da
    questions. Mami! Yaushe kika dawo? Ta sauke
    numfashi ta kada kai, kafin tace, tsoron na Allah
    tsorona kar ka xaunce al-ameen ka dawo cikin
    hankalinka mana! Yai sauri ya runtse ido yana
    fadin Hasbunnallu wa ni Imal wakil, Allahuma
    ajirni fi musibati wa akhlifini khairan minha. Ya
    bnude ido jajur ya dubeta, kiyi hrk mami....
    Takatshe shi ba xan bari rayuwar ka ta salwanta
    ba Al-ameen sai inda karfi na ya kare, Allah na
    gani yarinyar nan ta xalunce ni. Kafin yace wani
    abu, ta mike da sauri tai waje, ya bita yana kira,
    ba su hadu ba sai a dakinta... Mami.... Ta daga
    masa hannu. Ban son jin komai, ta mika masa
    wani ruwa da ke hannunta tace shnaye shi ka
    bani kofi. Yace na menen? Ban son tambaya ni
    na umarce ka kashanye, ka bani kofin. Ya daga
    kofin da sunan Allah, ya kafa aabki ya
    kwankwade. Ta karbi kofin ta aje gefe. Ya sake
    tambaya mami ruwan me nasha? Tace baba
    liman ya bani taimako na kawo maka, anjima
    zaka sake sha, gobe ka kara da safe da yamma.
    Jibi in Allah ya kaimu lfya za ka koma sch, domin
    fitar da dadin ka yayi bookin ya je maka, ina
    fatan kajini? Jikinsa yai sanyi, ya kamo
    hannnayenta 2 ya ja suka xauna bisa kujera yace
    Allah sarki mamina. Allah bar min ke. Nagode da
    karfafa min gwiuwar da kukeyi. Idanuwanta taf
    da hawaye tace, hankalina bai taba tashi ba irin
    na yau. Ban taba jin faduwar gaba ba irin ta
    yaukai da zobuna kake hira kana dariya, Al-
    ameen ban same xai faru ba nan gaba.
    Kafadunta 2 ya dafa yace sai alkhairi mamina,
    kawai xancen xuci ne ya fito fili mami... Tace
    daga haka sai tabin hakali al-ameen , yayi dan
    murmushi yace Allah ba xai sa ba mamina, ya
    san ni kadai ya baki, kuma shi mai tsananin
    tausayi ne. Allah sa ruwan da kika bani ba wanda
    xai cire min son sakeena bane. Ta xura masa ido
    cikin xafi tace, shine Al-ameen Insha Allahu
    sakeena ba xata zama ajalinka ba, ya numfasa
    yana murmushi da bai kai ciki ba mami kenan,
    wa ya gaya miki sakeena xata kashe miki tilon
    danki? Kuma wa ya gaya miki danki xai ji dadin
    rayuwa ba tare da soayyar sakeena ciknin
    xuciyarsa ba? Duka 2 tafiya suke kafada da
    kafada mami, Allah yayi hukuncinsa, don haka
    ban ji Baba liman xai iya cirewa. Bayin kaina
    bane, kiyi hkr mami. Tayi masa xuru duk jikinta
    ya mutu a hankali ta ce ko bai fita ba xaka ji
    sanyi cikin ranka. Tunaninn ka xai daidaitu da
    aikin kwakwalwar ka ta yadda xaka yi mu'amula
    kamar sauran mutane. Wannan shine farinciknm.
    Yace, Allah ya taimake ku akan burin ku. Nima
    ya taimakeni akan nawa.....
    Tace xamu ci gaba dayi da fada idan
    har kana gaya min irin wadannan kalaman. Ya
    kada kai ba xa muyi ba mami. To ka daina. Ya
    lumshe ido, ya bude yace na daina, Allah yayi
    maka albarka. Ya dora kansa kafadarta ya amsa
    da amin. Ta ciga da yi ma nasiha yana
    sauraronta sai dai can kasar xuciyarsa cike yake
    da xulumi, Allah ya sa ruwan da mami ta ba shi
    ya sha ba wanda xai sa ya mance da sakeena
    bane. Da wannan xulumin ya tafi yin sallah
    la'asar hankalinsa bai kwanta ba, sai da ya tura
    yatsansa ya arce makogwaronsa ya kirkiro wa
    kansa aman dole. Bayan sallar magriba dady ya
    shigo ya tsare shi yaci abinci. Sannan mami ta
    debo ruwan addu'arta ta mika masa, ya shanye.
    Allah Allah yake yi tashi ya koma dakinsa ya
    jawo aman, amma kmar dady ya sano ya ki
    barinsa tashi. Yayi ta jansa da hirarrakin duniya,
    wai don ya rage tunanu. Kafin ya bar wajen ya
    kwashe awoyi sama da 2 takaice ya ishe shi, don
    ya tabbata ruwn nan ya gama bin jininsa.
    Wannan karon bai nemi yin aman ba, gado ya
    fada ya fara tunanin iska, har bacci ya samuyi,
    da alama an fara samun nasara. Shi kansa yayi
    mamakin irin barcin da yayi bugu da kari ya rage
    jin xugin xuciyarsa ke y, hankali kwance suka yi
    karin safe. Mami ta kara bulbuo ruwan addu'ar
    ta a gora, ta mika masa. Ya kwankwada duk ba a
    son ransa yake sha ba, a yau takardun
    komawarsa Rasha xasu kammalu, haka dady ya
    gaya masa. Saboda haka ya umarce shi daya
    kasance cikin shiri koda yaushe xa'a iya basu
    tym din tashi. Jikinsa babu kasala ya koma
    bangarensa ya jwo jakar kayansa yayi ta lda
    kaya har da wadanda ya dade bai anfani da su
    ba. Ya wuce dirowar madubinsa ya jawo ya
    kashe takardun cikin kaf, dinsu ya dauko xai
    xuba jaka, wata ambula ta fado duk hotuna ciki
    suka watse bisa kafet daidadi shigowar mami
    dakin. Ya aje takardun gefen gadon yana amsa
    sallamarta, sannan ya tsugunna ya kwashe
    hotunan, akasarinsa duk na mama ne, sai kalilan
    wanda suke tare. Tayi tsye tana kallon katuwar
    jakar da yake lodawa kaya, ya akayi mami na?
    Tace kamar bada jakar nan ka xo ba? Ya mike
    dauke da hotunan a hannunsa yana amsawa, xan
    kara wasu kayan ne, shi yasa na sauya jaka. Ya
    matsya xai cusa hotunan, tayi wuf ta karbe ina
    xaka da dasu? Ai wadannan hotunan wuta ya
    kamata ka cinna musu. Wuta mami? Me ya san
    xan sa wa sakeena wuta? Saboda nan gaba xata
    xama matar wani, ka ga haramun ne gareka
    kallon hotonta. Ina fatan ka gamsu? Yayi shiru
    na 'yan dakikai kafin ya numfsa, ya dubeta
    idanuwan har sun kada, yace kin fadi gaskiyya
    mami, amma baxan iya cinna wa jikin sakeena
    wuta ba, sai dai ina rokonki dan girman Allah ki
    adana min su har xuwa tym din da xata halasta
    gareni. Tayi masa xuru tana shakku cikin ranta,
    addu'ar Baba liman batayi tasiri bane ko kuwa
    bata fara aiki bane tkunna? Ta kada kai ta dubi
    hotunan ta sake dubansa, amma shi ya riga ta
    magana. Mami pls ki ajeye min su inda ba xa su
    salwanta ba. Ta sauke numfashi, xan boye maka
    sun tunda kafi son hakan, gwaggo ce ta xo tana
    daki na. Ya ware ido sosai. Gwaggo? Da
    sasssafen nan? Dole tayo sammako, hankalinta a
    tashe yake, ka fito tana daki.Tayi waje da
    ambulan din a hannunta, shima ya biyo bayanta.
    Tana xaune a shimfida bisa kafet ya xube
    gabannta dauke da murmushi, uwargida ran fida,
    kuma sai ki bugo min sammako kamar ban aika
    da cefane ba? Duban tausayi take masa, ta dafa
    kafadarsa tace dole nai sammako, in xo in ga
    halin da kake ciki. Ina fatan xaka sanya dangana
    cikin ranka. Ka mance da yarinyar nan, domin
    dai.... Ya katse ta, ya kamata mu gaisa gwaggo
    kinxo lfya? Ya tsufa? Tace tsufa na nan kuma
    lfya lau na xo. Amma me yasa ka katse min
    magana? Babu komai gani nayi bamu ko gaisa
    ba, alhalin ya dace na fara gaisheki. Haka ne to
    ina fatan duk shawarwarin da kowa ke ba, kana ji
    ka kuma dauka? Ka manta sakeena... Da sauri ya
    katse gwaggo tuni na hkr da ita, hasalima yau ko
    geb xan koma sch. Ban xan dalilin katseni ba Al-
    ameen akwai abinda baka so na fadi. Mami ta
    amshe, sosai kuwa kina so ya mance da
    sakeena, kunnunwansa ba sa son ji, shi yasa
    yake katseki. Tace oho, to wahalar banxa kakeyi,
    domin dai labari ya tabbata tare da shashashan
    saurayinta suka tafi, kaga kuwa sai abinda Allah
    yayi. Gara ka kama kanka ka san inda ke maka
    ciwo. 'yan mata dai ga su nan birjik duk wacce
    kace kule xata ce cas. Rayuwa kawai sakeena ta
    xaba, don na tabbata yaron nan baxai aureta ba,
    nawa ya lalata, ya watsar tana gani kuma ta
    bishi, inm banda ita ma, rayuwarka ta sha
    banban da wacce sakeena ta dauka, kaga kuwa
    tafiyarka ba xata xama daidai da tata ba. Ka
    fahimce ni? Wasu kwalla masu xafi suka sauka
    bisa kuncinsa, hakan ya jawo mamaki ga gwaggo
    da Mami suka xuba masa ido baki sake. Xugum
    sukayi, daga bisani mami ta numfasa tace ikon
    Allah! Gwaggo ta xare tagumi tace, akwai sauran
    aiki, kuma ina mai tabbatar maka , bata tym
    dinka kakeyi. Ya jawo hankaci ya share fuska,
    yace, ko kadan gwaggo, labarin ki tsananin
    tausayin sakeena ya cusa min, sakeena ba haka
    take ba, nayi rayuwa da ita sosai na fahimci
    halayenta, xan iya cewa nafi kowa saninta, na
    fahimci halinta.
    ,Zan iya cewa nafi kowa sanin ta hakika ya
    zalunce ta tunda ya sauyamata rayuwa ya bata
    tarbiyarta ya gurbata mu'amalarta da iyayenta da
    yan uwanta ya datse tasananin soyayyar dake
    tsakaninmu ka ALLAH bazai kyale shi ba ta ko
    wace hanya ya bi yayi nasa a kanta sai ya ga
    sakayya,"ya mike da sauri zai bar dakin gwaggo
    ta kwala masa kira ya tsaya bakin kofa yana
    goge kwalla tace dawo ka zauna ai ban gama
    magana da kai ba yana daga tsaye gaskiya
    gwaggo kunnuwa na ba za Su iya sauraron irin
    wadannan labarurrukan
    akan sakeena ba,tausayin ta bazai barni sukuni
    ba gara a bar ni cikin bakin duhu ina laluben inda
    ALLAH zai sake hada fuskokin mu har ta zama
    mata a gare ni," jikin gwaggo yayi mugun sanyi
    tace dawo zauna nan ya dawo ya zauna gefenta
    ya hade kai da guiwa ta dafa kansa tace idan
    nayi kuskure kayi min afuwa amma ba laifi na
    bane ka sani ko wace uwa tana kishin danta
    kuma abinda ya faru da kai dole mai kaunarka
    yayi bakin ciki balle mu da muka fi kowa kusa da
    kai, na san kana son sakeena sai dai ba na son
    idon ka ya rufe ka kasa ganin aika aikar da ta
    aikata a garemu, ya cire kai ya dube ta ni kuwa
    hakan na fi so gwaggo domin na yi imanin ba yin
    kanta bane sace min ita akayi hure mata kunne
    akayi da kalmomin shaidan addu'a zatayi
    maganin abin, da zaki taimake ni da ita ma zan fi
    farin ciki akan wadannan labaran da ki ke son
    bani," gwaggo " mami ta karbe za a yi maka in
    dai addu'a ce ka samu tashi kaje kaci gaba da
    shirinka bai tofa komai ba ya yunkura ya bar
    dakin,kamar daman can ya kosa ya
    barshi,"gwaggo ta dubi mami hankali tashe tace
    bai kamata ku kyale yaron nan ya koma haka
    kawai ba tare da wani taimako ba tace tun jiya
    na je lafai na samo masa wajan baba liman wai
    nan yama sha ruwan addu'ar ke nan tafdijan ki
    na kallo fa ko laifinta baya son a fadi wannan so
    yayi yawa gara ma da auran bai yuwu ba da
    muna kallo zai zama mijin ta ce,abin haushi
    nama na jan kare, mami tace me ki ka gani
    gwaggo?ALLAH dai ya zaba alkairi abin cewa ke
    nan anan gwaggo ta wuni,
    Shi kuwa Alameen a dakinsa ya wuni don
    baya son ana daga masa hankali da labaran
    sakkena kazantar da baka gani ba tsafta ce,kai a
    yadda yake jin mama cikin ransa koda ya ga
    kazantar da idanuwansa zuciyarsa ba za ta
    amince masa ba bai fito ba sai da gwaggo zata
    koma suka yi sallama daga nan dakin iya ya
    shige ya kudundune kamar maraya sama da awa
    guda tana tausar zuciyar sa da kalamai masu
    dadi,ya kuwa ji dadin cikin ransa saboda kalaman
    iya sunfi rinjaye ga. Bashi tabbacin idan sakeena
    matarsa ce duk rintsi duk wuya sai ya aure ta
    karfe shidda dai dai dady ya dawo masa da
    takardun tafiyarsa sun kammalu kuma gobe da
    yardar ALLAH sha biyu ranan zasu tashi don
    haka yana gama cin abincin dare mami ta ba shi
    ruwan addu'a ya kwankwada kai tsaye asibiti ya
    wuce don yin sallama dasu abba,kowa yayi masa
    nasiha kuma sun jaddada masa ya maida
    hankalinsa akan anibda ya kaishi kar ya tsaya
    bata lokacinsa. Akan tunanin iska wanda ba zai
    fisheshi ba,sai dai abin yana basu mamaki yadda
    lafuzzan alameen ke nuni da tsantsan son mama
    a zuciyarsa. Wanda ko alama na bayyana har
    yanzu bai yarda sakeena. Taci amanarsa ba,
    akwai mishkila wani wuri shiyasa yake ta
    rokansu dasu taya shi addu'a ALLAH yasa wata
    rana sakeena ra zama mata a gare shi,gaba daya
    ya kwabe masu guiwa har suka yi masa
    alkawarin yin yafiya a gareta idan har ta dawo ta
    nemi gafara,kowa ya dubi alameen sai ya ji tarin
    kwalla cikin iadanuwansa lokacin da yake barin
    asibitin yana gugar fuska shi kansa yaya soja a
    yau zuciyarsa ta karaya,tausayi ya kwarara cikin
    jikinsa ya nemi haddasa masa abin mamaki
    domin kwalla ya ji tam da idanuwansa suna
    zubowa da saurinsa ya bar wajan bai gama ganin
    wucewar alameen ba
    [12/01 18:24] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2*** 11
    Karfe 8am suka dauki hanyar abj tare
    da mami. Hankalinsu bai gama tashi ba, sai da
    tym ya cika aka kira passengers. Al-ameen ya
    rungume su, idanuwan sa cike da hawaye,
    bakinsa na son yin magana amma kasa, haka su
    ma Allah ya doro masu nauyin baki, kallon juna
    sukeyi. Da sauri ya juya ya wuce, yana goge
    fuska da hankici. Shi yasa suke tafe cikin mota
    kowa shiru. Mami dauke da taguminta. Tunaninta
    yay rayuwar dan nata xata kasance a kasar da
    babu wanda ya damu da wani balle ya sami wata
    kulawa ta musamman. Dadi yayi tana share
    hawaye ya dan dube ta, kada kai. Amma bai iya
    cewa komai ba don ya san mami tana mukatar
    zubda hawaye ko ta ji dadi cikin ranta, amma da
    ya ga abin yaki karewa, dole ya tanka, ina ganin
    bai dace ki ci gaba da bata ranki ba, wanda kika
    yi ai ya isa, ko sai ya jefa ki wani hali ni in rasa
    da wanda xanji? Ta goge kwalla, tace Alh. Ba
    haka bane ganin Al-ameen na da abin fadi, amma
    yakasa ya wuce da damuwar cikin ransa? Wa zai
    gaya mawa a can? Kai tsaye ya bata amsa, Allah
    zai gaya mawa, kin kuwa san ya fini, ya fiki, yafi
    duk wanda kike tunani zai ba Al-ameen wanni
    taimako, saboda haka ki bar shi da buwayin sarki,
    shine xai masa dukkan gudunmawa. Ta zare
    tagumi ta numfasa, haka ne, Allah ya taimake
    shi, to amin kuma na tabbatar zai taimakeni shin,
    tunda kika furta, addu'ar uwar yankan wuka ne,
    don haka ki kwantar da hankalinki. Ina fatan kin
    ji ni. Tace, naji alh. Allah ya shige mana gaba,
    yace amin. Daga nan Mami ta saki jikinta suka ci
    gaba da hira. Suna shigowa gari, asibiti suka
    wuce gano jikin Umma. Alhmdlh, Umma na
    samun sauki, watakila ma xuwa gobe a
    sallameta. Ba su iske yaya abdulkadeer da Abdul-
    rahman ba, duk sun koma a wannan yammacin.
    Sun dan jima asibitin, sannan suka dawo gida.
    Mami ta dukufa rokon Allah cikin sallolinta, Allah
    ya sanyaya wa Al-ameen xuciyarsa, ya cire masa
    wannan makahon so sa ya ke wa Mama. Haka ta
    kwana tunaninsa har barci tayi mafarkinsa xaune
    yana wasa da xobunan guda 2. Shiyasa da ta
    fara tayi ta da na sanin da ta raba shi da
    zobunan kafin ya tafi. Suna karin safe karfe 8:30,
    waya ta dauki kuka, mami ta baro tebur ta zo
    duka tayi sallama. Muryar dan lelenta taji ya
    amsa. Farin ciki ya lallube ta tace, Allah sarki Dr.
    An sauka lfya? Yace lfya lau Mami, ina dadina?
    Ga shi nan, ya taso ya ji kaini, ina fatan ba
    matsala? Babu mami, na ma iske time table din
    jarabawar mu ya fito, karatu kawai xa mu
    fuskanta, ni da abokan karatuna. Dadi ya tsaya
    wajen tana fadin, kai naji dadi sosai, to Allah ya
    baku sa'a baki daya. Ga dadinka. Ya ce, to
    nagode Mami. Dadi ya amsa suka gaisa. Dady
    time table ya fito a taya mu addu'a. Yace kullum
    a cikinta muke, amma xa mu kara kaimi. Ubangiji
    Allah ya taimako. Yace amin. To xan wuce cikin
    sch, sai kun sake jina. Yace, yayi kyau, all d bst!
    Cike da fara'a ya amsa. Nagode Dadina. Ya aje
    waya ya dubi mami yace hankalinki ya kwanta?
    Bakinta har kunne ta amsa. Kai bari Allah ya
    kara masa hkr. Yace amin, muje muci abinci ko?
    Suka koma tebur. Mami tace abinci hankalinta
    kwance.
    Ba Haka al'amarin yake
    wajensu Umma ba, domin yau sun koma
    Fandagori sun iske da kuara da suka bari baya.
