• A BAKIN AUREN KI KASHI NA 1 ONE BY BABA MONO
    A BAKIN AUREN KI KASHI NA 1 ONE BY BABA MONO
  • Download Now @BABA MONO HAXOR
    FOR MORE INFORMATION 
    CALL OR MESSAGE
    08108811856
       OR
    08106384398

    9/29/16, 8:34AM - Queen Safiyyert馃憫: A BAK'IN AUREN KI...
    漏Feenat Ja'afar.
    1_Sauri take tamkar taci da k'a, kai daga ganinta
    ka ga marar gaskiya, a d'ai d'ai layin da zai
    sadata da gidanta ta t'saya tamkar munafuka ta
    d'an leka, da sauri ta komar da kai tare da dafe
    kirjinta mai barazanar fashe mata... "Na
    shigesu.. Ja'afar? Ta fad'a tana mai sake
    lekawa, sai karaf sukai ido hud'u dashi,tuni
    buguwar zuciyar ta ya k'aru, bata ta6a ganin shi
    a irin wannan yanayin ba.
    "Mey yasa kika fita bayan yace ka'rki fita?...
    Bak'in g'yalenta tasa tana t'sane gumin dake
    t'sat'safo mata, cikin jihadi ta fito daga inda ta
    boye harda d'aure fuskarta tamkar bata ganshi
    ba.
    Kanta na k'allon gefe tazo d'ai d'ai kofar gidan
    zata shige ba tare da ta k'alli yanayin nashi ba..
    Turus taja ta t'saya, ganin yadda ya d'aura wani
    mukulli kan wanda ta rufe gidan dashi, cikin
    k'arfin hali fuskarta na gefe tace "ya haka?
    Wanda bai nan ma yafita,hakan yasa ta kara
    fad'in "Ya Ja'afar ya haka?.. Tamkar kububuwa
    yake cika, ji yake tamkar ya rufeta da duka dan
    takaici, Ashe d'uk uban rat'suwar Salma ta mai
    kan ta d'aina a fatar baki ya t'saya?..
    Mota ya bud'e yana ko'k'arin shiga ta mot'so da
    sauri, "Ja'afar magana nake fa... A tunzure ya
    juyo da nufin kifa mata mari tai baya da sauri
    gabanta na fad'uwa.
    Lalle yau ta ta6o ran y'an maza, cikin bacin rai
    yai mata k'allon banza, "kin za6i gidan suna
    sama da sharad'i na koh? Toh mey kika dawo yi
    min gida? Koh kin manta da sharad'in da na baki
    na in kin fita toh kin fita "A BAK'IN AURENKI?...
    Ido ta zaro tana dubenshi, kawai sai ta dake,
    cikin k'arfin hali tace "A BAK'IN AURENA fa kace
    Ja'afar? Daga gidan sunan shine har kake
    wannan kumfar bak'in?.. Ta karasa tana y'atsine
    mishi fuska,kawai sai ya k'ada kai ya shige mota.
    Ganin da gaske tafiya zai yasa da sauri t ajiye
    t'siwar ta fara kiranshi, ina,tuni ya juya a kalar
    motarahi cikin zafin nama, da sauri ta mat'sa
    ganin sai ya iya bi ta kanta..
    Tana ganin da gaske yake hakan yasa tuni ta
    t'sure, hannu ta aza bisa kanta cikin nadamar
    fitar da tai sunan da ba'a ma gaiyace ta ba, "na
    shiga uku ni Salma.. Na ja ma kaina wani bala'in..
    "Yanzu igiyar Aure na biyu ta t'sinke kenan?..
    Tuni zufa ta kara zubo mata dan tunawa da
    kalaman Babanta, "d'uk randa zaki kara maimaita
    haka Salma sai na 6alla kafarki in kin doso
    gidana.... Fad'uwar gabanta ta t'sananta,t'saf
    Baba zai aikata mata hakan,
    ta k'alli gabar,da yamma, ta ma rasa ta ina zata
    fara? Gefen dakalin gidan ta d'an dosana, da
    d'ukkan hannunta biyu ta dafe kai,tuni kalaman
    Ja'afar ya dawo mata, "in kin fita kin fita A
    BAK'IN AURENKI....
    Ku biyoni Bayan sallah dan jin yadda zata kaya...
    By
    Feenat
    Ja'afar.
    9/29/16, 8:46 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAK'IN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. *3*-
    Kai ya k'ada mishi, _"aure ba shine mafita ba
    Ja'afar,ka g'yara wacce ke hannunka tukun,bana
    tunanin wannan shawara ce_. Murmushi yai tare
    da k'ada mishi kai _("I know)_.. _"Amma ka gane
    ba dan dad'i zanyi ba,nasan d'uk duniya ba
    abinda Salma taki jini irin nace zan kara
    aure,dole na d'andana mata mad'acin da ta
    d'andana min nima_. Murmushi Garba yai yana
    K'allonshi,wai yau Ja'afar ke maganar zai
    d'andanawa Salman sa mad'aci?.. Kai ya girgiza,
    lalle Salma tai wasa da damarta, dan yasan irin
    dimbin son da Ja'afar ke mata, sai dai gashi za a
    kaita a baro,dan ta fara sane ma abokinshi..
    _"Bana tofa tawa ba nikam,nasan da kai da
    Salma sai Allah,ni d'ai kai tunani abokina,kar ka
    yanke hukunci cikin fushi azo daga baya ai
    nadama_... Baki ya ta6e, kan ya ciro mukulli a
    aljihunshi ya mika mishi, _"k'ar6i mukullin
    motarka,dan aure kam nayi na ma gama,kuma
    *Bintu* zan aura kasa ido_.. Ido waje Garba yake
    k'allonshi,kan ya k'yalk'yale da dariya, _"lalle ka
    d'ebo aiki..za kuma ka dasa ma Salma zargin ka
    cikin ranta tunda kasan komai_... T'saki yai kan
    yace _"zanso hakan ya kasance, dan zata fi jin
    haushi sosai_.. Kai Garban ya k'ada yana kunshe
    dariya, _"muje na sauke ka toh na Salma da
    Bintu,kai (scene) din nan zai dad'in k'allo
    wallahi_.. Ya karasa da dariyar keta. Murmushi
    kawai yai suka shiga mota,har suka isa gida
    Garba na mishi t'siya..da ya had'o shi da Salma
    zai kicin-kicin. ************************ A wajen
    Salma kuwa,sai da dare yai tana k'wance
    d'akinsu na da sai juyi take,wanda ita kanta ta
    rasa dalili,har yanzun haushin Ja'afar na kasan
    ranta na ya mata wulakanci, sai dai da ta tuna
    rabuwar igiyarta d'aya sai taji fad'uwar gaba. Yau
    gata a katifa ba ta ita da Ja'afar d'inta ba?..yau
    d'aya ta raba alakar matashin kanta(kafad'ar
    Ja'afar) sai pillow... Hannu takai kuncinta,da
    mamakinta hawaye take,kawai sai ta ida
    karasawa ta fashe da kuka.. Wanda kai da gani
    na k'ewar Jafaririn ta ne da t'sant'sar
    nadama,amma ina,zuciya taki amsar hakan.. Ga
    uban sauro da ya damu k'unnenta da ihu duk da
    da Katanga a t'sakaninta dasu(net), ga uban zafi
    ba wuta ba (Gen), d'uk t'siya tasan da a gidanta
    ne da yanzu tana shan iskar injin da Ja'afar ke
    k'unna mata d'uk dare ta k'wanta dan bata bidar
    zafi.. Ga mama tace ba mai tada mata inji
    Babanta baya gari, kuma bata kud'in mai... ***""*
    Shima hakan take ga Ja'afar, kusan a hali d'aya
    suke,sai dai shi kawai ya kura ma fankar d'akin
    da ke kad'awa a saman d'akin ido. Tabbas har
    yanzun baida sama da Salma koh a kasan
    zuciyarshi.. Yana sonta, so marar misali,duba ga
    yadda suka gina soyayyar tasu kamin aure.. Da
    za'a ce mishi a da Salma zata sauya hali gaba
    d'aya musamman akanshi da zai mu sa... Juyi
    yai ya jawo filo,d'uk t'siya tanan yai k'ewar
    Salma.. Dan karamin t'saki yai kamin ya tashi yai
    waje dan kashe inji. *By* *Feenat Ja'afar*
    9/29/16, 8:48 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAK'IN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 4-
    Salma Umar Y'a ce ta biyu gun Mama(Haj Rabi'a)
    da Baba(Malam Umar),y'an asalin Yobe
    ne,kasuwanci ya kawo kakansu Kano da rabon su
    Salma. Su biyu kawai ne a gun kakan su Malam
    Bukar Mai buhu,baban su Salma ne karami, sai
    yayanshi Baba Aji, yaranshi a kallah za suyi
    (16),yayin da Baban Salma ke da uku,Aisha
    (Aunty A'i)dan tafi Salma sosai,Salma,sai Ummi.
    Kasuwanci ne gadon su Baba,dan koh bayan
    rasuwar kakan su Salma sun cigaba da juya
    abinda ya rage musu. Suna taimakon juna
    sosai,hakan yasa kansu yake a had'e, duk da
    rufin asiri ne kawai na Allah. Sannan d'ai-d'ai
    iyawa sun bama yaran su karatu da tarbiya,suna
    da t'sanani musamman Baban su Salma. Sai dai
    fa ita Maman su gani take kakarsu ta yanke
    saka,tunda Allah ya hore mata yara mata uku
    setin samira ta zuba jari,shi yasa d'ukkan wani
    abu akan A'i yake karewa dan ita tasa a lokacin.
    Ba lefi,ak'wai dan k'yau irin na ainashin mutan
    kanuri,sai kuma Maman dake asalin Shuwa,ba
    farare bane,za dai mu iya kiransu da _"black
    beauties"_sirrin su kuwa,diri ne da yalwar gashin
    ka da _"beauty point"_ _(dimples)_.. Wanda
    tamkar kowa diga mata ake. Hakan yasa kasuwar
    Aunty A'i ta daga da sauri,tuni k'wa Mama abin
    nema sai ya samu,hakan yasa ta kara sa ma
    sauran Burin da yafi na Aunty A'in.. Barin Salma
    dake doguwa ce cikin su. Ita kam Salma bata san
    ma ana yi ba. Kasantuwar shagonsu Baba ya
    zama biyu sai ya zamana aiki yai musu yawa,
    har bai samun damar dawo wa gida cin abinci sai
    d'ai Ummi koh Salma su kai mishi. Ranar kaiwar
    Salma ne,tai shirin Islamiya ta doshi shagon su
    Baba. Tunda ta ajiye abinci taki gaba taki
    baya,kamar dai da alamun an mata abu daga
    gida. Murmushi Baban yai kan yace tazo.. _"mey
    aka miki uwata?_ Hawaye ta dan matso halamar
    6aci. _"Mama ce ta hana ni kud'in tara_. Kai
    Abban ya k'ada yana murmushi kan ya sa hannu
    a aljihu ba chanji,gudar naira dari ya fitar kan ya
    nuna mata shagon kusa dasu taje tai chanji. Da
    sallamarta ta shiga,ta gaida shi,shago ne na
    kayan k'yallin mata na sawa, attamfofi da
    laces,ga materials kala kala,d'uk zuwanta bata
    ta6a shiga shagon ba sai yau. _"Salamatu y'an
    mata,ina su Ummi?_ Murmushi tai mishi,dan tana
    ganin shi gun su Baba, dattijon na da kirki da
    fara'a, banda yaron shagon shi da koh k'allo bai
    mata ba, _"suna gida,Baba ne yace aban chanji_.
    Kai ya k'ada, kan ya k'allo na zaune a acikin
    shagon rike da littafi halamar yana dubawa.
    _"amm *Ja'afar*_.. Kai ya dago karon farko,
    _"Na'am Abba_,, sai lokacin ya kula da Salma,
    _"Ba wa Salma naira ashirin ta tafi kar tai latti_.
    Kai ya k'ada kan ya kara k'allo Salman wacce sai
    hange take koh za taga wani dan islamiyar su
    tana mika hannu. _"k'ar6i man_.. Juyo wa tai
    taga yana miko mata kud'i fuska ba fara'a, da
    sauri ta k'ar6a tana tafiya tana fad'in _"na gode
    Abba_. Da k'allo Ja'afar ya bita,yana ganin Ummi
    ce mai rawar kai ashe sauran ma haka suke.
    _customers_ ne suka tada shi ya shiga shagon.
    Washegari ma sai ga Salma,wannan karan koh
    shagon su Baba bata je ba tai shagon su Ja'afar.
    Da mutane da kusan d'uk y'an mata ne suna
    siyayya, yana ganin Salma ya had'e rai, sam yaki
    jinin a 6ata yaro da kud'i, ita kam Salma harda
    mishi murmushi tana dago mishi hannu da kamar
    abu aciki. T'saki yai,kan ya cigaba da abinda ya
    ke,sai da ya sallami kowa kan ya ganta tana
    gaida Abban shi da ya fita yana nuna mata cikin
    shagon. Da dan gudinta ta shigo,a tunanin shi
    kud'i Abban yace ta kara k'ar6a gun shi,dan da
    zumudinta ta gaida shi. _"dama Abba ne yace
    in_..... Cikin fad'a-fad'a ya katseta, _"bani da
    chanji nima yau,jiya an baki kinji dad'i shin_....
    Shiru yai sakamakon idonta da yaga ya cika da
    k'walla tana k'allonshi. D'uk kuma sai jikinshi yai
    sanyi.. A hankali ta ajiye masa gudar naira
    ashirin akan benci ta juya tana goge hawaye. Ba
    dai kud'in shi ta biya shi ba dan ya mata fad'a?
