Download Now BALLAGAZA KASHI NA 1 ONE
@BABA MONO HAXOR
FOR MORE INFORMATION
CALL OR MESSAGE
08108811856
OR
08106384398
Tafe take kan hanya tana tafiya tana shan rake hijab dinta ta islamiyya tayi bakin kirin ta cire hijab din ta rike da dayan hannun ta silifas din kafarta duk sun tsinke bata damu da masu kallonta ba ita abinda ta saka gaba kawaii takeyi ASMA'U kenan tana karyowa kwanar da xata kaita gdnsu ta hadu da wata yarinya ta rabata ta wucce wuccewarta keda wuya yarinyar nan
Tace BALLAGAXA wani uban ihu ta fasa da daka tsalle ta koma gefe taci damara da hijab dinta ta jefar da raken da ke hannunta tare da jakar islamiyya tahau kan yarinyar nan da duk mutane suka taru
Akayi sama akayi kasa da an rabasu say ta koma wani mutumin yace ke yarinya meya hadaku
Budar bakin yarinyar tace wai dan nace BALLAGAXA kafin mutumin nan ya kula har fara dukanta fisgota yayi
Ke waike baki da hankaline tace ashema bani da hankali kaga alamar hauka a tare dani ne ??
Baka naji tacemin BALLAGAXA ba wllh in bata dena kirana da BALLAGAXA ba baxan gaji da dukanta ba ðŸ˜ðŸ˜ðŸ˜
2⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Shiru kawaii yayi danshi bay taba ganin masifaffiyar yarinya irinta ba
Hijab dinta ta dauka da sauran tarkacenta da ta rubar ah kasa babu inda ta xame say gd
Tun daga soro ta fara cire uniform dinta daga tsakar gd ta jefar da wandon da hijab din
Toilet ta nufa da gudu amman kafin takai harta yi fitsarin kawaii say ta tsaya ta saka ruwa ta cire rigar ta jefa daga ita say bst da short nicar say yan tsirmakun boobs dinta da suka fara fitowa cikin gdn ta nufa daman public toilet ta tsaya
Tana shiga mamansu ta kalleta ke miye hk wai ke har yanxu baxaki girma ba da daga ina kike kika taho hk ina uniform dinki da jakar islamiyya
Tace yo mama fitsari nakeji ni kuma na ciresu tun ah harabar gdn rigar kuma ta baci da fitsari
Fitsari husna da girmanki 14yrs ace kina fitsari ah wando jss 3 kike ina fitsari ah wando waike wacce irin kudar yarinyace dan wannan kinfi BALLAGAXA wllh kin xama kudar mata qatowa dake amman kina fitsari ah wando wllh kinji kunya kekam
Tace nifa mama ba ah wando nayi fitsari ba nacire wandon fa kafin nakai toilet ne fitsarin ya xubo
Kuma wllh ke kadai kecemin BALLAGAXA nayi shiru 😚😚 kafin ta karasa rufe baki taji an buge mata baki
Anje ance miki BALLAGAXAR sakarya tace mama kinajin sah fa wllh ya sake cemin BALLAGAXA baxan yarda ba
3⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh 😘 )
Ido kawaii mama ta saka mata tace lallai asma'u wuyanki yayi kwari har kinyi girman da xaki dauka mataki akan ammar
Kafin mama ta karasah rufe baki say dai taji ihunta juyowar da xatayi say ganisah tayi yana dukan husna ba tace komaii ba har say da ya gaji da dukanta dan kansan ya kyaleta
Amman tana mikewa say tayi masa gwalo 😜😜😜 ta sheqa da gudun tsiya say dakinta xabura yayi xay bita mama tace rabu da ita aii ta daku inka biye mata wllh wahalar dakai xatayi
Tana shiga daki ta nufi toilet wanka tayi ta kalli madubi taga yarda jikinta yayi jajir shiru kawaii tayi ita kadai tasan abinda ta kudirama ranta
Tun asuba mama ke tashinta amman taki ta tashi mama tayita fada ni bantaba ganin yarinya marar buri ba irin ki ba ruwan sanyi ta xuba mata tukun ta mike kafin ta gama shirin ma aikine say 8:00am ta fito daga gd
Tana isah schl class ta nufa direct tana shiga ta tarar da har uncle din ya shiga gashi in ya shiga class ba'a shiga itako hjyr tana shiga ko inda yake bata kallah ba ta nufi seat dinta babu mai xama kansah
Kafin ta karasah taji an daka mata tsawa juyowa tayi da sauri ta fita da gudun tsiya tana fita shop ta nufa ta siya choculate da biscut kafin ta gama shan choculate din say da hijab dinta yayi gaja2 da choculate din biscut din kuwa damashi dayi da ruwa da yake ah lunchbox dinta da ruwa ah gun shan damammen biscut din ta karasah bata hijab din suck's dinta ko, ko kyauta aka baka baxaka karba ba sbd tsabar datti fara qal ta taho da ita amman cikin 20mnt ta bata komai nata
Raudat ce taxo wuccewa tace yayi ma'u BALLAGAXA idanuwanta ta dago dara2 👀 tace kee duk mutuncin da muke dake kika sake cemin BALLAGAXA saina gurxar miki baki in kinji wasa kuma bismillah
4⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Aikam tsautsayi yasa raudat ta sake cewa anje ance MA'U BALLAGAXA bata karasah rufe baki taji saukar hannu ah bakinta 👊ðŸ»ðŸ‘ŠðŸ»ðŸ‘ŠðŸ»ðŸ‘ŠðŸ» ah take hakoranta biyu suka fado kasa tare da jini ganin jinin ne yasa husna tsorata aii say ta dau hanya duk nisan dake akwai tsakanin schl dinsu da gd amman tunda ta fara gudu bata tsaya ba ko juyawa batayi
Titi ta nufa anata yimata hon amman ina batama san anayi ba shigewa kawaii tayi duk ko karin mutumin dake cikin motar nakar ya bugeta amman say da ya bugeta
Hpstl ya nufa da ita say da ya kaita hpstl din ta fara dawowa dai2 tayimasa kwatacen gdnsu ta bashi nmbr yah ammar cikin kankanin lokaci say gasu shida mama da abbansu ah get suka hadu da schl bus din schl dinsu sun kawo raudat suma anan p.c din ke fadama abban abinda ke faruwa abban ya basu yace shi bayma saniba kiran su akayi akace asma'un na hsptl
Subhanallah meyasa meta wai motace ta kadeta eyyah kila garin gudune mutumin da ya banketa ne yake tambaya meya hadasu da raudat dinne p.c yace mai shop din dake gefensu dai yacemin raudar ce tace mata BALLAGAXA
BALLAGAXA kamarya wannan wanne irin sunane hk wai BALLAGAXA
5⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Abba yace wllh hk ake kiranta dan ta amsa sunanta duk inda BALLAGAXA take to husna takai gun
****************
ASALINSU
Sunan mahaifin husna Alhaji anwar dan kasuwane maiji da kansah kuma yana da rufin asirin Allah sunan mahaifiyarta hajiya aseeya yan uwane iyaye suka hada aurensu kuma cikin ikon Allah suka xauna lfy sun shafe 5yrs basu samu haihuwa ba kwacham ta samu cikin ammar tunda ta haifa ammar say da tayi 4yrs har taje hajj bata sake haihuwa ba tayita addu'a Allah ya bata "ya" mace cikin ikon Allah ta dawo bada dadewa ba ta samu cikin asma'u
Tun tashin husna daman can asali bamai natsuwa bace in mamanta na mata fada say mutane suyita cewa yarinta ce ta barta xata dena da ta fara hankali amman ina abu say yawa yake sakeyi shekaru nata ja amman ba chanji abin nata sake ta'axxara
********
Mutumin da ya banke husna yayi ajiyar xuciya yace kamar dai yarda ake ce muku yarintace to tabbas yarintar ce dan nima akwai yarinyata mai irin halinta kuma sunansu daya yanxu hk tayi aure da yaranta biyu kuma duk abinda husna keyi iri daya dana husna ta ne xata bari a tym din da bakwa tsammani
[11:43am, 10/3/2016] Halimatu Lawal Nv: 6⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Kwanan ta biyu ah hsptl ta addabi kowa har say da aka sallameta barna ba kama hannun yaro yarda kukasan karamar yarinya hk takoma musu
Raudat kuwa ko kwana batayi ba ah hsptl din abba yayita ba iyayenta hkr tare da alhaji abubakar suleiman wanda ya banke husna bata sake komawa schl ba say da tayi one week ranar da ta koma tana shiga class bata kula kowa ba ta nema gu ta xauna kamar dukka kenan wani uncle dinsu ya shigo wanda ya koreta rannan yana ganinta yace ba kece nagani yanxu fes-fes amman kafin ki karasow class dubi yarda kika bata jikin ki wai kuma ah hk har aka baki monitor qaxamiya dake da an ganki anga BALLAGAXA
Da sauri ta dako dara2 idanuwanta 👀 sun kada sunyi jajir bata ce masa komai ba yace yan class kuce mata BALLAGAXAR monitor juyawa tayi takallesu daya bayan daya class din yayi tsit kamar anyi mutuwa babu wanda yace qallah ya sake cewa ku kirata da BALLAGAXA mana naman shiru come on mana tsoranta kukeji baxakuce BALLAGAXAR ba wllh xan xaneku nan ma tsit
Tashi yayi yabi kowane cikinsu yayi masah bulala 5 yana cikin dukan nasu ta lallaba ta fita class din cafter schl din ta nufa daqar ta samu suka sammata gishiri babu inda ta xamee say gun da teacher's ke ajiye 🚗🚗 da machine tana xuwa tace au ashefa matsiya cine machine yake da shi
7⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Cikin kankanin tym ta xubawa salansar machine din gishirin nan tayi maxa tabar gun aranta tace dani kake xancen kaida machine din nan say gani say hange ka rinka dabo sayyada kana xuwa schl din
Uncle osy na fitowa ya nufi machine dinsa dan yaje gd yayi brkfst amman sayme machine yace baysan ya tashi ba ya duba yaga lfyr sah qlau say mai daketa xuba kamar wanda aka sakawa gishiri yana duba salansar saiga gishiri xoqare da salansar baysan tym din da idanuwansa sukayi jah ba suka kawo ruwa yana nan tsaye say ga p.c