    Hankulansu su kara tashi yadda xance ke ta
    yamadidi a agari. Zagi iri-iri babi irn wanda ba'ayi
    ba wasu suna ba iyayen Mama laifi, amma da
    dama sunfi zargin mama akan rashin hankali da
    ta aikata. Wani abinda yafi daga wa Ubandawaki
    hankali shine, wai gaba daya gundarin labarin
    daga bakin 'yan uwansa da matayensu ya fara
    fitowa. Bayan gaskiyya ga tarin karya da
    karairayin da suka yiwa labarin kawanya, don
    haka ya tara su falon sa bayan sallar isha'i.
    Wannan shine karo na 2 da na tara ku akan wasu
    maganganu na batanci da suke fitowa daga
    gareku. A zatona ku masu rufa min asiri ne ko
    bayan raina a matsayin ku na 'yan uwana da
    muka fito ciki daya. Amma bansan abinda nayi
    muku ba kuke min bita da kulli, ko kuma ince
    kuke farinciki don wannan abin ya sameni. To
    abinda nake so ku gane shine, da frko dai bamu
    mukayi kanmu ba. Allah ne yayi mu, mu kuma shi
    ya rubuta duk abinda zai faru da mu. Babu
    wanda yasan kaddarar mu2m bnalle ya share
    masa mummuna kafin tazo. Da anayi da na
    gogewa Mama, don na duk fadin duniyar babu
    wanda zai kaini BAKIN CIKI, sai kuwa mahaifyar
    ta. Idan kuwa hakane, bai kamata ace ku da
    matayenku, ku dauki wannan al'amarin ya zamar
    maku abin hira a gari ba. Kaddara na kowa, idan
    baku duba kusancin mu ba, ya kamata ku duba
    wannan. Allah yai sani ban zalunci kowa ba cikin
    ku ba, haka ban xalunci mama ba, kamar yadda
    kuke yadawa cewar mu ne muka dage sai mai
    kudi xata aura, alhalin kun san komai a game da
    alkawarin auran ta da Al-ameen. Kun fi kowa
    sanin gaskiyya, amma kuka boye ta, saboda son
    rai to na bar kowa da Allah, yayi min sakayya, Da
    yardar Allah BAKIN CIKIN Mama bazai kashe mu
    ba, haka zalika ina mata fatana shiriyar koda
    yaushe. Mai surutu da dariya kuma Allah ya
    bashi sa'ar yi. Amma kar ya mance kaddara bata
    fatan shiryar kowa! Yana sa aya, ya mike ya bar
    falon ba tare da wani yayi magana ba, ita ma
    umma tashi tayi ta bi bayansa, yayi sauran ke
    mazuran rashin gaskiya. Haj. Gaje ta buga tsaki,
    ta bar falon. Daga bisani Haj. Hajjo ta lallaba ta
    sulale, Alh. Basiru ya dubi Alh. Adamu. Yace
    mutane munafukai ne, wai daga dawowarsa, an
    sami wani kusugurmin ya feshe shi, don neman
    fada. Alh. Adam yace, wai me akace? Au ya faru
    ba za'a maida yadda akayi ba? Me za'a baoye
    bayan ta gudun kowa kuma ya sani tare da
    shegen yaron nan suka tafi! Ai ko ba 'a fada ba,
    amsar a bayyane take. Tace, bata so, ba sai a
    kyale ta ba, ta auri dan iskan da ake ganin ba shi
    da asali ba, ba ita zata zauna da shi ba? Wahalar
    tace tunda tasan halinsa. Tace sai shi. Wai kuma
    mu ake ganin laifin mu, don fin karfi! Mts.... Ya
    ja tsaki yayi waje abin sa. Alh. Basiru ya mike
    yana kada kai, shi ma ya fice. Zaman doya da
    maja yaci gaba da yaduwa cikin gidan, duk da ba
    gaba daya sukeyi ba, amma babu wata
    kyakkaywar fahimta atsakninsu. Shi uban dawaki
    yana ganin ya kamata su ba shi hkr a matsayinsa
    na babban su, sannan yana gani sun yi masa
    laifi, don sun bada labarin yadda akayi mama ta
    gudu, tunda ba su suka xuga ta ba, komai ya
    kwana gidan sauki saboda haka basu ga dalilin
    da xai sa Uban dawaki Ya dauki dalan laifi ya
    dora masu ba har ya rinka jiran kalaman tubansu.
    Su ma fah yanxun ba yara bane, girman 'ya'yan
    su ya kai, ya gane shekarun su sun cika daidai
    matsayin masu 'yanci. Zuwan Ali da Ya saed don
    duba jikin Umma da kuma jin labarin Mama ko ta
    bayyana, Al-amarin bai yi musu dadi ba, ganin
    Yadda iyayen su suka ware ubandawaki suna
    masa yankar baya. Musamman Ya ali, hankalinsa
    yayi mummunan tashi, babu bata tym ya gurfana
    gaban abba yana bashi hkr. Daga bisani Ya
    saeed ya shigo falon. Ya ali Yayi rantsuwa da
    ace mama zata dawo ta amince da auransa,
    maimakon Danliti, a shirye yake a daura masu
    aure. Ko a gaban iyayen sa haka ya maida
    zancansa. Haj. Hajjo ta rufe shi da bala'i Allah
    wadarn wannan so kuwa, tunda yake hana ka
    kishin kanka. To idan ma mafarki kake yi, ka
    wanke idon ka, ka saurareni, idan har ni na
    haifeka, ba xaka auri ragowar Danliti ba. Wannan
    kalma tayi masa ciwo, bai san tym daya tasshi
    ya tabbatar wa su Haj. Hajo cewa kashe miciji
    sukeyi basa sare kansa. Domin ko banza sun
    kwana da mamakin Ya ali da yayi tafiyarsa, daga
    magana, shima ya gudun kenan? Ko mene
    nufinsa? Muna iya cewa matsalarsu ce, ko dama
    abba ya fadi kaddara na kan kowa.......
    Inna saude ke xaune gefen gadon tana
    mata fifita. Kallo daya zakayi mata, ka gane
    cewa ta jima tana fama da ciwon tsananin
    damuwa, domin dai ta fyade ta fita kamanninta.
    Amma hakan bai hana ragargazar shagalin bikin
    da akeyi cikin gidan ba. Nasan xakuyi mamaki,
    idan na gaya musu cewar bikin yaya Ali da Ya
    Sa'ed akeyi. Iyayeyn sun hur masu wuta, tun tym
    din da suka lura da take taken shi Ya alin, sam
    hankalinsa ba shi akan abinda zai fishshe shi. Shi
    yasa suka matsa kwarai da gaske akn ya fiddo
    matar aure ko su su fidda masa, ya kuwa
    tabbatar da mahaifiya sa xata ita. Gudun kar ta
    manna masa alakakai ya sa ya fito da yarinyar
    da ta dade tana sonsa a birnin gwari. Amina
    sunanta, kuma makwabtansa ne a gidan daya ke
    xaune. Sa'ed tuni yake tare da Hassana a kd. A
    yau ne maza suka daura auran 11am. Daga can
    suka wuce kd, inda xa'a daura na sa'ed bayan
    azahar. 8pm wannan rana motocin amare ke
    shigowa layin gidan angwayensu, haka daidai
    wannan tym motar Danliti parkn a kofar shagon
    sa dauke da tasa amaryar. Cike da mamki ayuba
    ya taso, ya bude kofar yana fadin, wa nake gani
    kamar amafarki? Wai dama kuna tunanin gida?
    Dan liti ya fito yayi doguwar miki, yana dariya,
    yace ah gamu kuma mun dawo, ya juya cikin
    mota ya cigaba da fadin, ya Gimbiya anan zaki
    sauko ko na karasa dae gida? Ta kada kai, tace,
    naji tsoro ya kamani Danliti, bansan yadda xanyi
    ba? Yayi 'yar dariya. Yace tsoro kuma? To me xa
    suyi miki? Ta kada kai bari dai na sauka nan,
    canm ajima na karasa gidan. Ya kace da dariya.
    Amma ke shirmen ki yayi yawa, to fito ki shiga
    ciki. Ta ballo murfin ta fito, kai! Anya kuwa
    Mama ce? Tayi wata shegiyar kiba ta kara ja, ina
    ganin shi yasa Ayuba ya xura mata ido, tym din
    da take mika masa gaisuwa. Danliti ya bude but
    suka ciro manyan jakunkuna guda 2 da kit, sai
    manya ledoji guda 3. Ayuba ya taimaka suke
    shige da su cikin shago. Kai tsaye dakinta shige
    ta xube a katifa. Duk suka biyo bayanta. Danliti
    ya xauna kusa da ita. Yace kin gaji ko? Tace kai
    dai bari, kamar in kwanta inyi ta barci wlh. To ki
    kwanta mana, ai ba kya jin yunwa ko kinaji? Ta
    kada kai, banji, to ki kwnta ki huta ne, xuwa karfe
    goma sai in tashe ki, ki koma gida. Haka za'ayi,
    ta jawo filo ta yada kai, suna kallon juna suna
    musayar murmushi. Ya lukuce mata hanci, yace
    baby na kenan. Ta juya gefe tana 'ya dariya. Ya
    mike ya dubi ayuba yace, to muje dogari. Ya juya
    yana murmushi, ina tsarabata? Yace yauwa ka
    tuna min, ya suri jakar leda suka fice da ita. Ya
    xauna bisa kujera ayuba na kan tabarma, ya
    zazzzage kayan kedar a gabansa. Gaba daya
    kayan sawa ne. Na gayu ya siyo masa, ya dube
    shi suka hada ido, yace ga tsarabar legos nan.
    Baki sake yace babu wai, har ma ga tsaraba nan
    duka naka ne. Ya washe baki m amma na gode,
    watau shi ya sana kunyi jajur abinku, ashe kuna
    bakin teku. Yace, hutu ba karya bane ayuba, ga
    kuma lafiyayyar bebi na, nake gaya ma. Yayi
    shiru yana kallon sa, fuskarsa gaba daya
    tabayyana babu abinda bai faru ba. Ya numfas
    duk jikinsa ya mutu yace, bakaji Danliti. Me nayi
    ma tukunna? Ko kaji surutu ne a gari? Ya gyara
    zama yace ba'a tonawa Danliti, abinda nake son
    ka da shi, ku sasanta ka aureta kawai, ka ba
    masu surutu kunya, donn sunce ba auranta
    zakayi ba, tayi saki reshe ne, ta kama ganye, ya
    shafa habarasa yace, ko? To ai ba suyi karya ba,
    shagali kuma basu ga komai ba daga nan ma illa
    masha Allah ba za mu daina ba. Ya kada kai
    yace, meye nawa a ciki? Idan ka huta ko xuwa
    gobe mayi lissafi. Yace ina fatan akwai kudi
    sosai, don wanda na tafi da su naci uabansu, ya
    amsa ciniki na na ba laifi, sati biyu ma da suka
    wuce na je kno na karo kaya da cinikin yafi haka.
    Da kyau mutumina, shi yasa nke sonka wlh. Yayi
    'yar dariya yana daga kayan da aka kawo masa,
    ni kuma ina sonka da nutsuwa ba amma kakiji.
    Ya mike ya nufi daki yana cewa, kai ka fiye
    surutu, bari in baka wuri. Ya shige dakin ya bar
    ayuba da kallonsa. Ya kada kai yace aransa,
    Allah ka shiryemu. Shi kuwa Danliti komawa yayi
    ya hana mama barcin. Karfe 10 ta dan gota, dan
    liti ya umarci Mama da ta koma gidan iyayenta,
    su san ta dawo, dan su san matakin karshe da
    zau dauka. Watakila hakan su ta cimma ruwa.
    Watau su amince da auransu cewarsa madugu
    uban tafiyar. Ya hado mata kayanta taf! Da
    katuwar jaka, tana xaune tana kallonsa, kafin
    tace gaskiyya ba xan dauki jakar nan ba, guda
    uku kawai dauka cikin kit, in tafi dasu. Ido waje
    ya tambaya, sabda me? Ka sani ko su koroni? Ka
    bari tukunna mu gani, idan suka kyale ni, sai in
    dawo in kwashe sauran. Idan basu kyaleki ba
    fah? Sai na dawo nan ka yanke hukunci duk da
    zaka yanke. Ya xura mata do, ai iyayenki na san
    ba su ki karbarki ba, hasalima ai laifin su ne, na
    tabbata yanxun sun gane kuskurensu, dole su
    lallabaki. Ta doke kafadarsa tana dariya, har ma
    kasan dole su lallabani? Kai dai ka yi fatan su
    amince da auranmu. Yace shikenan, yanxun ki
    dauki abinda xaki dauka na rakaki, dare nakara
    yi. Ta bude kit ta xuba kaya kala 3, yasa hannu
    ya dauko wata 'yar karamar doguwar riga
    yace.....
    Yace ba xaki dauki wannan rigar ba?
    Tace wannan shegiyar rigar? Shegiya? Lallai ba
    ki san yadda take mi ki kyau bane, a'a ka dai
    barta anan, sanin kanka ne, su Abba bna za su
    barni na sanya taba cikin gidansu. An wuce
    wurin, ki barta kyasa a gidana. Ta yada kai kan
    kafadarsa tace ashe ka gane. Ya tsikare ta, ta
    mike xumbur! Ban fa so Danliti banso! Ta figi kit
    dinta, tayi waje baki a ture. Ya kwaso mata gyale
    da takalmi ya biyota yana fadin sorry 'yar bebi
    na! Taja ta tsya tana haraarsa, ya yafa mata
    gyalen, ya aje takalmin gabanta ya jawo
    kafufuwanta, sa abinki mu tafi. Ta xura kafar
    tace wa Ayuba, sai da safe. Yake yayi ya amsa,
    Allah ya kaimu. Suka fice, Danliti na cewa, har
    kin tabbatar da xamanki a gidan ne kike ce masa
    sai da safe? Tace gane min hanya wai, makaho
    ya so gulma. Ya ci gaba da dariya, suna tafe
    suna hira. Gab da gidan, ya tsaya sukayi sallama,
    idan kuma ya gan ta ta dawo shikenan. Y koma
    ita kuma taci gaba da tafiya hankalinta kwance
    yake, don bata saka komai illa in su koroto, ta
    koma inda ta fito. Daga bisani ma wata dabara
    ta fado mata. Tana dosowa kofar gidan, ta hangi
    kamar ana hada hadar jama'a, duk da dare ya
    fara yi, kana iya gane wa ana sha'ani a gidan.
    Bata yi wa kowa magana ba,a haka suma babu
    wanda ya shaidata. Sai da ta shige xauran
    karshe ta aje kit dinta, ta xauna akai ta hade kai
    da guiwa ta kirkiro kukan dole ta shiga yinsa har
    da shesheka, sannan hankulan masu wucewa ya
    fara xuwa gunta kuma, Ya ali shine mutum na
    farko daya fara dosar ta da tambaya, wai wacece
    xaune? Gida kike son komawa? A zata son cikin
    'yan kawo amare ne, yayi dan murmushi, don ta
    bashi dariya. Da girmanki da komai kike
    kauyanci? Dan Allah tashi ki koma cikin gida tun
    kafain yara su fara miki dariya. Ko an yi miki
    wani abu ne? Daga ji ta gane mai magana, shi
    yasa ta dago sosai ta dube shi, kawai batare da
    tayi magana ba. Gabansa ya tsinke ya fadi
    xuciyarsa ke ambato sunan, mama? Sannan ya
    tsugunna gabanta ya furta a hankali, mama!
    Hawayenta suka kara tsunkewa, ta sadda kai,
    tana gogewa da bayan hannu. Innalillahi wa Inna
    illaihir raju'un! Ya waiwaiga babu mai kallonsa
    yayi sauri ya ja mayafinta ya rufe fuskarta, yace,
    taso muje, kar ki bari kowa ya ganki. Ya ja
    hannunta suka sulale dakinsy Danlami. Babu
    kowa cikinsa, duk suna can wajen fatin da sukeyi
    da abokansa. Ya xaunar da ita gefen gado ya
    tsugguna. Yace, yaushe kika dawo mama? Baki
    na rawa ta amsa, yanxun, idanuwansa suka kawo
    kwalla a raunane. Yace abinda kikayi kin kyauta
    kenan mama? Da mtuncin ki da komai? Iyayen
    mu masu girma da daraja a gurin jama'a, kika
    tozarta su? Haba mama, kamar baki sami tarbiya
    ba? Ta goge kwalla. Tace, ba haka bane, Ya ali
    me yasa zaku rinka ganin laifi na ni kadai? Nace
    ga wanda nake so, ba sai a ba ni shi ba. Ina
    ruwan kowa da rashin asalinsa? Ai dai ba daga
    sama ya fado ba, da uwarsa da ubansa. Yace,
    Maganar banza ce wannan mama, don na
    tabbata Daliti bai fi miki iyayenki ba. Kin kuwa
    san halin da umma ke ciki tun ranar da kika sa
    kafa kika bar gidan nan? Kin daure min kai, ban
    taba xataon zaki aikata irin wanan mummuna aiki
    ba. Tace hakan kadai xai memin mafita kuma
    akan bakana na dawo ko Danliti, ko su rasa ni
    baki daya. Ya xura mata ido, yana kada kai.
    Afuwa ya kamata ki nema ku sulhunta da
    iyayenki, su sa miki albarka, ko kin ga rayuwa
    mai kyau da anfani nan gaba. Saboda haka ki
    xauna anan ki jirani, xan shiga wajensu in
    kwantar musu da hankali tukina, gaskiyya bana
    so ayi miki taratsi cikin jama'a, kuma gidan cike
    yake da baki. Baki? Me akeyi a gidan? Ya amsa,
    biki na akeyi dana seed. Kana nufin kunyi aure?
    To Ya xanyi, tunda kinki ni Mama? Akan
    dole na yi auaran nan, su Baba sun matsa min.
    Ina muku murna, nima Allah yasa ni a danshinku.
    Ya xura mata ido gwanin tausayi. Yace, nasan ba
    xaki ji komai a ranki ba, tunda ba so na kike ba,
    amma ni har kwanan gobe ina sonki, shi ya sa
    abinda ke faruwa da ke ya xame min ciwon cikin
    raina, ki yiwa girman Allah mama ki sanya
    tunanin ki dawo sak! Yadda kowa ya sanki. Karka
    damu dani Ya Ali, ko da yaushe ina gaya ma kai
    dan uwana ne, kauanar mu ta jini ce mai asali.
    Kwanciyar hnakalina kuwa Danliti ya zama
    mijina. Ina fatan iyayen Al-ameen sunyi xuciya
    su fasa? Ko baka ji komai akai ba? Ya xuba mata
    ido yana mamakinta, ya jima bai amsa ba, kafin
    yace, Al-ameen ya koma Rasha da ciwon xuciya
    Mama..... Ta katse shi ido rufe ta dafe kirji.
    Tace, nagode Allah! Har naji sanyi cikin raina. Ya
    kada kai yana kallonta. Yace, baki masa adalci
    ba, baki tsoron amanarsa ta ciki? Akan me? Bafa
    dole bane na aure shi, ina son kowa ya gane
    wannan, kawai kaje ka gaya masu na dawo din,
    kaji me xasu ce? Yace ni ne nayi niyyar yin
    hakan, ba sai kin bani umarni ba. Yi hkr Yaya, bai
    tanka ba, ya tashi ya five, ta bi bayansa da kallo
    tana fadin cikin ranta, je ka dawo, duk na kosa in
    san babin da nake. Cikin dakin yayi sallama, abba
    ya amsa masa yana kokarin hadawa Umma shayi
    ta samu ta dan sha, ya akayi Ali? Ya xauna gefe
    kusa da shi, yace babu komai abba, wata alfarma
    naxo nema wajenku. Hankalin abba ya dawo gare
    shi, yace ina jinka. Allah ya sa batafi karfi na ba.
    Ya kada kai ya amsa, bata fi ba Abba, duk mai
    laifi idan ya nemi afuwa, me yakamata ayi masa?