    Da sauri ya d'auka da niyar k'wada mata kira ya
    mayar mata sai dai tuni tai nisa sosai. D'uk
    kuma sai yaji bai k'yauta ba. Yana nan zaune har
    Abba ya dawo, _"kaga Salamatu wai kud'in ka na
    jiya ya hau shine ta dawo ma dashi ba"_.. K'allon
    Abban yai da sauri, _"Abba kud'i kuma?_
    K'allonshi yai kan ya k'ada mishi kai, _"sai da
    nace ta tafi wai A'a tana da wani,Salma ak'wai
    hankali, ashe batai ma magana ba?_ Shi dai
    Ja'afar yai shiru yana jin Abba,sai ya kara jin
    wani iri. *By* *Feenat Ja'afar*.
    9/29/16, 8:50 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAK'IN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. *5*-
    Washegari sai zuba ido yake yaga Salma
    shiru,dan d'uk jiya ji yake bai k'yauta mata ba.
    Sai d'ai Salma har k'wana biyu shiru ba koh kalar
    ta sai Ummi ke zuwa kawo abinci. Ranar Ummi
    ta kawo zata tafi ya t'sayar ta da tambayar ina
    Salma k'wana biyu? "tana gida Yace "ya bata
    kawo abinci sai ke?.. Tana zungura baki tace
    "sai gobe ne nata kawowar. Dan koh ita Ummi
    Ja'afar ke hanata zuwa gun Abba mai k'yautar
    naira biyar goma.. Sam baida fuska,shi yasa taki
    jinin shi. Washegari kuwa tun da ya ga lokacin
    kawo abinci yayi yake k'allon shagon su
    Baba,yau ga k'ananan shi a shagon baida
    mat'sala. Kamar ance ya dago,sai gata kuwa
    sanye da kayan islamiya,sai dai duk tai kicin
    kicin fuska ba walwala. Yana k'allon yadda ta
    t'suguna ta gaida su Abba kamar kullum, tana da
    nut'suwa ba kamar Ummi uwar bankaura ba.
    Tashi yai kamar mai tafiya wani gun,dai dai
    k'wanar da take bi gida ya t'saya,sai gata
    kuwa,har zata wuce ya kira ta,suna had'a ido ta
    had'e rai,sai ta bashi ma dariya. Hannu yasa ya
    ciro naira ashirin d'in ya mika mata yana
    murmushi, a dan sace ta k'allo shi kan ta kawar
    da kai tare da girgiza mishi kai. *"Salma*..K'all
    onshi ta kara,ganin yana murmushi sai abin ya
    bata mamaki,bata t'sinke da lamarin ba sai ji tai
    yace tai hakuri, kai ta kawar kawai, kin huce?
    tana wasa da hijab d'inta ta daga mishi kai, "toh
    ki k'ar6a in kin huce,na bar miki.. Kai ta kara
    girgiza mishi,kan tace "A'a ka barshi fa.. "baki
    hakura ba kenan Salma?.. Kai ta k'ada mishi,
    yace "toh ki k'alle ni ki amsa maza kar kiyi latti
    kinji K'anwata.. Da lallami yasa ta sakko harda
    dariya,har kusan makaranta ya rakata ya
    dawo,yana mai mamakin fara'ar shi yau ga
    yarinya Salma,sam shi baida sakin fuska
    musamman ga mace d'uk k'ank'antar ta k'wa.
    Tun daga ranar ya zamo in Salma ta kawo abinci
    sai Ja'afar ya rakata ya kuma bata ashirin d'uk
    bayan k'wana biyunta. Sosai sun saba,har in
    batazo ba baya jin dad'i, har su Abba suka kula
    da sabon kawancan Ja'afar da Salma,ana haka
    Baba yasa ya dinga ma wa su Salma _lesson_
    tare da kannenshi tunda ya gama _secondary_
    _admission_ yake jira. Koh a gun _lesson_ misalin
    Ja'afar a Salma yake t'sayawa, in k'wa duka ne
    koh t'sawa Salma bata ciki,sai dai yai ma
    k'annenshi, hakan yasa tun tana karama yaran
    suke ce mata Salma budurwar Ya Ja'afar. A
    lokacin takanyi bori kan bata so,har takai da ta
    kai kara gunshi,sai dai mamakinta dariya ma yai
    mata,yau da gobe har Salma ta saba da tsokanar
    k'annen Ja'afar . Karatu ake sosai za ai _coming
    interest_, sai dai ba Ja'afar dan ya tafi Zaria
    sakamakon _admission nashi da ya fito. Sosai
    Salma tai k'ewar shi,har hakan yasa ta d'aina kai
    abinci shago sai almajiri,a hankali har k'ewar ta
    sake ta suka gama jarabawa sai zaman jiran
    sakamako... Sai dai Ya Jaafar na chan k'wance
    kasan zuciyar ta. Yau ga Salma a _boarding_
    babban burunta kenan makarntar k'wana.
    ************************** Lokaci ya shud'e,
    kamar wasa yau ga nan Salma an zana
    _J.S.C.E_, hutun mai dan nisa ne na yau. Mai
    nut'suwa ce a d'uk y'an gidan su,a layin su,dama
    unguwar gaba d'aya, Salma abar k'watance
    ce,musamman rashin yawanta,kullum kaje in tana
    hutu toh za ka samu Salma a gida. Batta
    k'warafniya irin ta y'an mata masu tashen
    tashi,asalima fitar ta in tai yawa toh islamiya ce
    ta yamma, sa6anin su Ummi da tuni tun kar ta
    far ta kone, dan wanka iya wanka Ummi ta
    iya,hakan yasa Mama ta kara d'aure mata gun
    siyan kayan k'arya. Dan a ganinta ta gama da
    kason Aunty A'i tunda har an kawo sadaki, kuma
    irin wanda mama ke da muradi. Ita kam Salma
    zai wuya ka ga tama sanya g'yale bare har ta
    zauna k'yali. Gata dai mama ita tafi sawa buri,
    ga ta kuma y'ar _boarding_. *By* *Feenat
    Ja'afar*.
    9/29/16, 8:52 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 6-A
    dai-dai k'wanar su Ja'afar take,dawo warta daga
    islamiya kenan,sanye take da dogon hijab ruwan
    kasa mai yashi har kusan kasa,rataye da jakar
    littafai da Qur'ani a hannu,sai dan asirin _skirt_
    nata na attamfa da ya fito _green_ da ruwan
    kasa, duguwa ce,ba zangal ba,tana da kaurin
    jiki,dan ta fita sahun ramammu,tafiyarta a
    nut'sue tafi komai d'aukar hankali. Kamar kullum
    ta daga kai dan k'allon gidan su Ya Ja'afar
    kamar yadda ta saba k'ewar shi ta kawar da kai,
    sai dai taku biyu taja ta t'saya tamkar an t'sayar
    ta. Kanta duk'e dauke da murmushi,cikin
    nut'suwa ta kara k'allon kofar gidan dan tabbatar
    da wanda ta gani.. *"Ya Ja'afar*?...ta fad'a a
    zuciyarta lokacin da ya taso yana mata
    murmushi. Ikon Allah,wai kunyarshi kuma take
    ji,cikin nut'suwa ta d'auke kanta daga gareshi
    ganin ya karaso. "Assalam Alaikum Malama
    Salma.... Wani irin buguwar zuciya taji ya ziyarce
    ta,shekara uku da wani abin ba wasa ba,hatta
    muryar Ya Ja'afar ta sauya mata. Cikin nut'suwa
    ta dago da murmushi ta amsa mishi,kamin ta
    gaida shi a kunya ce, shi dai kawai k'allonta yake
    yana murmushi, kamar mai mamakin kara
    girmanta,ga wata nut'suwa da ta kara shigarta.
    D'uk sai ya kara yaba Salman nashi,ganin shirun
    yai yawa yasa da hannu ya nuna mata hanya
    halamar su wuce. Dan satar K'allonshi tai kan ta
    sunne kai suka fara tafiya. "Salma koh murnar
    gani baki yi,ba koh tambayar yaushe nazo? Kai
    duk'e tace "yi hakuri,yaushe kazo?.. Kai ya k'ada
    da murmushi,kan yace "jiya. Tambayar yaushe
    gamo yake mata, yadda take kunyar tata gun
    bashi amsa d'uk sai ya ji shi wani iri,mace mai
    kunya itace muradinsa. Da haka har kofar gida
    ya rakata yana mata tad'in makaranta da yadda
    suka juma basu gamo ba. Ummi ya k'allo achan
    dan nesa dasu tana tad'i, sai ya tuna mata yasha
    zuwa ai. Ita dai daga murmushi sai k'ada kai da
    Umm,a'a,d'uk ta takure yau a gaban Ja'afar
    d'inta. Ganin haka yasa yai mata sallama tai
    gida.. A katifa ta zauna tana cire hijabi,ta rasa
    wani irin farin ciki take ciki na ganin Ya Ja'afar
    d'inta yau. Sai murmushi take saka cike da
    kunya ita kad'ai kamar yana ganinta. A haka har
    Ummi ta cimmata, dan harara ta sakar mata
    gami da had'a rai. "Yanzu Ummi kinyi dai dai
    kenan? A y'atsine ta k'allo ta tana ninke g'yale,
    "da nai miki mey? Iya jaraba.. Kai Salma ta k'ada
    kan tace "dan t'sabar wulakanci ashe Ya Ja'afar
    yasha zuwa gidan nan nema na in yazo gari
    muna sa6ani sau biyu yana fad'a miki amma
    koda wasa baki fad'an ba? Allah kin ban haushi..
    "Mtsww.. T'saki Ummin tai kan ta ta6e baki,tuni
    Salma ta kule,sam ta t'sani t'saki, bare ga Salma
    K'anwar ta. "Na zata wani abin kirkin ne wallahi,
    toh meye nawa dashi da zai mayarni y'ar aiken
    shi?.. Anki a fad'a miki d'in ki d'au mataki toh.. A
    tunzure Salma ta tashi tayo kan Ummin sukaji
    Mama na magana a kofar d'aki, "Kun fara cin kan
    koh? Yara kamar masu ganin hanjin junansu?
    Baya Salma tai tana harar Ummi, "Mama kimin
    tsakani da ita toh,ta fita harkata dan bata da
    kunya sam wallahi.. A y'atsine Ummi ta harare
    ta,"ka ga kunya manya,akan wannan mai dan
    uban d'acin ran kike wannan kumfar
    bak'in?...baki ta ta6e kan tace "Kin k'wa kama
    abga in dai Ja'afar ne.... "Ke Ummi... Bana son
    fit'sara fa,kullum ina sanarki Salma yayarki
    ce,dole ki bata girma, koh nai mugun sa6a miki..
    Maza bata hakuri. Tana chunno baki ciki ciki ta
    bawa Salma hakuri,ita kam har ta fara hawayen
    bak'in ciki. "Toh fito ki biyoni.. Mama ta nuna ma
    ummin kofa da hannu.. *By* *Feenat Ja'afar*
    Like 路 Reply 路 Report 路 Jul 20
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 6-A
    dai-dai k'wanar su Ja'afar take,dawo warta daga
    islamiya kenan,sanye take da dogon hijab ruwan
    kasa mai yashi har kusan kasa,rataye da jakar
    littafai da Qur'ani a hannu,sai dan asirin _skirt_
    nata na attamfa da ya fito _green_ da ruwan
    kasa, duguwa ce,ba zangal ba,tana da kaurin
    jiki,dan ta fita sahun ramammu,tafiyarta a
    nut'sue tafi komai d'aukar hankali. Kamar kullum
    ta daga kai dan k'allon gidan su Ya Ja'afar
    kamar yadda ta saba k'ewar shi ta kawar da kai,
    sai dai taku biyu taja ta t'saya tamkar an t'sayar
    ta. Kanta duk'e dauke da murmushi,cikin
    nut'suwa ta kara k'allon kofar gidan dan tabbatar
    da wanda ta gani.. *"Ya Ja'afar*?...ta fad'a a
    zuciyarta lokacin da ya taso yana mata
    murmushi. Ikon Allah,wai kunyarshi kuma take
    ji,cikin nut'suwa ta d'auke kanta daga gareshi
    ganin ya karaso. "Assalam Alaikum Malama
    Salma.... Wani irin buguwar zuciya taji ya ziyarce
    ta,shekara uku da wani abin ba wasa ba,hatta
    muryar Ya Ja'afar ta sauya mata. Cikin nut'suwa
    ta dago da murmushi ta amsa mishi,kamin ta
    gaida shi a kunya ce, shi dai kawai k'allonta yake
    yana murmushi, kamar mai mamakin kara
    girmanta,ga wata nut'suwa da ta kara shigarta.