Yace aah osy lfy naganka tsaye baka tafi ba harsay tym yayi yace wllh machine dinne nasamu wani ya saka masah gishiri gishiri kuma?? Eh sir gishiri daga wanne class ka fito yace jss 3a. 3a class dinsu asma'u anwar ko ?? Osy yayi maxa yace eh can class dinsu wannan BALLAGAXAR yarinyar
P.c yace kardai kacemin a gabanta kace mata BALLAGAXA nan take uncle osy ya fadawa p.c yarda sukayi kaff p.c yayi murmushi yace kayi kuskure kuma itace ta xubama gishirin nan shakka babu ita ce ran osy ya baci ya kara daura mata karan tsana ranar say dai left akayi masah aka kaishi gd
Tana isah gd tayi wanka tayi sallah akaci kwalliya mama na ganinta tace aah yau kuma yan tsaftar ne ah saman kan naki shiru tayi ta nufi kitchen tana xuwa ta dauka manja duk ta goga ma kayanta fuskarta duk tayi bakin kirin tana fitowa mama ta dubeta ta sake dubanta ta rasa abinda xata ce mata sbd ta gama kasheta da haushi kallon takaici kawaii ta bita dashi sunanan sukaji sallamar abbah tare da alhj abubakar suleiman mutumin daya kadeta da mota
8⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Suka gaisah da mama ta tashi xata kawo musu ruwa abbah yace xauna mana ga husna nan taje ta kawo mana harda abinci mana mama dai batace komaiii ba amman jikinta bay bata xa'ayi abin kirki ba
Lfy lau ta dauko abincin ta ajiye ta dauko ruwa da drinks say da ta bari taxo tsakiyar falon ta rabasu tsakiya tukun ta saki tire din ya fadi kasa glass cup's din da ke sama duk suka tararratse kuma tabi takai ta wuce abinta (kunji aikin BALLAGAXA fa) abba ya rikota da sauri ke bakida hankaline xaki yi barna kibi takaii
Tace abbah xan dauko tsintsiyane karna taka glass din yace yo na nawa gashinan kin taka kafarta ta dake xubar da jini tace auuu abbah wai daman kafatace ah cikin aii nayi tunanin kafar bakokace abbah yace aah ta uwaki ce kujimin shaqiyiyar yarinya alhj abubakar yayi daria yace ku bita ah hankali na fada muku xata bari wllh insha Allahu mama tace Allah dai yasa yace amin
Daya tashi tafiya ya dauko 1k ya bata aikam tayita murna dan tunda take duniya ko dari biyu bata taba rikewa tata ta kanta ba yau gashi an bata dubu aikam taji dadi da kudin nan take barci dasu take tashi
One week da bata kudin nan ta fito harabar gdnsu da duba dayar nan suna da rijiya han can gefen gdn tana nan tana shirmenta say ga mama ta fito tayi karaf tace mama na iya xan ruwa bari na jayanyo miki kafi ta bata amsa harta kai bakin rijiyar ta bude
9⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tana xira gugan dubunta nabin gogan aikam dubu ta fada rijiya wani ihu ta saka tare da fadi mama dubuta kafin mama ta bata amsa tuni tabi dubun nan cikin rijiya dai2 da shigowar abbah da yah ammar
Cikin tashin hankali mama take fadama abbah yah ammar ya leqa ya kwala mata kira amman shiru kafin kuce kwabo gd ya cika makil da mutane aka samu wani dan uguwar yaxo ya fito da ita amman ana fitowa da ita ta dubi mama ta dubi umma tace abbah kudina ta xabura xata sake nufar rijiyar yah ammar ya fisgota waike meyasa bki da hankali ne yah ammar 1k faceee wllh say na dauko kayana in ban bita ba waye xay ban wata kafin ta karasah rufe baki abbah ya dauka 1k ya mika mata yace gashi nina baki shikenan ko ??
Tace eh say kuma ta saka kuka ni wllh wacce abbah dan gayu yabani tafi kyau kuma sabuwace har kamshin masu kudi takeyi gashi kafata say ciwo takeyi wllh baxan yarda ba a barni in dauko tawa kafin ta rufe baki say ga alhj abubakar
Yace lfy dai ko yar gdn abbah kafin tayi mgn abbah yayi masa bayani ya sake dauko 2k yace gashi kinga na kara miki tace eh abban yan gayu yaushe xaka kaini gdnka
🔟BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Yace ki shirya gobe xanxo na kaiki tunda kunyi j.s.c.e say kije yiyo hutu kuma kinga ni abbanki ne ba abban yan gayu ba ko kece yar gayun
Tace uhm aah ni ba ruwana da wani gayu yace to shikenan xaki xama yar gayu kinji tace uhm to ai na iya gayun kawaii bana sow ace nayi kyaune mutum yayita wanka kullum kamar agwagwa murmushi kawaii yayi
Aikam washe gari tun safe ta shirya amman har 3:00pm bay xo ba aikam tayita gunguni daman kayan da ke jikinta tun na jiya ne bata changer ba wanka kawaii tayi say 5:30pm yaxo daqar ya samu ta bishi
Suna isah gdn ya kira hjy ameena matarsah yace ga husna part 2 babu abinda ya rabata da husnarki aikam hjy ameena tayita murna tayita nan nan da ita
[11:43am, 10/3/2016] Halimatu Lawal Nv: 1�1⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Hjy ameena tace aii wannan ba irin ma'u na bace ita ma'u na da bata da bambanci da BALLAGAXA wata irin harara husna ta aika mata da ita ta dubesah tace nifa abba kayi mata mgn ina ganin girmanta karta sakemin xauranci taci fuskata
Murmishi kawaii yayi yace to yar gdn abba baxata sake ba abba ya dubi umma yace to kinji fa tace to "yata na dena tashi tayi tace ki biyoni na kaiki dakinki batace komai ba tabi ta abaya
Daki aka kaita mai rai da lfy hadadden daki umman ta bude weadrop din daki xokare take da kaya tace mata husna wannan kayan yar'uwarki ne amman ita ta rasu sanadiyar hatsarin mota da tayi shekaru biyu kenan dan hk ga kayanta nan kici gaba da amfani dasu
Wacece yar uwata chap aini banda wata yar uwa yah ammar ne kawaii dan uwana shima na ciresah daga jerin yan uwan nawa ni babu ruwana da yaya ko qani danni kadaii nake harkata
kuma daman wadan nan aiinasan nawane dan abban yan gayu ne yacemin kar naxo da kaya shine xakixo ki wani cemin kayan watane nifa tsaya kiji tun da kika min xauranci kika cemin BALLAGAXA shikenan kika gama sireemin
1�2⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Duk masifar nan da takeyi umma na jinta kuma babu alamar bacin rai ah tare da ita murmushi kawai taketa yi mata ita burgeta takeyi dan tabbas bata da bambanci da husnar ta hk ta tashi itama
Kwananta biyu ah gdn ta hada kayanta ita amayar da ita gdnsu wannan gdn ba dadi da qar aka rarrasheta abban yace yanxu ki shirya usman yaxo ya kaiki yawo da gudu ta nufi daki tayi wanka ta dauko wani less golden ta saka aka xauna an mata 30mnt ana kwalliya tana gamawa ta daure kan nan gam da dan kwalli dan rabon da kanta yaga kitso itama kanta ta manta
Da gudu ta fito ji tayi kawaii ta banke mutum kamar wata mota ta watsar masa da wayarsah dake hannunsa tare da key din motar amman ko juyowa batayi ba tayi gaba abinta tana xuwa harabar gdn ta tar da abbah da uncle osy na schl dinsu ah waje amman say ta basar kamar bata gansah ba tace abba na shirya
Yace to usman ta shirya ku tafi har saloon ka kaita yace waii abba wacece xan kai wannan hatsabibiyar yarinyar chap aii abbah kafin mukai saita lalata motar yarinyar nan daga nace mata BALLAGAXA ta batamin machine ina sown machine din nan amman yarinyar nan ta lalata shi
Cikin tsiwa tace karka sake cemin BALLAGAXA wllh yace anje ance BALLAGAXA takalman da ke kafar ta hill's ne ta cire ta kalmin nan ta saita bakinsah takuwa jefa masa kafin abba ya ankara ta sake cire dayan ta jefa masa ah bakin
1�3⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tace gobe naga bakin da xaka sake cemin BALLAGAXA bakinsah ya fashe jini kawaii ke xuba ya xabura xay biyota abba ya rikesah kofar da xata kaita falo ta sake banke mutum kafin tayi yinkurin guduwa tuni ya chap kota wani wawan mari ya kifa mata say da tagano taurari guda ukku
Dago kan da xatayi say taga soja kikam ah gabanta da uniform dinsah dogone sosai dan duk tsayita say ta ganta wada ah kansah indai gun tsayi ne farine sol kamar balarabe doguwar fuska yake da ita hancin sa har baka bakinsah dan karami kuma pink yana da faffadan kirji kyakyawane na ajin farko
Bata tabajin tsoran wani mutum ba a duniya say shi SAS kenan SULEIMAN ABUBAKAR SULEIMAN ( SAS ) nickname dinsah kenan da fanx dinsah ke kiransah dashi
Sake juyawar da xatayi ta kallesah taga wayam aikam tayita ihu nan ta fadi kasa tana ta mirgina ita ah dole aljani ta gani yama shiga jikinta aikam da gudu umma ta fito ta riketa ke lfy tace wayyo umma gamo nayi aljanine har ya shiga jikina aikam umma tahau salati ta kira atee mai aikinsu tace kawomin ruwa ah cup
1�4⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Ana kawo ruwan umma tayi mata tofi ta bata ta shanye say ta fara fisge2 wai ga aljanin nan ya fita jikinta xay tafi umma bay tafi ba gashinan xay shigo daga kan da umma xatayi sai taga suleiman tsaye ah gabanta ta sake juyowa ke ina aljanin tace umma gashinan yana tahowa