    Ya dube shi da kyau da mamaki yace, ayi masa
    afuwar, domin Allah yana son masu yafiya ga
    bayinsa. Su kuma masu laifin su yi alakwarin ba
    xasu sake komawa ga wancanm laifin ba. Laifin
    me kayi? Ya amsa, laifin mai girma ne Abba, a
    misali Mama ta dawo ta nemi gafara, abba xa ka
    karbi tubanta? Ba abba kadai ba harda Umma
    dake kwance ta xubo masa ido, abba ya jima
    kafin ya numfasa. Yace Bansan dalilin da yasa
    ka min tambayar nan ba, amma ina so ka sani,
    mama ta aikata laifi mafi muni a shafin tarihin
    gidan nan, da mu karbeta da kar mu karbeta,
    bakin fentin da ta shafa mana yana nan baxai
    goge ba, ina so ka sani Ali, xaiyi wuya a fadin
    gari na Mama ta sami wani mijin, face katon
    daya dauke ta ya boye wani wuri tsowon watanni
    3. Abu na karshe da nake so ka snai, shine bai
    kai kadai ka rokeni ba. Al-ameen ma ya rokar
    mata gafara kuma nayi masa tare da alakwarin
    ba xanki karbarta ba. Saboda haka ka kwantar da
    hankalinka, muddin Mamma ta dawo gidan nan,
    ba xan ce ta koma ba, haka xalika idan bata
    sauya ra'ayinta ba, ba xan ce mata a'a ba, Allah
    na kallo, nayi kokarin na, don nuna mata hanyar
    kwarai da samun abokin zama na kirki mai kyan
    asali. Ko duniya ta zageni, alhakin Na suka duka
    kuma zamuyi shari'a da su gobe kiyama. Kawai ji
    yayi kwallah na xubo masa, saboda tausayin
    Abba, yasa hannu ya goge, abba ya riga shi sake
    magana, ka daina kuka Ali, kaddara ce, tashin
    hankalina daya, mahaifiyarta da ta kasa samun
    nutsuwa. Ina jin tsoron kar ciwon xuciya ya
    kamata kamar yadda likitocin da ke duba ta suke
    gargadin ta kullum. Dalilin da yasa kenan nake
    fatan Allah ya sa mama ta dawo, watakila ya
    zama waraka ga mahaifiyarta. Na tabbata
    hankalinta xaifi kwanciya idan tana ganin ta koda
    a dakin auran Danliti ne. Ya Ali ya gyara xama
    yace, gaskiyya ne abba, kuma naji dadin bayanan
    ka. Saboda haka ina mai farin cikin shaida maku
    cewar mama na nan ta dawo. Abba ya xura
    masa ido. Umma kuwa ciccibawa tayi ta tashi
    xaune. Ba fahimce ka ba Ali? Inji Abba, yace
    Mama na nan a cikin gidan nan, idan kun ban
    izini, zan shigo da ita ta roki gafararku. Suka dubi
    juna shi da Umma baki sake, tuni hawaye suka
    tsinke mata, tana kada kai tare da salatin Manzo.
    Abba ya dube shi yace, je ka ashigo da ita Ali.
    Har ya mike ya sake komawa ya xauana, yace
    Abba ina fatan ba xaku daga mata murya ba,
    kasan gidan na cike yake da baki. Yace Insha
    Allahu, ba xan daga mata ba. Yace nagde abba.
    Ya mike ya wuce, abba ya bishi da kallon,
    sannan ya dubi Umma, ashe haka Ali ke da
    hankali? Nayi kuskuran hana masa auran Mama
    tunda farko. Umma ta goge hwaye tace, hakika
    mama tayi asara masoya 2. Haka Allah ya so, ba
    mu da abinyi, dai yi masa godiya, abba ya sauke
    numfashi, sukayi xugum suna sauraron ta yadda
    mama xata bayyana garesu. Jimawa kadan suka
    tsinkayi muryar Ya Ali yana fadin ki shigo mana!
    Na gaya miki komai ya wuce, ki shigo kawai.
    Make-maken munafurci takeyi ba wai ainihin
    tsoron bane cikin ranta, da su abba xa suyi
    kuskuran cewa ta juya, fes! Zata juya babu
    waiwaye sukayi sallama dakin. Ya ali na dauke
    da kit dinta. Ta toge bakin kofa, yasa hannun ya
    janyo ta har gabansu abba dake sake da baki
    suna kallon abin al-ajabi. Gata abba, umma ga
    Mama, ku mance da abinda ya faru, ku amince
    da xabanta, ku sa musu albarka, sai kuka ga
    Allah ya basu zuri'a abin alfahari. Mama ki
    durkusa ki roke su gafara. Ko dama a durkushen
    take kuma tuni hawayen suka tsunke mata,
    murya na rawa, tace..
    [12/01 19:16] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***12
    Abba kuyi hrk, Umma ki yafe min. Abba
    ya numfasa yana kada kai. Ya ce a rayuwata
    gaba daya Mama ba tba xataon xaki min irin
    wannan mugun butulcin ba. Na dauke ki 'yar da
    na dauki burin duniya na dora a kanki. Kece kika
    bambamta da kowa cikin xuciyata, kuma na nuna
    miki dukkan gata amma dare daya, kika numa
    mana akwai wanda ya fi mu muhimmaci a
    rayuwarki. Tabbas na yarda da hakan, don a
    tunani na xan ga kin dawo kin bushe a lalace
    saboda tunanin kin barmu cin BAKIN CIKI sai
    gaki Fes! Kinyi kiba. Ban miki baki ba, ba kuma
    xan miki ba, amma ina mai tabbatar miki in rasa
    masoyi, kin rasa mai tsanin kaunar ki tsakani da
    Allah, kuma a yau na kara nadamar hana Ali
    auaranki tun farko. Maganata karshe itace, tunda
    kin nace sai Danliti to ki gaya masa ya turo
    magabatansa, muyi magana, sannan kiyi wa
    Yayanki Ali godiya, domin yayi miki dukkan
    taimako. Zaciyarta fara sol! Jin Abba ya ambato
    Danliti ya turo. Ta kara dukawa tana goge
    kwalla. Tace, ngde abba, kuma ina kara baku hkr,
    don Allah ku yafe min. Ta rarrafa gun Umma ta
    cusa kanta jikinta, umma kiyi hkr! Ta share
    hwaye tace ai ya wuce Mama, kinci albarkacin
    al-ameen da ali. Amma gyara kayanka, ai baya
    zama sauke mu raba ba. Ki bi duniya a sannu,
    domin ita duniya budurwa ce mai kyale-kyale da
    yawa, da zarar ka biye mata, to ka bace ka kuma
    shiga uku ka lalace. Ban da abin kari a gareki,
    don nasiha anyi miki, amma kin rushe saboda
    batan basira. Allah ya ganar da ke, ya sa ki a
    hanya madaidaiciya. Ya ali ya amsa da amin,
    yayin da mama ke ci gaba da gugar hawaye. Alin
    ne ya cigaba da cewa, don Allah abba karku
    nuna kowa ta dawo har tym din bakin nan xasu
    koma. Ko su Baba a kyale su tukuna. Ke mama
    ina son ki cigaba da xama cikin dakinku dan
    Allah, na san xuwa gobe da yamma kowa xai
    watse, sai a kam magana ta gaba, kinji? Ta amsa
    da kai, Abba yace shikenan Ali, kana son ka
    rufawa 'yar uwarka asiri, asirin kuwa da ya riga
    ya tonu. Yace kayi hkr dai abba, yace babu
    komai, ta tashi ta koma dakinta, idan tana jin
    yunwa, akwai abinci, yace xaki ci abinci ne? Ta
    kada kai, to taso na raka ki dakinki. Umma mun
    gode, tace Allah yayi albarka, ya amsa da amin.
    Tare suka mike suka bar dakin. Umma ta tafa
    hannu tana salati, sannan ta buga tagumi.
    Yanxun alh. Danliti xata aura? Yace, t ya xamuyi,
    wa kike ganin xai fito neman auranta, bayan ya
    san wannan kwamacala? Haka nan xamu hkr da
    abinda Allah ya kaddaro, yanxun dai bana ce ya
    turo ba? Sai mu sa ido mu ga wadanda xai turo
    din. Ta numfasa, tace Allah shi kyauta yace
    amin. Ke dai ki kwantar da hankalinki, ki daina xa
    damuwa a ranki don Allah. Tace naji alh. Ya ciga
    ba hada mata shayin suna tattaunawa. Kamar
    yadda ake tattaunaea da mama da Ya Ali.
    Shawarwari kawai yake bata, tana sauraronsa
    kamar gaske. Har kusan sha daya da rabi suna
    tare. Dagab bisani yayi mata sallama ya barya
    cike da farin ciki da baya misaltuwa. Nan da nan
    ta fada bayi tayi wanka, ta kintsa jikinta ta
    kwanta. Kewar Danliti ta lullube ta, fadi take
    cikin ranta, ba dan dare yayi ba da naje yiwa
    sweety Na albishir. Da kyar barci ya sace ta
    saboda murna. Washe gari hidima taci gaba,
    mama na cikin dakin na kulle babu wanda ya san
    ta dawo, daga Ya Ali sai su Umma. Kuma anyi
    sa'a taji maganar Ya Ali batayi marmarin fitowa
    ba, sai shi ne ma ya kan saci jiki ya shiga
    wajenta, ya ganta yaji dan ji sanyi aransa. Allah
    sarki! Garin dadi na newa, iska na ta wahalar da
    mai kayan kara, bayan sallahr la'asar baki suka
    koma muhallin su aka bar amare da angwayensu.
    Shi kuwa Ubandawaki 'yan uwansa ya tara falon
    baki yace, naki ku ne a matsayin ku na kannena
    na in shaida muku cewar Mama ta dawo daren
    jiya, kuma har na yanke hukuncin ta gayawa
    Danlitin ya turo magabatansa, muyi maganar
    aure. Ban san yadda zaku karbi abin ba, ko da
    mahimmanci ko ya zama abin dariya a gareku,
    duk daya ne, ni dai na fita hakkinku. Suka dubi
    juna cikin sigar tsarguwa, sannan Alh.basir yace,
    ai shikenan yaya, amma banji dadin yadda kayi
    mana fassara ba, ya kamata kayi mana uxuri
    tunda mun ce maganar nan bada wata manufa
    muka fadeta ba. Amma ace mama ta dawo tun
    jiya, sai yanxun mukeji? Ba komai. Alh. Adam ya
    cage, tabbas naga Danliti a shagonsa, sai dain
    banyi tunani tare suka dawo ba, tunda banji
    labarin ba a cikin gida. Sai dai Yaya a gaskiyya
    muna so mu ganar da kai cewa ba farinciki
    mukeyi da abinda ya sami mama ba, mutuncin
    gidan nan, ai duk namune, me zai sa muyi murna
    da rugujewarsa? Abba yace duk naji, magana ta
    gaskiyya, Allah kadai yasanta, don shine masanin
    sirrin xukata. Abinda ya sa bau san Mama ta
    dawo ba, sai yanxun. Ali ne ya fara ganinta kuma
    ya xo ya sameni guiwa 2 ya roke ni da kyale
    mama kar in daga murya, saboda baki fa ke cikin
    gidan nan. Idan sun tafi ayi su wacce xa ayi. To
    maga ma ta kare, nacewa Danliti ya fito a daura
    musu auran, su karata. Allah dai ya gani ba da
    son raina bane. Fuska Ya mutse Alh. Basir ke
    cewa, Dan liti xata aura? Yace bamu da abinyi,
    haka Allah ya so, sai dai muyi mata fatan
    alkhairi. Saboda haka bana son abin yayi tsawo,
    yana turo sai aure.
    Ya turowa za'a sa rana kuma ba zata
    wuce sati 3-4 ba duk abinda Allah ya hore min
    shi xa'a kai mata. Ita kenan maganara, kowa na
    iya tafiya harkokinsa, mu saurari xuwan
    magabatan nasa shikenan, Allah ya nuna mana.
    Haka suka fadi baki dayansu. Abba ya amsa da
    amin, suka bar falon ba yabo ba fallasa, cikin
    xukatansu, ma'ana intayi ruwa rijiya in ba tai ba
    masai. Suna shuga sasan su, suka bajewa
    iyalensu babu bata tym suka fara xuba sharhi.
    Haj. Gake kuwa har da guda. Daga bisani suka
    baxama sassan Uban dawaki, don gain Mama
    tare da yiwa Umma murna dawowar Mama fida,
    amma a zahiri a cikin xukantasu yanayin Maman
    suke son gani. Suka kwarara sallama, umma ta
    amsa, sai mukaji daddadan labari! Ina maman?
    Inji Haj. Hajjo, tana dakinta, gaba daya sukace
    Allah shi kyauta na gaba. Yanxun da Danliti
    xa'ayi auran? Tace, nufi ne Allah, duk abinda ya
    rubuta bamu isa mu goge Ba. Haj. Hajjo tace
    gaskiyya ba haka muka so ba. Sai dai hkr kwai.
    Haj. Gaje ta tabe baki tace, ya xama dole, amma
    a hakikanin gaskiyya mama ta bamu kunya. Ajin
    ai ba daya bane in banda batan basira. Koda
    yake ance so mako ne. Allah ya sanya alkhairi.
    Sukayi dan shiru, kafin suka nufi dakin Mama, ina
    kike? Kina jin mu amma ba xaki fito ki gaishemu
    ba? Tana xaune gefen gado, ta fesa ado kyanta
    ya kara bayanna, banda haka da ibar da ta kara
    suka kalli juna sabe da haba, kafin Haj. Gaje ta
    soma xuba, lallai Mama, watau hankalinki a
    kwnace kika je, ki ka dawo! Wannan kiba haka?
    To Allah yasa ki sami irin wannan a gidansa. Haj.
    Hajjo ta amshe amin dai, kin dai riga kinsan
    halinsa, komai yayi miki sai ki hadiyewa cikinki,
    kar ki doshi kowa, tunda kin nace shi kike so! Ko
    kuwa gaje? Tace haka yake yaya, ai kowa ya
    sayi rariya yasan zata xubda ruwa. Mayafinta
    dake bisa filo ta figo ta mike tsaye ta xura
    takalmanta tayo waje tana yafa gyelenta, ta
    barsu anan sake da baki, suna kallon juna. Ko
    kinga dibar albarka? Inji Haj. Hajjo, Haj. Gaje
    tace, mamaki kikeyi Yaya? Karfa ki manta
    watanni 3 ta shafe a bariki, an kuwa ce xama da
    madaukin kanwa, shike kawo farin kai. Mu meye
    namu? Ta malam ai bata wuce amin. Can suka
    sameta dakin Umma tana neman izinin zuwa
    wajen Danliti, don ta shaida masa sakon abba,
    suna isowa, umm ana fadin bance kije ki xauna
    ba, mutunciki shine ya biyo ki nan kofar gidanku.
    Saboda haka daga yau kar na sake jin kin koma
    shagonsa. Tace, to Umma, insha Allah yanxun
    xan dawo. Ta sa kai ta fice, ba tare da Umma ta
    kara wani abu ba. Nan su Haj. Hajjo suka xauna
    suka cigaba da kwasar tsegumi, ita kuwa tana
    fitowa xauran farko, angwaye ta ci karo dasu,
    saeed Ya maka mata harara, ya wuce abinsa
    cikin gida. Ta dubi ya Ali, tace me nayi masa?
    Yace kin fi kowa sani. Taja dogon tsaki, aikin
    banxa, to shinme me? Don ya ki min magana?
    Yace, kin baci da Rashin K mama, me yasa? Da
    ba haka kike ba. Ta dan tabne baki tace, ni ina
    da wurin xauwa, ba na fito magana da Ya Saeed
    bane. Yace amma ba kije kinga amare ba. Xanje
    ai, so nake in sauke wannan nauyin ko ni,a na
    kama dahir. Yayi dan murmushi yana kllonta,
    mama kenan, to a dawo lfya, nasan sakon bai
    wuce na Danliti ba. Tayi 'yar dariya. Shi ysa nake
    sonka Yayana, bari dai in dawo amaryarka ka xan
    fara xuwa na in gani. Ta wuce tana cigaba da
    dariya, ganin yadda yayi tsaye duk jikinsa ya
    mutu. Ya bita da kallo, sannan ya kada kai, yace,
    ni ma ina mutuwar sonki Mama. Ina ma ace
    hankalinki xai dawo gareni? Ya sauke numfashi
    ya shige wajen amaryarsa. Bakinta har kunne
    take sallama kofar shagon, ayuba ta gani xaune
    ckin shagon ya amsa mata cike da fara'a
    amaryarmu kenan, ya gajiyar tfya? Tace tabi lfya,
    ina mutumin? Ya amsa yana ciki tun azahar yake
    barci saboda ragwanci. Ta fara dariya, lallai
    kuwa ragwanci, barin inshiga dole ya tashi ya
    bani goron albshiri. Ta wuce ciki, ayuba na fadin,
    ya dai kamata ya tashi ko salla ya samuyi. Kan
    tsaye bisa katifar ta fada, ta dada masa duka
    cinya, don Allah tashi rago! Ka wani baje kana
    gugar barci, ni ina can ina tunaninka. Ya bude ido
    firgigi yana kallon ta jim, sannan yayi dan gajeran
    tsaki. Yace kash! Wlh ba don ke bace, marin
    Mutum zanyi. Kin ji dadin barcin kuwa? Tayi far
    da ido, tace ko? To ka tashi, na tabbata dadin
    barcin bai kai albishir din baki na ba. Ya xuba
    mata ido yace fadi ina jinki. Idan kuma bai fi ba,
    kinsan Allah sai na sanya ki kuka, ai kin san
    gamuwar mu babu tausayi. Tayi 'yar dariya, tace,
    haba duk wannan kukan wasa nakeyi, kama
    daina hura hanci. Yayi murmushi, haka kikace?
    To shiknen, fadi ina jinki. Ta gyara xama
    albishirnka? Yamasa goro. Xaka bani Ah! Me xai
    hana? Ke dai gaya min inji. Abba yace in fada
    maka ka turo, ranar auren mu za a sanya. Ya
    xuba mata ido, ya kasa ko motsi, kayi shiru? Ya
    sa hannu 2 ya mutsutsuke idanuwansa yace, dan
    Allah karki xalayeni! Ta ware ido, kana nufin baka
    yarda ba? Gaskiyya ban yarda ba, yaushe Abba
    xai yarda ya bani ke, bayan ya san bani da kowa
    a garin nan? Sannan suna min kallon dan... Tayi
    wuf ta rufe bakinsa, sau nawa xan gaya maka ka
    daina dorawa kanka maraici? Ina sonka
    Danliti.....
    su abba kuma sun amince ka turo asa mana
    rana da gaske na ke gaya maka maganar nan ba
    wasa ba da sauri ya figo ta jikinsa yayi wani irin
    ihu wai shi murna ayuba ya kwaso a guje ya fado
    dakin ya same si kankame da juna dan haka. Bai
    tsaya tambayar komai ba ya juya ya fita yana
    kada kai cikin ransa yana fadin "Danliti akwai
    dan iska"ya jima bai kyale mama taci gaba dayi
    masa bayani ba yanzu yaushe. Zaka turo? Ya
    yunkura ya tashi zaune yace bashine matsalar ba
    wadanda zan turar sune matsalar ta dan bata
    fuska tace ai ba za ka rasaba "Danliti ko yan
    dattijan daku ke gaisawa sun isa su wakilce ka
    ko kuwa? Ya zura mata ido duk sun juye, yace
    haka ne sai ki baru in gan su mudaidaita tukunna
    sannan in gaya miki ranar daza su zo ko" tace
    shi ke nan bari in kwashe sauran kayana in koma
    gida ya kara matsarta haba tun yanzu ?" Umma
    ta ce kar na dade kuma tunda sun amince da kai
    ai zaka rinka zuwa ne kan ka tsaye,"ya
    kankameta ya na fadin haka ne amma ban so ki
    tafi yanzu sonki kawai ke azabtar da ni ina
    kewarki da yawa jiya da kyar nayi barci kinji
    yadda ki ke tashin kamshi?gaya min dame dame
    ki ka shafa in karo miki irinsu?"Bata iya bashi
    amsa ba don tun tafiyar su yake koya mata irin
    wannan renon ya gama da rayuwar ta gaba daya
    kai ALLAH ka raba mu da sharrin masu
    sharri,magariba ta wuce wadan da sukaje
    masallaci ma sun koma gida yayin da mama ta
    fito daga shagon Danliti jaye da katuwar jakar
    kayanta.