    D'uk sai ya kara yaba Salman nashi,ganin shirun
    yai yawa yasa da hannu ya nuna mata hanya
    halamar su wuce. Dan satar K'allonshi tai kan ta
    sunne kai suka fara tafiya. "Salma koh murnar
    gani baki yi,ba koh tambayar yaushe nazo? Kai
    duk'e tace "yi hakuri,yaushe kazo?.. Kai ya k'ada
    da murmushi,kan yace "jiya. Tambayar yaushe
    gamo yake mata, yadda take kunyar tata gun
    bashi amsa d'uk sai ya ji shi wani iri,mace mai
    kunya itace muradinsa. Da haka har kofar gida
    ya rakata yana mata tad'in makaranta da yadda
    suka juma basu gamo ba. Ummi ya k'allo achan
    dan nesa dasu tana tad'i, sai ya tuna mata yasha
    zuwa ai. Ita dai daga murmushi sai k'ada kai da
    Umm,a'a,d'uk ta takure yau a gaban Ja'afar
    d'inta. Ganin haka yasa yai mata sallama tai
    gida.. A katifa ta zauna tana cire hijabi,ta rasa
    wani irin farin ciki take ciki na ganin Ya Ja'afar
    d'inta yau. Sai murmushi take saka cike da
    kunya ita kad'ai kamar yana ganinta. A haka har
    Ummi ta cimmata, dan harara ta sakar mata
    gami da had'a rai. "Yanzu Ummi kinyi dai dai
    kenan? A y'atsine ta k'allo ta tana ninke g'yale,
    "da nai miki mey? Iya jaraba.. Kai Salma ta k'ada
    kan tace "dan t'sabar wulakanci ashe Ya Ja'afar
    yasha zuwa gidan nan nema na in yazo gari
    muna sa6ani sau biyu yana fad'a miki amma
    koda wasa baki fad'an ba? Allah kin ban haushi..
    "Mtsww.. T'saki Ummin tai kan ta ta6e baki,tuni
    Salma ta kule,sam ta t'sani t'saki, bare ga Salma
    K'anwar ta. "Na zata wani abin kirkin ne wallahi,
    toh meye nawa dashi da zai mayarni y'ar aiken
    shi?.. Anki a fad'a miki d'in ki d'au mataki toh.. A
    tunzure Salma ta tashi tayo kan Ummin sukaji
    Mama na magana a kofar d'aki, "Kun fara cin kan
    koh? Yara kamar masu ganin hanjin junansu?
    Baya Salma tai tana harar Ummi, "Mama kimin
    tsakani da ita toh,ta fita harkata dan bata da
    kunya sam wallahi.. A y'atsine Ummi ta harare
    ta,"ka ga kunya manya,akan wannan mai dan
    uban d'acin ran kike wannan kumfar
    bak'in?...baki ta ta6e kan tace "Kin k'wa kama
    abga in dai Ja'afar ne.... "Ke Ummi... Bana son
    fit'sara fa,kullum ina sanarki Salma yayarki
    ce,dole ki bata girma, koh nai mugun sa6a miki..
    Maza bata hakuri. Tana chunno baki ciki ciki ta
    bawa Salma hakuri,ita kam har ta fara hawayen
    bak'in ciki. "Toh fito ki biyoni.. Mama ta nuna ma
    ummin kofa da hannu.. *By* *Feenat Ja'afar*
    Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 20
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    7_Washegari ma ta fito zata makaranta sai gashi
    shi da abokinshi Garba suna tafiya. Ido ya kura
    mata ganin tai kasa da kai tana murmushi. Sai
    ya k'ada kai suka karasa,cikin sanyin murya ta
    gaida su,Garba kad'ai ya amsa,shikam Ja'afar
    k'allonta kawai yake yana murmushi, kamar mai
    son sai sun had'a ido. "Malama Salma fa kar tai
    latti a mata bulala abokina.. Kasa ta kara da kai
    tana dan dariya, shikam gogan sai binta yake
    kawai da k'allo,kan ya nuna mata hanya kan wai
    su rakata hanya. Ba musu ta wuce suka
    jera,Garba sai shakiyanci yake zuba
    musu,murmushi kad'ai ne nasu har suka zo bakin
    _gate_ d'in islamiyar. Ka'ro na farko suka k'alli
    juna cikin ido,da sauri ta K'awar da kanta tana
    murmushi, shikam harda k'ada kai, tuni Garba ya
    harbo jirgin nasu,sai ya hau shafa ha6a yana
    k'allonsu,musamman abokinshi da yace bai san
    so ba.. Hannu Ja'afar ya kai aljihu yana lalube,ita
    kam sai ta hau satar k'allon shi ganin mey zai yi.
    Da mamakinta k'wa sai gashi ya fito da naira
    ashirin yana mika mata. K'alloshi tai tana kunshe
    dariya,sai ta k'ada mishi kai, "Kud'in tara ne fa
    Salma, ki k'ar6a ki sai hambididi... Dariya Garba
    ya fara harda rike ciki,itama wacce take rikewa
    ta fito fili, sai ta sa hannu a baki dan rufe sautin
    ta.. Shikam Ja'afar kawai sai ya hard'e hannu
    yana K'allonsu, musamman Garba yadda yake
    k'yak'yata dariya. Shikam ba kasafai ya iya
    dariyar keta ba irin ta Garba,shi yasa wataran
    yakan kularshi a abu. "La Malam Ja'afar......
    Gaba d'ayan su suka juya k'allon mey magana.
    Ja'afar take k'allo tana murmushi halamar jin
    dad'in ganin shi, shikam tuni ya had'e rai yana
    k'allon ina ma ya santa. Kamar tasan mey yake
    tunani tace *"Bintu*(Na Rufaida Omar) ce,dalibar
    ka a day... Salma ya k'alla wacce itama ke kallon
    Bintu,kan ya k'ada kai, "toh Bintu.. Salma Bintun
    ta k'alla jiki a sanyaye ganin ko in kulan da
    Ja'afar ya mata,"shiga za kiyi ne Salma? kai ta
    kada mata, jiki a sanyaye tai gaba Salma ta daga
    musu hannu halamar sai anjima tana murmushi.
    Da k'allo ya bita cikin wani yanayi, da ko shi
    kanshi bazai iya fassara wa ba. Kai ya k'ada kan
    ya k'allo Garba wanda k'wachokam ya maida
    K'allonshi kan abokin yana dariya kasa-kasa.
    Harara ya maka mishi kan ya juya,sai k'wa
    Garban ya kara sa dariya yabi bayanshi. "An
    fad'a tarko makal ana hura mana hanci,sai anyi
    magana kace wani "mey nene so? Ni ban sanshi
    ba.. Karyan kawai,koh makaho ya laluba yaji ka
    afka so ai yanzu kam. Chak! Ja'afar ya t'saya
    tare da juyo wa gun Garba. "Mey kenan haka ke
    nufi?.. Harara Garban ya k'wada mishi kan
    yace"kar ka maida ni yaro fa malam,kana nufin
    baka san kana son Salma ba ko mey?.. K'allonshi
    kawai Ja'afar ke yi cike da mamaki,a hankali ya
    furta *"SO"*?... Hararar shi Ja'afar ya kara,gani
    yake kamar ya raina mishi hankali ne. "Kaga
    Malam kawai kai saranda haka,tuni tun yadda ka
    ke ta yawan fad'in Salma nasan a rina,ka bar
    wani k'wane-k'wane. Shi dai Ja'afar ya
    t'sunduma tunani maganar Garba,wai So? Salma
    kuma?. *By* *Feenat Ja'afar* 庐NWA.
    9/29/16, 8:56 AM - Queen Safiyyert馃憫: [7/21, 12:28 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    8-Har Ja'afar yazo k'wanciya yana tunanin
    kalaman Garba,tabbas biri yaso kama da mutum,
    dan yana jin sauyi tun ranar farko da ya dora
    idonshi a Salma bayan dawowar shi.
    "So"... Ya furta a hankali, murmushi yai kan ya
    k'ada kai,dan yana da aiki a gaba,dan bai san
    kom ba game da lamarin.
    Tun daga ranar ya zamto kusan kullum da
    yamma yakan raka Salma islamiya,koh da yana
    shago zai zo ya ganta kawai,hakan na sashi
    nishad'i, yau da gobe har ta fara sakin jiki dashi
    a karo na biyu.
    Sai ya zamana itama in bata ga Ya Ja'afar a
    ranar ba batajin dad'i sam,haka zata k'wana
    sukuku.
    Shirye-shiryen bikin Aunty A'i suke,duk sun shiga
    _busy_.
    Da yamma sun fito bak'in shagunan su Abba
    siyayyan kayan fitar biki, tasan kuma d'uk layin
    ba inda ya kai shagon su Ya Ja'afar kawo kayan
    k'yali, amma da tayi magana Ummi sai ta tanka.
    Kai duk'e yana duba takaddu,kamar
    _papers_,chak ya t'saya da abinda ya yake yana
    murmushi kai duk'e, ajikinshi ya ji kamar Salma
    na kusan shi,itama dai satar k'allon shi take,tana
    ganin zai dago tai sauri ta juyar da kai tana
    murmushi.
    Fara'ar shi ta karu dan hango Salman.
    A hankali ta dan kara K'alloshi,sai k'wa suka
    had'a ido,da azama tai kasa da kai tana
    murmushi har suka karaso.
    Tuni Ummi ta had'e rai ganin Ja'afar a shagon,a
    takaice ta dan harari Salman ganin sai wani
    munafukin murmushi suke sakar ma juna,baki ta
    ta6e kan a ciki ta gaidashi tai cikin shago ta
    barsu nan.
    _"My_ kanwa,.. Kai ta kara duk'ar wa tana
    gaidashi,sai ya k'ada kai,ya rasa irin kunyar
    Salma gare shi yanzu,abu kad'an duk'ar da kai.
    "Biki ya karato ba? Kai ta daga mishi tana dan
    k'allon _net_ d'in gefenshi da murmushi.
    Tashi yai zuwa gun inda take k'alla ya fara
    saukar mata dasu.
    A hankali ta tako gun dan zabi,d'uk sun mata
    k'yau.
    Sai ta dan kallo shi, "malam Garba fa? Murmushi
    yai yana k'allonta, "yaje inda aka tura shi
    _service_ nashi yaga gun,gobe zaki ganshi.
    Kai ta k'ada, d'uk sai taji ta kasa za6a ganinshi
    kusa da ita.
    Kamar ya sani ya kara s'akko mata da wasu.
    "Bari na tayaki za6a.
    Kai kawai ta k'ada mishi tana k'allon kayan,kan
    wani _purple_ idonta ya kai,a hankali ta kai
    hannu zata ja shima ya kai zai d'akko shi yana
    fad'in
    _"purple_ zai miki k'y... Shiru yai ganin itama shi
    ta rike,ya rike rabi ta rike rabi.
    D'uk sai suka k'alli juna ba koh kiftawa da wani
    yanayi...
    Tamkar wanda aka lika _poster_ a gun haka suka
    kame da k'allon juna.
    Ummi ce ta kat'se su da fad'in
    "Ga nan wasu materials y'an leda Salma masu
    kaman _lace_....
    Shiru tai ganin wani ikon Allah,baki sake take
    k'allon su,tuni Salman ta sakar mishi tai baya
    tana sunke kai da murmushi tare da amsar kayan
    hannun Ummin tana sunyi k'yau ba dan ta gani
    ba.
    Murmushi ya sakar mata shima,har yanzu yana
    rike da _net_,ya rasa mey ke damun
    K'wak'walwar shi akan Salma.
    *By*
    *Feenat Ja'afar*
    [7/21, 8:05 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    9_Baki ta dan ta6e,kan a y'atsine tace ma Jafaar
    d'in "mun zabi wannan, zamu nuna ma Baba sai
    ya bada kud'in.
    Murmushi yai yana k'allon gun Salma,itama
    idonta na kusan hannunshi.
    "Koh na tafi ne Salma? K'allo Ummin tai,kan ta
    k'ada kan suka yi hanyar fita a shagon,a hankali
    ta dago mishi hannu halamar _bye_.
    Kai ya k'ada mata shima ya dago mata nashi.
    Tai k'walli da Ja'afar ta ji dad'i,har aka je gida
    bata umm ba um um,sai Ummi ke ta zuba kamar
    kanya, yadda zata zuba wanka a bikin Aunty A'i
    har ta kule.
    Da dare sai ga yaro wai ana kiran Salma.
    Rai had'e ta k'allo yaron, "je kace bana nan...
    Shiru tai ganin yadda mama ke mako mata
    harara, "anya yarinyar nan kalau kike kuwa? Wato
    sai dai ai ta min asarar hoda da kazal a banza
    ina tufka kina min warwara koh?
    "Farin jini Allah ya bayar kina ma kanki bak'in
    ciki? Haka zan ta barar miki ni baki ban bare na
    maida g'urbin abinda na fitar Salma?..
    Maman ta k'allo da mamaki,toh rokon samari
    mama take so ta fara komai? Allah yaga ta t'sani
    fita zance.
    Amma ganin yadda mama ke wanke ta yasa ba
    shiri tace ma yaron "yace ma waye?.. Kai ya
    daga mata,"wai ince inji
    "Ja'afar in kin tambaya... Ai koh karasa wa nai
    ba ta mike,tuni murmushi ya maye g'urbin 6acin
    rai, da k'allo mama ta bita, kamar ba ita ce
    yanzu ba.
    Yau kam ga su Salma harda mit'sika hoda da
    _lips stick_ har ta d'au hijab ta kara k'allon
    madubi,kawai sai ta janyi g'yalen Ummi tai waje.
    Shine kuwa yana jingine da gidan,wani murmushi
    ta saka na farin cikin kara ganinshi a daren.
    Da sallama ta karasa d'uk da ba wani haske gun
    sosai,amma sai dan sinke kai take kamar rana.
    Bayan sun gaisa kowa yai shiru kamar basu abin
    fad'a.
    Chan dai ya nisa ya miko mata ledar hannunshi.
    Kamar mai neman ba'asi ta t'saya bata k'ar6a
    ba.
    "Ajiya na kawo kimin zuwa gobe ne,ba wani abun
    ba naga kina tsoro.
    Murmushi tai kan ta amsa tana k'allon Ummi
    zata wuce,koh ci kanku bata ce ba ta shige gida.
    D'uk sai Salman taji wani iri,Ummi sam taki jinin
    Ja'afar ta rasa dalili.
    Ba jimawa yai mata sallama dan ya rasa abin
    fad'i shima.