Umma tasake kallonsah tace mai sunan manya mekayima yarinyar nan ne ta firgita dan babu shakka kaine aljanin da take mgnr sah ya daga kafada cike da kasaita da isah ya fadawa ummu abinda ya hadasu ya ci gaba da cewa ashe usman ta basawa baki dan yace mata BALLAGAXA dan danan ta xabura ta mike karka sake cemin BALLAGAXA
Yace keni kike ta sow mawa hk xan ballaki wllh say da ta matsa nesah dashi tace eh anje an taso ma kumani wllh mai ballani ko uwarsah ba'a haifa ba bare shi dan kana ganinka soja to ba soja ba ko bindiga ne ka sake cemin BALLAGAXA say na dauka mataki tana gamawa ta baxa daki da gudu harda saka key daria ya saka yace umma ina kuka samo nan commedian girl hk aini rabon da naga yarinya irin wannan tun husnar ashe akwai irinsu ah dunia umma tayi murmushi tayi masa bayaninta
Yanan tsaye abba ya shigo yace mai sunan manya dauka asma'u da usman ka kai usman hsptl ita kuma kadan shiga da ita gari taga gari xabura usman yayi yace wht abba aii kafin mukai ta karasah halakani gsky tsoranta nakeji daria sas yayi yace ai nima baxan dauketa ba say day na hada ta da driver
1�5⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tana daga cikin daki tace baxan je ma abba rabu dasu baxanje ba din shi wannan mai kama da nunar ranar ka fada miki wollah kar ya yarda mu hadu mugu mai kama da aljanu dariya su abba suka saka gaba dayansu
Abba yace fito kiji "yata" rabu dasu kinji tace abba ka fadama wannan bindigar wollah na fito ko kallona kar yayi yace to fito kinji say gata ta fito taci damara da dan kwallinta koda rigima xata kama abba yace ki bisu kinji kiga kanki yayi datti kuma ba su xasu kaiki ba driver ne kinga ko haduwa ma baxakuyi ba tace to
Suna fita gun saloon driver ya kaita say da aka gama gyara mata kanta tukun suje yawon daqar aka gama gyara mata gashin say da ta karya musu kum guda biyu sun ranar taje yawo taga gari tana komawa gd tafara shirin tafiya gd tace itafa wllh gdnsu xata tafi baxata iya xama ba aikam suka gyalleta
A daren ranar ta kwana yi musu ihu da kuka ita wllh a kaita gdnsu kawaii sai ah satota a ajiyeta nan babu kowa harta fara ganin aljanu abu kamar wasa karamar mgn ta xama babba abbah yace ta bari da safe xa'a mayar da ita tace to tun asubah ta shirya tana nan xaune ta fara gangadi barci ya dauketa abba ya tafi office umma tana dakinta usman nacan kwance sas kuwa ya fita aiki bata farka ba sai 12pm tana tashi ta fito waje ta rinka rusa ihu tana turje2
[11:43am, 10/3/2016] Halimatu Lawal Nv: [5:43PM, 11/8/2015] Serdeeyerh😘: 1�6⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Da sauri mai gadi ya isow yace kee yarinya lfy meya sameki cikin kuka tace ba nace su mayar dani gdnmu ba sunki mayar dani kafin yayi mgn yaji horn din mota yana budewa bataliyar sojoji suka shigo sas ne dare da fanx dinsa fitowa sukayi daga cikin motar har xasu wucce falo ya tsaya yace ke mekikeyi nan tayi shiru ya daka mata tsawa mekikeyi nan
Ta xabura tace yo waikai bindiga ina ruwanka dani ai bakai ka kawoni gdn nan bah kuma nace ah mayar dani anki mayar dani 😘 fanx dinsah suka kwashe da daria yace bari abban ya dawo ya mayar dake ni aii bansan gdnku ba tace ni aii nasan gdn in kabi can kasha kwana ka sake shiga kwana kana miqewa xaka sake ganin wata kwana da tayi left hand dinka ita xaka shiga nan ne gdnmu
Wata irin daria suka saka shida bakin nasah dayan yace wow sas ina kuka samu yarinyar nan ne kamar wata sakarya tana ta bayani aikam ta xabura a mike tsaye tace kai dakata kaji dan kunji ina cemuku bindiga to wllh ko kabarine ya tabani sayna taba shi karka sake cemin sakarya 👈🻠danni ba sakarya bace ðŸ˜ðŸ˜
Sas ya daga mata tsawa keee sa'an kine shi daxaki xauna kina fada masa mgn tace yoni sa'ar sace da xaycemin sakarya sas yace waike wacce irin yarinyace ah tsaye in an ganki kamar mai hankali amman baki da hankalin kome naki na mahaukata kinci sunanki BALLAGAXA wllh da sauri ta dauko dara2 👀👀 tayi masa wani mugun kallo
1�7⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Ta xabura tayi waje da gudun tsiya daria suka saka shida fanx dinsa wani daga cikinsu yace ka tsoratata kaja ta gudu yarinyace fa yace wllh hk qanwata husna ta tashi batajin mgn suna nan tsaye suna mgnr say gata ta shigo da wani abu cikin dan kwalinta
Ashe duwatsune tsaune ah cikin dan kwallinta tun daga nesah ta fara aika musu sakon jifa ta rinka jifarsu ko ta ina duk say da ta musu tabo ah fuska da kai a sukwane suka shige cikin falo suka maydo kofar suka rufe sas kuwa dandana gefen idonsah ya kumbura bakinsan ya fashe daman say da tayi saitin bakinsah ta jefa na karshen shiko hamxa qeyarsah ta kumbura faisal kuwa ah goshi ta jefa masah
Sas ya kira umma cikin tashin hankali yce umma wannan yarinyar xata kashemu tace wacce yarinya yace wacce take gdn nan kiyi sauri kixo part dina tana bakin kofar falon umma na iso wa ta ga batanan tayi nocking sukaki budewa say da tayi mgn tukun yana budewa ta kallesu ta kwashe da daria tare da cewa soja wuta soja bindiga uhm umman kenan anya yarinyar nan ba mahaukaciya bace daria ta hana umma mgn suna nan tsaye abbah ya shigo yaga part din bude say ya nufo part din yana xuwa ya kallesu yace lfy meya sameku accident kukayi ???
Hamxa yace ai abba in accident ne ma kila da abin xayfi xuwa da sauki tofa meke faruwa ko yan fashine faisal yace aah abba yar daba ce abba yace yar daba kuma ? Ah ina kuka hadu da yar daba ina 🔫🔫🔫 kuma ina kuna ma maxa har mace ta muku wannan abun cikin daria ummah tace to ai baka saniba husna ce ta musu wannan aikin
1�8⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Abbah yace kamarya husna meya hadaku faisal fadama abba komaii abba ya saka daria yace shiyasa nake sown hadaka aure da yarinyar dan jarumace
Sas ya xabura yace wah Abbah yace kaii yace yo abbah wannan aii wata rana sayta kasheni wai kuwa kaga yarda ta rinka yimana ruwan duwatsu kamar daga sama fa mukaji ana ta saukar mana da duwatsu tana ma karamarta kenan wannan ita girma halakani xatayi abbah yace kune baku iya xama da ita ba ita fa sunan da ka kirata dashine bata sow kuma jiya har worning tayima amman kuma ka kirata da sunan yau ku tashi ku tafi asibiti
Sas yace waye xay fita wannan hatsabibiyar yarinyar ta kashesah aini koda naje training ba'a yi mana training din tare jifa ba na harbi kawaii na sani kuma har cewa tayi ba bindiga ba ko kabari ne ya tabata say ta tabashi ina gani ni kaina ina tsoran bindigar bare kabari kawaii abba ka kira doctor ya dubamu abba yace bari na tafi mayar da ita gd say ku tafi
Umma kuwa daria ta hanata mgn da ta kalli bakin army's da qeyarsu say daria tace wollah kun bani kunya sas yace uhm umma kenan yarinyar nan in namiji ce wllh da yau sayna kaita gardroom umma ta saka daria tace ay gashinan ku ta sakoku falo ko 😀😀 hamxa yace waini umma ina kuka samota nan ta xauna ta basu lbr da irin abinta tayi mata itama suka rinka daria
1�9⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Abbah ya dauketa ya kaita gd ya bata 5k wayyo Allah ina aljanna ta sakashi yayi mata kyautar kudi aikam tasha murna
Kwananta biyu da dawowa aka koma ta tashi da safe taje tayi fitsari tayi alwallah tana fitsari taga jini nabin fitsarin ta wanke ta sake ganin ya sake fitow aikam ya saka ihu da gudu umma tashigo toilet tace asma'u lfy tace umma shikenan mutuwar xanyi fitsarin jini nakeyi wayyo Allah ummah na mutu in xa'a tafi rufeni kice ah tafin min da kudina da abban yan gayu ya bani wani dogon tsoki umma taja mtswwww
Tace ke ki natsu kimin bayani tacema umma kinji2 umma ta bata sabon pant da always ta nuna mata yarda ake sakawa tayi mata fada tace yanxo say kiyi hankali nasan ana gaya muku ah islamiyya kuma nasan a bokonma kinsani
Kidai sake kama kanki wannan sakarcin da kikeyi ki dena kuma ki rinka tsafta inba hk ba warin arna xaki rinkayi ki rinka wanka sau ukku ah rana inba hk ba tsamin hamata xay isheki shiru tayi karama ba ita ba to ku tayani ido kodaii asma'u ta fara natsuwane
[6:35PM, 11/8/2015] Serdeeyerh😘: 2�0⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Kwance tashi babu wuya gun Allah asma'u na ss3 yanxu amman babu abinda ya sauya saidai abinda baxa'a rasah ba yanxu tana wanka tana kwalliya amman in banda kwalliya da saka kayan babu abinda takeyi
Gashi tayi boobs kuma irin wadanda suke tsayen nan ne qiqam gashi bata saka bra kuma kullum say anyi mata mgn ah schl ah gd amman ina ita ah dole say yan iska ke saka bra ( kunji fa halin BALLAGAXA)
Rannan ta shirya taje gdn abbah ta sukasha fira da umma tace waini husna meyasa bakya kimtsa kankine gashi bakya sown ana cemin BALLAGAXA gashi kuma kinata BALLAGAXANCIN meyasa ne ??
