ZAWARCI
Kwance take a tsakar ɗaki sai muɗiɗɗiƙa take a ƙasa, yunwa kawai take damunta, ga kudaje sun cika ɗaki kamar toilet in daya shekara bai samu wanki ba,,,,, wasu zafafan hawaye suka zubo mata masu zafin bala"i, a bayyane tayi magana , wayyo Allahna, da ina can naci mai kyau , babu ruwana da wata yunwa ko ganin ƙazanta,,,, goge hawaye tayi da bayan hannu lokacin da taji mahaifiyarta tana kiran sunan ta,,,,,
Raihana baki ji na ne?""" umma ina zuwa, tsaki tayi , sannan tace idan ma baza ki zo, kin huta, dama wankau ne, aka kawo sunce yau suke so, idan zakiyi to kizo ki karɓa, idan kuma bakya yi ki faɗa masu, a daidai lokacin da ta fito a tsakar gida,,,,,,,
Tashin kayan wankin ta gani, ta gyara ɗaurin zaninta, sannan tace umma zanyi, umma ta kace da dariya, sannan ta taɓa hannu, tace yo kice ma baza kiyi ba, zama raihana tayi a ƙasa ta jayo wanki ta fara irgawa, sannan ta kalli yaron tace to wankin na ɗari da hamsin ne, yaron yace Eh, tace ga kuɗin, ya miƙa ma raihana ta ƙarba, tace bayan la"asar ka dawo ka ɗauka yace to yace sannan ya fita daga gidan,,,,,,,,,,,,,,
Umma tace to yanxun dai kafin ki fara wannan wanki, ki fara wanke kayan babanki sannan, raihana tace tou umma,
ZAWARCI
Saida ta wanke kayan babanta kala biyu, sannan ta fara wankin kayan wankau, yinin ranar nan haka ta yini ta wanke kaya,,,,,,
Lokacin da ta gama wankin hijabinta data gama koɗewa ta jawo daga saman iyiga, ta rataya a wuyanta ta fita tabar gidan............
Tana fita umma tayi dariya tace munafikar Allah, ai tunda dai *zawarci* kika zaɓa sai kixo mu zauna kice uwar da nake a gidan,,,,,,,,,
Raihana tana fitowa wani shago taje, suka gaisa da mai shagon, bayan sun gama gaisawa tace don Allah fulawa za"a bata kwata ɗaya, yace to, ya ana mata, tace don Allah ka bani bashin manja na hamsin insha Allah zan kawo maka , yace gaskiya raihana bakya san biyan bashi wallahi, tace kayi haƙuri wallahi zan kawo maka dana samu, shamsu yace, baia san ranar samu ba kenan,
Idan zaka bani kawai ka bani idan baza ka bani ka faɗa man, gaskia bazan bayar ba, tace to yanxn naji magana, ta ɗauki fulawarta da canjin ishirin ɗinta ta fito daga shagon,,,,,,,,
Sallama tayi ta shigo cikin gidan, matar babanta da ta dawo daga unguwa tace ina kika je ne?""""raihana tace fulawa na siyo gwaggo, cikin tashin hankali gwaggo tace waye ya baki kuɗi?""" tace nayi wankyau ne, tsaki tayi sannan taje inda fulawar take ta ɗauketa, tace wallahi saidai a ajiyeta da safe ayi fanke kowa ya samu, raihana tace gwaggo nifa nayi wankin nan na samu kuɗina gwaggo tace koma uwarki tayi haka za"ayi, ta ɗauke fulawar ta shige , cikin ɗakinta,,,,,,,
zawarci
Bayan ta ɗauki fulawar ta shige cikin ɗaki raihana ta miƙe ta nufi ɗakinsu, kwanciya tayi saboda tun safiya bata ci komai ba, ga azabar yunwa dama tana ji kuma tayi wanki har ta gaji, kuma hdama kowa dai yasan wankindasa jin yunwa,,,,,,
Raihana wasu hawaye suka zubo nata , abinda ta fara tunawa, hango tsareren gidanta, tayi da tsaruwarsa da kuma yanda yake a tsabtace, cikinta ta laluba, lokacin data tuna irin abincin da take ci, uhum Allah sarki rayuwa tace
@BABA MONO MONO
Dan Neman Karin Bayani Ka Aika Sako Da Buka Tunka Zuwa Wannan Lambar Or Whatsapp Chat 08106384398
Download Book Here
No comments:
Post a Comment