    Dama da Garba ne yau kam da zai iya fad'in
    komai ga Salma.
    ***
    Tunda daga lokacin Ja'afar ke zuwa gun Salma
    jefi-jefi,d'uk da har yanzun bai furta mata so
    ba,amma ita a ganinta d'uk acikin so ne.
    A k'wan a tashi gashi har ta kammala secondary,
    wannan itace tafiya mafi tsawo da Salma tai bata
    ga Ja'afar ba,kusan wata bakwai.
    Tun tana damuwa har ta hakura ta rungumi
    karatun ta na fita.
    Gasu yau sune a gida,d'uk an rame anyi baki.
    By
    Feenat Ja'afar.
    [7/21, 10:10 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    10_Babban tunaninta bai wuce d'uk t'sawan
    lokacin nan da aka diba ba Ja'afar ba labarin shi
    ba,tasan yakan je mata ziyara makaranta koh a
    t'satt'saye ne,ga ita ba waya ba balle ta neme
    shi koh lafiya?
    K'wana biyu da dawo wa yau d'ai ta kudiri niyar
    fita jin ba'asi,koh Garba in ta gani.
    Hijab d'in _mss_ d'inta har kasa ta sa harda
    nikaf.
    Sai d'ai har ta gama zagayen layin ba wanda ta
    gani ciki,kawai burinta ganin Ja'afar ne.
    Iyanzu kam tasan tai nisa kan sonshi ba kad'an
    ba,sai d'ai ita yanzu ta fara tantama.
    Har zata juya ta tuna da shago,d'uk da tasan
    yanzu ba kasafai yake zama ba tunda ya samu
    g'urbin koyarwa.
    Sai dai tai chan d'uk bata tunanin ganin nashi.
    Daga d'an nesa ta t'saya kusa da wata bishiya ta
    d'an kare ba mai ganinta, da sauri ta juya tare da
    dafe kirji,zuciyar ta sai bugawa take da k'arfi.
    Yanzu ta samo amsarta da kuma kokwantan ta
    da ya zama gaskiya... Bata aune ba sai jin
    hawaye tai na bin kuncinta cikin nikaf d'in.
    A hankali ta fito daga bayan bishiyar tare da kara
    k'allo shagon.
    Murmushi yake harda darawa, ita kuma budurwar
    sai washe mai baki take tana ta mai zuba,rike
    yake da hannun wata y'ar k'yak'yawar yarinya
    fara kamar yayarta.
    Ji tai wani abu ya tokare mata kirji,da sauri tasa
    hannu ta dafe gun,ga hawaye yaki ya d'aina
    malala.
    Lalle tai wautar kin kula kowa sai Ya Ja'afar da
    bai furta mata so ba.
    Ido ta rint'se ganin ya d'akko mata wani
    had'adan net purple yana bata,wato har kalar da
    yasha sanar mata yana so ya bata?
    Tai imani mai irin wannan zankadediyar budurwar
    fara ba abinda zai da ita Salma baka.
    Hannu tasa ta cikin nikaf d'in tana goge hawayen
    dake zuba mata.
    K'allo sun da zatai taga Ja'afar ya zuba ma inda
    take ido,har budurwar na k'allo itama,da sauri ta
    juya gabanta na fad'uwa, kar dai ace ya gane ta?
    Tab,da k'wa ta bada kanta wallahi.
    Juyo wa ta kara,sai karaf suka kara had'a ido da
    Ja'afar. Ba shiri ta tare mai adaidaita ta
    shige,tana k'allo ya bi napep d'in da k'allo yana
    girgiza ma budurwar kai.
    Kawai sai ta sa kuka mara sauti tare da cire
    nikaf d'in.
    Lalle tai wautar zurmuwa ga soyayyar Ja'afar,
    soyayyar da ba'a ma bayyana mata ita ba... Ya
    Ilahii.
    **************************
    "Oh! Man Ja'afar, dama kana k'allon mata har
    haka? Bafa koh kiftawa?
    Murmushi yai mata tare da girgiza kai, "Hala tai
    kama da Salma ne? Danma da hijab ga kuma
    nikaf..
    "Kusan hakan ne, jikina ya bani kamar Salman ce
    kam..amma nasan ba ita ba ce ma.
    Dariya ta danyi har hakorinta farare suka
    baiyana,kan tace "sannu _Romeo_ toh, ni
    sallameni kan Amal ta fara neman mamanta,
    amma ina mamakin yadda ka iya zaben kaya da
    color, halama kana son _purple_? Murmushi
    kawai yai mata,kan ya k'ada mata kai halamar
    eh.
    Ita kam Salma tana zuwa gida ta taho da yaro a
    kofa ya kaima mai Napep kud'in shi.
    Allah yaso ba kowa t'sakar gidan mama na d'aki.
    A katifa kawai ta zube ta sau kuka,sai da tai mai
    isarta tai shiru tana maida numfashi.
    Chan kuma kamar wacce aka t'sikara ta mike
    zaune.
    Tabbas Ja'afar bai ta6a nuna yana sonta ba
    kam,d'uk zuciya ke yaudarar ta.
    Asalima da "K'anwata" yake kiranta, kila hakan
    ne tun da,ita kad'ai ke kidanta, gaba d'aya ta
    gama kore masu sonta ita a dole ta riki Ja'afar.
    Hawaye ne ya kara zubo mata tunawa da yadda
    yake washe ma budurwar nan baki.
    Tasan yadda Ja'afar yake a gaban mata baya
    wargi,baya sake fuska ma bare har yai musu irin
    wannan tad'in.
    "Tabbas budurwar sa ce,nai wauta ni Salma...
    "Lafiyar ki kuwa kike maganganu ke kad'ai ya
    sabuwar kamu?
    Kai ta dago jin batun Ummi tana wannan y'atsine
    matan.
    Sai dai ganin irin yadda idon salman yadda yai
    ja,ga kuma hawaye yasa ta mat'so
    "Mey ya faru kike kuka haka?.. Ai kamar mai jira
    a ta6ota ta kara sa wani kukan mai sauti.
    Tuni kuma sai Ummin ta zauna tana lallashi da
    fad'in lafiya?
    Ita de sai kukanta take baji ba gani.
    Tashi Ummin tayi,"bari na fad'o ki da mama
    toh,kila k'ya fad'a mata ita... Da sauri ta rike
    mata riga, "ni ba komai.. Marata ke ciwo da
    bayana kawai.
    T'saki Ummin tayi, "Allah kina da aiki a gaban ki
    Salma,kukan jinya sai kace wata yarinya.
    Ita dai tana jinta ta karaci kardinta tai waje,a
    hankali ta zame ta k'wanta,sai sauke ajiyar
    zuciya take.
    *By*
    *Feenat Ja'afar*
    庐*NWA*
    [7/22, 12:02 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    11_Kan safiya har ta gama tunanin abin da zai
    fisshe ta.
    Hakan yasa t'saf ta tashi kamar ba ita taci kukan
    nan ba. Aunty A'i yau za'a kaima wuni,tun (12)
    suka fice ita da Ummi.
    Chan suka yini har dare,a kafa ta ratso ita kad'ai
    sakamakon Ummi da ta biya kar6an _style_.
    Tunda tazo layin su Ja'afar d'in taji gabanta na
    fad'uwa, duk da bata koh k'alli hanyar gidan ba.
    "Abokina ina ka tafi ne daga lissafi kai shiru?
    "Ba kaga kamar Salma ba waccan mey tafiyar?
    Ido Garba ya k'wara, da mutum,amma a duhun
    nan bazai tantance ba,kawai sai ya k'ada mishi
    kai,
    "A cikin duhun daren nan ne har zaka gane wake
    tafi.... Shiru yai ganin Ja'afar d'in yai gaba,da
    sauri yace "wai mey ke damunka ne? Ina za
    ka?.. Binshi yake shi kuma yana bin mai tafiya a
    duhun.
    "Salma"... Chak! Ta t'saya dan jin kamar an kira
    ta,a hankali ta juya,da dan tazara a tsakanin su
    kad'an, amma hakan bazai sa ta kasa gane ya
    Ja'afar ba koh a cikin dubu,hakan yasa cikin
    sauri ta juya ta chigaba da tafiya,har dan gudu-
    gudu sauri-sauri take.
    "Mey zai fad'a min kuma? Ta fad'a cikin ranta.
    Har kusan layinsu ya bita, tsammanin shi koh
    tsorata tayi,amma tabbas wannan Salma
    ce,kawai sai ya t'saya a dai-dai layin nasu yadda
    bazata ganshi ba,da hasken inji a layin, yana gani
    ta t'saya ta waiga,kan da sauri ta shige gida.
    "Amma fa baka aiki sam Jaa, wai har nan ka
    biyota kage ma koh aljana ce a daren nan?
    Juyawa yai yana girgiza mishi kai,"Allah Salma
    ce,toh yaushe ta dawo?.. Baki sake Garba yace
    "hadda rantsuwa? In Aljana ce fa mai siffar ta?.
    Harara ya sakar mishi kan ya juya suka tafi.
    Ita kam tana zuwa gida Abba da Mama suna
    t'sakar gida ta shigo sai haki,tuni k'wa Abba
    fad'a ya karu, kan mey yasa sukai dare?
    Tuni tai zuru zuru,fad'a sosai tasha,saura
    Ummi,d'uk da laifin Ummin har sukai daren.
    Washegari kusan yamma sai ga nan yaro kan ana
    kiran Ummi da Salma inji su isma'il.
    Harara Salman ta k'wada ma Ummi, kan tace
    "yanzu sai da kika fad'i ma mutanan gidan mu
    kika huta koh? Allah ban san yayi6e ni.
    Hararar itama Ummin tai mata,"arziki na binki
    kina guduwa,kowa yazo kice bai miki ba,ki mayi
    karatun ta nut'su wallahi,dan aure zanyi ni ba
    jira..
    "Keai Kowanne dan chaburos ma yazo Ummi a
    shirye kike, toh ba dani ba.
    Yankan farcen Ummin ta bari tai hanyar d'aki
    tana fad'in"sai kiyi ta zama kar kiyi aure,har
    mahadi ya baiyana.
    Cikin kuluwa zatai magana sai ga Mama ta fito a
    d'aki, ashe d'uk tana jin su, "toh k'wa maza ki
    wuce ki je tun kan na sa6a miki,daga yau na
    d'aina zuba miki ido ba fus bare ass Salma...
    Yarinya sai taurin kai,ace koh kishin yadda y'ar
    uwarki take shiga take fita da y'an k'wabai ba
    kiyi? Toh na gaji da gafara sa dan ban hangi
    kaho ba... Maza ki shiga daga ciki ki g'yara ki
    wuce...
    Kai kasa Salma tace "toh.. Ita kam tana
    mamakin halin Mama har kullum akan su,sai dai
    tana tuna Ja'afar tuni taji tana da muradin
    fita,tunda wanda take danshi bai ma san tana yi
    ba.
    G'walo Ummi tai mata,kan tai waje tana sai ta
    fito.
    Bata aune ba taji mama a d'akin nasu, bani waje
    ki ga,da kaina sai na g'yara ki...
    Baki sake take k'allon Maman,aikwa ta zage ta
    hau cha6a ma Salma k'walliya irin wacce bata
    ma san mama ta iya ba.
    Fad'i take "na rasa gane wace iri ce ke
    Salma,arziki na binmu kina zura da gudu,d'uk
    wani buri da na sa kanki kin rushe shi, in banda
    haka a jiya kad'ai kina ga irin bajintar da Ummi ta
    shigo dashi daga gun isma'il yake ko wa?
    "Haba k'alle ki a madubi man,san kowa kin
    wanda ya rasa... Tana yi tana g'yara mata
    d'aurin dank'wali.
    "Maza ki fita kan Abban ku ya dawo ya hana
    ruwa gudu..
    Kai ta daga zata d'au hijabi,da sauri Mama ta
    warce, "g'yale zaki sa matar Malam,koh a
    Shari'ar a haka ake son a ganki,ta ina za'a yaba
    in kin maka hijabin? Toh ba walima nace kije ba..
    Kai ta k'ada, ta zama tamkar rakumi da akala,sai
    yadda mama tace.
    "A'a, ko ke fa,k'alli kanki a madubi ki ga man,ai
    da banbanci, maza je ki... Kai ta kara k'ada
    mata, har zatai waje da sauri Mama ta kara
    kiranta.
    Turare ta fesa mata,kamar tace ba k'yau
    mama,sai dai taja tai shiru.
    "Ki murmusa man Salma,haba..murmushi ma ado
    ne ga fuskar Y'a mace...
    A yadda maman take yi bata ma san sanda abin
    ya bata dariya ba.
    Allah ya gama su da uwa "LASHE MONEY", har
    ta fita kuwa tana murmushi, mama sai barta.
    Suna t'saye gaban wata jar _CRV_ tare da
    Ummi,d'uk dinsu sun zubo mata ido.
    Ita kanta tasan tayi ne, fari da manyan ido kawai
    budurwar Ja'afar zata fad'a mata tasan.
    Doguwa ce ita dai dai misali,farin jinin samarin
    zamani,fatarta a goge take mai launin Wankan
    Tarwada(black beauty), tana gashi ga gashin
    ido,gata fuska doguwa,gata tana da diri dai dai
    so,d'uk komai ya ji ba bau ba.
    Ya dace kam tai amfani da lokacinta tun yanzun.
    Cikin takun da ba irin na Salma ta da ba ta
    karasa gun su Ummi,ga murmushin nan dan
    _beauty point_ din nan sai lot'sa wa yake.