Tace to yanxu umma mexanyi ni wllh bana sow ana cemin BALLAGAXA umma tace ki rinka kama kanki yanxu sbd Allah duba fa ki gani gaki da boobs kamar gugan roba amman baxaki iya saka bra ba duk inda kikayi ana kallonki kuma da kin wucce xa'a ce dubi wata BALLAGAXAR yarinya nan kuma da kinji say ki tsaya kiyita fada da mutane kamar ba mace haba husna miyene hk kinyi wanka kinsha kwalliya amman da anje gdnku xa'a tarar da mamanki na aiki dakin ki kuwa ko inda mutum xay ajiye kafarsah babu sbd tsabar kaxanta
Tace too umma xan gyara ywwa "yata" yaushe xaki xo mana hutu da sauri tace ywwa ummah ina wannan aljanin mai kyaun tsiya nan gdn umma tayi daria tace eyyah ai bayana ya tafi wani cos yanxu shekara daya kenan amman karshen watan nan xay dawo tace to Allah ya dawo dashi lfy umma tace amin
[11:43am, 10/3/2016] Halimatu Lawal Nv: 2�1⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tace to umma ni xan wucce tunda abba yaki dawowa in ya dawo kice masa nxt week nakeyin candy ya hadamin kayan dadi ina uncle osy?
Tace ya tafi gun aiki kilama ki gansah yanxu bayan kin barshi da kumburarren baki daria tayi tace umma aii shi ya jani kuma wollah ko yanxu ya sake jana damben tsiya xamu dashi dan nima na kawo karfi umma tace xonan husna
Tana xuwa tace xauna waini ba yanxu nagama yimin fada akan fadan da kikeyi ba tace umma aii cewa nayi in sake jana kinga yanxu ai bay jani ba ko tace to ai nan halin BALLAGAXANCIN ne ta tabe 😟😟😟 chap nifa umman dai akai in an jani nefa baxan iya hkr ba
Tace to in bakya sow ah jaki aii sai ki dena binda kike tace tsaya umma waini menakeyi ne da kiketa cewa abinda nakeyi
2�2⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Umma tace tofa kaina abin ya dawo tace yo kema dai umma nakai xuciyata nesa nayi shiru inata sown in hkr amman kin nace kinata mgnr ni bari nayi tafita da gudu ta fita dai2 da shigowarsu sas shida fanx dinsah hamxa nd faisal aikam sas na gaba faisal na binsah hamxa na karshe
Tana tahowa tayi awon gaba da sas yayi baya faisal yayi baya shima ya fadama hamxa shi kuwa hamxa tuni yakaii kasa say ga sojoji ah kasah xube gashi sunsha farar shaddah ta juya ta kallesu ta kwashe da daria sas ya tashi ya bata lafiyayyen mari tace ni ka mara kafin ta rufe baki ya sake mauje mata baki
Aikam ta saka ihu wllh ban yarda say na rama mugu aljani kawaii dubi kanka kamar na muxuru kanata saki baki kamar wani dolo ba shakka wadan da suka daukeka aiki basusan mace suka dauka aiki ba hamxa da faisal kuwa tuni sunyi cikin gd dan kar ah kuma na rannan tace da wasu munafukan fanx dinka yan kwakwa ko xuciya basu da ita kullum say sunxo
Ya sake daga hannu ya mareta saiga abbah yayi masa tsawa miye hk ya fadama abba abinda tayi masa abban ya tambayeta ta fada masa tare da cewa nifa abba banma san sun taho ba wllh kuma abinda yaban daria nagansu dirma2 shida fanx dinsah amman ni yar ficcila sani daga dan ture mutum daya say gasu kasa duk sun fadi
2�3⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tace anya abbah wadan nan ko aiki sukaje baxasu iya komaii ba wollah damani sojace in xama offiser su wollah sayna basu wahala amman yanxu ma xan fara aikina abbah yayi daria yace aah yata yafa kamata ace kin girma hknn gashi ina sown ki auri mai sunan manya kuma gashi tsoranki yakeji dai2 da fitowar sas
Yace wllh abbah Allah ya sauke ni in akwai mutumin da na tsana ah duniya bayan yarinyar nan yake yarinya kamar aljana tace nikuwa wllh sayna aureka har naji nama fara sownka wllh ta hada da cewa yo kai in banda abinka har kana da bakin cema wani aljani bayan duk sufarka ta aljanuce
Yace sakarya tace i luv u yace marar xuciya tace ba komai nakai kasuwa na siyar abba ya rinka daria yace mai sunan manya ku ajiyeta gd yace amman abba......... yace bana sown musu nace ka ajiyeta gdn harta shiga mota ta fito tace abbah nxt week candy na fa yace Allah ya kaymu kinga say a hada da sa ranar aurenki ta rufe ido da hijab alamar kunya
Hamxa da faisal sukayi sauri suka shige gaba dole ita da sas xasu xauna ah baya ya hade raii itama ta hade rai 😠😠sun kusa kaiwa uguwarsu ta hango mai siyar da rake tace ku tsaya nasiya rake sukaki tsayawa tace au baxaka tsaya ta arxiki ba da sauri yaci burki ta fita da gudu ta siya rakenta ta dawo
Suna ajiyeta gd suka wucce ah guje ta shige gd tayi sama da yah ammar aikam ya kwasheta da mari kafin ya dire hannunsah 👊ðŸ»ðŸ‘ŠðŸ»ðŸ‘ŠðŸ»ðŸ‘ŠðŸ» takai masa ah baki say tym din ta daga kai taga waye tace au waii yah ammar kaine sowrie plx nayi tunanin gamo nayi amman aii nasan baxaka sake marina ba tunda yau kadan jini kadan kafin ta tufe baki ya hauta da duk amman yarinyar nan tayi qiqam tana kallonsah batace masa kala ba kuma da alama dukan baya shigarta
2�4⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tayi kukan kura ta cha2mushi tayi masa kyakyawan riko ta jijjigashi waikai ni sa'ar kace dan kaga ina kyale ina dan baka girmanka shiyasa kake sown ranani??