    -yar tafiya kadan ya taka mata ya dawo
    abinsa bata sami dan dakon da zai daukar mata
    kayanba ba don haka da kanta tayi ta ja har gida
    abba da umma na zaune a falo dauke da bakin
    ciki maras misaltuwa mama ta turo kofa ta shigo
    sa sallamar ta dauke da uwar jakar kaya babu
    wanda ya amsa mata ta wuce ta gabansu ta
    tsugunna tace sannu abba, wani irin kallo yayi
    mata mai isar da sakon haushi da takaici kafin
    yace daa ina kike?ta dan sunkuyar da kai tace
    naje gaya wa Danliti sakon ka ne ai na gayawa
    umma kafin na fita ko um..."Ya daka mata tsawa
    rufe min baki don ALLaH shine zakije ki zauna
    har bayan magariba kiji tsoran ALLAH mama ki
    sani cewar mutuncinki ki ke zubarwa wannan
    uwar jakar da kika shigo da ita tawace tukuna?
    idanuwanta suka kawo kwalla ta fara rawar
    murya na...nawa ne.. Kayan da...Danliti ya siya
    min ne yace to ba a gidan nan ba idan yazo ki
    maida masa kayansa ya baki can gidan sa,ai kinji
    ni ko,?ta amsa da kai umma ta cire tagumi ta
    kare mata kallo sannan tace Alhaji ya kamata a
    tuhumi yarinyar nan idan idan tabada kanta
    gareshi kasan istibira'i ya kamata, kafin a daura
    auransu domin ni banyarda da mama ba a yadda
    suke tare da yaron nan,ya numfasa ciki da bacin
    rai yace ki na da gaskiya don ni ma wallhy ina
    wasi wasi cikin raina ke mama ki gaya min
    tsakaninki da ALLAH ki fi jin tsoran sa akan
    komai na duniya ki gaya min gasjiyar abinda ke
    tsakanin ki da Daliti kar kisa muyi kuskure da
    gangan idan kin san da wani abu to ki gaya
    mana mubi tsarin da ALLAH ya shimfida.
    -sosai ta goce da kuka murya na rawa tace
    ALLAH abba babu abinda ya shiga tsakanina da
    shi duk sukayi shiru suna dubanta kamar sun
    gaskanta ta kamar basu yarda ba amma dolensu
    yarda tunda basu da wata hujjar kama ta don
    haka abba ya daka mata tsawa ya isa don
    ALLAH tana wani bare baki kamar mummuna
    tashi kiba mu wuri kuma na gaya miki yana zuwa
    ki maida masa jakar kayansa,ta goge hawaye ta
    dan sunkuyar da kai tace yace ya gode insha
    ALLAH zai turo din suka yi banza da ita shiyasa
    da dago ido ta dube su uwar hararar da ta yi
    arba da ita tilas tasa tayi saurin maida kanta
    kasa jim sun kikara cewa komai yasa ta mike
    simi simi ta janye jakar ta, ta wuce daki bakin
    nan tamkar na agwagwa kai tsaye bayi tashige
    tayi wanka ta dauro alwala ta fito ana ta kiran
    issha'i,don haka tana yin magariba ta dora
    issha'i
    bayan ta kammala ta fito neman abinci nan falo
    sukayi kicibis da yaya ali wai me ki ke nufi baza
    kizo kiga amarya ba?ta kama kugu hannu biyu
    tace wannan amarya an damu nazo na ganta
    hala tafini kyau ne ya kama dariya kafin yace
    soosai kuwa tafi ki kyau muje ki ganta tace haka
    yake amma duk kyanta dai ni aka fara so kifin ita
    saboda haka a daga min kafa inci abinci
    tukuna"kalamanta sun ruruta wutar zuciyarsa ba
    kadan ba koda ganin yadda jikinsa ya saki kasan
    ya fada wani yanayi ya zura mata ido
    hannayensa rungume a kirjinsa murya sanyaye
    ace zancan ki dutse yar uwata,.
    [12/01 21:52] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***13
    hasalima rashinki yasa na aure ta koda
    yaushe ki kace da ni kule da sauri xan ce cas
    mama don son ki ya zauna a raina, tayi yar
    dariya tace yaya ali ke nan kar kasa amaryar ka
    ta tsane. Ni daga wasa sai ka hau jera zance!ba
    haks nake nufi ba yaya ali muje kawai naga
    amarya in na dawo na ci abincin bata jira yace
    wani abuba ta yi gaba abinta tilas ya biyo
    bayanta yana kada kai!Amare kam masha ALLAH
    suna dauke da tasu baiwar da ALLAH yayi masu
    musamman aminar yaya ali har mama na masa
    tsiya wai ya kamata ya maida sunan sa aminu
    dan su kara dacewa da juna kallon ta kawai yake
    yi cikin ransa shi yasan babu wacce tafi dacewa
    dashi face ita kanta maman,bata wani dade ba ta
    dawo sasan su ta dauko leda cike da kayan
    garar amare bayan ta gama cin abinci ta zauna
    gaban madubi tayi wa fuskar ta kwaskwarima
    tayi zaman jiran Danliti har barci ya fara dibarta
    bataji aiken yaro ba,ta kwana zullumi da juyayin
    abinda ya hana Danliti zuwa alhalin ya sami
    izinin yin hakan ko har yanzu bai amince wa
    ransa bane?ya gudun kar yazo ya fuskanci
    wulakanci!wannan tambayar taso ta hana ta
    barci domin ta kai sama da karfe dayan dare
    bata sami barci ba,Da sassafe ta tashi da ciwon
    kai wanda ya haddasa mata jiri akai akai duk da
    haka ko karyawa bata yiba karfe bakwai da rabi
    tasa kai ta fice babu wanda ya sani ta nufi
    wajen Danliti dauke da ledar kayan garar amaren
    da aka bata jiya ita ta tashe shi barci ya tashi a
    gigice yana tambaya lafiya kika bugo sammako
    haka?tace nayi zaton zaka zo jiya hira me ya
    hana ka zuwa.
    ya ja dogon tsaki ya kauda kai jim sannan ya
    juyo ya dubeta wai me ke damun kine?ba kinzo
    nan ba sai bayan magariba kika tafiba?to kuma
    me zanje in yi maki saboda ALLAH ta zura masa
    ido ya kare mata kwakwazo nan take idanuwanta
    suka tara kwalla murya na rawa ta ba haba
    Danliti laifi ne don ban gan kaba na biyo in duba
    ko lafiya?ya bita da kallo tana ta gugar kwalla ya
    kece da dariya kamar mahaukaci hakan yasa ta
    daina hawaye ta zuba masa ido yayi dariya mai
    isar sa sannan ya natsu shima ya bita da kallo to
    meye abin kuka ni ina can ina ta billayin neman
    mana waliyai ai banga ta zaman fira ba
    sakeena"nan da nan ta hadiye tashin hankalinta
    ta fara murmushi duk kin wani daga hankalinki
    don baki ganni ba jiya kawai " kawai ne? In gaya
    maka dai dai da sakwan daya bana son zama
    babu kai,yayi wata budurwar dariya yace ko to
    na kara baki tukuicin kaina ta kwanto masa tana
    dariya kasan ALLAH da ciwon kai na tashi ga
    wani jiri na diba na amma na kasa daurewa na
    fito ko karyawa banyi ba, yace ai ya bebi na
    sannu ko ya kamata mu karya ki sha magani bari
    inzo. Ya fice ya bar ta kwance bisa katifar
    wucewar minti ashirin ya dawo da soyayyun kwai
    da naman kaza da doya itama hade da kwai ta
    hada masu shayi suka batse cikinsu harda ayuba
    anan ta yada kafada daga fira barci ya kwasheta
    Danliti ya dawo shago ya zauna tare da ayuba ya
    zura masa ido yace don ALLAH ka tasheta ta
    koma gidan su yayi banza dashi ya fito yana
    zuba fito kamar katon arne.
    -Ayuba ya kada kai yace karshen alewa kasa
    Danliti idan an ciza a rinka hurawa ya ballo masa
    harara ya ce ba ruwanka malam ka kyale ni in ci
    lokacina ya tabe baki yace na barka zaifi kyau
    suka yi shiru kowa na harkan gabansa, a gida
    kuwa tunda suka shafa babu mama a dakin ta
    suke ta kwasar BAKIN CIKI don sun tabbata tana
    can shagon Danliti karfe tara uban dawaki ya
    gama shirin sa zai fita ko karyawa bai yi ba
    saboda tsabar takaici yasa umma ta fito masa da
    jakar kayan da mama ta shigo dasu ya sunkuta
    yayi waje da ita kalla ya tarbe shi da sauri ya
    amsa ya bude but ya saka Abba yace minna
    zasu tafi amma zasu tsaya shagon Danliti, kalla
    yaja mota suka wuce yayi fakin kofar shagon
    abba ya umarci daya fito masa da jakar nan kai
    tsaye ya wuce shagon lokacin da su Danliti ke ta
    harkokinsu yayi tsaye babu sallama har
    hankulansu suka juyo gareshi Danliti ya matso
    yana fadin sannu alhaji ina kwana yace nasan
    mama na nan tare da kai ina take baki sake yace
    tazo amma ta tafi yayi jim yana kallonsa kafin
    yace ba shi ya dame ni ba wannan ya rage kuda
    ubangiji ina fatan. Ta gaya maka yace ta gaya
    min kokarin da nakeyi ke nan na samu na turo
    yace kar ka bata lokaci domin na kosa na kauda
    kazantar da nake gani ya dan sunkuyar da kai
    yana murmushin izgilanci naji abba in ALLAH ya
    yarda zuwa anjima ko gobe zan turo yace shike
    nan ina sauraronka amma ga kayan ka nan ka
    aje idan ta tare gidanka sai ka bata ba na
    bukatar komai daga gareka sai sadakin da
    ALLAH ya wajabta ga jakar nan bai saurari wani
    abu ba yasa kai ya bar shagon ya fada motarsa
    kalla ya ja suka dauki hanya
    Ayuba ya matso gare shi yace, Allah na
    tabaka dama, don ka gyara kuskuran ka Danliti,
    kar ka bari ta subuce maka, ka dawo kana cizo
    yatsa. Ya watsa masa harara yace bana bukatar
    wa'azinka alaramma karfa ka manta da ni da kai
    duk daya ne. Na ma dai san abinyi, ayuba ya
    xuba masa ido ya rasa ta cewa babu abinda ya
    sami Danliti, yasa hannu ya dauki jaka ya shige
    da ita. Hannu 2 ya rike kugu, yana kallon mama
    xucyarsa na masa sake-sake. Kusan 5mins yana
    tsaye, sannan ta tsugunna ya bubbugata. Ta
    farka tana yamutsa fuska, menene? Tashi kiji? Ta
    yunkura ta tashi xaune, yasa hannu ya kara janyo
    jakarta, don ta ganta sosai. Cike da mamaki tace
    waya kawo ta? Yace, abbanki mana! Wannan
    kadai ya tabbatar min baya sona, baya kaunta.
    Bai dameni ba, amma me yasa zai uzzura min
    dole sai na turo magabata na yanxu-yanxu?
    Hankalinta ya tashi, ta matso a hankali ta dafa
    kafadarsa. Don girman Allah kar hankalinka
    yatashi Danliti.... Cikin sababi. Yace ki daina
    gaya min wannan maganar! Kora da hali abba ke
    min, saboda haka ki hkr, kije su baki wanda suke
    so! Tashi ki bar dakin nan, kar kuma ki sake
    xuwa, ni babu ruwana! Ta narke da kuka, murya
    na rawa tace, karka yi min haka Danliti, ina mai
    tabbatar maka xan kashe kaina idan ka juya min
    baya. (Kuji banza mtsw ). Ya cire hannunta
    daga jikinsa yace, ni ban aikeki ba ya kamata ki
    gane ki gane ba dole bane na aureki. Don me xa
    a daga min hankali akan magabata? Banda su,
    uban wa xanje na tura idan ban nema ba? Kinga
    ki tshi kije ki gaya musu na fasa. Ta marairaice
    kamar ranta xai fita ni ina sonka Danliti ba xan
    iya rabuwa da kai ba, ai dai ni xa'a daurawa
    aurenko? Xan gaya musu su kyaleka, sai ka
    shirya. Shikenan? Ya kara murtue fuska, yana
    kallonta bai tanka ba. Takara matsarsa sosai taci
    gaba da fadin, muddin suka ki yarda da uxurinka
    wlh na yi rantsuwa xasu sha mamaki dan wlh
    nan xan dawo na tare..... Ok, ki sa a daureni
    kenan? Tace wa xai daureka? Don Allah ki
    kyaleni ni bana son surutu, tashi ki tafi kawai, sai
    na nemeki! Dan..... Ya daga mata hannu, idan
    baki so raina ya baci to ki tashi kawai ki bar
    dakin nan! Ta cigaba da share hawaye, ta xura
    takalmi ta dauki mayafi ta mike xata wuce,
    amma ta kasa, tayi tsaye tana kallonsa, don
    Allah kayi hkr Danliti. Ya dago ido ya dubeta,
    hawaye keta ambaliya, yayi dan jim, kafin yace
    nayi hkr, amma kije tukunna xan nemeki. Xaka xo
    gidanmu? Eh xan xo ki share hawayen, ba wani
    abu. Ta share da sauri ta duro bayansa, Nagode
    Danliti na! To kayi dan murmushi mana ko naji
    dadi mana. (mayya ) Ya banbare hannayen ta
    ya mike tsaye, karki damu da murmushina, muje
    in rakaki, kafin tace wani abu, ya fice, dole ta
    biyo bayansa, bakin shagon kawai ya tsaya, yace
    sai nazo ko? Tace, daga nan xaka tsaya? Xan
    wuce neman wadanda xan turo din ne. Nan da
    nan sanyi ya ratsa mata xuciya, baki har kunne.
    Tace, Allah sarki nawan, to sai mun hadu anjima.
    Ya daga gira yana fadin, sai mun hadun, yana
    sakin tsaki. Tana shigowa dakinta, ta shige,
    motsinta kawai Umma ta jiyo ta biyo ta dakin,
    tana kokarin cire kaya, don shiga wanka. Umma
    ta kare mata kallo, ta kada kai, tace don girman
    Allah mama ki rinka xama a gida. Tunda Danliti
    na sonki kuma abbanki ya bashi dama ai shi xai
    biyoki. Kullum inaga ya miki babu mutunci ga 'ya
    mace ta rinka bin saurayi har makwancinsa. Ko
    bai aikata miki komai ba jama'a ba za su dube ki
    da mutunci ba. Me yasa Danlit ya sauya miki
    tarbiya.? Tayi shiru tana ciccika tana batsewa,
    Umma tacigaba ni rokonki nakeyi, ki taimakemu
    ki taimaki kanki, don mu tsira da 'yar martabar
    da tareg mana a idon jama'a. Kinji? Ta amsa da
    ka, kafin tace, Umma idan abba ya dawo ki fada
    masa ya daina matsawa Danliti akan turo
    magabatansa...... Ta katseta kamar ya? To
    umma tunda an gayama sa kuma ya amsa xai
    turo din, ba sai asa masa ido ba? Ta mako mata
    harara, bangane asa masa ido ba? Shi daman
    can bai shirya auran ba, ya hanaki sauraron
    wandan ya shirya? To baku isa ba, mu ba wasa
    mukeyi ba, tunda ya hure miki kunne dole ya
    gaugauta turowa, ya raba da mu da bakin ciki da
    muke gani, kinji nagaya miki. Tayi ta tashi tana
    fadin, to shikenan ai matsa masa ba shine xaisa
    ya turo din ba. Me kikace? Ta shige bayi da sauri
    ta rufe kofa. Mama ni kike wa rashin kunya?
    Lallai kin rika, kina gab da tsinka min mari akan
    Danliti.
    Sallamar da jiyo, shi yasa tayi shiru. Ta
    mike ta fito tana amsawa. Inna saude ce da
    Baraka, saude sannunku da xuwa. Duk suka
    amsa, yayin da Baraka ta tsugunna ta cigaba da
    gaisawa. Bayan sun nutsa a falon, inna saude
    tace, tun jiya naso fitowa, wani axababben ciwon
    kai ya addabeni. Tace ayya ina fatan yayi sauki.
    A'a da sauki, ina maman? Tana ciki ta shiga
    wanka.... Wai dama saboda ita kika zo? Ai da kin
    yi kwanciyar ki kin huta, domin al'amarin Mama
    ya zama jiki. Tace, ya xama dole in taso yaya.
    BAKIN CIKI kuwa baya taba zama jiki sai dai
    imani. Allah dai ya bamu ikon cinye jarabawar, ta
    nisa tace amin. Tace, yanxun me kuke ciki? Ta
    fada mata yadda al-amarin yake, ta cire tagumi.
    Tace haka shi yafi dacewa, in ma banda sakarci
    ba ita xata taimaka mana ya turo da wurin a huta
    ba. Tace ina fa, ai ina mai tabbatar miki tafi son
    shi akan mu. Allah dai shi kyauta. Ta amsa da
    amin. Suka ci gaba da hira har suka ji motsin
    fitowar Baraka ta tashi ta shige dakin. Ba suyi
    wata hirar kirki ba, domin ra'ayinsu yasha
    bambam yanxun. Duk mai zagin Danliti Mama
    bata ganinsa da kima haka ta fada ma baraka,
    shiyasa ta shiga taitayinta, tafito daga dakin tace
    xata ganin amare. Mama dataga shirinta can ta
    sameta dakin amaryar Ya Ali, nan suka shantake,
    sama da 2hrs sai da Inna saude ta shiryo tafiya
    tasameta can, ita ma bata yi ma Mama maganar
    komai ba akan abinda ta aikata. Domin a
    tunaninta babu wata bakuwar kalmar da xa
    agaya mata wacce bata sani ba. A wannan daren
    mama tasa ido taga xuwan Danliti shiru kakeji
    yasa ta jin haushin rashin dawowar abba. Al-
    amarin nata cizon ta taga ba xata daure ba, karfe
    goma harta goa, ta fito ta bude kofar ta fice
    abinta. Ko kafin Umma ta fito taga wanda ya
    bude kofar mama har ta kai kofar gidan, ganin
    bata a dakin ya tabbatarma da Umma ita ta fita.
    Ta nemi kujera ta xauna hannunta a kunci BAKIN
    CIKI ykamar ya kasheta. Take nan taji xuciyarta
    na ciwo, wani abu dum! Cikin kanta kamar xai
    makantar da ita, tasbihi ta shiga jerawa ko ta
    samu saukin kan. Ita kuwa mama Tunda ta
    kwashi sauri bata sausauta ba sai da taje shagon
    mutumin nata ta ja birki. Ayuba na xaune daga
    ciki, taga kanta ta shiga tare da sallama. Ya
    amsa mata ta wuce tana fadin sweetyna naciki
    ne? Da sauri ya amsa mata ai bayana nan bai
    gaya miki bane? Ta tsaya cak dauke mamaki, ina
    yaje? Ya amsa gaskiya bai gaya min ba, cewa
    yayi xaiyi tafiya kawai. Na xaci ya gaya miki
    daxun. Ta kada kai, bai gaya min ba wlh, amma
    xai dawo gobe ko? Yace watakila, ta danyi shiru
    sannan tace to shikenan sai goben. Allah ya
    kaimu. Taga kanta ta fice, ya bita da kallo. Duk
    tasuayinta ya lullbe shi, aransa yace Allah ya
    kubutar dake daga sharrin Danliti. To nima nace
    AMEEN! Da babbar murya. Tana tafe tana sakar
    xuci, wai duk fushin ne yasa Danliti yatfi ba
    sallama? Ina xansa kaina idan kalaman Abba
    suka korar min Danliti? Bata samo amsa ba taji
    ann fige mayafinta, 'yammata ji mana! Firgigi ta
    waigo hankalinta ta dubi gungun samarin da suka
    kai kusan shida, kowanne su dauke yake da tabar
    wiwi. Ta dora hannu bisa kai wayyo nashiga uku,
    duk suka fashe da dariya, ina kika nufa mu
    rakaki? Ta durkusa kuyi hkr dan Allah, dariya
    kwai suke kyakyatawa, 2 daga cikinsu suka kawo
    mata cafka. Ta xabura ta mike, Allah ya
    taimaketa ta kutsa ta cikinsu ta xura aguje, dawa
    Allah ya hada su ba da ita ba, ta watsar da
    takalma, ko daman gyalen yana hannunsu, taci
    gudun fitar rai, ta rufta cikin gida, yayin da alh.