    Tuni ta kara tafiya da imanin Muzammil,har yake
    ji kamar ya taro ta kan ta iso.
    By
    Feenat Ja'afar.
    [7/22, 4:57 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    12_Ita kanta Ummi tai mamakin Salma da
    sakewar ta.
    Sun gaisa da isma'il saurayin Ummin su kuma
    suka zaga dayan bangaren motar,
    Kusan kawai d'aurewa take tana mishi yake,
    amma ita sam taki jinin saurayi mai shegen
    surutun t'siya.
    Hakan yasa d'uk taji ta gagu su k'auce, ga tasan
    Abba gaf yake da zuwa da magriba tayi.
    Kamar ance daga kanki, Ja'afar tagani kusan su
    kad'an, tamkar gunki yaja ya t'saya, ga nan
    wannan budurwar da ta ta6a ganin su itama tana
    k'allo su,sai ta k'alli Ja'afar, kawai sai ta d'auke
    kai kamar bata gansu ba.
    Harda kara bawa Muzammil wani _attention_ na
    daban tana murmushi.
    Cikin sanyin jiki ya juya,tana dan satar k'allon
    shi,a baya budurwar tabi shi tana waiwayen
    Salman,ji tai kamar ta k'wada mai kira,So ba
    k'arya bane Salma.
    Da k'allo Ummi ta bisu lokacin da suka zago ita
    da isma'il, sallama sukayi,suna kokarin jan mota
    sai ga wata bakar mota ta _parker_.
    Ganin su Garba yasa da sauri Salma ta daga ma
    muzammil hannu tana mishi murmushi.
    Ja'afar dake k'allonta ta glass din ya rint'se ido
    da sauri.
    Ganin zata juya yasa Garba fad'in "Salma" da
    sauri.
    Juyo wa tai lokacin da yake yafito Jafar da
    hannu halamar ya fito.
    Koh ta kansu Ummi bata bi ba tai gida.
    Yake tai mishi lokacin da suke karasowa,sai dai
    koh inda Ja'afar yake bata k'alla ba shi da
    budurwar shi.
    Cikin barkwanci Garba yace "duniya da alkawari
    kuwa Malama Salma?.. Murmushi tai mishi iya
    le6e, "ashe kin dawo amma koh mu sani..
    Karon farko ta k'allo gun Ja'afar, idonshi k'wa a
    kanta girrr...ba koh kiftawa.
    Da sauri ta d'auke kai daga kanshi.
    Gaidasu tayi,budurwar na mata an dawo. Lafiya?
    A ciki ciki ta amsa,Garba yace "yaushe a gari?
    An gama lafiya _hope_?
    Da mamaki take k'allon shi,yanzu dama da
    wanda zai ce bai san y'an makaranta sun dawo
    ba?
    Kawai dai sai ta maze, "yau kusan satin mu da
    dawo wa.
    K'allo Ja'afar d'in Garba yayi,kan ya dawo da
    K'allonshi ga Salman.
    Ba wannan dawowar ba,yau k'wana uku da
    zuwan mu K'anwarki tace mana kinyi tafiya...
    Da sauri ta dago kai da mamaki,tana k'allo gun
    Ja'afar d'in ya d'auke kai.
    Garba yaci gaba, "zuwan mutumin kenan daga
    Zaria yace sai ya zo ya ganki ya miki murna,ashe
    ke har kin ma fice a garin.
    Batta bakin magana,dan bata san amsar basu
    ba,amma Ummi tana mata daya a rayuwa..wai tai
    tafiya?
    "Ga nan mutumin jiya har sururu yake yaganki da
    dare ina mishi t'siya, ashe ke ce.
    Kai ta daga,kan ta kara k'allon Ja'afar, d'anna
    wayarshi yake kamar bai wajen.
    Cikin wasa Garba yace "toh ni zan gabatar mata
    da ita ko mey da kai mikis?..kasan ba kunya zan
    ba ni.
    Murmushi budurwar tayi kai duk'e, dan sam bata
    ga fuska gun Salman ba.
    K'allon Ja'afar din take,yayin da yake k'allon
    Garba yai shiru.
    "Toh,mu bama sanya, sai ya juyo gun Salman,
    "Salma ga nan budurwa,kuma matar... Da sauri
    ta rint'se ido,kan ta karasa da "Ja'afar"... Na
    sani Malam Garba...
    D'uk ido suka zuba mata har Ja'afar baki sake,jin
    shirun yasa ta bud'e ido akansu,yadda suke
    k'allonta tasan tai su6ul da baka...
    Cije le6e tai,amma ta bada kanta wallahi....
    Dariyar keta Garba yasa harda k'yak'yatawa, sai
    ta dago tana k'allonshi.
    Sai da yai mai isarshi kan ya k'allo Billy,
    "Haba,Yanzu na ji batu,ni fa naga kowa yana
    sassahan kamshi,ashe-ashe...uhm uhm
    _Jealousy_...
    "Toh wannan Matar Garba ce bata Ja'afar
    ba,sassauto madam.
    Wani irin sanyi taji ya ziyarci zuciyar ta,har
    batasan sanda murmushi ya su6uce mata ba.
    A kunya ce ta k'allo Billy,sai ta mat'sa kusan da
    ita kan tace "sannu da zuwa...
    Dariya suka sa mata banda Ja'afar da ya dan
    dara,idonshi kir a kanta,bazai iya fassara mey
    hakan yake nufi ba, shin Salma na son sa da
    kishin sa ne koh mey?
    Ita dey sai dan satar K'allonshi take,amma
    bazata iya fassara ina ya dosa ba.
    Mota su Billy sukai suka barsu,ga nan magriba ta
    gabato,gaidashi ta kara yi itama ciki
    ciki,t'sayuwa ya g'yara kan ya amsa,tare da mata
    murnar kammala karatu,shiru ba mai cewa
    uffan,kowa miskilin kanshi,kawai sai sukai
    sallama kan gobe zai zo.
    Tana shiga gida dan takaici kasa ma Ummi
    magana ta cikin fad'a."yanzu Ummi kina k'yauta
    min kenan a rayuwa? Mey Ya Ja'afar ya t'sare
    miki ne ki ka ki jinin shi?
    Rai ta had'e, kan tace "oho,kawai bai min bane...
    Ga nan sakon daga Muzammil,kinga in da ake
    harka ai...
    Kai ta k'ada dan takaici tai d'aki batabi koh ta
    kayan ba.
    Washegari dan kalata sai ga su sun dawo, ana
    la'asar, mama ta fita unguwa.
    Ado Ummi ta ciwo da tafi na jiya,sakare tai ganin
    Salma koh mot'sawa batai ba.
    "Koh ba zaki bane Salma?
    A tunzure tace "ba zani ba..
    Baki Ummin ta ta6e,kan ta daga kafada,
    "mat'salar ki ce wannan kuma... Sai tai waje.
    Aiko yaro sau biyu ana yi daga waje daga
    Muzammil amma fur taki fita.
    A ka'ro na uku ne yaron suka shigo da Mama da
    ta dawo daga unguwa.
    Dole ta tashi badan rai naso ba,sai dan ganin
    Ummi ta shigo ta had'a ta da Mama kan taki
    zuwa gun Muzammil.
    Tana had'a rai ta fito,sai dai da mamakinta taga
    Ya Ja'afar t'saye yana aiken yaro kan tazo. Da
    sauri ta koma cikin zauren kan ya ganta.
    Jim tai kad'an bayan fitar yaron kan ta fito,kanta
    t'saye tai gun Ya Ja'afar, kan tace ya bata minti
    biyu dan Allah.
    Kai kawai ya k'ada mata,sai tai gun su Ummi,a
    mutunce suka gaisa,kan tace da Muzammil
    sakon shi sai gobe.. Bata jira amsa ba tai gaba.
    Shi kam Ja'afar k'allonta kawai yake,amma tuni
    har yazo wuya.
    Tabbas dole ya bayyanawa Salma yau ranshi ba
    sai an k'wana ba,dan wannan samarin tsaf sai su
    iya kasa shi yana k'allo.
    "Bissmillah, muje zaure... Bai yi musu ba yabi
    bayanta.
    Har ya dan saki fuska, dan sam ba kaunar zaman
    ta a layi yake ba.
    Bayan sun gaisa yake bata labarin abinda yasa
    bai je mata ba.
    "Kinsan Mamana tana a Zaria ne,sun rabu da
    Abba tun ina dan shekara biyar,hakan ya zamana
    Abba ya k'ar6e ni a dalilin tai aure,nakan kai
    mata ziyara haka,sannan dan ita na zabi zuwa
    Zaria karatu.
    A _time_ d'in da za ai _visiting_ aka aiko bata
    lafiya,chan naje har t'sawan wata uku.
    "Taji sauki sosai,har tana ta fad'an na koma
    bak'in aiki na,ana haka y'arta K'anwata ta dawo
    sun gama makaranta,hakan yasa na tuna da
    Salma.. Nan nai shiri na dawo,duk dan na
    ganki,sai aka samu akasi, Ummi tace kinyi
    tafiya... Shiru yai kai duk'e, itama tai tsam tana
    sauraren shi.
    "Salma"...kai ta dago ta dan k'alleshi, shima
    idonshi a kanta. "Yanzu kam lokaci yayi da zan
    sanar ki wani sirri,sai d'ai ina fatan wani bai
    rigani yad'awa ba...
    "Salma"... Cikin wata siga ya fad'i, kan yace "na
    jima ina dakon son ki azuciyata,tun ma kan
    Salman tasan itace...
    K'allonshi take baki sake,shikam ya zage sai
    tona sirrin ranshi yake a gare ta ido bud'e..
    Dad'i, farin ciki har ya kasa misaltuwa a gun
    Salma,So d'aya ne, tasan Ya Ja'afar tai ma.
    By
    Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 8:59 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 13_Har
    yai shiru ita kam idonta na kanshi,kan dafa bisani
    tai kasa da kai cike da kunya,kawai shima sai ya
    zuba mata na mujiya yana murmushi. Magana
    suke jiyo wa kasa-kasa,duk sai suka zuba ma
    kofar ido. "Ba mutunci ace kowa yana wuce wa
    yana ganin ku a t'saye a titi, gaba na fad'a miki
    ki nemi koh zaure ne koh cikin gid... Shiru Abban
    yai dan ganin Ja'afar a zauren da Salma.
    D'ukawa ya danyi kan yai ma Abban sannu da
    zuwa. Cikin sakin fuska Abban ya amsa,Salma
    ma ta mai kai duk'e. Sim-sim Ummi tazo ta
    wuce,dan duk iskancin ta tana bala'in tsoron
    Abban su sosai. Yana shiga gida shima yai mata
    sallama da alkawarin gobe zai zo dan jin amsar
    shi. Da t'sananin farin ciki ta shiga yau, haka
    dashi ta tashi. Tun jiyan Ummi ke ci mata kunu,
    tasan kuma d'uk akan Muzammil ne,shi yasa koh
    bi takanta batai ba. Washegari tun kan Ummi ta
    shiga wankan yamman ta na kullum Salma ke
    gaban mudubi, sosai take k'yali, yau d'aya ta
    bata lokaci dan Ja'afar d'inta. Ummi da tun dazu
    ta fito tana jira ta ta6e baki, ''kiyi kare ni ki ban
    waje na zauna Malama... Juyo wa tai da tana
    yage mata baki, "dan Allah Ummi nayi k'yau?..
    Bar zancen wasa. Baki ta ta6e kan ta juyar da
    kai gefe, "oho miki ni kar ki daman. Murmushi tai
    kan ta tashi ta bata gu. Bincike ta fara,a babu
    babu Mama kala 5-5 ta musu kayan _candy_ na
    ke ce sa'a, ciki masu ruwan _purple_ ne kusan
    duk. Cikin nishad'i ta ciro attamfa wata mai
    _purple_ da rat'sin _yellow_ riga da siket,
    murmushi tai dan tuna wa da kalar da Ja'afar
    yafi so kenan. Tunda ta zura kayan ta nad'a
    d'auri take bin kanta da k'allo a mudubi ta gefen
    Ummi. MashaAllah tai k'yau, gashin da ya fito ta
    kasa take turawa cikin dank'wali,ta kai dubenta
    ga Ummi wacce sai ko'k'arin fiddo nata take tabi
    dank'wali ta kansu. Murmushi kawai ta
    mata,tasan da tace ta mayar su ciki ma a iska.