Hankalinsah ya tashi duk tunaninsa aljanune dan rikon da tayi masa ko namiji baxay iya yi masa shi ba ta sakesa ta ta cire hijab din jikinta ta ajiye ranketa ta yanki fili tace dan datajar Allah ka sake tabani yau kayi kallon ikon Allah wllh saynayi kasa2 dakai ah gun nan
Kamar daga sama mama ta rinkajin hayaniya ta fito harabar gdn taga yarda husna ta nan nade sket ta cire hijab tace kee lfy da sauri ta dauka kayanta tayi cikin gd da gudu mama ta dube ammar da fuska ah kumbure tace lfy yayima umma mgn tare da cemata wllh mama yarinyar nan karfin maxan ðŸªðŸªðŸª
2�5⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘)
Mama ta saka daria harda kyalkyatawa tace kaii amman fa ka bani kunaya wllh shekara wajen biyar ka bata amman kana tsoranta aii yanxu shikenan raini ya shiga tsakaninka da ita
Yace mama kenan aiko namiji yamin wannan naushin sayna durkusah na basah hk wllh na daku anya yarinyar nan xata samu mai aurenta kuwa dan wllh saita halaka mijin har lahira mama daria kawaii takeyi tace ba bakinka ba wollah
Tana xaune harabar gdnsu ita da mama tace mama ki siyamin brexia dan ranan umman yan gayu tace wai say nayita yawo hk anamin kallon sakarya tace to xan siya miki sallama sukaji ammar ne tare da wata yarinya yace mama ga suruka na kawo miki ku gaisah sunanta maryam ya dubi yar mulkin yace husna ga auntynki
Daga kanda xatayi sai taga mairos senior tace ah schl ta jimgeta kamar kamar me ta dade tana nemanta yau gashi Allah yakawo ta har cikin gdnsu bataga mai hanata dukanta ba yau kuwa itakam say murmushi takeyi ita taga wacce ta sani
[11:43am, 10/3/2016] Halimatu Lawal Nv: 2�6⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Kamar dukka kenan ta tsaya suka gaisah da ita lfy lau tashi tayi ta fita waje ta boye ah wani kwararo da bulalarta lafiyayya say da ta bari taxo ta wuce bayan yah ammar yayi mata sallama har tayi nisan ta nitsa tsakiyar uguwa ta kwala mata kira
Tace mairos ta juyo da murmushinta tace ina kika shiga munata nemanki xan tafi tace gdn uwarki naje kafin tayi mgn ta fara xaneta say da tayi mata rudu2 tukun ta rabu da ita juyawar da xatayi say taga sas tsaye shida yah ammar idanun yah ammar sunyi jah sbd tsabar bacin rai wani wawan mari sas yayi mata ta dago dara2 👀 ta kallesah tayi wani shu'umin murmushi tace bashine ka dauka karka damu xan dawo kanka wllh
Ta juya ta sake dauke mai ros da mari tare da nuna sas da yatsa tace kinga wanda ya ja miki nan yah ammar ya fara dukanta aikam tace wllh ka sake dukana sayna sumar da wannan shegiar yarinyar mai kama da "ya"yan arna kalli kafar muguwa kamar doya in ma banda abinka yah ammar me xakayi da wannan mai sufar maxan
Sas ya fisgeta yayi gd da ita dakin ammar ya xaunar da ita haba husna ni bana sown abinda kikeyi wllh a hk xamuyi auren baki ganin mutunci kowa koda yake kinsani shirmene akanki pls bana sow indai kina sowna ki dena kinji husna
2�7⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Wani kallo ta mashi tace to daman waye yace yana sownka bare har ya aureka Allah ya sawwaka na auri mai kama da aljannu wanna ai say ka rinka firgitani kainifa tsaya kaji banda ra'ayin auren kyakyawa kuma banda ra'ayin auren saurayi ko xan aura saurayi say mummuna in ma kasa rai da xan iya aurenka to wllh kwalelenka tana gama fadar hk ta tashi tayi tfyrta mama batasan abinda ke faruwa ba tana cikin gd
Ammar ne ya samu mama yayi mata bayani mama tace addu'a kawaii xaku rinka mata wllh yarinyar nan har tsoro take bani in tana wani abun kamar ba mutum ba anya ba musayarta akamin ah asibiti ba danni duk xuri'ar mu babu mai irin halinta wllh ance yarinta ce gashi ta girma babu abinda ya sauya kila say tayi aure dan ko ciwon kanta bata sani ba bare na wani ammar yace to Allah ya shirya mama tace amin daii
Ammar yace mama gafa suleiman can yaxo abbansah ya turoshi gun abbah wai yaxo neman ixinin wannan yarinyar ne tace wacce yarinya yace husna mana tace husna kuma?? Aikam indai aka bashi husna an cuceshi yaro na tsatse ah hadasah da wannan BALLAGAXAR yarinyar fit tayo waje tace wllh mama nima bana sownshi mutum kamar aljani mama tace ai shima nasan ba sownki yakeyi ba kawaii yabi umarnin iyayensah ne wanda kema dole ki bisah daki ta shige abinta bata sake cewa komaii ba
2�8⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Kwana biyu da wannan mgnr su asma'u sukayi candy aikam ranar husna ta natsu ( koni serdeeyer nayi mamaki yarda kukasan ba ma'u BALLAGAXA ba ) ranar abbansu sas ya siya mata waya goine m5 cikin natsuwa ta karba tayi godia umma tace husna baki lfy ne yau tace lfy ta qlau tace anya naganki yau so silent tace Allah umma babu komaii tce to shikenan Allah ya tabbatar da alkhairi kinji tace amin
Cikin dan lokaci husna ta changer gaba daya kamar ba ita ba duk wasu makaman yakinta ta ajiyesu gefe daya babu abinda ke damunta kamar ba ita ba tun yan gdn na tambayarta meke damunta har sun dena abba yace kila tym din natsuwarta ne yayi mama tace Allah yasa dai
Kwance take tana karatun wani hausa novel ah whtsapp na pherty mai suna herleematu da ka ganta kasan tanajin dadi karatun littafin ya dauka hankalinta tana xuwa page din karshe tayita daria harda kyalkyatawa da sauri mama ta shigo tace lfy tace lfy qlau mama ina karanta wani novel ne yaban daria ne mama ta ayyah aii nayi tunani ko haukan ne ya dawo shiru tayi abinta
2�9⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Daukar nmbr pherty tayi tamata mgn amman shiru gata online ta sake mata mgn shiru say ta tafi taje tayi sallah tana gamawa ta kwanta barci ya dauketa tana tashi wanka tayi ta shirya ta tafi gdn abbantah tana xuwa da osy ta fara cin karo da sauri ya ja baya ya bata guri tare da cewa
Manya-manya inji kanana murmushi tayi ta durkusa ta gaishesah yace lfy qlau cikin gdn ta nufa shi kuwa ya tsaya yanata yi mata kallon mamaki anya yarinyarnan ce kuwa kaiii gsky da sake
Tana shiga cikin gdn ta gaishe da umma cikin natsuwa umma tayita murmushi dan taji dadi yarda taga husna ta natsu say ga abbah ya shigo shima suka gaisah yace "yata ya kike ya gd nace lfy qlau abba mutanen gdn na gaisheku yace muna amsawa mai sunan manya kikaxo gani tace aah ni ku naxo gaishewa yace to madallah aii nayi tunanin kinxo ganinsah ne bay lfy tace eyyah Allah ya bashi lfy umma tace amin
Yana ina na ganosah tace yana dakinsah part dinsah ta nufa tana shiga ta gansah kwance yana ta kyarma ta karasa da sauri tace sannu yah suleiman da sauri ya dago kai ya kalleta yace nine yayan yau kuma?? ashe kasan ashe kinsan sunana ??
Tace uhm ashe baka lfy sannu ya jikin naka yace da sauki tace to Allah ya sawwake yace amin wai kema baki lfy ne kwanan nan say inyita ganinki wani iri meke damunki tace babu yace owk Allah ya kyauta amin tace amin ni xan wucce yamma nayi yace to ki gaishesu tana fitowa tayima umma sallama tayi tafiyarta gd ta barsu cike da mamakin sauya warta lokaci daya
3�0⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tana isah gd tayi magrib da isha'i ta dauka wayarta ta kunna data ta sake dubawa pherty na online amman har yanxu bata mata rply ba taji haushi tace
"Ku marubutan nan say ayita muku mgn kuyi shiru ku kyale mutum"
Cikin 5mnt sayga rply din pherty tace
"Kiyi hkr ban lura bane ina wani abu shiyasa amman arinka mana uxiri pls"
Tace "uhm nidaii ay namiki uxirin 4hrs bakimin rply ba amman shikenan ya wucce yah kk "
Tace
"Qlau wh ix dt ? "
Tace
"Am asma'u by name ina karanta novels dinkine shine na samu no dinki nace bari na gaisheki "
Tace
"Eyyah ngd"
Tace
"Wai ya kike yimin yanga kafin ki amsa nifa macece inda hali ki sakani group dinki "
Banxa tayi mata itama bata damuba taci gab ada abinda takeyi
Washe gari aka kawo kudin neman aurenta da kayan sakayan sah rana ansa date din biki december on 28 amman babu wata kwakwarar jituwa tsakaninta da ango
[11:43am, 10/3/2016] Halimatu Lawal Nv: 3�1⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
2dys da sa ranar aurensu say gashi yaxo gdnsu yaje suna gaisawa da mama yace ina ammar tace ya fita bay dawo ba kila ka gansah yanxun kafin ta karasa rufe baki say gashi kamar daga sama ah firgice ya shigo mama tace lfy yace inafa lfy ga yan gdnsu maryam can sun tare husna ah hanyarta ta dawowa islamiyya mama tace shine ka barota yace aah nima yanxu ake fadamin shine naxo na duba ko bata dawo ba kafin ya rufe baki sas da mamah har sun fita
Tun daga nesah suka hangeta taci damara da hijab dinta tana ta xuba dambe da qarti gun ya cika tab da mutane anata raba fadan yaki rabuwa da an rabasu say ta koma an kasa rabasu gashi say dirkar maxa takeyi kamar turon giwa ammar ya karaso da sauri ya riketa ke miye hk anata rabaki kinki rabuwa wani mugun kallo tayi masah tare da cewa