    Adamu, ke kokarin rufe gidan, bakara min figita
    yayi ba, amma yayi axama ya maida kofar ya
    jefa sakata. Mama kuwa tuni tana sassansu, ta
    fadi warwas! Tana maida numfashi tamkar xata
    mutu, Alh. Adamu ya biyota, ya isketa daidai
    kasa, ya xura mata ido kafin yace, wai daman
    mama ce kartin Maxan nan suka biyota? Me kike
    a waje har 11pm? Umma tayo waje tana sallami,
    ganin mama a kasa yasa ta dafe kirji lfy? Ya
    dubeta ido waje, yace, yanxun saboda Allah me
    yarinyar nan take a waje cikn duhu? Kinga kartin
    da suka biyo sunyi su 10, wannan ai diban
    albarka ne da iskanci. Jiri ya soma dibar Umma
    tana fadin me? Innalillahi Wainna ilaihir raju'un
    kasan Allah, Alh. Adamu har na rufe kofa naji
    motsin fitarta, xaune nake kawai narasa inda
    xansa kaina dan BAKIN CIKI! Ban san yadda
    mama ta maida rayuwarta ba.........
    Tana rufe baki, tayi kasa da dafe kirji,
    saboda ciwon da yake tsananin yi mata. A
    hankali hawayenta ke fita tana fadin, BAKIN
    CIKIN ki zai kashe ni Mama.... Alh. Adamu ya
    daga murya yana masifa, kin shiga 3 mama! Kin
    maida kanki 'yar iska da karfi da yaji, to ki bi a
    hankali, muddin kika bari BAKIN CIKI ya kashe
    mahaifanki, kin buga babbar asara, tashi ki ba
    mutane wuri, kafin in taka ruwan cikinki. Ta
    yunkura ta tashi da kyar, amma ta kasa mikewa
    tsaye, a duddauke ta shige falo a tym din har
    mutanen gidan sun fara taruwa, don ji me ya
    faru, Alh Adamu ke daga murya cikin dare? Nan
    take ya maida yadda akayi har ya dora karya,
    wai kartin har sun turmusheta, tsawat da yayi
    masu, yasa suka gudu. Kowa tafa hannu yakeyi
    yana salati, kusan 12am suna xuba magana.
    Sannan kowa ya koma sasansu, aka bar Umma
    kwance da ciwon abubuwa barkatai. Ya ali ne
    kadai bai tanka ba, don BAKIN CIKIN sa na gaske
    ne, tamkar yadda UMMa takeji cikin xuciyarta.
    Dakin amaryarsa ya koma yana kuka da
    hawayensa. Amina tayi rarrashinsa tana nuna
    masa addu'a Mama tafi bukata ba kuka ba.
    Mts!.... Amina ba zata gane ba, BAKIN CIKIN
    dake cin angonta ba xai iya jurewa ba, tilas sai
    ya matse shi. Hasalima ba zai iya zama yana
    kallon irin wadannan abubuwan ba, gara ya koma
    bakin aiki ko ya kauracewa idanuwansa ganin
    abinda ya fi komai daga masa ciwon xuciya.
    Saboda haka yacewa amina ta shirya kayansu
    gobe zasu koma birnin gwari da yardar Allah.
    Al'amarin ya daure mata kai, kuma tayi
    tambayoyin da bata sami amsarsu ba. Washe
    gari da suke shirin tafiya, taji fashin baki na
    bakin Haj. Hajjo. Eh lallai biri yayi kama da
    mutum. Nan take kumallon mata ya taso mata,
    ya dasa mata kyamar Mama cikin ranta har tafi
    Ya ali kosawa su bar garin. 12pm kuwa ya samo
    shatan mota suka damki hanya. Mama bata ma
    san anayi ba, tana can tana murkususun ciwon
    ciki ita kadai a daki. Don ko daya shigo yin
    sallama da umma bai shiga wajenta ba. Sai
    wajen azahar barci mai nauyi gaske ya dauke ta.
    Haka ita ma Umma ke ta gyangyadin takaici bisa
    kujera. Rabonta da abincin kirki tun jiya da
    daddare motsi taji a falo ana shigowa da kaya, ta
    taso da sauri ta leko falon. Kalla ta gani da tsirin
    kwalaye ya aje gefe yana gaisheta. Ta amsa da
    fara'a ta karfin hali. Bai karasa ficewa ba, abba
    ya kawo ka falon tilas ya rabe gefe ya bashi wuri
    ya shigo, sannan ya fice. Alhajin yana fadin,
    agaida Iyali, yace xasu ji. Kallo daya yayi wa
    Umma gabansa ya fadi, ya amsa sannu da
    xuwan da tayi masa. Ya xauna falo. Yayi da ta
    shiga kitchen dauko masa ruwa ta kawo masa ta
    xauna gefe tana kara masa sannu da xuwa.
    Bayan yasha ruwa ya numfasa. Tace an dawo
    lfy? Ya amsa lfya lau, duk suna gaisheki, ni ne
    har abuja, daga can na xarce kd yau da safe.
    Tace, wai kunsha hanya, ina fatan duk lfya ka
    baro su? Yace kalau, amma sai naga kamar kin
    rame, ina fatan ba ciwo ne ya tashi ba? Ta kada
    kai. Kai dai bari Alhaji, ciwo na ba zai taba
    warkewa ba, idan ban ga yarinyar nan dakin miji
    ba. Kaci abinci tukunna, kaji abinda ya faru jiya.
    Yayi dan shiru har ta mike xata dauko abinci kafi,
    yace ki gaya min kawai Halima, nasan babu
    bacin ran da xanji wanda ya wuce na baya. Ta
    dawo ta xauna ta fede masa abinda ya faru. Ya
    kada kai. Yace ya rage nata, ba burinta ta fita
    duk tym da ta ga dama ba? Jikinta xai gaya
    mata, xata gane akwai wadanda suka fita
    iskannci. Yanxun tana ina? Tana daki, ni yau ko
    kalarta ban gani ba. Bata xo ta gaisheki ba ke
    nan? Tace ni a suwa? Bana ma bukatar
    gaisuwarta, amma tun jiyan na gaya mata idan
    na mutu, ta sani BAKIN CIKIN tane ya kasheni.
    Yace, ba xaki mutu ba Halima da Yarda Allah
    mama ba zata salwantar min da rayuwarki ba.
    Karki manta, su hudu kika haifa, kuma Allah ya
    albarkace su dubi tsibin kwalayen nan, duk
    sakonki ne, kowa na da sa nau'in tsarabar, zabi
    kalar abubuwan da kika fiso. Bayan haka, jibi
    asabar duk zasu hadu anan, don su share mana
    hawayen kukan da Mama ta samu. Don kuwa zau
    tsaya tsayin daka dole Danliti ya turo wakilnsa a
    daura masu aure a cikin satin nan. Saboda haka
    ki kwantar da hankalinki, ki na dasauran 'yal3an
    da suke bukatar ki kusa da su a koda yaushe.
    Kinji ni da kyau? Ta goge 'yar kwallan da suka
    xubo mata, tace naji alhji, Allah yayi musu
    albarka baki dayansu. Yayi murmushi yana fadin,
    amin kina iya dauko abincin yanxun. Ta tashi da
    saurinta, ta wuce, ya raka da ido tausayinta ya
    kwarara cikn ransa. Ya numfasa yace, mun gode
    maka Allah da wannan jarabci. Ta fito masa da
    abin, ya gaugauta ci, domin gab ake da kiran
    la'asar. Ya kammalawa kuwa tym yayi, ya mike
    yana fadin, ki shiga ki tasheta tayi sallah. Ta
    amsa da to, ya wuce dakinsa. Umma ta kwashe
    kayan ta maida kicin, sannan ta nufi dakin
    Mama, don tashinta. Tana kife ruf da ciki, Umma
    ta dada mata duka ta tashi a firgice. Umma ta
    xura mata ido, tace, in kin ga dama ki tashi kiyi
    sallah! Tayi waje ta bata wuri. Da kyar ta mike
    zaune, kanta ya sara mata, ta dafe shi hannu
    biyu, gaba daya miyan bakinta ya kafe. Makoshin
    ta ya bushe. Tana daga xaune, amma jiri ne ke
    dibar ta....
    Idanuwanta na ganin duhu, don haka ta
    runtse su tamau! Tana maida numfashi, ta wuce
    minti sama da goma ahaka, sannan ta iya tashi a
    daddafe ta shiga bayin. Tunaninta kawai tayi
    wanka ko tafi jin dadin jikinta. Nan da nan ta
    kwashi ruwa a bokiti ta fara wanka. Kamshin
    sabulun( Joy) Ya gauraye bayin, ba xato ba
    tsammani taji xuciyarta ta tsani kamshin, kan ka
    ce kwabo ta goce da amai. Ta kwarara mai
    isarta, wai don ma babu komi cikin nata. Tana
    gamawa ta dauki bojitin ta juye ruwan ajikinta,
    tun daga kai. Ta jefar da shi ta yayo xani ta
    daura, ta banko kofa ta dawo daki, ta bar bayin
    face face da amai. Ruf da ciki ta sake fadwa
    gado fadi take, wash! Wayyo Allah xan mutu! Tun
    daga tym din al'amura suka kwance mata, ta
    rasa kanta ta rasa meke damunta tana rashin
    son abinci da yawan tashin xuciya, ga wani cikin
    safe da jiri wani tym din jikinta yayi xafi, don
    kansa kuma ya sauka ba tare da tasha magani
    ba.
    Duk ba wannan bace babbar Matsalarta
    ba, Ina Danliti ya shiga kwana 2 babu labarinsa?
    Me kuma yake nufi da tafiyarsa? Duk da cewar
    tasan dole ya dawo, idanuwanta da xuciyarta sun
    gaza jure rashin sa na 'yan kwanakin 2. Shi yasa
    koda yaushe tana kunshe a dakin matsalolinta
    masu yawa na neman xautar da ita. Umma da
    kanta bata gane kanta ba, musamman rashin
    xuwanta neman abinda xat ci. Amma yawan
    xaman daki umma ta jingina da rashin ganin
    Danliti da ta rataywa xuciyarta, balle ayi maganar
    jingina shi da wanccan Matsalar. Ta kan kada
    kai, tace, kaico! Abincin wani, gubar wani! Allah
    ka raba mu da muguwar kaddara... A yau asabar
    ake sa ran xuwan yayyin Mamma, ga shi babu
    magana mai kwari ko kuma muce uban gayyar
    baya gari, shi da kansa abba xaune yake shiru
    dakin ta same shi, ta xauna gefensa tace, kana
    xaune baka shiga wanka ba? Yayi gajeran tsaki,
    yace maganar nan ke damuna, da yarinyar nan
    xata gane da ta amince cewar Dalinti ba xai turo
    kowa ba. Banda aikin rashin gaskiyya, menene na
    kama hanya kabar gari, kai da aka ba damar ka
    aiko a baka mallakar abinda kake so. Wane bata
    tym xakayi saboda Allah? Ta numfasa, tace
    yaushe xata fusknaci hakan yadda ta makance
    gaba daya, bata ganin kowa sai shi? Ai na gaya
    maka ko abinci bata ci, duk ta fige saboda bala'i,
    ni yaran nan ma dasu wahala suke nake
    tausayawa ba su gama warware gajiyar biki ba,
    ga aikinsa mai dan banxan wahala, da da halin da
    xa'a ce da su dakata, wlh da ance suyi xamansu.
    Ya gyara xama kyale su suzo ko hira mukayi, ai
    maji dadi, ko ba haka ba? Haka ne, Allah ya kawo
    su lfya. Amin ke ki kira min Mama ta zo yaushe,
    dan liti xai dawo? Ta mike ta nufi daki Mama ta
    tura kofa kakarin amai ya fara dibar hankalinta,
    cikin fargaba ta nufi kofar bayin ta murda ta
    bude, Mama! Tana durkushe kame da ciki, kamar
    xata mutu. Kan Umma ya kara daurewa, domin
    bata taba ganin Mama na kwarara amai haka ba.
    Ko rashin lfya takeyi, bata amai, sai dai xafin
    xaxxabi. Don haka ta nufe da sauri ta dafe ta, me
    xan gani haka Mama, baki da lfya ne ko yaya ne?
    Bata iya amsa mata ba, tana tsaye kame da
    haba, tagama kakarinta, ta kuskure baki hade da
    fuska, tayo waje abinta, ba tare da kula Umma
    ba. Bisa gado ta fada ta datse ciki tana
    numfarfashi. Umma ta biyo a fusace tasa hannu
    ta birkito ta, ba kyajin ina magana ne? Nace lfya
    kike sheka amai? Ido jajur! Cike da kwalla tace,
    cikina ke min ciwo, tun yaushe? Yau 3days. Ta
    jawo ta waje cikin haske sosai, ta kama
    hannayenta ta dudduba, sannan ta gwale
    idanuwanta, ta duba cikinsu, a tsorace ta
    tambayeta ke, kina yi al'ada kuwa? Tayi shiru
    tana xaxxare ido, baki na rawa tace, nima ban
    sani ba Umma. Ba ki sani ba? Ke xaki gaya min
    ko sai na farfasa bakinki? Ta goce da kuka, don
    ita ma ta kideme, ta mance rabonta da a'alada.
    Umma ta xura mata ido, jinin ta na kara
    hauhawa, da sauri ta wuce ta bar mama tsaye.
    Dakin abba ta koma ta xauna, ta rike kai tana
    maida salati. Me akayi? Tace alh. Magana takare
    ka dauki mama ka kaita asibiti ayi mata
    gwajegwaje! Gabansa ya fadi gwajegwaje? Name
    kuma? Na komai Alh. Ina shiga na sameta tana
    sheka amai a bayi, wai cikinta ke ciwo, amma
    alamu a bayyane sun nuna Mama juna 2
    gareta........ Tsaye ya mike tare da fadin me?
    Hawaye suka kara tsunke mata, ya koma a
    hankali ya xauna bakin sa na karanto salatin
    Manxon rahma. Gaba dayansu tsit! Sukayi
    tsawon lokaci sai Umma ke shatatar hawaye,
    baiyi aune ba kawai ya ga ta dungura ta fadi a
    sume. Ya xabura ya tarairayota, yana kiran
    Halima! Halima!! Don girman Allah karki kara min
    tsahin hankali akan wanda nake ciki, ya jawo
    goran ruwa ya xuba a hannunsa, ya yarfa mata,
    ya cigaba da shafa mata ruwan bisa fuska,
    ahankali har ta dawo hayyacinta. Ta bude ido,
    jim tana kallonsa, sannan ta sake fashewa da
    kuka, nan take tausayinta, yasa kwallan
    Ubandawaki suka fara sauka bisa kuncinsa.
    BAKIN CIKI kamar ya aika shi barxahu. Kiyi hkr,
    ki kwantar da hankalin ki Halima, wannan
    jarabawa daga Allah Ubangiji take, babu wanda
    ya isa ya kankare mana ita, bana son tsanin
    damuwar nan da kikeyi, tana jefa ni mummunan
    matsayi, ko dogara da Allah Halima shine xai
    magance mana komai. Ta goge hawayenta tayi,
    iyayinta don ta tashi xaune amma ta kasa. Yace
    kar ki damu da sai kin tashi yanxu kiyi
    kwanciyarki ki huta, bari in kwaso magungunan ki
    in duba wanda ya dace kisha. Ya mike da sauri
    wani duhu ya rufe masa idanuwansa, bai ganin
    komai face wasu miliyoyin taurari kanana, tilas
    ya dawo ya xauna ya fadin Hasbinallahu wa
    nimal wakil. Yayi ta maxa ya sake mikewa.
    Umma tace ka xauna Alhaji kar kaje ka fadi ka
    nakasa. Bai tanka ba, ya fice. Jimawa kadan ya
    dawo da kwanndon magungunan ta ya xauan
    yana bincikawa, jikinsa na rawa saboda bacin rai.
    Sallama sukayi daga falo kuma babu tantama
    muryar Ya abdurahman ce, abba Ya amsa, ya
    kara da fadin gamu nan, ku karaso ciki. Ganinsu
    jugun2, Yaya take ya rasa kuzarinsa. Yaya dai
    Abba? Jikin nata ne ya tashi? Yace shine
    abdulrahman, nan da nan ya xube gabanta, da
    dauko kanta ya dora bisa cinyoyinsa, sannu
    Umma! Sannu!
    Ta matse kwalla, ta dube shi, kaxo lfya?
    Ina safiyya? Ya amsa lfya lau take, tace in
    gaisheki. Ina amsawa, me yasa baka xo da ita
    ba? Ya goge mata kwalla, tayi nauyi ne Umma
    bata jin dadi, idan tayi doguwar tafiya, koda muka
    koma, bayan daura aure sai da tayi xaxxabi. Ta
    dan kada kai, tace Allah sarki, Allah ya raba su
    lfya. Amin. Ya amsa sannan ya dubi Abba suka
    gaisa. Kafin su kama wata maganar, muryar
    Manyan yayin ta gauraye cikin falonm. Abba ya
    gaya musu suna ciki, kowa ya shigo da kuzarinsa,
    ya ga Umma a kwance sai yayi turus! Bayan sun
    gaisa tasha magani. Abba ya kwashe abinda ke
    faruwa kaf, ya gaya musu, kowa yayi shiru,
    kawunansu sunkuye tsawon tym kafin Ya soja,
    yace, yanxun Ina Maman take? Oho inji Abba,
    gaba daya sukace oho? Ta bar gidan nne, Umma
    tace tsakar gida na barya tsaye, ban sani ba ko
    ta koma daki ko ta fice don ba sani xamuyi ba.
    Duk tym din ta so fitarta, ficewa ta takeyi.