    Sai dai tana d'akko turare ta hau feeeee ba ko
    kakkautawa. "Haba Ummi,turaren nan kinsan
    haramun ne sashi ki fita koh?.. Ga gashi kullum
    sai ance ki alkinta shi.. Allah kina *TABARRUJ*
    da yawa.... Galala take k'allonta, kan ta ja t'saki
    tai waje. Iya wuya Salma tazo, ta bala'in t'sanar
    t'saki. Ba'a jima ba Ja'afar yazo.. Tabarma yau
    ta d'aukar musu,shima yasha wankan farin kaya
    da farin takalmi _half cover_ sosai yai mata
    k'yau. Yadda yake fara'a da bin k'allonta tasan
    itama ta wanke shi. Suna t'saka da gaisawa
    cikin nishad'i yaro yazo,wai tazo a waje inji
    Ummi. Tuni ya sauya,dan yaga zuwan su
    Muzammil. "Minti biyu kawai.. Kai ya k'ada mata
    da dan yake. Tana fita suka ware gefe,tsakani da
    Allah ta fad'a mishi yai hakuri. Baki sake yake
    binta dashi har ta kule cikin gida. Amma Ja'afar
    ya bala'in k'wada shi da kasa,dan haushi koh
    isma'il bai jira ba yai gaba. Ita kam tana zuwa ta
    bashi amsa gamshasshiya, wanda tasa fara'ar
    Jafaririn ta dad'u ba shiri. Tad'i suke kamar ba
    gobe, mot'si kad'an yace "kinyi k'yau..... Itama
    cikin kunya tace yayi shima. ***************
    ************** "Naga sai zarmewa kike fa akan
    Ja'afar salma,sam kinfi k'arfin shi kima ji da
    wai,gaba ake son ci ba baya ba wallahi,d'uk da
    ban san wacce iriyar amsa kika bawa Muzammil
    ba... Da harara Salma ta bita, kan tai k'wafa, "ina
    ruwan ki da sha'anina? Ke har kin isa ki fad'a
    min wanda ya dace dani Ummi? Baki Ummin ta
    ta6e, "ke dai kika sani,dama ni meye nawa? Ni
    koh ana saurayi mey zanyi da Ja'afar mai shegen
    dacin ran t'siya... "Wai ku baku zama inuwa
    d'aya ne da juna Salma? Mey yasa baki iya daga
    ma Ummi K'afa sai kin tanka mata kullum kuna
    sa makota na jin ina daga murya.. Kasa Salma
    tai da kai kawai,tasan yanzu in mama taji ta
    kad'e.. Kamar k'wa wacce Ummi ta karanci
    zuciyarta ta amshe.. "Wai fa mama daga
    shawara ta tsaya min masifa,yau akan wannan
    dan gidan Malam Kabiru mai shago ta kori
    Muzammil,daga fad'a mata gaskiya ta hau ni da
    masifa.. Dan Mama daga ganin yadda Muzammil
    ya tafi rai 6ace nasan cewa tai bata son shi...
    "Eh bana son shi,koh ana son dole?.. Ja'afar d'in
    da kika rena ni shi ya min ki ji da wai.... "Kunga
    ku min a hankali,koh yanzun nan na sa6awa
    mutum... Shiru sukai,yayinda Salma taci ka tai
    dam. "Ke ummi wani dan wajen Malam Kabirun
    kike fad'a? Da harara Ummin ta k'allo Salma kan
    tai ma Mama bayani,"yanzu haka mama Malamin
    makaranta ne wallahi yana chan yana kokawa da
    alli.. Jim Maman tayi kamar mai tunani,chan ta
    nisa tace "Ikon Allah..anya yarinyar nan Salma
    ba'a min misanye dake ba a layin jarirai a
    haihuwa ba?... Mutum arziki na binshi yana
    ki?...Ina laifin yaran nan?har kasa suka gaida
    ni,ga mota ga boko..amma in banda abinki mey
    na sama yaci bare ya bawa na kasa? Da shagon
    uban zaku dogara koh da kud'in malami?.....
    Shiru Maman tayi ganin yadda Salman ke
    hawaye... "Au,au,Salma kuka? Daga fad'an
    gaskiyar? Kai ta k'ada ma Maman. "A ni tawa
    mai sauki ne Salma,ina d'ai hanga miki gaba ne
    kawai... Amma banga abin kuka.... "Wa ke
    kuka?... Assalamu Alaikum. Shiru sukai salman
    na goge ido,sai Mama da ta amsa mishi sallama.
    "Sannu da zuwa Abba. Kai ya daga musu kan ya
    amsa. D'uk suka tashi sim-sim sukai d'aki. Sai da
    Abban ya gama komai yasa Mama ta kira su.
    Kowa tai ladab kai kasa suna saurarar Abba. "Ni
    ke Ummi na ma kasa gane alkiblar da ki ka kama
    sam,kullum da wanda za'a ga yazo gunki,sai
    aukin shegen zance a titi ba wanda ya iya yazo
    ya samu iyayen ki.. "Ga nan yayarki yau d'in nan
    yaron nan na wajen Alhaji Kabiru yasa Baban shi
    yazo muka zanta kan yana son Salma da
    aure,kuma har sun sasanta da ita.. "Koh ba ai
    haka ba Salma?... Kai duk'e cike da kunya ta
    daga kai halamar anyi. "Haka shine musulunci, ta
    haka kuma ake gane da'ar yaron da zai auri
    y'arka... Shiru kake ji Ummi anyi lakwas. Nan ya
    kara ja ma Ummi k'unne kan tara samari da
    zancen waje,ya kuma ja mata k'unne kan ta
    fidda na aure koh ya fiddawa mutum. ***** ***
    Zancen aure dai ya kank'ama tsakanin Ya Ja'afar
    da Salma. Itama Ummi Isma'il yace da gaske
    yake.. Mat'sala d'aya tafi damun Salma,yadda
    komai Ja'afar ya bata na alheri a rene yake gun
    su Mama, barin Ummi. Dan ita fachaka isma'il
    yake mata kamar ba gobe. Tun abin bai damunta
    yau da gobe har ta fara ganin kamar Ja'afar
    mammako yake mata. Zuciya bata kashi. By
    Feenat Ja'afar. 庐NWA.
    Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Jul 24
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    14_Anyi bikin su Garba. Ana haka saurayin Ummi
    ya d'allo mata wata sabuwar waya,ita kam tun
    wata Zain da ya bata,nan habaici ya karu gun
    Ummi. Biki ya kusa sukai shirin zuwa Borno
    dangin Abban su. Sunyi sallama da Ja'afar ta
    shigo gida rike da farar ambalan,d'uk suna zaune
    t'sakar gida har Aunty A'i da yaronta. Hannunta
    Ummi ta k'alla, kan cike da shakiyanci tace "ta
    Ja'afar mey aka samu ne haka har a farar
    takadda?.. Harara ta dan mata kan ta mikawa
    Mama. Kai Maman ta k'ada, kan tace "a rabani
    da kayan haushi,rike abinki kawai ki kirga...
    Dariya Ummi ta sa,wanda tuni ta kara kular da
    Salma. "Mama ba ma sai ta kirga ba,dan wallahi
    ba kaffara nasan kud'in nan bai fi dubu biyu ba...
    Kanta Salma ta yiwo a tunzure mama tai musu
    iyaka. "Meye na jin haushi?.. K'yautar tashi tana
    wuce nan ne?... Ba dai d'an d'an kasuwa zaki
    aura ba? K'wafa tai,kan tace "baki fara ganin
    komai ba ma Salma. Aunty A'i ce ta k'ar6a ta
    kirga,ai kam sabbin hamsin hamsin ne ta dubu
    biyu. Mama tace "Ahab,na sani ai. D'aki Salman
    tai tana hawaye,sam bata kaunar abinda ake ma
    Ja'afar,amma shima da laifin shi,dubu biyu ina
    zata kaita? ****************************** Biki
    kam yazo,gashi yau har anje jere, k'warai sunyi
    mamakin gidan Ja'afar da gina kuma da kanshi.
    D'uk da ba wani babba bane,dan koh t'sakar
    gidan karama ce,babban _parlour_ ne sai _bed
    room_ da band'aki aciki,ga _kitchen_ a ciki
    karami,sai d'aki d'aya daban a waje, d'ai d'ai
    zaman mutum d'aya de,rufin asiri dai ak'wai
    shi,Alli da shago sunyi rana. Sa6anin Ummi mai
    tafkeken gida da mai gate yasha alatu. Yanzu
    lefe ake wat'sa ido aga na Ja'afar, dan tuni na
    Ummi yazo san barka,sai zuzutawa ake. Salma in
    ta tuno gabanta har fad'uwa yake,fatan ta Ya
    Ja'afar ya fitar ta a magana. Dan tun a kud'in
    anko taga tasku,dan isma'il ankon k'yauta yai ma
    k'awayen Ummi da dubu ashirin nata na fitar
    biki. Shikam sai hakuri yake bata,kan shi bai
    d'aura ma kanshi abinda bazai iya ba,bare daga
    baya ya dame shi. Kawai sai ta toshe k'unnenta
    gun su mama,komai ta samu ta samu,wanda ta
    rasa tasan bai da hali. Mamaki kam Ja'afar ya
    bama su mama, dan ak'wati shidan nan y'ar yayi
    sai da aka bat'se ta da kaya, ga uban
    _cosmetics_ har a jakar Ghana must go. Aciki da
    swiss d'aya, holland biyu,engla biyu,sai su code
    dav'ior,sauran kam duk kana na ne su dangin
    material. Salma baki har k'unne jin ba wanda ya
    kushe a dangin sai d'ai ace na Ummi yafi t'sada.
    Anyi biki lafiya kowa ya wat'se an bar amare da
    halin su a gidan su. Kauna ziryarta taga gun
    Ja'afar mai t'sayawa a rai,sosai sukai amarcin su
    cikin kula da tarairayar juna,musamman ga
    Ja'afar d'in. _kitchen_ tare,wanki tare,shara
    tare,duk aiki in dai ba ya fita bane yana a makale
    da Salman sa, d'uk wata kulawa tana ganinta a
    gun Ja'afar,shi yasa sai abinda yace take
    aiwatarwa matukar bai sa6a Shari'a ba. Yadda ta
    fuskanta ma kamar bai kaunar tai nesa dashi,koh
    dan ganin har wata biyu kenan da bikinsu amma
    ba inda taje sai barkar Aunty A'i da makotansu
    da taje tun tana sati daya da zuwa. Sai dai tai ta
    jiyo shewar su ta katangar gidan halamar ana ta
    _chapter_. *Farin Bacin komai* Yau tun tashinta
    sallar asuba ta kasa komawa bacci,sakamakon
    tun dare da yace yau ta shirya da wuri zata gida.
    Dan farin ciki ji take kamar a wani garin zata je
    musu. Waya tai da Ummi kan zata fito yau gida.
    Gaban madubi take tana yi tana k'allon agogo
    har sha d'aya saura. Karar _machine_ d'in Ya
    Ja'afar taji a kofar gidan,sai ta cigaba da
    shiryawa. Sallamar shi taji,daga d'akin ta amsa
    tana fara'a. Yana shiga ya jingina da kofar d'akin
    yana mata murmushi,ta mudubin ta mishi tana
    d'auri. Kan ya tako gaban madubin ya t'saya ta
    bayanta. "Sannu da dawo wa.. Kai ya daga
    mata,sai kare mata k'allo yake, kayan sun mata
    k'yau, "Kinyi k'yau... Tashi tai da jin dad'in
    kalaman shi,sai ta dan ja mishi kumatu kan tace
    "na gode... Muje koh?.. Ta fara nad'a lifaya. Sai
    ya rike mata daya gefen tana nad'a dayan da
    murmushi. Da kanshi ya yafa mata akai ya rufe
    ko'ina ruf. "Ba dan kin nace sa abar nan ba da
    hijab d'inki za ki sa zai fi min k'wanciyar
    hankali.. Murmushi tayi kan ta lang'wa6e kai, "ai
    ba g'yale bane Ya Ja'afar, Allah ina son lifaya.
    Kai ya k'ada mata yana d'aukar mata jaka. "Toh
    naji,amma ni banga maraba ba. Murmushi kawai
    tai tana d'aukan mukulli. Machine d'in ya karkata
    mata kirar lifan,a hankali take ko'k'arin hawa sai
    ya dan girgiza machine din,da sauri k'wa ta dafa
    kafad'arshi suna dariya. In kagansu g'wanin k'yau
    suna ta nishad'i har suka zo gida. Tana g'yara
    lifaya tace "bazaka shiga ba?.. Kai ya girgiza
    mata da murmushi,"ki gaida su Mama, anjima in
    nazo d'aukan ki zan shiga, yanzun makaranta zan
    koma. Kai ta k'ada mishi,kan ta bashi hannu,sai
    ya bata suka gaisa suna dariya. "Abincin ka yana
    a kitchen a bisa faranti,na had'a komai, a dawo
    lafiya... Kai ya daga yana mata murmushi,jin yaki
    tafiya tace "kaje man.. Kafad'a ya make yana
    nuna mata gefen fuskanshi, kai ta k'ada mishi
    cikin kunya. "A layi muke fa... Shima sai ya kada
    kan tukun ya tada sukai sallama. Har ya kule
    tana daga mishi hannu,kan tai cikin gida. Da dan
    gudunta ta shiga tana kiran Mama. D'uk suna
    d'aki, Ummi an hakimce a kujera ana d'anna
    waya. "Har kun rigani ashe d'uk saurin nan
    nawa?.. K'allonta Ummi take ganin tana since
    lifaya,ga flasks da jaka an ajiye. "A ina zaki zo
    da wuri,ke dad'i miji ce ai.. Banza tai da ita tana
    gaida Mama, itama Maman a dan ciki ta amsa
    mata. D'uk sai taji ba dad'i, jikinta yai sanyi,da
    murnar ta tazo amma sun dakushe mata. "Sai ya
    barki ki waiwayo mu?.. Maman ta k'alla, kan tai
    kasa da kai, "ai na zata irin ta y'an da zai
    miki,sai kin shekara koh kin fito yawan arba'in....
    Baki Ummi ta ta6e,kan tace "d'uk mai irin halin
    Ja'afar ai dole yai k'ulle Mama,in banda haka
    wata biyu wai sai yau za kizo gidan ku,ni nazo
    yafi a girga,wallahi tun wuri ki mawa tufkar
    hanci.. Dan in kika sabar mishi da haka zai mike.
    Dagowa tai da niyar yi wa Ummi magana Mama
    ta tari numfashinta. "Y'ar uwar ki ce,dole ta fad'a
    miki gaskiya, ke zaki nema mana mutunci a gun
    miji ki ma ji da k'yau. Kasa tai da kai tana
    murmushi, duk da a zuciyarta bataji dad'i ba
    sam. "Mama baza'a a sake ba inshaAllah. Da
    haka aka ware kuma zancen nawa ta tara a
    banki. "Ni fa ba'a ban kud'in cefane Mama, komai
    yana kawo min har katin waya,sai dai in ina da
    bukata yana cewa na mai magana... Baki Ummin
    ta ta6e,kan ta zuge jaka, sai ga nan kud'i tumi.