Dallah malam sakarni aii kana tsaye aka fara fadan kaki tsayawa ayi dakaii yaki sakinta tace wllh inba sakeni ba xan raunata ka sakeni nace da sauri ya saketa sas ya karaso gun ya riketa xo muje gd yi hkr tace dan Allah ku sakeni kun rikeni sunata dukana yace baxa'a sakeki ba tace ka sakeni nace yace kiyi abinda kikaji xaki iya bata tsaya saurarensah ba ta saka guwar hannut ta dakar masa baki ba arxiki ya saketa cikin sauri juyawar da xatayi ta dauke maryam da mari say ta mari mamansu
3�2⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL
BALA
( serdeeyerh😘 )
Aikam aka rinchabe da dambe ita daya su ukku harda mamarsu su hudu mata ukku namiji daya da suka rufar mata gaba dayan su say ta durkushe kasah ta dauko wani katon dutse ta jefe kan uwar ta kara dauka ta jefawa namijin tana sake dauka suka ruga cikin gd tace kananan yan iska to wllh dai2 nake daku mama na tsaye ita husna bata haushi ba bata bata mata rai ba hasalima burgeta tayi tunda ga namiji ya kasa tsayawa ya gudu gd da ya gudu kuma ya mata karya
Tana juyowa taga anata kallonta tace lfy akaxo akamin tsaye ko na xama bakuwane yau ah uguwar?? Shiru sukayi say wata xaqaqiya tace eh kin xama bakuwar dan kinga ana daga miki kafa kika kowa iskanci sown ranki to wllh duk wanda kika sake tabawa saynayi maganin ki kafin ta rufe bki taji saukar duka
Ta rinka dukanta kamar Allah ya aikota say da ta gaji dan kanta tukun ta rabu da ita tace kije ki fadawa wanda ya turoki shine dai2 dani bake ba in yaxo ya daureni dan makullin ya bace yan iska kawaii tunda abin iskancine babu wacce xan sake dagamawa fuuuuu ta wuce gd yah ammar na biye da ita sas ko ya tsufa gd tunda aka mishi kamm daya yayi gd yana mamakin jarabar yarinyar anya xay iya aurenta kuwa dan ba shakka xata iya hallaka mutum
Suna komawa gd abbansu na dawowa mama ta bashi lbrn abinda ya faru yace to Allah ya kyauta da ina ganin ta natsu ashe bata natsu ba mama tace aah ta natsu fa aii su suka jata na gwammace da inkai karar anma yarona abu gwara ah kawomin tashi Abba yace to Allah ya kyauta tace amin yace mata gobe xanyi tfy xanje wata samminer xanyi one week tce Allah ya kaymu yace amin
3�3⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Bayan abba ya tafi wajen 10am akayi sallama babu kowa ah gdn say ita kadai tana jinyar inda tasha jimga mama tace ki leqa kiga waye say ki fada musu abban naku baya nan tace to tana ko xuwa ta tarar da yayan ruky ne yarinyar da tayima duka jiya
Tace waye ke sallama yace nine bake nake nema ba ubanki nake nema dan shine dai2 dani bake ba bare yayanki mai kama da mace fittt tayo waje gaba daya tace me kace ya sake maimaitawa kafin ya rufe tace kaii dan samari gyara mgnr ka tun kafin na sauyama hallita yayi mata wani kallon raini
Yace ke ki kiyayeni wllh dan yanxu xan karairayaki an barki cikin uguwa kinata yiwa mutane iskanci babu mai iya kwabarki da kowa fada kikeyi ah titi sbd tsabar BALLAGAXANCI wani ihu ta kurma ta daka tsalle ta wanke sah da mari tana juyawa ta hanko motar sas ta karyo kwana aikam ta rinka kurma ihu shi kuwa wancan ya daga hannu ya dauketa da mari lafiyyayu guda ukku dai2 da tsayawar sas
Aikam jini ya fara xuba hancinta da bakinta ta xube kasa ko motsi batayi da sauri sas ya fito daga mota yayo kanta amman makirar yarinyarnan tayi laqwam kamar marar raii cikin kankanin tym yayi waya brck say ga xugar sojoji ta cika uguwar cikin 5mnt kota ina
3�4⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Mama na cikin gd tanata jin haniya tace bari dai nje na gani kar ace da yarinyar nan ake fada da fitarta taga uguwa ah cike da army's duk wanda suka gani say su jefashi mota ba mace ba namiji hankalinta ya tashi da sauri ta juya ta rufe get
A rikice ta dauka waya ta kira abbah yace lfy tace inafa lfy anyi sallamah nace husna ta leqa naji shiru inata jin hayaniya ina leqawa naga sojoji cike da uguwar duk wanda suka gani say su kama yace subhanallah aii kinji tsiyar jiya ana miki mgn kikace burgeki tayi ga irinta nan
Ni nasan mutanen nan baxasu kyaleta ba yanxu bari na kira alhj abubakar in yana gari koshi ko suleiman yana kiran no din abban a kashe ya kira ta suleiman taki tafiya sake kiran mama yace to nmbr's dinsu basa tafiya mama tace innallillahi to bari mu xubama sarautar Allah ido
Acan kuwa tana hsptl hankalin sas ah tashe yanata du'a'e tana ji ana komaii amman sbd tsabar jan sharri tayi liff harda numfashi sama2 doctor yace masa ta fara numfashi amman jikinta yayi kumburi accidet tayine ??
3�5⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Yace eh doctor yace to Allah ya kyauta yace amin in ta farka ta samu koda tea ne tasha cos xa'a mata allura kuma kashe jiki takeyi inba mutum bayci abinci ba say tym din ya tuna da ko yan gdnsu basu sani ba cikin hanxari ya fita daga hsptl din ya nufi gdn nasu ah hanyarsah ta xuwa gd yayi yaransah waya yace dawa2 kuka ma suka mashi bayani yace ah sakesu arike wanda suka fara kamawa suyi masa kasa2 dashi karku barshi say kunga ya wahala sukace owk sir
Yana isah gd ya tarar da mama tanata sallah tana addu'o'e tanajin sallamar sa tayo waje tace suleiman ina ka shiga dan Allah ka dubomin husna daga yin sallamah nace ta leqa shikenan najita shiru har yanxu gashi gdn babu kowa yace karki damu mama tana hsptl nina kaita yanxuma ana bukatar bata abincine b cos xa'a mata allura ne jikinta duk ya kumbura ina tunanin suma tayi
Cikin rudu mama tace yau an shiga ukku meya sameta harta suma ko sojojin ne suka daketa yace aah mama inajin wanda kikace yayi sallama shine nagani kofar gd akan idona ya daketa kuma ta fadi nine naturo sojojin sukama sah shine suka kama dukka wanda ke waje uguwar amman nayi musu mgn yanxu su sakesu su mama tace alhmdllh Allah ya tsare gaba yace amin hsptl din ya kaita ta kira abbah ta masa bayani kwanan ta biyu aka sallameta
[11:43am, 10/3/2016] Halimatu Lawal Nv: 3�6⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Ranar da aka sallamesu ranar aka kira sas ah gun aiki xay tafi cos na 6month a sudan amman sai nan da 2weeks xay tafi daga gun gd ya wucce ya samu ummansah yayi mata bayani tace to yanxu ya xa'ayi da mgnr aurenka yace umma to mexay hana ah bari say na dawo tukun tunda daman can ni ba sown yarinyar nake ba wani mugun kallo tayi masah wanda yasa shi dole yayi shiru tukun tace ai bani xaka fadamawa ba say ka bari say ya dawo ka gaya masa yace Allah ya huci xuciyarki umma ni ba wani abu nake nufi ba wllh yarinyar batajin mgn yau aka sallameta daga asibiti tace meya sameta nan take ya fada mata komaiii harda kama wanda ya mareta da yasa akayi tace to aini banga laifinta ba hk nake sown mace mai kamar maxa shiru yayi can kuma yace umma to ya xanyi meenah umma tace wacece hk kuma umma wacce na kawo miki nan ta gaisheki wani dogon tsoki taja mtswwwwwww wannan makaryatan tana farawa ya tashi yabar gun
ASALINSU
alhj abubakar suleiman shine cikakken sunansah dan asalin garin nager ne aikin gwamnati ne ya kawosah garin katsina da matarsah hjy aysha Allah ya axurtasu da yara ukku suleiman shine babba say husna qanwarsah wacce ke u.s tana aure say usman shine auta ah tym din sas ya sow yayi aure ya akwaii wata qawar husna dake xuwa gdn gunta yayan yarinyar yaga husna yace yana sownta anyi komaii na biki say da tym yaxo yace ya fasa shi baxay aura mahaukaciya ba tym din meenah bata gari har wani frnd din sas yace yana sownta akayi auren shi kuma sas sunyi promise na aure da meenah gashi ta tafi ghana karatu iyayensah sukace baxay aureta ba say gashi Allah ya kawo ma'u BALLAGAXA 😉
3�7⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Da tashinsah gdnsu husna ya wucce yaje ya sameta ah kitchen mama batanan babu kowa gdn say ita daya tana ta aikinta yashigo da sallamarsah ya ta amsa tare da gaishesah tace aikam mutanen gdn basanan sunje uguwa amman suna gab da dawowa shiru yayi ya xuba mata ido tanata koro masah bayani shi mamaki take basah in tana hauka kamar ba itaba amman yanxu yaga ta natsu tanata harkar gabanta koda yake ba natsuwa tayi ba silalawa takeyi
Yace aii ba gun mutanen gdn naxo ba gun yar aikin gdn naxo tsike da tsokana ya fada mgn aikam ta juyo ta sauri tace owk aikam itama batanan taje ganin gd kila ta dawo yau but kana iya xama ka jirata ko ka bari da nyt ka dawo or tomorrow duk dayane xaka iya samunta tana mgnr cikin nuna halin ko in kula yace aah yo har wata mai aiki ke akwai ah gdn nan bayanke to bari na miki gwari2 gunki naxo tace owk aii bansaniba danni nasan nafi karfin yar aiki ah gdn nan goo on yaron gd fada abinda ke tafe dakaii cikin gaggawa dan ina da abinyi wani kayatacan murmushi yayi