    [12/01 21:55] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***14
    Ya soja ya dubi Ya abdulrahman, yace
    je ka kawo mana ita nan! Ya miki cikin hanxari,
    ya nufi dakinta, tana kife bisa gado aikin kuka
    kawai takeyi. Ya sa hannu ya fisgota, ba karamin
    tsoro ya bata ba, ta kwala ihu, wani BAKIN CIKI
    ya kara turnuke shi, bai san tymda yasa hannu
    ya doke bakinta ba, yace rufe mana baki
    shashasha. Da sauri ta kame baki, wanda take
    kyautata xaton hakoranta xasu iya xaxxagow
    idan bata dafe shi ba. Ahaka ya ciga da jan ta
    har dakin abba. Gaban babban ya direta, ta xube
    har tana karo da guiwarsa. Ya xuro mata ido
    kamar zasu fado kasa. Yace matsa kdaga kusa
    dani, xan iya tokarinki, ki mutu idan baki matsa
    ba. Ta janye jikinta baya, ahankali hawaye na
    ambaliya, sunfi minti 5 babu wanda tanka saboda
    takaici, kafin Ya abdulkrm yace, gaba daya kin
    rusa rayuwarki Mama kin lalata cikar asalinki da
    martabar iyayenmu. Yanxu wa ya isa ya kankare
    bakin fetin da kika shafawa kanki? Wa ai daura
    miki aure da ciki? Wa kuma xai jagoranci kisan
    kai? Wannan cikin dole ki haife shi, domin
    yunkurin xubda shi, ya fi yinsa barna da tarin
    xunubi. Kin ga tun daga nan idan kinyi tunani
    cikin hankalinki, xaki gane babu soyayysa
    tsankaninki da Danliti. Burinsa dama ya ruguxa
    rayuwarki, burinsa kuma ya cika tare da hadin
    kanki. Saboda haka dabara ta rage wa mai shiga
    rijiya, sannan karki xargi Danliti, idan ya tsallake
    auranki, gaba daya abinda yake bukata ya samu,
    abinda yai saura shine ki haife masa wannan
    ckin, in ya ga dama ya karbi dan, idan bai yarda
    ba ya kyaleki da shi, ku wulaknta. Dama wannan
    shine karshen son xuciya. Babu uwar kudi balle
    riba ga mai cinikin son xuciya. Kuma duk wanda
    ya hau motar kwadayi da son xuciya, babu
    tantama tashar kunya da nadama xata kaishi ta
    aje. A koda yaushe karshen danasani, ina fatan
    wannan xai xama darasi gareki, ki gane cewa
    abinda Babba ya hango, yaro ko ya hau gwauron
    dutse ba xai hango ba. Ya goge 'ya kwallan da
    suka xubo bisa kuncinsa sannan ya sauke
    numfashi ya dubi sauran, yace yanxun mene
    abinyi? Abba yace abinyi babu shi abdulkrm,
    tunda maganar aure ta rushe a halin yanxun. Ya
    Soja yace duk da haka, dole ya san tana dauke
    da cikinsa, bayan ta haihu xa a daura musu aure,
    su tare da yaronsu! Su karata can da abin
    kunyarsu! Ya abdul rahman ya kara sanyaya
    muryarsa mai taushi, yace wannan dole ne,
    amma abu na farko shine, ina xata xauna? Ta
    kula da kanta? Umma dai ba xata jure ganinta a
    wannan yanayin ba, ya soja ya gyara zama yace,
    gaskiya ne, kuma waje na ya kamata ta xauna,
    sai dai ba xan iya daukarta ba saboda xan iya yi
    mata dukan mutuwa yadda nake jin na tsani
    ganinya. So a cikinku, wanda yake ganin xai iya
    hkr da ita, yana iya tafiya da ita Allah ya
    shiryeta, mu kuma kullum addu'a muke mata,
    idan ta dauki wannan mtsayin darasi a gareta,
    xamu fi kowa farin ciki. Ya Abdulrahman, yace ni
    xan tafi da ita, no ka bari ni in wuce da ita
    Minna. In ji Ya abdulkrm. Abba yace ba xata biki
    ba nan da xata xauna...
    ban ce mata yin ku za su yadda ta ba
    amman yau da gobe sai Allah. gara ta zauna
    anan, domin anan ne suke aikata abin kunyar u
    kun ga ganinta da juna biyu ba zai girgiza kowa
    ba sanin cewar daman can sakamkon da zai biyo
    baya kenan. in ba wani gyaran Allah ba. saboda
    haka ku kwantar da hankalinku kuci gaba da yi
    mata addua sannan ku kwantar da hankalinku ku
    tallafa wa mahaifiyar ku ta kowace fuska don
    ganin ciwon BAKIN CIKIN bai tagayyara ta ba,
    dukkan su suka jinjina kai alaman uban dawaki
    gaskia ne. yaya soja yace da yardar Allah umma
    ba za ta tagayyara ba, idan mama bata son ki mu
    bamu da wacce ta fi ki. bamu da wani buri. da
    ya wuce mu rayu tare da ke. kar bacin ran mama
    yasa mu dakatar da dukkan farin cikin mu. mu
    ukkun nan mun ishe ki kallo ki samu sanyi a
    ranki ko umma? hawaye na suka malalo mata
    yaya abdul yayi maza ya rungumota ya na share
    mata hawayen ki daina kuka umma in kina kuka
    mama ba zata taba ganin haske ba, duk adduar
    da zamu mata tace ba komai wallahi bana
    jayayya da ikon Allah amman ku sani BAKIN
    CIKIN ba zai goge cikin raina ba, domin FARin
    ciki da bakin ciki duk halitta ce cdaga Allah fata
    na kawai Allah ya bamu ikon cinye jarabawarnan
    Allah yayi maku albarka
    Kowa ya numfasa, yace amin, abba ya
    dubi mama da hawayenta yaki yankewa yace, ina
    fatan kin ji abubuwan da 'yan uwanki suka fadi,
    idan kinyi anfani da su, ki ga daidai, idan kuma
    kin ce ba haka ba, mu babu abinda xamu iya yi,
    sai mu kyale ki, ki ci gaba da rayuwar da kika
    xaba. Ko dama kin riga kin ruguza ta, karashe ne
    kawai. Allah ya shiryeki, ki na iya bamu wuri mu
    sha iska, ki jira dawowar Danliti, amma ki sani
    auran ku ba shi yuwuwa, sai bayan kin haihu.
    Tashi ki bamu wuri. Ta kara makurewa, kukanta
    ya karu, duk suka xubo mata ido. Ya soja yace
    wa yace kiyi kuka? Cewa akayi mun gaji da
    ganinki, ki koma dakinki. Ta yunkura kamar xata
    tashi, amma ta kasa, da sauri ta rarrafa jikin Ya
    abdulrahman, ta kudundune ta rushe da kuka.
    Nan da nan ta karya masa xuciya, ko dama shi
    akwai sanyi da saurin jin tausayin mutum.
    Idanuwansa suka cika taf da kwalla, tun baya
    son kulata har ya kai hannunsa, bisa knta
    muryarsa na rawa yake fadin, imani kawai xai sa
    akalleki Mama, amma ke ba abar tausayi bace,
    tunda baki tausaywa kanki ba...... Ya soja ya
    katse shi, pls abdulrahman, fita da ita, Umma
    tace sai ma ya fita da ita? Gata kenan, ya
    kyaleta, ta tashi da kanta ta wuce. Ya tarairayo
    ta suka mike tare, ya janyo ta xuwa dakinta ya
    xaunar da ita bakin gado. Ya tsugunna gabanta
    yace, dube ni Mama. Da kyar ta dube shi,
    hawayen ta na xuba, yace kukanki bai da wani
    anfani, muddin ba nayin nadama bane. Nadamar
    ma ta gaskiyya, tsakani da Allah. Saboda haka
    ina shwaratar ki da ki kama kanki, wannan ya
    xama na farko kuma na karshe. Ba soyyaya vace
    wannan, ki dauki jikinki ki ba da ga namiji, daga
    ranar da ya sanki a waje. Wlh kin gama yawo,
    duk wulaknci da ya ga dama xaiyi miki, ko da
    kinyi sa'a ya aureki, abanxa xai rika kallonki,
    sannan wulakanci ba xai daina shi ba, a karshe ki
    ga auran ya bantale, tun ba aje koina ba. Kuskure
    ne, kin riga kin yi Mama, irin wanda bamu taba
    xato ba, babu yadda xa muyi mu gyara shi, sai
    dai kiyi tuba wajen Allah, sannan ki nemi
    afuwarsu Abba, kin jini? Ta xura masa ido,
    hawaye na ta bulbula ta kasa fadin komai, domin
    ita kanta bata san ainihin abinda ke damunta ba,
    cikin ranta agame da samun ciki ba tare da aure
    ba. Saboda haka, sake fado masa tayi, ta
    kankame shi, kukan ta kamar xai fasa xuciyarta.
    Ba karamin rikita shi tayi ba, domin nan take ya
    goce da kukan shi ma. Da kyar ya banbare ta ya
    mike da sauri ya bar dakin, ya dawo falo ya
    cigaba da gugar kwalla, xuciyarsa na masa ciwo.
    Kai! Sun dandani BAKINCIKI, da akwai yadda
    xasuyi su goge wa Mama wannan bakin fentin da
    sun goge mata shi, ko da shi xasu rasa komai
    nasu. Sai dai kash! Babu hali, shi ya sa ko abinci
    tsakurarsa sukayi suka ci, ba don yayi musu dadi
    a baki ba. Haka suka juya bayan sallar la'asar
    makare da BAKIN CIKIN da baya misaltuwa.
    Haka zalika sun bar Mama cikin wani yanayi na
    kunci rayuwa, wanda ya wanxar mata da
    cututtuka masu dama ajikinta. Kafin yamma ta
    fadi, kamar ba ita ta dawo Legos dambasheshiya
    ba. Sati 2 kenan yau babu labarin Danliti, yayin
    da rashin lfyar mama ke cigaba da yaduwa
    tamkar yadda labarin samun cikinta ya gama
    baza gari, ta bakin Hajiya Gaje. Amma don tsabar
    yaudara su suka matsawa Mazajensu su akan su
    kai ta asibiti ko ta sami dan taimakon da xai rage
    mata larurar jikinta. Da kyar abba ya amince.
    Alh. Basir ya kaita babban asibiti da garin
    Kagara. Suka ga likita, yayi gwaje gwajen sa ya
    gano, lalurar shigar ciki ne ke wahalar da ita.
    Saboda haka ya bata 'yan taimakon da xasu rage
    abubuwan da take ji a jikinta, sauka dawo gida.
    Sun wuce kofar shagon Danliti shi kuma yana
    karasowa wajen. Yayi fakin ya fito tare da yin
    daguwar mika mai isar da sakon gajiya. Ayuba ya
    fito ya tarbe shi, sai dai fuskar sa babu fara'a ko
    alama. Yaya dai mutumina? Naga kamar kana
    ciwo? Ya numfasa, amma bai tanka ba har suka
    shige shagon. Ya dube shi da kyau, yace ina
    magana ka kyaleni, lfya nace? Ya kara sauke
    numfashi. Yace ina fa lfya, magana ta cika
    gari..... Ya katseshi Mama na da ciki ko?
    Gabansa ya fadi ya saki baki yana masa kallon
    Mamaki, Dan liti ya kece da dariya, kwalla na
    gangara bisa kuncinsa kafin yace, shiege ni, dan
    buzu mai shayi. Raina kama gaiyya, ka tabani ka
    ga tsiya. Watau labari har ya bazu ko? Kaga
    burina na farko ya cika, amma har yanxun akwai
    saura, don na san dan xagin kalilan za'ayi mata.
    Ido jajur! Ayuba yace, kaji tsoron Allah Danliti, ka
    kyale yarinyar nan haka. Tunda ba xaka aureta
    ba, ka barta taji da wannan bala'in! Ai ka gama
    ruguzamata rayuwa, babu sauran wulakanci da
    yafi wannan.....
    Ya ja Kujera ya xauna, yace haka kake
    gani, nasan akwai saura, sai dai ba xan shanye
    maka dadin labarin ba, idon ka nake son ka gani
    kamar yadda ka ga wannnan. Ya bishi da kallo,
    yana kada kai. Murmushin keta Danliti yayi, ya
    sake fadin, babu wani abu mutumina, kai kanka
    kasa ramuwar gayya, tafi gayya xafi. Dadin abin
    a gabanka mama ta xageni, ta xagi Mahaifina, ka
    manta kawai! Yace wannan ba hujja bace Danliti,
    ina gaya maka barnar da kakeyi tayi yawa. Allah
    ba xai kyaleka ba. Ya ja dogon tsaki ya mike
    tsaye, kai wannan ya dameka, ni yanxun gidan
    ma xani kuma lfy lau xaka ga na dawo, see you!
    Ya juya ya daga kanta ya fice abinsa, ayuba ya
    koma a hankali, ya xauna ya dora tagumin
    mamaki da takaici. Danliti ya sake gani ya dire
    masa bakar leda tare da kwalin juice kato bisa
    kanta. Yace ga sauran kazar da na ci a mota
    nan, idan ka gama laulayin, ka ci. Ya juya ya
    wuce mota, yayi tafiya sa ya bar shi da tagumi.
    Kansa tsaye yayi fakin kofar gidan Uban dawaki,
    akwai yara gidan suna wasa, don haka bai yi
    wahalat neman yaro ba, take nan ya aika yana
    kiran Mama. Yarinyar ta shiga, jim kadan ta fito
    ta gaya masa tana xuwa. Yana nan jingine da
    mota yana kada makullai. Abba ya fito. Nan da
    nan ya tsuguna kai sunkuye, mummunin kare
    kenan. Yace, ah! Sannu abba, ina yini? Abba ya
    bishi da kallo, amma kash, ya kasa ganin bakinsa
    balle ya gaya masa bakaken maganganu. Ya
    amsa gaisuwasa, sannan yace mike ka biyoni. Ya
    wuce kofar falon bakinsa, ya murda ta bude suka
    shiga, xauna, ya nemi waje ya tankwashe
    kafafuwa. Abba ya xauna ya dube shi da kyau
    yace, yanxun saboda Allah Danliti abinda kayi, ka
    kyauta kenan? Me ya sa duk abinda xakuyi baku
    sa tsoron Allah a xukatanku? Ya xa kace kana
    son yarinya da aure, sannan ka aikata mata
    abinda ba shine ba? Danliti ya kara sunkuyar da
    kai, kamar xai tsaga kafet din falon ya shige don
    gulma, abba ya ciga da cewa, to ta faru takare,
    ahalin Yanuxn Mama juna 2 gareta, kaga xancen
    auranku ya rushe kenan dole tayi zaman istibra'i
    xuwa tym da xata haihu. Wannan abu ya bani
    kunya kuma kun xubar min da mutunci da kima a
    garin nan. Hannaye 2 Danliti ysa ya rufe fuskarsa
    yayi xugum, ko mtsi ba yayi. Abba ya numfasa
    ya kada kai ya cigaba, ni bani da abinda da xan
    iyayi, tunda kaddara ta riga fata, abinda kawai
    nake soka sni, shari'a ce ta tsara haka, saboda
    haka dole ku kauracewa juna, don gudun karku
    kara maida hannun agogo baya. Ina fatan kaji?
    Sai ka koma jira ranar da xata haifamaka danka,
    kaga kun sami dan aike, ba sai kun nema ba.
    Kana iya tfiya, mu jira abinda Allah xaiyi.
    Shawara da xan baka kawai, ka nemi tuba wajen
    Allah, domin ka saba masa, ka keta rigar
    mutuncin yarainya. Shiru yayi ya kasa tashi, abba
    yace tashi mana, ni nakare magana, ya dago kai
    da kyar, amma bai kalli fuskar abba ba, cikin
    sanyin murya yace, abba kayi hkr ka yafe min?
    Wlh sharrin shaidan ne. Ya goge kwalla, abba na
    kallonsa kafin yace, haka ne, amma wani tym har
    da son xuciya. Si yasa nace ka nemi tuba wajen
    Allah, don ta ni mai sauki ne. Ya kara
    rankwafawa yace, je ka kawai. Ya tashi simi simi
    ya fice babu ko waige. Abba ya raka shi da ido,
    sannan ya numfasa ya kada kai, yace Allah ya
    shirya mana. Shi kuwa Danliti yana fita yayiwata
    'yar girgiza ta jin dadi, ya wuce motarsa cike da
    farin ciki ya koma shagonsa. Ledar kazar da ya
    ajewa ayuba suna nan bisa kantar bai taba ba.
    Wai don ya ba ayuba haushi sai ya dage kantar
    kayan suka watse kasa. Ayuba ya bishi da kallon
    kafin ya ce ni baka ban haushi ba don ka xubar
    kudinka ne, ba nwa ba, gaskiyya ce dai ba xan
    daina gaya maka ba, watakila ma baiji shi ba,
    domin bai tsaya ya saurare shi ba, cikin daki ya
    shigr. Yayi kwance yana tunanin shirinsa na gaba
    akan mama. Abba kuwa ys jima falon xaune yana
    tunani rayuwa kawai. Sannan ya mike da kyar ya
    koma cikin gida, ya maida wa Umma yadda
    sukayi da Danliti ta kada kai tace , shikenan,
    Allah yasa ta nutsu ta xauna gidan. Yace amin,
    amma ina mai tabbatar miki muddin tace ba xata
    nutsu cikin gida ba, xan bata mamaki, domin,
    dole ta xaba ko mu ko shi. Umma tace gaskiyya
    ne, ace wannan abu ya sameka, baka yi nadama,
    ai kuwa sai a sallama mutum asa masa ido. Allah
    yasa mu dace. Ya amsa da amin. Tunanin uwar
    gayyar ba anan yake ba, domin kuwa jin ga
    Danliti yana kiranta, ya tabbatar mata da cewar
    ya dawo kuma taso ta ganshi, su Abba suka taka
    mata birki. Duk da haka taji karfi a jikinta kwarai
    da gaske, har wasu daga cikin cuttuttukan da ke
    damunta suka yaye nan take. Sai dai tana ganin
    babu adalci a hukuncin dasu abba suka yanke. A
    zaton su zan iya zama tsahon tym banga
    masoyina ba????????
    Ta tabe baki tana daga kwancw tace,
    ba xan iya ba gaskiyya, sai dai suyi hkr wlh. Ai
    dai maga juna, ya san halin da nake ciki, ya
    tausaya min. Ta goge kwalla ta cigaba da sakar
    xuci. Ana ta sallar magriba, tym ne da ita mama
    ta sami damar satar jiki ta sulale ta isa shagon
    danliti. Shi kuma kaida ke xaune cikin shagon.
    Ayuba ya shiga sallah. Yana ganinta ya dafe kirji
    ya wani lumshe ido. Yace wayyo Allah na gode
    maka! Ta daga kanta ta shiga, ta nemi t barma
    ta zauna, saboda bata jure tsayuwa. Tana xama
    ta hade kai da guiwa ta fasa kuka ya kare mata
    kallo, a dage yana dan murmushi, sannan ya taso
    ya dawo gunta yace haba bebina! Meye abin
    kuka? Ya xauna gefenta ya rungumota jikinsa,
    bana son kukan hakan nan....... Ta cira kai da
    sauri ta dube shi, ba xanyi kuka ba? Ciki fah
    gareni, kowa ya tsaneni ana ta zagina. Shine
    xaka ce ba xanyi kuka ba? Yayi dan murmushi
    yace, bebi kenan, to don kowa ya tsaneki shine
    me? Bayanni ina son ki kuma ina son ciki na!
    Kina so yi kukan ne, wata kila kuma na dadi ne
    yayi miki yawa. Ta mako masa harara tace, jin
    dadi? A zageni, a tsaneni shine jin dadi? Son ka
    ne kawai yake sawa bana damuwa, amma kai ina
    ganin abin baya damunka, daya dame ka, da
    baka wanke kafarka ka bar garin ba, tsawon sati
    2, alhalin an ce ka turo a daura mana aure. Da ka
    maida hankali ka turo din, ai da duk hakan bata
    kasance ba, koda cikin xai bayyana adakinka xai
    fito. Tunda ni ban ma taba nuna wa akwai wani
    abu tskanin mu ba. Sannann.... Ya da ka mata
    tsawa, ya ida don Allah! Haba! Wannan maida
    xancen na menene? Ko kuwa turo ki akayi ki zo
    ki batan rai? Ko dan kinga ina ta rarrashinki?
    Babu fah dole, kin ganne? Abban ki cewa yayi ba
    dole bane ya bani ke, ko bayan kin haihu. So pls
    ki daina damu na da irin wadannnan surutun
    banxan, ban son jinsu, idan har kin son mu
    shirya! Kin gane? Ta xura masa ido hawaye na
    xuba, ta ma rasa me zata ce? Ayuba yayo
    sallama ya shigo ya riske su cikin wannan halin.
    Shi ma yayi tsaye yana kallon su, jim kadan
    Danliti ya buga tsaki ya tashi ya shige daki ta
    goge hawayen itama ta tashi ta bishi, ayuba yaa
    kada kai ya ja kujera ya xauna yana fadin Allah
    ya kwaci yarinyar nan. Tana shiga ido ya xubo
    mata. Yace au biyo ni kikayi? To ranki xai baci
    kuwa, gara ki koma. Ta marairaice tace, kayi hrk
    Danliti, ba don ranka ya baci bane ya sa na gaya
    maka abinda ke damuna. A xatona xaka tausaya
    min a halin da nake ciki. Bani da wani gata wajen
    iyayena. Tun ranar da na nuna kainake so Danliti,
    ka tausaya min. Yayi lum da ido ya bude, ya
    cigaba da kallonta tana tsiyayar hawaye kusan
    3mins sannnan ya yafito ta da hannu, yace xo
    nan! Da sauri ta isa gunsa, ta fada jikinsa ta kara
    fashe da kuka. A'a, kinga ni fa kukan ne bana so.