    "Kinga kud'in cefane na,nima ai ba abinda na
    rasa,ina ruwana da wani ni kud'in kati? Kawai naji
    dumus ni... Gashi nan na banki ne dana sa Mama
    ta sai min. Kai Maman ta k'ada, tabbas Ummi
    tasan ta kan maza,shi yasa take burgeta sosai.
    Itade Salma an sata duhu,dan sun raba
    hankalinta biyu. T'saka mai wuya kenan. By
    Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:00 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 15_Sai
    dare yazo a dalilin yadda take fad'in bata gama
    ba,har cikin gidan ya shiga,kawai kuma sai yake
    ma Mama k'warjini, dan fuska sake ta amsa
    mishi,kan suka tattara suka tafi. Koh da Salma
    tazo k'wanciya maganganun su Ummi take ta
    tunawa. Ita babban haushinta ma yadda aka fa
    fad'in koh tsoron Ja'afar take. Washegari ma
    haka ya yakaita gidan su Abban shi,nan ya wuni
    suka biya gidan Garba. Yau tun (7:30) ya fita,
    sakamakon an fara jarabawa a makarantu. Sha
    d'aya ta gama aiki ta fara jiyo hayaniyar y'an
    unguwa a makotanta,halamun sun hallara za'a
    fara chapter. D'uk yau sai hankalinta yai
    gidan,duk da ba sabawa tai dasu ba. Waya ta
    d'auka,ta d'anna kiran Ja'afar _no answer_.. Ji
    take kamar ta zaga in ya dawo ta fad'a mishi,sai
    dai ta daure. Da yamma kam kamar kullum yazo
    fita shago tace zata leka makota. Jim yai ba
    amsa,sam tarbiyar matan unguwar bata mishi
    ba,baya so Salma tai sabo dasu a samu
    mishkila,amma kawai sai ya k'ada mata kai, "Sai
    kin dawo. Cike da murna ta rakoshi har bak'in
    kofa ta koma d'aki. Da sallamarta ta shiga,tun
    daga bak'in kofar gidan zaka fara jiyo karad'in
    matan. Da fara'ar su suka amsa,d'uk sun baje a
    tabarma, wasu ba koh dank'wali. A dan kunyace
    ta gaida su, dan ganin duk sun girme ta,sai wata
    mai kamar shekarunta da D'a a goye. Chan hira
    taci gaba, zabiyar ciki sai karanta musu makamin
    kama wuyan maza take. Salma tai shiru tana jin
    su,tabbas babban burinta shine Ja'afar ya so ta
    har karshen rayuwa. "Su amarya yanzu ai farin
    take gani kan a juya mata bak'in bayan.. K'allo
    matar tai,bata gane nufinta ba,sai dai bazata iya
    tambaya ba. Haka firar yau ta tashi kan makamin
    rike miji har Salma ta fito. Tunda ta zauna a gida
    take tariyo firar sun. Tabbas shawarar nan tayi ta
    makamin rike miji, ta hakan kam ba yadda
    Ja'afar zaiyi ya raina ta... Toh amma Ja'afar
    yana sonta,batajin zai mata dabi'a irinta mazajen
    sauran Matan da ke fad'i. Nan ta jefar da
    dayawa a hudubar da taji a makota tai kitchen
    dan k'unna ritio. Sai d'ai Washegari ma da
    yamma Salma ta sake tambayar shiga makota.
    Karan nan kam kir ya fito yace mata a'a, da ido
    kawai take binshi, "Ya Ja'afar yafi zaman kad'aici
    ne,ba jimawa zanyi ba ka ji... Ta langwa6e kai.
    Ba dan yaso ba ya k'ada mata kai. Minti biyar
    bata kara ba tai makota,gidan chapter. Yau kam
    a sa'a taje,dan suna a kan firar rashin fitar matar
    gidan,sai bata dabaru suke akan yadda zatai mijn
    ya rika barinta fita. "Kar ki fara tambayar
    unguwa kina fara'a, sosai zaki dake mishi,mud'in
    yaga 6acin rai toh jiki na bari zai barki. Ni da
    farko haka Salisu ya t'siro min da k'ulle,tun farko
    nai ma tufkar hanci,da yace A'a yana fita zan
    arce, gashi yanzu har ya saduda yana barina duk
    inda na tambaya. T'sam Salma tai,tana tariyo
    maganar Ummi da Mama ta ranar,ga nan ta
    makotanta. Daga ganinsu sun san takan duniya.
    Tabbas ta yarda itace tun yana d'anye ake
    tank'wara shi. Tun yanzu ya dace ta takawa
    Ja'afar birki koh dan ta t'sira daga zargin wai
    tana tsoron shi. *Wasa farin Girki.* Daga ranar
    Salma ta tsiri dan hali,fita makota,tambayar fita
    gida,ga wani t'sarewa da take in tana tambayar.
    Kamar kullum tazo rakiya taja ta t'saya a gefe,
    "Ya Ja'afar... Jiyo wa yai shima rai ba dad'i,tare
    da zuba mata ido,yasan abu daya zata tambaya.
    "Zan leka gidan Maman Ummi gobe suna za ai
    k'ulli... K'allonta kawai yake, yadda tasha mur
    tamkar wanda take bashi umarni. "Anya Salma
    wani abu bai shiga kanta ba kuwa?.. Gaba daya
    ta sauya mishi hali k'wana biyu in dai akan fita
    ne.. G'wara tun wuri ya taka mata burki dan yaki
    jinin yawan fita sam shi. "Kiyi hakuri Salma,ki
    bari ki leka goben tunda suna ne... Tuni ta
    k'ank'ance ido, "gaskiya kar ka maidani saniyar
    ware a unguwa ya Ja'afar, yau k'ulli kowa ya je
    sai ni ce bazani ba?.. Ai sai a chake ni gobe
    dama suna fad'in ni dad'i miji... "Kuma ma ba
    wannan ba,nima sai ina zuwa za'a zo min in
    nawa yazo ai.... Shiru tai ganin yadda ya zuba
    mata ido yana kallo, chan ya nisa "amma Salma
    kin fuskanci kin fara sauya hali kuwa?... Kin koyi
    ja dani,kin koyi gantali k'arfi da yaji.. K'alloshi tai
    a wani iri, "au gantali ma nake Ya Ja'afar?..
    Fisabilillahi wace fita ce nake yi ba dalili? A satin
    nan sau biyu koh uku ne fa na fita kuma dubiyar
    Ummi ne ba wani waje ba, koh shi ka ke nufi da
    gantalin? Kai ya k'ada,"kar mu rika ja in ja dake
    Salma,kiyi hakuri kawai gobe ki je... Juyawa yai
    ganin tana neman wata maganar yai waje, baki
    ta ta6e,kan tai cikin d'aki. Tana jin tashin
    machine d'inshi ta zaro hijabi ta k'ulle gida tai
    cikin gidan k'ulli. "Ai na zata bazaki zo ba,da har
    zanyi aike naga machine din maigidan. Hijab ta
    cire ta jawo jarka, "bari ke dai Maman
    Ummi,dak'yar na fito fa.. Murmushi tai kan ta
    d'akko wani abu a bakar leda,"yanzu saratu ta
    fita an kawo sabbin kaya dakakku wallahi,tai ta
    jira baki zo ba zata tafi na dau miki wannan...
    K'ar6a tai tana dubenshi kan ta kunce ledar,roba
    ce karama da wani abu mai d'anko. "Takalmin
    Kaza ake fad'a miki,nasan yafi haka,kawai ta
    mana sauki ne.. Amma abin ba magana,sai an
    g'wada akan san na k'warai... Dariya suka sa aka
    tafa harda shewa. "Wannan ne kawai makamin
    wulakancin D'a namiji,tunda kuka d'aurani kan
    _network_ nake son raina Allah. "Dari biyu ai ma
    yai araha... Bari yazo dari biyar zan tat'sa, dan
    asusu nake kan zuwa watan haihuwar Ummi na
    tara da yawa... Sai da aka gama k'ulli ana firar
    duniya,a debo gulma har aka gama,ana kiran
    magriba ta tuna Ja'afar, da sauri-sauri tai gida
    dan yau abinci ta zarce tayi. Kamar kullum ya
    dawo bayan magriba ana kiran isha'i, sai dai sam
    ranshi ba dad'i,nan tasha jinin jikinta,koh ya
    dawo bata gida ne? Har yaje masallaci akai isha'i
    bai dawo ba har ta gaji da jiranshi ta k'unna inji.
    Sai chan kusan tara ya shigo,har yanzu jiya
    iyau,sam kuma sai taji ba dad'i, tun kan ya fad'i
    lefin da tayi,amma de sai ta dake. Komai
    yayi,dan har abinci ya ci,sai dai fur yaki sakar
    mata. "Wai Ya Ja'afar mey nai ne ka ke ta shan
    kanshi?.. K'allonta yake da mamakin anya
    Salman shi ce wannan?.. Bai da amsa,sai a
    gunta kawai,saboda haka ya tashi yai hanyar
    d'aki. By Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:03 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 16-Ya
    fito a band'aki ya ganta zaune a gad'o,kai ya
    dauke yana goge jiki da _towel_,d'uk sai jikinta
    yai sanyi,tabbas tasan Ja'afar kila zuciya
    yayi,har ya gama shirin bacci uffan bai ce mata
    ba,tuni ta fara kuluwa ganin ya ja filo bai bi
    takanta ba. "Wai mey in ma ina ta maka magana
    tun dazun?.. Kai ya dago ya k'alleta da tuhuma,
    "mey kika ce ban amsa miki ba?... Baki ta turo
    gaba kad'an, kai ya kada,tukun yace "Salma!...
    Salma!!.. Dagowa tai ta bashi hankalinta dan jin
    kiran da yawa. "Na'am.. Ido ya tsura mata,sai tai
    gefe da nata. "Ina kika fita dazu har magriba?..
    Jin tambayar tai ta bazata,hakan yasa ta kasa
    K'allonshi, sai da ya maimaita tukun ta amsa a
    hankali da "gidan k'ulli... "Gidan k'ulli?.. Mey
    mukai dake toh kan na fita?... Duk t'siya ta ki
    jinin kuma taga ran Ja'afar ya 6aci, sai dai an
    rinjayi zuciyarta. "Kai hakuri... Itace Kalmar da ta
    fad'i. Tashi yai ya jingina da pillow,kan cikin
    nut'suwa ya fara mata magana. "Ba wannan ne
    ba karon farko da ki ke fita ba'a son raina ba
    Salma,nasha aiko yaro da sako yace gida a k'ulle
    yake,amma nai ta daga miki kafa. Duk gantalin
    da take bada yardar shi ba sai da ya sanarta,ga
    t'sinuwar mala'iku dake binta har ta dawo...
    "Sam wannan ba Salman da nasani a wata 5 d'in
    baya ba... Wannan cikin wata d'aya ta sauya,bata
    jin magana ta,duk abinda tasa kanta take ganin
    shine d'ai dai shi take... Sosai ya kasheta da
    kalamai,har ta fara hawayen wai bata jin
    magana. Murmushi yai kawai,kan ya dan taso ya
    janyo ta ya hau kuma lallashi,da alkawarin
    bazata kara ba,sosai ya ji dad'i,dan yana son
    mutum mai gane kuskure in ya yi. Washegari
    _week end_suna ma haka tai shiru,sai dai kasan
    ranta ji take kamar tai filfilwa taje gidan. Tasan
    iyanzu an kusa sauke abinci ana ta cin chapter
    ba ita. Sai dai tai ko'k'arin ganin bata tambaya
    ba. Shi kuma ganin haka yasa yaji dad'i,fatanshi
    yasa Salma ta g'yara ne. Ce mata yai yana
    zuwa,yana fita ta kasa zaune ta kasa t'saye.
    Anya bazata leka ba kan ya dawo?.. Dan tasan
    yanzu ana chan an kafa da ita uwar son miji. Sau
    biyu tana k'wata fita tana dawo wa,a na ukun taji
    dirin machine d'in Ja'afar ta koma. Sai gashi da
    leda baka a hannu. Sannu da zuwa ta
    mishi,burinta ya fita ta fice, amma fur yaki. A
    jima kadan ta k'alli agogo,kafarta har kaikayi
    take,da ya k'allota ta sai ta sau mai murmushin
    dole. Kamar ya kula sai yace bari yai wanka,yau
    sha biyu yake son yaje shago. Ita dai ta samu ya
    fice,Allah koh satar hanya sai taje gidan sunan
    Maman Abba. Toh sai ma ya barta harda mika
    mata ledar riga ta barka. Abu kamar gaske
    Salma kamar anyi hankali, sai hali ya dawo sabo.