Yace naxo ne na fada miki xanyi tafiya nan da 2weeks i thing xankai wajen 6month shine naxo naji xaki iya jira har na dawo tukun ayi mgnr aurenmu ko ah daura auren say na dawo ayi bikin? Tace oho yace kamar ya tace kamar yarda kaji daman bakaii keta mgnr aurenka ba ni bansan kanayi ba cos baka tabajin nacema ina sownka ba yace karya kikeyi ah gaban abbana kince u will luv mee
3�8⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Kai kuma da yake karamar gwalwane dakaii say ka saum am really ko ? Sakin baki yayi yana kallonta lallai yarinyar nan yace toni kuma ce miki akayi ina sownki yarinyar da ko hankali bakida shi kin girma amman kullum say hauka kikeyi in banda darajar iyaye wllh da ko dauramin ke akayi ah kafa xan kwanceki na yar tace kaiiii ammanfa kayi kokari gyara kaban gu naci gaba da abinda nakeyi yaki gyarawa tace malam ka gyara kaban hanya yace in ban gyara bafa tace na bugeka na wucce yace to bismillah aikam ta taho da karfinta ta bangaje sah amman ko motsi bayyi ba tce pls kabani hanya na wucce yace baxan bayar ba kiyi duk abinda kikaji xaki iya tace sowrie plx kaban gu na wucce kar abincin nan ya kone yace ya dade bay kone ba ta kasan hannunsah tabi ta wucce shima yayi tafiyarsah
Abbansah yaxo ya samu abbanta yaxo ya fada masa yace yanxu ya xa'ayi xa'a daura auren ne say ya dawo ayi bikin abbah yace aah kawaii a daga bikin in ya dawo aii say ayi abban yace owk babu matsala Allah ya kaymu tym din yace amin ya rabbi
3�9⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Washegari da safe tana kwance shiru ita daya tace da wayata bata lalace ba ai da yanxu ko da novel ne ai da karanta tashi tayi ta saka after dress dan riga da wando ne ah jikinta jeans ne black da top pink kayan sunyin mata kyau ta dauka hand back ta nufi dakin mama tace mama xanje gdn abbanah tace to kardai kikai magrib tace to harta fita mamah ta kirata tace husna dan Allah banda fada ah hanya duk wanda ya jaki karki biyesah dan Allah kisan kin girma kinji tace to mama
Machine na hau dan yah ammar bayanan mama kuma bata barina driving ni kuma nasan sas baya sown hawan machine shiyasa ta hau dan ransah ya baci ne aikam machine na ajiyeta shi kuma yana shigowa senter gdn wata muguwar harara ya sakar mata itakam ta saki wani qayattacen murmushi najin dadi batama lura da mutanen da suke tare dashi ba ta shiga cikin gdn tana shiga harabar gdn yana kara sowa hamxa yace mr sas waccan kamar mrs sas ko yace uhm mrs hauka daii daria faisal yace nifa wollah tsoran yarinyar nan nakeji sas yace chap wllh ka dena tsoranta dan wllh xata raina ka jiya aii say da mukayi da ita nan ya basu lbr tare da cewa amman fa wollah ta maxa nayi jikina yayita dukan tara2 dan karta nausheni wollah ta kware da iya naushi daria suka saka gaba dayansu
4�0⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tana shiga cikin gdn ta tarar da umma da atee ah kitchen da sauri ta ajiye jakarta da after dress din tace umma fita xan karasah tace aah yaushe kika shigo tace yanxun nan tace to daga shigowarki sayki shiga kitchen tace ba komaii ummah nan ta shiga tana ta ci gaba da aikin atee nadan kama mata tana cikin aikin ne say ga sas dasu faisal sun shigo shi ya fara shigowa ya hangota ah tsaye wani iri yaji xuciyarsah babu dadi cos baysan xasu sameta ah hk ba da bay shigo dasu hamxa ba wani kishi ya xiyarci xuciyarsah da sauri ya karasah kitchen din ya tsaya ah bayanta juyowa yayi yace ku shiga ummar tana ciki wuccewa kawaio sukayi da sauri ta juyo tace lfy xakaxo ka mana tsaye anan yace anje an tsaya din atee na ganin hk tabar kitchen din
Yace kee meyasa baki da hankaline dubi yarda kike bakya tunanin mutanen xasu iya shigowa ko ayi baki kar na sake ganinki da wannan shigar tace to abbah yace ke bana sown shashancin banxa ina miki mgn kina fadamin mgn tace naje na fada kiranka nayi ina ruwanka da shigata nifa bana sown takura wllh hannunsah ya saka ya mude mata baki yace wllh in baki denamin masifa da tsiwa ba sayna yanke wannan bakin naki marar kunya kawaii tace nicee kaii ðŸ˜ðŸ˜ðŸ˜ðŸ˜ me kikace oho
[11:44am, 10/3/2016] Halimatu Lawal Nv: 4�1⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Umma ta fito tace aah mai sunan manya miye hk tana aiki kaxo ka tsareta yace umma dubi fa yarda take banda nayi saurin kara sowa da hk su faisal xasu ganta ummah tace to miye ina ruwanku da shigarta yace umma dubi kayan jikinta fa tace to waii saime yace uhm babu da yaxo fita say da ta take masah kafa ta murxa tukun fisgota yayi umma tace miye hk waii da sauri ya fita say da ta gama abincin nan kab suna xaune da umma tace waini husna ina wayarki ne say ayita neman nmbr ki a kashe tace eyyah umma lalacewa tayi aii yau wajen one week tace amman mai sunan manya bay sani ba tace ya sani umma dan ah gabansah ta fadi ta lalace tace ashha kila bari yayi say xay tafi ya baki wata tace uhm xan tafi umma nabar mama ita kadaii
Tacd to baxaki bari abbanku ya dawo ba tace aah xan wucce ne tace bari na kira mai sunan manya yaxo ya mayar dake gd nace aah umma ki barshi na tafi kawaii tace aah bana sown musu shiru kawaii tayi say gashi ya shigo umma tace ka ajiyeta gd yace nifa umma wllh in na dauke hauka xatayita min ah mota
4�2⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tayi karab tace Allah ya hadaka da mahaukaciya wllh can kaga mahaukaciya an gayama daman ina sown binka ne in banda darajar umma me xaykai ni shiga motar aljani ðŸ˜ðŸ˜ðŸ˜ yace kee nine aljanin tace eh kaine aljanin bashi bane wani mari ya wanka mata har say da bakinta ya fashe dandanan say ga jini aikam ta tsorata dan bata taba ganin wanda ya daketa har taji xafi hk ba aikam hankalinta ya tashi wani irin tsoransah ya shigeta sosaii koda suka tafi tunda ta shiga motar batayi kwakwaran motsi ba ummah ko kafin su fito tayita masa fada duk say yaji ba dadi
Har suka isah gd tace komaii ba ko kwakwaran motsi batayi ba salula place ya tsaya shiga yayi yabarta ah cikin motar waya ya siyo mata iphone6 qirar LG bude gaban motar yayi ya daura mata kwalin wayar akan cinyarta ya shigo motar
4�3⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Yana shigowa yace ga waya nan nasiya miki ki buda ki gani in tamiki kasa mgn tayi sbd wani irin xugi da bakinta keyi da qar tace ngd da sauri ya juyo ya kalleta yace sauke hannunki ah bakin ki da sauri ta sauke sbd yanxu tsoransah takeji yace lalalah ya kayi bakinki ya kumbara hk a ranta tace dan rainin hankali ka fasamin bakin kuma ka rinka tambayata
Tsawa ya daka mata ba dake nake ba waii kikamin shiru da sauri tace marin da kamin ne ah firgice ya sake kallonta yace eyyah sowrie dear bansan xanji miki ciwo ba shiru kawaii tayi suna isah gd ta fita da sauri tanaji yana kiranta amman ko juyowa batayi ba kasa daurewa yayi har fito xau bita kuma say ya fasa a ransah yace tunda ta fara tsorona bari na rabu da ita
Tana shiga dakinta ta nufa da ruwan xafi wani irin xafi taji har cikin ranta dan2 xaxxabi ya rufe aikam cikin kankanin tym ta fara karkarwa kwancia tayi ta rufe da blanket mama ta shigo dakin batama san ta dawo ba aikam da sauri ta karaso ta taba jikinta taji xafi xauuu tana tace meke damunki bkinta ya sake kumburi baxata iya mgn ba say dai tayita kallon mama tace yaushe kika dawo ma waiii nanma ba mgn say ido umma bata lura da bkin ta ba say tym din
4�4⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Cikin tashin hankali mama tace meya sameki ah baki nan ma shiru dan bata iya daga bakin da sauri mama tayi waje tacema abba xokaga asma'u inajin accident tayi gun dawowarta da sauri ya nufi dakin cikin sauri yace kamota mukaita hsptl
Acan kuwa bangaren sas bayji dadin abinda ya mata ba gashi yaga bakinta har jini yayi kuma yayi fushi Allah day yasa hakorinta kar yayi ciwo shi kadai yake yan sake2 dinsah har ya isah gdnsah yana shiga ya tarar da meenah ah xaune ta daura kafa daya kan daya tana ta jijjiga tana ganinsah da sauri ta tasow xatayi hog dinsa kome ta tuna say ta fasa shikam tsayawa yayi yana ta kallonta yana mamakin yarda akayi harta shigo cikin brck din tace sas kenan shikenan ko irin neman nan nawa bakayi kuma kuka yana yayanah husna aii xaman tare bayce hk ba yace ke dallah yimin shiru bayan duk wulakancin da kuka xuba mana mu bamuyi mgn ba sayku xakuyi mgn sbd tsabar rashin kunya da rashin mutunci ficcemin daga gd tun kafin na wulakantaki cikin sauri ta fita dan bata taba tunanin sas nada fada ba dafe kansah yayi ya xauna sakwab kamar marar lakka yace ba shakka idanun yarinyarnan ah bude suke