    Yanxu menene damuwarki? Ta goge hawaye,
    tace kullum in rinka samun kulawarka, hakan shi
    xai tabbatar min da kana sona kana son abinda
    ke cikina. Yayi dan murmushin nan nasa, ya kara
    janyo ta jikinsa, yace, kin samu bebi, karewa ma
    da kewarki na dawo. Kin ci abinci? Ta kada kai,
    saboda me? Bana iyawa ne, jikina gaba daya ya
    canza, sai amai kamar xai kasheni. Yace ayya
    sorry ko? Amma duk da haka ba za a rasa abinda
    kike sha-awa ba, gaya min in nemo shi, na kosa
    in kore kishirwata. Ta mako masa harara, ya
    kyalkyale da dariya, meye na harara ta? Ko ke
    ma xaki min BAKIN CIKI ne, irin na 'yan sa ido?
    Masu shiga tsakanin masoya suna son suga
    bayansu. Haushi su nake ji wlh. Tace ai ko ni din
    ma haushin su nake ji, ah haba? Wlh kaji na
    rantse. Ya cacume ta tana dariya tana fadin, ban
    da lfya Danliti, bai saurare ta balle ya tuna ya
    nemo mata abinda take son ci. Karfe 8 ya fito ya
    barta can kwance tana murkukusun ciwon ciki,
    ya wuce waje wani mai suyan nama, ya karbi
    danyan naman da yasa ya aje masa. Ya dawo ya
    bade shi da magani, ya maida cikin leda ya
    nade. Yana xaune bakin shgo bisa benci, yana
    tunanin tafiya yayi wanka ko ya samu yayi
    sallah. Mama ta fito tana yafa mayafinta, ya bita
    da kallo yana murmushin keta, ya cikin? Tace
    yayi sauki ni xan koma gida sai gobe. Haba haka
    da wuri? Yanxun fa 8 ta wuce? Kar a neme ni ne.
    Wa xai neme ki? Don Allah xaumna muyi hira, ba
    wanda xai nemeki, bayan sun san kina nan. Bata
    da xabi, don haka ta xauna kusa dashi, ya shiga
    bata labaran banxa. Jimawa kadan wani kare ya
    xo gilmawa nan take ya hau kiransa, tace me
    xakayi da kare kake kiransa. Kasan karen
    okundiri fada gareshi ko?
    Yace bai sami nama bane don ubansa
    okundiiri, ya kece da dariya, okundirin ne ubansa?
    Lallai ka samo shi. Yacee to da waye ubansa?
    Kinga bude ledar nan nama aciki dauko ki ba shi.
    Yana magana yana shafar kan karen. Tace, taf
    ya cafke min hannu? Kai dai ka bashi kai da ka
    siyo masa,don raka asara. Yace karki bani kunya
    mana, me xai sa ya cije ki, bayan yasan ke
    bebina ce, ko kare? Ai ka santa ko? Sweetheart
    dina ce kar ka cije min ita. Tuni kanta ya fasu,
    ya jawo leda ya bude ta dauko katon yanka ta
    mika masa tana fadin, abin har da yaji? Sangarta!
    Ya kwashe da dariya, yace ina ruwanki? Ke dai
    mika masa gudan. Ta dauko ta mika masa, ya
    cafke, Dan liti ya runtse ido yace yes! Ya xarce
    da dairya. Ta xuba masa ido tace, menene abin
    dariya har da wani cije labe? Yace ji nayi kamar
    ya hade da hannunki ya gartse. Takai masa bugu
    a kirji tace amma kai mugu ne! Yace sosai ma
    ashe baki sani ba yarinya, to tashi kije gida an
    gama hirar, kinga karen yayi tafiyarsa. Ka gaida
    okundiri kaji? Ta ci da kyakyata dariya. Yace, ah!
    Tashi karki sa yarona ya fito yana fito yana
    kyakyatawa kamar dolo. Ta shi kije gida sai safe.
    Don Allah kiyi hkr, so nake nayi wanka inyi
    sallah. Ta fido lah nima har ka tuna min banyi ko
    magriba ba. Ta juya da sauri tana cewa, sai da
    safe! Yace Allah ya kaimu. Ya bita da kallo, yace
    yarinya kin gama yawo kin shiga 3 kin lalace, ya
    daga murya ki fa sami abinci ki ci. Ta juyo ta
    amsa, kar ka damu xanci. Suka ja hankalin
    mutane, don haka yama didi ya biyo baya, masu
    tsinuwa nayi, masu addu'ae shiriya nayi. A tsakar
    gida ta iske su Abba na jiran dawowar ta, shi da
    su Alh. Basiru. Tana shigowa tasha jinin jikinta,
    ta shiga bin bango, tana so ta shige falo. Alh.
    Basiru ya daka mata tsawa, ke dawo nan! Simi
    simi ta matso gun su ta durkusa guiwa 2, batayi
    aune ba, taji saukar wani wawan mari. Gaba
    daya ya ratsa kanta, ya gigita ta, ta dunkule ta
    fasa kuka. A cikin ba tace ga wanda ya xabga
    mata wannan marin mai tsanannin xafi ba. Sai
    dai taji muryar Abba na fadin wannan shine
    gargadi na karshe da xanyi miki, shi ya sa na
    tara kowa su xama shaida! Idan har ba xaki bi
    umarni na, ki xauna a gida ba, to wlh sai dai ki
    xaba, ko mu ko Danliti! BAKIN CIKIn nan ya ishe
    mu mama. Gara in sallama ki, in tabbatar da kinfi
    karfina xaman kanki kikeyi. Saboda haka daga
    yau kika kara sa kafarki kika fita kikaje gun yaron
    nan, to kar ki dawo, ki yi zaman ki can wajensa
    ku sha shagalinku yadda kuke so. Duniya ce
    Mama, mai dauke da axuxuwa babu adadi! Ina
    fatan kinji kuma kowa ya shaida! Alh. Basir ya
    karbe karuwa kike so ki xama ko? To Allah ya
    baki sa'a, mu dai ba xa mu hana shi ba, duk
    ranar da koreki. Alh. Adamu yace dama saboda
    me xamu hana shi? Cikin shege ne fah ajikinki,
    amma bai sa kinyi nadama ba, to me xai sanya ki
    kuwa? Karkiji da wai, mun tsame hannun a kanki,
    haka xuri'ar gidan nan kaf! Kar ki ce kin san daya
    daga cikinsu, duk ranar da wuya ta koro ki! Ta
    shi ki bace mana da gani shashasha sakarya. Ta
    mike da gudu ta fada dakinta, ta dasa kukanta, a
    fusace abba ya bar wajen kowa ya kama
    gabanmsa, suka cigaba da yada xancan a sasan
    su. Daren nan su ma Umma basuyi barci ba,
    musamman Umma da tabbatar wa kanta ciwon
    xuciya ya kamata. Da safe ta atashi xuru-xuru
    baki daya idanuwanta sun xurma, shi kansa Abba
    ya rame ta maxa kawai yakeyi yana wa Umma
    fada kar ta salwantar da rayuwarta akan Mama.
    Ita Mama ba wannan ta aje ranta ba, kawau
    burinta kasance tare da Danliti, don haka take
    ganin kowa ya tsangwame ta saboda kiyayya.
    Kafin safiya ma ta mance duk kalaman su Abba
    da kawunninta. Allah Allah takyi ta sami saukin
    laulayin safe dake damunta ta lababa taje ta
    gano Danlitin ta. Xuwa 12noon ta iya shiga kicin,
    ta dan tsiyayi ruwan lipton, ta dawo ta shanye.
    Xufa ta keto mata, danji dadi ajikinta, kana ta
    shiga bayi tayi wanka da sabulun wanki maras
    kamshi. Ta kimtsa, tsaf, duk da tayi haske sosai,
    ta kuma rame kwarai, kana iya gane kyanta na
    asali mai daukar hankali. Ta koma ta kwanta
    yana kllon agogo 1:00 ta tashi tayo alwala tayi
    sallah, ta dauko gyalemnta ta xura takalma ta
    leko falo bataji motsin kowa ba, ta kwahi sauri ta
    fice abinta. Yara suna ce mata sai kin dawo
    aunty Mama! Jin haka yasa Umma yanke sallah,
    ta fito da sauri ta tambayi yaran ina maman?
    Sukace yanxun ta fita. Tabi xauran, yaran suka
    biyota ta tura su tace, ku kira min ita. Yara suka
    fice da gudu suna kwala mata kira, Aunty Mama,
    ki zo Umma na kira! Haka suke ta gudu suna fadi
    har suka isketa, ta dube su tace, sai na ci
    ubanku in kuna kwala min kira haka! Ni sa'ar
    kuce don Ubanku? Ku tafi ku ban wuri kafin in
    fallawa yaro mari! Mts..... Taja tsaki, ta wuce
    abinta, yara suka dawo a guje suka iske Umma a
    xaure sukace, wai sai ta ci ubanmu idan muka
    sake kiranta! Ta dafe kirji tace, ta kyauta, kuje
    wasan ku. Ta dawo cikin gida a salube tare da
    mamakin taurin kai irin na Mama, me take nufi
    kenan? Ta xauna a falo tana juyayi. Da kyar ta
    sake mikewa ta shiga dakin Abba, ta tashe shi
    barcin ramakon da yakeyi. Ya farka yana
    kallonta......
    Yace, azahar tayi ko? Tace tayi alhaji.
    Ya yankura ya tashi yace menene na ganki a
    salube? Tace tasake fita, wa? Mama mana. Cike
    da mamaki yace ta fita? Yanxun nan kuwa,
    kamar fako na takeyi, har yaran nasa su kirata,
    ta dinga kunduma musu xagi, taki dawowa. Ita
    Maman ta zage su? Tayi murmushin takaici, tace
    kana mamaki ne? Bai kamata kayi ba alhji. Ta
    kuwa tafi kenan, kinsa Allah ba zata dawo ckin
    gidan nan ba. Kiyi hkr, duk abinda ke ranki na so
    da kaunar Mama, ki cire ki dangana da ita, nima
    na hkr da ita. Umma ta fasa kuka, ta tashi da
    asauri ta bar dakin. Hankalin Abba ya kara tashi,
    ya taso ya biyota dakinta, tana xaune bakin gado
    kukan kawai takeyi. Ya tsaya kanta, yace saboda
    Allah ya kike so nayi Halima? Ta cira kai murya
    na rawa. Tace har ga Allah ba korar Mama ke
    sanya ni kuka ba, tausayin rayuwarta ke bani,
    yadda ta ka sa gane cewar mu ba tsangwamarta
    mukeyi ba, saboda tana son Danliti. Yanxun
    shikenan ba xata gane cewar alabarkar mu itace
    kwanciyar hankalinta ba, duk tsananin son da
    Danliti ke mata, shikenan ta xabi cigaba da
    xaman shashanci akan ta nutsu, dn tym kankani
    a daura masu aure? Wannan rayuawar tana cike
    da tausayi da ban Mamaki, kamar Ya asirce
    Mama? Ta kada kai ta ciga, ba haka Mamar mu
    take ba alhji, ta sauya saboda soyayya, kenan ta
    fi son shi a kanmu? Ina xan samo amsoshin nan
    Alhji? Ina xan..... Ya rufe bakin da sauri, ya ace
    ya isa haka! Kar ki jefa kanki damuwar da xata
    tada miki ciwo, ki kauda kanki ki akan komai,
    sannan ki nisanta xuciyarki ga irin wadannan
    tambayoyin da kike wa kanki. Xaki xautu saboda
    yarinyar da bata damu da lfyarki ba, xamani ne
    Allah ya kawo mu da yara ke rufe idanuwan su
    akan abinda suke so. Suyi ta fada da iyeyensu
    har xuciyoyin iyayen su fara xargin asirce su
    akayi. Xan ji dadi da farin ciki idan xa'a ce, duk
    wannan abubuwan da suke faruwa, ki dauke shi
    amatsayin mafarki mai wucewa, tamkar baki
    taba haihuwar wata mai suna sakeena ba. Ta
    dube shi xai yuwu ko? Mai hana? Idan har zaki
    dage da adduoi, ubangiji ba xai barki haka ba, ta
    goge hawayenta ta sauke gwauran numfashi
    tace, xan yi iya kokarina Alhji. Ya jinjina kai.
    Yace haka nafiso sadiya, kin san ina jin dadin
    xama dake, kuma tun ina saurayi ban taba son
    wat 'ya mace ba sai ke. Ban fatan abinda xai
    salwantar min da rayuwarki, ya kasance wata
    kaddara tasa kin fara barina cikin duniyar nan.
    Kullum nayi sallah, sai na roki Allah ya fara
    daukar raina saboda ba xan iya ganin gawarki ba
    halima. Idanuwanta suka kara tara hawaye. Tace
    ka daina fadar maganar nan Alhji..... Ya katse ta,
    ni ma ba ason raina na fadi ba, domin sirri nane
    wanda nake xaton shi kdai ne ban taba gaya miki
    ba, sai yau, dole ce ta sanyani, don ina son ki
    sami nutsuwa sadiya. Ta matse ido kwallatana
    suka kwararo ya mika hannu ya goge mata yace,
    sha kurkuminki Maman abdul 3, gwarazan
    samarin nan masu takama da baiwar Allah. Ta
    numfasa tace, Allah yayi masu albarka baki
    dayansu. Kina nufin har da sakeena ko? Ta amsa
    da kai, kafin tace, ai mu na mata fatan shiriya
    ko? Yace haka ne, toh Allah ya shiryta. Amin ta
    amsa. Haka yayi ta rarrashinta, ta samu
    nutsuwa, sannan sukayi sallah suma mika kukan
    su ga Allah. Na san kilan kuyi musu ko mamaki
    idan nagaya muku Mama bata dawo gida ba, sai
    bayan sallar magriba. Abu na farko da ta fara cin
    karo da shi a kofar sasansu dake kulle, shine
    akwatin kayanta. Taja cak! Ta tsya ta xura masa
    ido tsawon tym, kana ta matsa ta tura kofar taji
    ga,! A kulle. Ta tabe baki tare da jan tsaki, ta figi
    akwatin ta juya tana fadin a ranta, sai aga na
    kwana a titi. Kai tsaye Danliti ta dosa, yana
    xaune kofar shagonsa, inda ta basa. Yana
    hangota da akwati, ya mike ya shige daga ciki
    yana gayawa Ayuba ga mutuniyar can tafe da
    akwati, ko maganarta tace ta tabbata? Ayuba ya
    murtuke fuska yace ni xaka tambaya? Au haushi
    kaji? Amma dai kana ji na gaya mata kar ta
    kuskura ta bari su koreta, don bani da wurin
    ajeta, ko ban gaya mata ba? Yace oho! Wai kai
    wani irin banxa ne? Yace Ni banxa bane, ai rainin
    wayau yasa ka gaya mata hakan. Wa ke jan
    ragamar rayuawarta, in ba kai ba? Ai sanin bata
    da xabi shi yasa ka raina mata hankali. To ya isa
    malam, sai gata tsaye gaban kanta, tana kokarin
    dagawa, duk suka xubo mata ido, ta karasa
    shigowa, ido waje ya dubi shirgegen akwatin, ya
    ce ya dai? Bata saurare shi ba, kofar dakin ta
    tasarmawa xata shige. Yayi azama ya shawo
    gabanta, magana fa nake yi, kona kokarin
    shigewa kamar gidanku? Ta xubo masa ido a
    marairaice tace, me na gaya maka? Ni kuma me
    na gaya miki? To yaya xanyi? Ina komawa na
    iske akwatina akofar gida sun kulle gidansu. Ya
    gayara tsayuwa, da yake kuma ke sakarya ce sai
    kaka kamo hanya kika taho baki tsaya kika nemi
    sulhu ba! Yanxun menene nufinki? Anan xaki
    xauna? Cikin shago? Lallai kin cika dakikiya,
    Jaka! Kuka sosai ya kwace mata, ta tsugunna ta
    rungumi kafafwansa, murya na rawa tana fadin,
    karkayi min Haka Danliti! Saboda kai suka koreni,
    ina kake so naje, idan ba nan ba?
    [12/01 21:58] ‪+234 818 701 7363‬: BAKIN CIKI 2***15
    Ayuba ya daga kanta, ya fice
    hankalinsa tashe, shi kuwa ko gezau beji ba
    ajikinsa, a dage yake kallonta, tsawan tym
    sannan ya fizge kafarsa ya kama hanya xai fita,
    da sauri ta mike ta cukuikuyo rigarsa, fadi take,
    kayi hrk don girman Allah. Wasu samari 2 suka
    iso wajen siyen taba sigari, ai sai suka buge da
    shari'a, kaya-kaya hayaniya har waje Danliti na
    daga murya shi ba xai aje ta cikin shagonwa ba,
    ta koma ta nemi sulhu da iayeynta. Kan ka ce
    kwabo jama'a sun cika makil a gun. Kai Mama ta
    sha zagi da la'anta, Allah shi kara kwando-
    kwando. Kalilan ke cewa Allah ya shiryeta, Dan
    liti ya gacciye banci kofar shagoin ya xauna yace
    yaga uban da ya tsaya mata agarin nan, wnada
    xai sashi ya ajeta. Baiwar Allah kuwa na tsugene
    gaban akwatinta, tana ruasar kuka har karfe
    10pm. 'yan ganin kwakwaf suka gaji suka koma
    gidajen su dauke da labari mai ban al'ajabi. Wasu
    suna ganin bai kamata Uban dawaki ya koreta ba
    a matsayin sa na Uba, kuma babban mutum mai
    sarauta, wasu kuwa suna ganin hakan shine
    daidai, imna xai sa BAKIN CIKI? Idan bai sallame
    ta ba, tunda ta tara masa, ya cika masa xuciya,
    tana neman fashewa ta hallakashi? Ai gara da ya
    sallamata duniya ta koya mata hankali. Ga darasi
    na farko nan ta fara gani, duk iskancin Danlitim
    yace baxai aje taba. Alhalin saboda shi aka
    koreta. Wannnan ya nuna a fili ita ta nace masa
    kamar sauran 'yan mata marasa xuciya. Mutane
    na mamaki abinda Danliti yake da shi wanda
    yake tsonewa 'yan Mata ido. Su mutu cikin
    soyayyar sa. In bata ga kyau me yake da shi? Shi
    babu hali babu kwakkwaran asali. Amma duk
    wacce ta fada tarkonsa sai gagari iyayenta. Ko
    don kudi da ya ke kashe mus ne? Shiya sa suka
    dauki laifi kacokan suka dorawa 'yan Matan masu
    biye masa don kwadayi da kyalekyalen jikinsa.
    Wayyi, kai bai san dawan garin ba, dai bai yi
    tunanin kutsa kansa ciki ba. Tun ciki dare surutai
    kala-kala suka fara baza gari. Shi kuwa gogan da
    ya ga kowa ya watse sai ya matso ya xunguri
    Mama da kafa, ta dago kai da sauri ta dube shi,
    matso mana nan kiji, ta matsa gareshi, tana
    hawaye. Ya dubeta da kyau yace, ke banxa ce
    wlh, shi ya sa kika bani haushi. Nace ba xaki
    xauna anan ba. In banda hauka irin naki, ya
    xa'ayi ki xauna tare da mu cikin shago? To ina
    sane da abinda nakeyi, kin gane? Saboda haka ki
    koma ki nemi wani wurin ki xauna, ki bani nan da
    sati xan san abinyi. Murya dushe tace, ni bansan
    inda xani ba, a'a ko gidan 'yanwanku ba xaki je
    ba? Ko baku da su ne? Sai dai inje gidan su
    Baraka, yace ko gidan su Mubarak xaki, sai kinm
    dawo matsalar kice. Amma ba xaki kwana
    shagon nan ba. Yauwa, tashi ki sungumi
    akwatinki, ki wace kar su kulle gidansu. Tace to
    nagode, sai da safe, Allah ya kaimu 'ya bebine.