Acan kuwa ringa2 aka nufi hsptl da husna hankali tashe cikin gaggawa aka karbeta aka bata taimakon gaggawa abbansu sas ya kira abba yana kiransah nan yake fada masa suna hsptl husna ba lfy
4�5⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Cikin 30mnt say gasu sun isow abbah osy ummah umma naganinta tace Allah sarki baywar Allah ai daman nasan sai hk ta faru tunda naga jini ya fita bakinki abba yace kamarya nan ta fada musu duk yarda akayi mama tace maganinta kenan wllh aio gwara da ya mareta abbah yace aikam say ransah ya baci wayarsah ya xaro ya kirasah yace kaxo ina neman ka ka sameni amfani clinic cikin sauri ya amsa yace ganinan xuwa insha Allah
Cikin kankanin tym ya isow abba ya rufesa da masifa yarinka bashi hkr amman ina ran abba ya baci sosai say da abbansu husna yace kayi hkr dan Allah aii laifinta ne gobe xata sake ba aii gwara arinka maketa ta natsu yanxu aii umma tace aii ba duka take bukata ba qatuwar burduwa kamar wannan ace arinka dukanta aii in bera da sata daddawa da wari addu'a ya kamata ku rinka mata bawai duka ba mama tace hkne dakin sas ya shiga
Can ya hangota kwance an rufeta da blanket kanta ya dafa yaji xafi bakinta ya kallah tare da shafawa yace Allah sarki husna da nasan hk da baxan tabaki ba Allah ya baki lfy ah bayyane yake mgnr surutun sah ne ya tasheta daga barci daqar ta bude idonta suka hada ido yace sannu dear kai kawai ta daga masah yace kiyi hkr kinji shima babu mgn kai kawai ta daga masah yace waii bakya iya mgn ne ta daga masa kay yace subhanallah
[11:44am, 10/3/2016] Halimatu Lawal Nv: [9:18PM, 11/15/2015] Serdeeyerh😘: 4�6⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Yace ashe abin har yakai hk dan Allah kiyi hkr ki yafemin wllh bada niyya nayi pls kiyi hkr kinji kaii kawai ta iya daga masa kamata yayi ya tasheta xaune yace ko xaki iya kuskure bakin kila ki samu saukinsah ah hankali tace eh da sauri ya sabo ruwan xafi da roba ya tarba ah gabanta yace kuskura ah hankali aikam tayita kuskurawa dandanan taji bakin kamar ba nata ba yayi sayau sai kumburin da lebbanta sukayi tea ya hada mata mai kauri ah hankali yayita bata dandanan ko ta shanyesa kwanan ta 2 aka sallameta yayi dai2 da tym din tafiyarsah ranar da yaxo gdnsu xay musu sallamah ya samu abbah ya rokesah yace dan Allah abbah in nayi 2month xan dawo ina sow in naxo ayi aurena da husna dan xan danyi one month kafin nakoma abba yace ba matsala suleiman Allah ya kaymu lokacin yace amin
Kiranta yayi ah waya yace ina waje fa ke nake jira da sauri ta shirya ta fita dan yanxu bala'een tsoransah takeji hijab kawai ta saka tukun ta dan fesah turarenta pure luv tun kafin ta kara sow yake kallonta daga sama har kasa ah ransah yace dubeta kamar dukka kenan baysan ta kara sow kamshin turarenta ne ya bugi 👃ðŸ»ðŸ‘ƒðŸ»ðŸ‘ƒðŸ» yaji kamshin har cikin ransah tace ina yuni yace lfy qlau gobe xan wucce amman ko kyakyawar sallama baki tsaya mukayi ba ki dena tsorona inhar kinsan bakiyi laifi ba inko kinyi laifi kiji tsorona domin kuwa ba shakka sayna hukuntaki are u owk kai ta kada masa yace munyi mgn da abbah nan da twoo month xan dawo kuma in na dawo xa'ayi aurenmu tym din dan hk nabar komai ah hannu ammar da usman kome xa'ayi su xakima mgn da sauri tace bama xa'ayi komaii ba daga bangarena say day in nayi shawara da husna yace whch husna tace he ur sister yace owk it right Allah ya kiyaye yace amin i will call u lttr batace kome ba ta shige gd da sauri
4�7⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Tana komawa gd tayi create din whtsapp dinta tanayi taga pherty tayi addn dinta ah hausa novels group 1 aikam ba karamin dadi taji ba ta bita prvt tace Allah ya xuqa miki ruwan albarka ya baki miji nagari pherty tace amin tana shiga group din tayi introduce na kanta humayda da bombour harda saurin cewa remean picture tace kuyi hkr in nayi xan turo muku ( nima dai serdeeyer nasow ganin pix din ma'u BALLAGAXA abinda ya hanani mgn kar inyi mgn ace na cika tsegumi shiyasa nayi tsit amman say da na bita prvt inata kwakwarta har na sakata groups dina nima can suka hade da meenah ah matan kwaraii ita meenah daman ta santa itakam husna bata santa ba tofa ku tayani ido na hada bomb ah group dina )
Akwana atashi babu wuya gun Allah har sas yayi 1month da tafiya amman ko sau daya bay taba kiranta ah waya ba tunda ya tafi basuyi waya ba shi bay kiraba itama bata kira sah ba kwatsam rannan say taga an kirata da wani nmbr mai plus har wayar ta tsinke batayi picking ba say da akayi mata waje 3 mss clls tukun ta daga koda ta daga shiru tayi abinta say da taji mgnrsah tayi saurin gaishesah yace kee shikenan tunda ban nemeki ba baxaki nemeni ba tace banda credit ne kuma vani da no dinka yace amman kullum kina online aii
Tace aii yah ammar yamin sub owk shine baxakice ya baki nmbr na ba ki kirani shiru tayi har yayi surutunsah ya gama tace yi hkr yace inma banyi hkr ba ya xanyi tunda Allah ya hadani careless taji haushi har cikin ranta kuwa amman ta danne tsoro yasa kuma takasa bashi amsa yace kunyi shawarar tace eh munyi tace ayi dinner da kamu amman ummah tace ayi dinner kawaii yace aii bani xaki fadamawa bako hjy kije kisamu ammar or osy ki fada musu ni abinda xanyi da fanx dina in na shirya xan fada miki tace to mgnr ankon bikin fa yace ki samesu ki musu mgn nace miki ko kashe wayarta tayi
4�8⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Ammar tasamu tayi masa mgn yace mata aii yace anko din ke xaki siya ki raba musu dan ya tsara komee nasa tace kenan yasan yayi tsarinsah shine xay wanita damuna da tambaya ammar yace bani xakima masifa ba kirasah ki fada masa dan yanxunan sayna tattakaki wllh tashi tayi tsaye tace to bismillah ðŸ˜ðŸ˜ rabata yayi ya wucce bayce komaii ba dan yasan yanxu sa kwashi yan kallo
2month nayi ko say ga sas ya dawo aikam hidima ta kankama rigi2 pherty tabi prvt tace dan Allah writters nake sow ki gayyatomin aurena ya kusa banda qawaye ina sown kuxomin biki pherty tace ba matsala xanyima mss aysh mgn duk da bata damu da harkar writters ba amman nasan xata xo kuma nima xanxo insha Allah tace ngd xanxo duk garuruwanku na kawo muku i.v
Aikam duk say da husna taje ah satin sukaje sukayi picx din auren ita dashi ta tura ah groups din da take aikam meenah nagani hankalinta ya tashi ranta duk ya baci tace say taje gdnsu husna taci mata mutunci aikam washe gari misalin 4:30pm ah uguwarsu husna tayima meenah tayita tambayar gdnsu harta gane aikam taci sa'a gdn babu kowa ma'un ce kawaii aikam ta fito daga ita say 3quater da wata body hug tana fitowa ta ganta tana ta jijjiga ah tsakar gd da gani kasan bala'ii ne ya kawota tana ganin husna ta fara masifa da xage2 ko inda take husna bata kallah ba bare ta bata amsah aikm can tace BALLAGAXAR BANXA
4�9⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Da sauri ta dago dara2 😳😳 dinta tofa ran mata ya baci
QASHI DA RAI JIJIYA DA BALA'EE MACE MAI KAMAR MAXA HANKAXAMA BUDURWAR DOKI MAI KARFIN MAXAN RAQUN MA TORAN GIWA SA GABANKI INDA KIKE SOW YARINYA MAI DUKAN MAXA AH XAUNA LAFIYA YAU GA MACE TA HAYE MATA
Wani kukan kura tayi ta chakumeta suka rinka damben bala'eee tun meenah na iya ramawa harta kasa say da husna tayi mata ligib Allah ya jefo sas kamar daga sama da qar ya kwaci meenah ah hannunta say da ya fitar da meenah daga uguwar tym din da ya dawo ita harta shigewarta wanka ma xama yayi yajirata harta gama abinda takeyi yace mata miye hadinki da wannan qatuwar budurwa kee waii abadan baxaki girma ba wata irin harara ta sakae masa tace toni na santane da xata xo har cikin gdnmu ta xageni kuma in kyaleta tafita ba tare da na raunatata ba aii wllh tayi kadan yace kidai rinka hkr da rayuwa shiru tayi masa
Aikam kmar yarda tace say da osy ya kaita ko ina takai musu i.v yan hausa novels kuwa say sake fada mata sukeyi kifa tabbatar da munsamu take away dan wllh in bamu samu ba say munyi miki gori kuma ko kin haihu baxamu xo ba ( hahh yan hausa novels fa akwaii kwakwar take away )
[9:40PM, 11/15/2015] Serdeeyerh😘: 5�0⃣BALLAGAXA
NA HALEEMATU LAWAL BALA
( serdeeyerh😘 )
Aikam amarya tasha kyau ranar dinner anyi mata kara kamar daman can munsan juna pherty ko nachan bangaren take away tana kokarin sama mana nida ita da gudan jinina ( mss aysh ) yan hausa novels ko say binmu sukeyi da suka ishemu say pherty ta daga rigarta ta tura ciki
M jabo ita da m shakur da m khadee sun kure daman su gun boye take away humayda ko tunda ta samu ta karba tsit tayi kamar bata gun nan atee ko tana can wanke2 kamar xay kasheta
@BABA MONO HAXOR
FOR MORE INFORMATION
CALL OR MESSAGE
08108811856
OR
08106384398
No comments:
Post a Comment