    Muyi fada mu shirya ko? Kar ki damu xan ganki
    goben. Tayi murmushi, dadi ya rufeta, ta mike
    tana kara masa godiya, taja akwatinta ta nufi
    gidansu Baraka. Ya mike janye da benci yana
    kyalkyala dariya, ya shige shago. Kai mugu dan
    gidan buzu mai shayi! Yayi wa kansa kirari ya
    shige daki. Ayuba na kallonsa yana kada kai.
    Gidan su Bara akulle yake, saboda sha dayan
    dare tayi ma. Ta shiga bugawa har aka xo aka
    bude mahaifin Baraka ke tsaye cikin xauran, ya
    dubeta da kyau yace, Mama ce? Daga ina haka?
    Ta fara kuka yace shigo shigo ciki! Ta wuce da
    uban akwati ya maida kofa ya rufe. Tana gaba
    yana biye da ita yana fadin, subhanalillahi! Dakin
    Inna saude suka shiga tana tsaye tsakar daki,
    lfya? Ta xube sharaf! Cikin kuka tace, abba ne ya
    koreni..... Ina saude ta nemi waje ta xauna, yayin
    da malam kasim ke fadin, me ya sa Uban dawaki
    xaiyi hak? Inna saude tace BAKIN CIKIN ta ne ya
    ishesu. Ace kamar Mama ta gagari kowa duk
    abinda ya sameta da abinda ake gaya mata ba
    su isheta nadama ba, idan ba su koreta ba me
    kike so suyi miki? Ba shashanci kike sha'awar yi
    ba? To sun baki hanya, meye kuma na kuka?
    Mal. Kasim yace hakan ba hujja bace, duk abinda
    xatayi, gara tana gabansu suna tsawata mata,
    yau da gobe ana hada mata da addu'a, sai Allah
    ya taimaketa ta gane illar abinda take aikatawa.
    Saboda haka ta xauna, gobe Allah ya kaimu lfya,
    xanje in ganshi. Ke kuma je ki kwanta kiyi tunani,
    meye amfanin lalata rayuwarki da kikeyi? Har
    jikokinki sai an yi musu gori, wannnan abinda
    kika aikata! Kina da babban laifi mama, sai kin
    tuba kin bi Allah kin bi iyayenki sannnan xaki ga
    daidai a rayuwarki, kinji ni? Ta amsa da kai, yace
    ta shi ki shiga wajen 'yar uwarji kafin Allah ya
    kaimu goben. Ta mike simi-simi ta ja akwatinta,
    inna saude ta xuba mata ido tana mamakinta. Ta
    kada kai, taca baka ce xata aikata ba, yarinya
    kyakkyawa, ta lalata rayuwarta. Allah ya shirya
    mana, yace amin albarkar annabi. Atsakar gida
    taga Baraka tsaye tana share hwaye, ta matso ta
    kama mata akwatin suka shiga dakin, kowacce ta
    nemi wuri ta xauna bakin katifa. Baraka ta
    dubeta.........
    Tace anya mama abubuwa da kike yi
    kanki kalau? Ke bakijin kinya? Baki tunanin gaba
    daya idanuwan garin nan sun dawo bisa kanki?
    Baki da martaba da darajar Abba agarin nan?
    Haba Mama, kamar ba tare muka taso ba?
    Tarbiyarmu iri daya, nutsuwa da kamun kai, kowa
    na yabon mu. Mutane na rububin mu, da son
    hada xuri'a tagari. Ta daga kai sama, idanuwa
    cike da hawaye ta cigaba, Allah ya isa
    tsakaninmu da Danliti! Ta dube ta sukayi ma juna
    xuru kafin Mama tace kar ki sake xagin Danliti
    Baraka, alhakin sa xai kamaki, laifin mune? Tun
    tym din da mukace muna son juna, ya kamata su
    Abba su rungume mu hannu 2 amma suka ki,
    suka gwammace in kwashe kayana in bishi. A
    tunanin ki wane sakamako ya kamata su gani?
    Bayan wannan dake jikina? Baki sake take
    kallonta, kafin tace, maganar Banza ce, idan duka
    jina kunnuwa ne xai taba sauraronki ba, wa kika
    burge don kin aikiata wannnan sakarcin? Shi
    kansa Danlitin adage yke kallonki. Kin dawo an yi
    miki afuwa, cikin nman ya bayyana, duk sun hkr,
    sun shanye, amma ki ntsu xuwa tym din da xaki
    haihu, a daura maki aure, kar fa ki manta xaman
    nan naki agida ibadane tunda Allah ya shifida
    hakan, sai ki ga dalilin xaman, duk xunubunku
    sun kankare, auran ku yayi karko tare da xuria
    masu albarka. Ki kwanta kiyi tunani mama, ko
    asiri Dan liti yayi miki, xakewar taki tayi yawa. Ta
    sualala kafita ta kwanta, tace, na kwanta shekiya
    Baraka, sai da safe ko? Ta bita da kallo ta
    numfasa, tace Allah ya sa ki gane. Amin, ta
    amsa da gatse ta juya baya abinta. Baraka ta
    mike ta rufe daki ta dawo ta kwnta. Ta jima bata
    sami barci ba, saboda juyayin halin da 'yar
    uwarta ta shiga. Da farar safiya M.kasim ya usa
    gidan Ubban dawaki yasa aka yi masa sallama da
    shi, jin cewa shine ke sallam ya sa yace ya shigo
    cikin gida. Bayan su gaisa. Umma ta fito suka
    gaisa. Sannan ya maida jawabinsa, a karshe
    yace, alhaji kar bacin rai yasa ka yanke wannan
    hukunci, ni ina ganin gara yarinyar nan ta xauna
    agaban ku, kuna tsawata mata, sai Allah ya
    taimakemu ya shiryar da ita. Don girman Allah ka
    yafe mata dawo gida, tunda tayi tunani taxo
    wajenmu, ta kawo mana kukanta. Abba ya gyara
    xama yace, a tunanin ka a kashin kanta, ta yanke
    shawara taje wajen ku? To ba haka xancen yake
    ba, kila ba xaka sani ba ne, saboda kuan cikin
    lungu. Amma ni tun jiya na sami labarin
    wulakancin da yaron nan yayi mata, ya tara mata
    jama'a, ya tozarta ta, ya kuma ce ba xata xauna
    masa a shago ba, kaji dalilin nemanku, amma ba
    nadama tayi ba. Yace, duk da haka ina son ka
    duba girman da martabar ka agarin nan. Kayi hkri
    ka amshi rokona, ba don ni ba, sai don girman
    Allah da darajar iyaye. Ya sunkuar da kai yana
    kadawa, kafin yace, M.kasim ban ki ta taka ba,
    amma ba xan iya xama da yarinyar da ban isa in
    bata umarni ta bi ba. Ta fita tayo shashancinta,
    ta dawo min gida ta wanke najasa ta kwanta.
    Mts! Ban jin idanuwana xa su iya jure gainin
    wannan kaxanta. Gara ta tafu su cikashe. Wlh na
    hkr da ita, kuma ina rokon Allah ya sanya mana
    dangani nida Mahaifiyarta, ba kuma xamu gaza
    ba wajen yi mata addu-ar shiriya. Watakila wata
    rana taga uwar bari, ta dawo da kanta ta neme
    mu. Kaga a tym din xan tabbatar da tayi nadama.
    M. Kasim yayi shiru, jawabin Uban dawaki na
    cike da tausayi, ya numfasa, yace, na yarda da
    kai Alh. Sai dai har yanxun ina rokonka, da ka
    sake bata dama ta karshe, mu gani.idan bata
    daina ba, to muma sai mu tsame hannayen mu.
    M. Kasim ya cikwa Abba ido kwarai da gaske, ya
    jima kafin ya numfasa, yace, shikenan ba komai
    nagode. Yace nima nagode, Hajiya akara hkr, a
    bata damar karshe, tace babu komai M. Kasim,
    Allah saka da alkhairi. Yace amin, barin in koma
    in turo saude ta dawo ita. Tace to ka tsaya kaga
    abin kari akawo maka mana, ya mike cike da
    fara'a, yana fadin alhmdlh, kar ki damu nagode,
    to nabr ku lfya, Allah ya shige mana gaba, suka
    amsa amin. Yaka hanya fice. Bayan tafiyarsa
    kamar da hadin baki, jama'a sukayi ta xuwa suna
    ba uban dawaki hrk tare da rokonsa ya daure ya
    maida 'yarda gabasa xai fi kyau agareshi. A cikin
    su har da abokansa da yaron gidansa, watau
    kalla. Duk ya karbi rokonsu, kuma yaji dadin
    kulawar jama'a gareshi tare da tausaya masa
    akan kaddarar da ta fada wa iyalinsa. Karfe Tara
    saura, Inna saude ta taso Mama xuwa gida. Bata
    ma biyo da ita ta shagon Danliti ba, balle ya
    gansu, haka suka taru da matan gidan kamar
    zasu cinye ta danya, sannan matza suka shigo
    suka dasa nasu. A gaban kowa suka tilasta, ta
    dauki alkawarin ba xata sake xuwa ko ina ba,
    kidan kuwa ta saba, to a yanke mata hkunci da
    yafi wannan. Kwana 2 hatsaniyar nan ta kwnata,
    mama na xaune cikin gida bata fita daidai da
    tsakar gidan sasansu. Muna iya cewa Danliti bai
    murda kambunsa bane haka? Saboda haka
    xuciyar Mama ta sami 'ya nutsuwa. Bata ita
    kadai ba, su abba ma sun sami 'ya nutsuwa har
    tana debo 'ya'yan itatuwan da Abba ya ka siyo ta
    kawo mata, tace ta sha saboda rashin cin abinci
    da take fama da shi.....
    ***************** A wannan
    asabar din ma abdulkrm ya xo daiyalinsa duka.
    Su ameera nata murnar ganin auntynsum domin
    sun jima basu ganta ba. Dr. Na ta dabo, yana son
    ya taka, sai 'yar banxar kuiyam shi ya sa yaki
    yarda Mama ta daukeshi. Aunty Rabi ta tasa ta
    da nasihohi, ayoyi, hadisan Manxo SAW akan ta
    dage ta yaki xuciyarta ta dawo kan kanya,
    sannan ta nuna mata wannan ba shine soyayya
    ba, duka saurayin da ya nemi lalacewa da
    yarinyar da yake so, a hakikanin gaskiyya ba son
    gaskiyya yake mata ba. Sha'awar sassan jikinta
    kawai yakeyi. Haka yayanta ta tsatsagge mata
    gaskiyya, har yayi mata alkawarin idan ta nutsu
    ta xauna gida kamar yadda aka umarceta, to
    bayan ta haohu za'ayi bikinta, duk abinda take
    so, shi xai sayo mata. Mama ta wani kuka tana
    ba su ameera tausayi. Anann suka kwana,
    washegari lhadi karfe 12noon suka juya. Su
    ameera nata tambayar antyn su yaushe xata xo?
    Tace kar su damu tana nan xuwa nan bada
    dadewa ba, suna isa gida, yayan ya kira 'yan
    uwansa, ya labarta musu abinda ya gani game
    da Mama, idan har ya dore a hakan, alhmdlh! Ana
    iya cewa an fara samun nasara. Kowa yayi farin
    ciki jin wannan labarin da fatan Allah ya shige
    mus gaba. Allah, da ikonsa a yammacin yau din,
    tun bayan sallar la'asar mama ke cike da kewar
    Danliti, kafin 5pm ra mance kaf! Da alkawuran da
    dauka, babu abinda take so face gain Danliti,
    kewarsa ta gigita kwakwalwarta, ta birkita ta.
    Kamar an tsikare, kawai ta tashi ta suri gyale da
    takalmi ta fito kanta tsaye ta fice abinta. Dan
    gogan ta samun cikin dakin barcinsu, tana
    shigowa yana xubawa wani kaskon rushi ruwa,
    ya dago ido ya dubeta, yace ba xan miki sannu
    da xuwa ba. Ta xaune gefensa tana murmushi,
    saboda me? Ya xubo mata harara, yace kwanaki
    nawa rabon ki da nan? Sabo da nayi miki fada
    ko? Ta rungomoshi tana dariya, ayya nawan ba
    haka bane, kowa yasa min ido, sai surutai sukeyi
    kamar ni kadai na fara soyayya agarin nan.
    Amma kana cikin raina, kaima ka sani, bani da
    burin da wuce in kasanxe tare da kai, ta bae baki
    yace tsarani, au baka yarda ba? T yanxun ba ni
    na xo ba? Dana kiraki ba? Ka kirani? Kamar ya?
    Ya ture kaskon ba xaki gane. Sai dai na yarda
    kina sona, tunda kika amsa kiran. Ta xura masa
    ido tace ngode, tunda kasan hakan, me kake yi
    da kasko? Ke duk xamanki a dakin nan baki taba
    ganinsa ba? Da shi fah muke turaren daki. Kai
    amma wannan bai hadu ba, kauri gare shi, kin
    kuwa san tsadarsa? Ai ku maza ba gwabe bakin
    ku ake wajen siyayya? Kabari xan kawo maka
    mai kyau, idan ka sanya shi sai makwabta sun
    tambayeka ina ka samo. Ko? To sai kin kawo din.
    Yanxun mu ake maganar turare, ina kuka kwana
    da su Abba? Ta tabe baki, me ma? Wai an bashi
    hkr ya kyaleni, amma idan na sake xuwa nan,
    dole in tafi. To kice kin karya doka, tunda gaki
    kin sake xuwa, ni kuma da har nayi cinikin wani
    gida can bayan tasha, ina fasa kenan? Bakinta
    har kunne, tace ka fasa kuma? Ai xai mana
    anfani idan munyi aure ko? Ya shafa kai,
    gaskiyya ne, xan biya kudin in sa a gyara shi, ai
    sau muje ma ki ganshi ko? Ya xama dole, yaushe
    xamu? Duk tym din da kika shirya. Ko yanxumn a
    shirye nake, mu tafi kenan? Bismillah. Ta
    sumbace ta yace, amarya ta kenan, maman bebi!
    Ta rausaya da kai tana dariya. Tare suka fito
    yana rike da hannunta, har gaban motarsa. Ya
    bude mata ta shige, ta dawo maxauninsa yaka
    suka tafi. Gidan ginin kasa ne mai dauke da
    dakuna 2 kicin da bayi, tsakar gidan turbayar
    kasa ce, haka ginin babu digon siminti ko kadan,
    zallar kasar ce kawai, illah iyaka cikin dakunan
    anyi masu dabe, suna tsaye kafada da kafada, ya
    dubeta yace, kinga gidan, ina fatan yayi miki? Ta
    yake baki ta makalo wuyansa tace, ya fiye min
    kowannne irin gida muddin da kai xan xauna
    cikinsa. Kar wani abu ya dameka,a hankali na
    gyara shi, kyau xaiyi fa, yayi dan murmushim ya
    falla ido sannan yace, toh shikenan, tunda yayi
    maki, yau din xan nemi dillalin in bashi kudin. Ta
    kara kankame shi tace, ina tayaka murna. Ya
    xubo mata ido yace ni xaki taya murna, ko ke xan
    taya murna, gidan ki ne fa? Tayi dariya sosai. To
    dukkan mu Congratulations! Ya sumbaci labbata,
    tace thnk U! Sun jima cikin gidan suna
    sharholiyar su, ana kiran magriba, suka fito, ya
    kulle kwadaon gidan suka koma shago, maimako
    ta koma gida sai ta rashe nan, tana nishadantar
    da shi, kamar yadda ya bukata, ya siyo mata
    abubuwan da take so, tace, tayi hani'an, kai barci
    sace ta mana, ta yada kai bisa filo tai tayi
    kuwa......
    11pm za su kulle hsago, ayuba yayi
    juyin duniyan na Danliti ta tashe ta, ta tafi gida
    amma yaki, ya kuma hana Ayuba ya tasheta. Da
    ita suka kulle shago, ayuba ya kwana tsakar
    shagon, shi kuwa dan gogan yana tare da
    gimbiyar. Tsakar dare ta farka da ganta tare da
    mutum. Ta tashi xaune ta bubbuga shi ya tashi,
    menene? Tace dama ban tafi gida ba? Yace ga
    shi nan kin gani, ai da ka sani ka tasheni Danliti.
    Yace waya gaya miki ana tashin mai ciki barci?
    Kiyi kwanciyarki kawai da safe kin koma, Abba
    xai koro ni Danliti, yace akwai gida na biya
    kudinsa, baki da haushin wannan. Idan kina
    kwanciyarki, ki kwanta ida kuma yanxun xaki fita
    2am ga hanya nan babu ruwana. Bebi na kawai
    nake ji. Ta watso masa harara ni banda ni ko?
    To! Na ga kin wani hakikance ne, meye sabo idan
    kin kwana anan? In banda gulma! Ta dare ruwan
    cikinsa ta kai masa duka, ni ce magulmaciya?
    Kai din fa? Todama mai neman kuka ne aka jefa
    shi da kashi awaki, sai yaya? Washegari, yadda
    bata sallaci magriba da isha ba haka batayi
    asuba ba, karfe 7am ta dauko hanya. Gata nan
    ga nan har gida, salalau-salalau ta karaso ciki, ta
    iske duk sammakonta Abba ya riga ta tara
    jama'am don haka tana xuwa tsakar falo, tayi
    sanrada. Gwiuwa 2 ta xbe ta fara kuka. Kowa ya
    saki baki yana kallonta, M.kasin ya fara magana,
    yanxun saboda Allah Mama duk maganganun da
    aka gaya miki ta bayan kunnunwaki suka wuce?
    Ashe haka kike da taurin kai? To mu babu ruwan
    mu, dama rokonsa mukayi, ya ga girman mu ya
    hkr, tunda ke baki gani ba. Shikenan ga hanya
    na, ki bi duk wacce kika xaba. Abu yaya kamari
    har da kwana? Ke Mama kiji tsoron Allah ki
    tausayawa iyayenki. Ba xata suka ji tana
    magana, wlh Baba bada niyyara kwana ba na fita,
    Danliti ne ya sayi gida, yace muje na gani, mun
    dawo ina hutawa, ban tym din da barci ya
    kwasheni ba, abba ya xaburo yana fadin, kunaji
    Maganar Banxan da take fadi ko? Kun tabbatar
    da cewa abinda nake fadi gaskiyya ne? To ya
    isheni haka! Ya isheni haka!! BAKIN CIKI ba xai
    akshe mu ba. Daga nan ki juya ko koma, idan har
    ki na son kanki da arxiki, wlh! Wlh!! Babu wanda
    ya ya sake roko na in kyaleki cikin gidan nan!
    Duniya ce da fadi, karki saurara wajen bin ta
    kwararo-kwararo har ki gano iyakar ta! Tashi ki
    bace min da gani, kafin in kusa kashe ki da duka.
    Gaba daya falon yayi tsit, sai shasheshekar
    kukan Mama, jim kadan muryar abba ta kara
    gauraye falon, kai Jama'a! Ina xan kai takaici da
    BAKIN CIKI? Me nxan yi wa yarinyar nan a dniya
    na huce, banda in sallama ta, tamkar ban taba
    haihuwarta ba? Ki tashi fice min nace, in daina
    ganinki a gabana..... Ki ta... Kawai sai ya yanke
    jiki ya fadi, gaba daya suka mike da sallalami
    sukayi kansa......
    Toh masu karatu, wannan fa shine
    wasa farin girki. Nayi iya kar kokarina ace nayi
    muku sallama anan. Amma ina abin ya faskara,
    kuyi min hkr karshen badakalar wannan littafi
    yana cikin 3, ku biyo ni, kada ku gajiya nayi
    gaba....................THE END!!!
                                                                        Download Book Here Part 2


    No comments:

    Post a Comment


Pages