    Shiga makota kam Ja'afar har yai hakuri ya zuba
    ma Salma ido, Gashi yanzu su Salma har ketare
    ana t'sallakawa,kusan duk yanzu unguwar sun
    san da Salma,ga surutu da t'sabar manyance da
    ta koya zama cikin manya. Ranar Garba suka zo
    gidan a 6ame da mukull,sai ya d'au waya ya kira
    Ja'afar din. "Ba kowa fa a gidan nan Aboki,dan
    da mukulli a 6ame.. Daga chan Ja'afar yai t'sam,
    kan yace "oh,sorry pls,na manta tace zata je
    dubiya, ga wayanta ba chargy... Kai Garban ya
    kada "toh dai mun fita,dama ita ke mitar madam
    shiru,yanzu kam ma had'u suna. Murmushin dole
    ya k'akalo,yana cewa ace Billy tai hakuri. Bayan
    sun gama ya ajiye waya,Salma tasa ya tafka
    karya,dan da abin kunya ace yana mai gida
    amma bai san matar gida bata nan ba... Toh mey
    zai wa Salma ne?.. Ya mata d'ukkan nasiha,yayi
    fad'a, yai lallami,amma tamkar a iska yake
    zubawa. Sai tayi kamar ta d'aina, gobe ta fidda
    sabon hali. "Assalam Alaikum... Kai ya
    dago,ganin mey sallama yasa ya fad'ada
    murmushin shi, cikin girmamawa yace "a
    Abba,sannu, yana sunne kai, murmushi Abban
    yayi,kan yace ''yauwa Ja'afar,ka ga na dawo,zan
    dan zaga ne, baya,dayan shagon nan ba kowa ne,
    nazo arar Sadi minti biyu.. Kai kasa yace "Bari
    na zauna kan ka dawo nan bana komai. Yasan
    zai samu ma damar yau amar da abin da ke
    ranshi. Yana shagon Baban ya k'wance ya
    d'aure, ya fad'a ya je gida ya shiga uku gun
    Salma.. Shawara d'aya ya yanke, gun Mama, dan
    yaga ita batta zafin Baban. Tun yamma ya
    tashi,bayan sun gaisa da Maman faran faran
    yake sanarta halin da Salma ta t'suro mishi.
    Kamar abin kirki harda bashi hakuri,da fad'in zata
    t'sawatar mata. Sai d'ai tana fita Ummi da tun
    shigowarshi tai zamanta a d'aki ta fito. "Kai
    amma mama mutumin dan rainin hankali ne,wai
    kinji fitar Salma tai yawa? Matar da sai tai sati
    biyu wataran ba tazo gidan nan bama bare har
    fitar ta tai yawa.... K'wafa Maman tai,kan tace
    "ke lefin shi ki ka ga?.. Ai lefi na gun Salma da
    ta zauna yake juyata kamar waina... A zamanin
    y'ancin kai ake yanzu, bana tsawalawa dana..
    Kaza kaza,har Abba ya shigo zaure ya dan t'sinci
    wani zancen,amma bai gane kanshi ba. Kullum
    Ja'afar na sa ran yaga Salma ta sauya,sai dai
    shiru,sai yai tunanin fad'an Maman ma bai shige
    ta ba. Ranar Garba yace a gidanshi zai magriba
    yace Salma tai musu irin gurasar nan tun tana
    amarya. A gabanshi ya kirata, a lokacin an zube
    ana ta firar kashe wando a makota bayan
    layinsu, Koh da ta sauke waya ta cigaba hirarta.
    Chan kusan magriba ta kusa ta tuna da zancen
    Ja'afar,kusan ma d'uk y'an firar an wat'se amma
    Salma matar gida ta riketa wai suna firar su zata
    tafi? Yaron gidan tasa yai gudu bayan layinsu ya
    siyo mata gurasa mai siga ta karbi kud'i gun
    matar gidan. Cikin nishad'i suka zo sai dai gida a
    6ame,ga yau ta bar mukullin shi a ciki. Ranshi in
    yayi dubu ya 6aci,basu jima ba sai gata
    tanan,duk tabi ta burkice, duk da koh k'allon inda
    take Ja'afar bai ba. Sai da Garba take magana
    tana ko'k'arin bude gida. By Feenat Ja'afar.
    Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Jul 25
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 17_Shi
    dai Garba har suka shiga gida yana zungurar
    abokinshi kan ya saki fuska. D'aki ta shiga tana
    mai adu'ar Allah yasa a samu gurasar nan,in ba
    haka ba yau ta kad'e har ganyenta a gun Ja'afar.
    Suna t'sakar gida suna alwalar magriba sai ga
    yaro yai sallama rike da k'wano,da sauri ta fito ta
    amsa,har ta shiga Ja'afar na bin bayanta da
    ido,k'wafa yai kamin yai ciki, shi dai Garba duk
    ya gane da wata a kasa. Kitchen ta sameta tana
    jera su a faranti. Tasan shine amma fur taki daga
    ido ta k'alleshi. "Nagode Salma, kinji? Na
    gode,amma ba zanci gurasar titi ba ki sani...
    Kofar kitchen din ya rufo sukai waje. Ita kam koh
    a jikinta,tunda de ta t'sallake fad'a ai shikenan.
    Yau dai ya kasa d'aurewa, har sai da ya sanar da
    Garba halin Salma ba ragi. Sosai yai mamaki,wai
    Salma ce da halin nan? Sai dai kawai ya bawa
    abokinshi hakuri, da kuma ya rage saurin fushi...
    Haka ya wuce gida ba tare da shima yaci ba. Da
    dare ya d'au pillown shi ya koma parlour,baki ta
    ta6e tai k'wanciyar ta. Sai dai koh minti ashirin
    ba ai ba ta hau juyi,ta ture pillow,dan Allah yaga
    bata saba k'wanciya ba'a hakarkarin Ja'afar
    ba,duk fad'a kuwa. Ba shiri tazo bada hakuri dan
    tasan ya bala'in jin haushi. Shi kuma haushin shi
    d'aya da hakurin Salma,tunda ba wai zata g'yara
    bane. Kuka ta fara mishi harda shura kafa kan
    wai ya juya mata baya yaki kulata. Juyo wa yai
    yana k'allonta, duk da a kule yake da ita amma
    har kusan dariya yaso saka. "Ba nace kai hakuri
    ba,Allah kasan ban ta6a kin yi maka abinci ba da
    gangan... Tashi yai ya zauna a kusa da ita. "Toh
    naji na hakura,bar borin...ya sa hannu zai goge
    mata hawaye sai dai kamas... "Au kukan ma na
    karya ne ashe?... Dariya ta fara ta d'au mishi
    pillow sukai d'aki. "Ina a gidan nan Allah ba kai
    ba k'wanan parlour. Murmushi yai yana mai
    tausayin kanshi, ina ma Salman shi ta da ta
    dawo mishi... Ina ma zai yuwu ace kullum yaso
    ganin Salma zai sameta a gida haka?... Ya sani
    da yana son Salma,so ba na wasa ba,amma k'arfi
    da yaji so take tafi k'arfin shi,ga ko kadan bai
    kaunar yaga fushin ta. Ina ma itama haka take
    nannan da nasa fushin... Yasani da *Mai Hali
    Baya fasawa* **************************** Sauri
    take tayi,dan yau gidan mai gumama suka
    je,tasan kuma tabbas Ja'afar yana hanya. Aikwa
    tana zuwa ga nan machine d'inshi a kofa
    halamun yana ciki. Duk da tana jin dan shayin
    shiga su ar'ba, haka ta d'aure ta shiga. Takaddu
    yake nema, da sallama ta shiga, a chan ciki ya
    amsa yana cigaba da abinda yake. "Sannu da
    zuwa... "Uhmm.. Kawai yace, sai ta ta6e baki.
    "Gidan fa mai gumamar nan da na fad'a ma jiya
    ta aiko mana za'a kawo muka je..kaga zuwan
    banza mukai ma wai sai gobe. A dirare ya
    k'alleta lokacin da yake tashi, ganin yai banza
    yasa tace "ni fa nan kad'ai naje,sai gidan Maman
    Ummi dana biya mata muka tafi.. Kai ya k'ada,
    kan yace "yayi k'yau... Maman Ummin ce mijin ki
    koh mai gumamar?... Ido ta zaro,sai ya kada kai,
    "no ba wannan ba ma, wai d'uk inda kike
    azarbabin zuwan nan wa kike gani yana zuwa
    gidan ki yafi minti goma aciki?... Koh d'uk suna
    da aikin yi sai ke kad'ai ce bakki shi?.. Salma ki
    nemi mutuncinki da hannunki,a ganina zai fi
    mu.... "Ka ga malam,ba sai ka zage ni ba zan
    san dama kana kule dani ba,daga fita nan da nan
    din shine har zaka na cemin wata gantalalliya?...
    Haka kawai,in ma kayan ne naga kai zan sawa
    ba wani ba,toh meye abin zafi aciki?. Kai ya
    k'ada kan yace "babu... Amma wallahi kar gobe
    ki sake ki kara fita gun wata mai gumama,in ba
    haka ba zan mugun sa6a miki... Waje yai rai
    6ace, "Ja'afar?... Ni zaka sa6awa?... Chak! Ya
    t'saya ya kasa gaba, a hankali ya juyo fuskarshi
    d'auke da mamaki. "Salma... Yau ni kike kama
    sunana garangatsai ba koh rufi?... K'ugu ta rike
    tana girgiza, "ai sunan ka ne naga.. Kuma muna
    kama sunan Allah ma bare wani chan... Na gaji
    ne da hancini. Kai ya k'ada yana murmushi,
    tabbas ba abinda yai saura da gantalin Salma bai
    gur6ata ba,ciki kuwa harda iya fit'sara. Sai ya
    k'ada kai ya fice,dan yasan komai zai iya faruwa
    in ya tanka. ~~~~~~ Washegari haka aka tashi
    kowa rai ba dad'i, yau ce ranar farko da har aka
    waye gari ba'a shirya ba. Ga yau week end,yana
    gida yaki fita shago. Har yamma ba bayani, sai
    dai yai bacci,ya je masallaci ya dawo. A sama
    take,dan gani take da gayya yaki fita dan ai ba
    ita gidan gumama. Ya dawo daga masallacin
    la'asar ya shiga wanka. Maman Ummi ta turo
    tazo suje kan a za6e,yana jin lokacin da tace dan
    aiken yace tana zuwa. Yazo fita ta biyo shi,dan
    tambaya a ganinta ta wanke lefin jiya ya barta.
    "Ya Ja'afar zamu gidan wannan mai kayan
    Maman Ummi na jirana. Ja yai ya t'saya, kan ya
    juyo ya koma parlour,ba musu ta bishi ai wacce
    za ai. "Tun jiya ai mun gama magana dake,babu
    fita... "A gaskiya sai na je, gashi nan ai kai ka ke
    jawo komai, da lallami na tambaya ba zaka barni
    ba,sai na fita cibi ya zama kari... Haka kurum
    yanzu haka jirana ake ka ce wani bazani ba..ta
    karasa tana kunkuni. "Sai kinje koh?.. Cikin
    fusata tace "eh.. Murmushi yai ya k'ada kai,
    "Bazan hanaki ba toh, sai dai wallahi ki sani,
    mud'in kika sa kafa kika fita,toh *A BAK'IN
    AURENKI*.... Bai jira komai ba yai waje,yana
    jiyota tana ai wallahi bazaka sani kaffara ba,fita
    kam nayi na gama. By Feenat Ja'afar. 庐NWA.
    Like 路 6 路 Reply 路 Report 路 Jul 25
    Ummu Maryam Tahir
    Sannu da qoqari 6ter
    Like 路 Reply 路 Report 路 Jul 25
    Kareema Wakeeli
    Tnx
    Like 路 Reply 路 Report 路 Jul 25
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 18
    _Kitchen_ kawai ta leka,ta d'aura guntun ruwa a
    tukunyar silver a _hot plate_ nata karama nepa
    suka d'auke wuta. Kamar zata kashe,kawai ta
    bari,a ganinta ba komai. Kan su kai gidan
    gumama kuwa 5 tayi,fatansu Allah sa ba'a za6e
    ba. Kaya kam gasu masu k'yau, tuni ta fara
    daddagawa tana ware na wara. "NEPA"... Cewar
    yaran gidan, sai dai da halamun su Salma hankali
    yayi kan gumama. Suna nan a gidan har kusan
    k'arfe 6,amma basu gama da mai kaya ba.
    Kamar ance daga kai sama,sai ga nan dan
    hayaki na yin sama halamar daga nesa ana
    gobara a wani gu. "Ina ga wutar dazu tai ma
    wasu aiki,hayakin nan gobara ce duk yadda
    akayi.. Kai Salma ta k'ada, "koh taya ake konawa
    ba... Sai dai kan su farga ihun gobara har kusan
    layin da suke. Maman Ummi tace suzo su je,in
    yaso daga baya sa dawo suyi bayanin. Da sauri
    Salma ta tare, "A'a Manan Ummi,nasan yanzu Ya
    Ja'afar na hanya 6 saura. "Muje dai koh gobe
    tunda ta kirga wanda muka d'auka ma dawo ai
    sabon lissa... "Umma!..Umma!!... Da gudu yaron
    mai gumama ya shigo, matar tace "lafiya irin
    wannan gudu? Ince dai ba daga gun gobarar ka
    ke ba? Yana haki yace "a gidan Aunty Salma ne
    fa Umma.. Ana ta neman inda za'a shiga a k'ulle,
    yanzu aka kira Malam Jaaf... "Na shiga uku... Ni
    Salman koh wa?.. Kai yaron ya daga,ai ina,da
    gudu ta fice ta wat'sar da kayan a nan ta bar
    Maman Ummi da kira. Kamar wata sabuwar
    kamu haka ta iso wajen,kofar gidan cike da
    jama'a wasu na kok'arin sanya t'sani su haura. A
    ka ta d'aura hannayenta d'uk biyun,tama rasa ihu
    zata kurma koh kuka. Baban Ummi ne yace ina
    mukullin gidan?.. Nan ta fara tunanin mukulli?..
    Innalillahi, ta barshi shima gidan gumama... Baya
    ta fara yi ganin Ja'afar da Garba sun faka mota a
    chan gefe, a gigice suka karaso, "Innalillahi
    Wa'ina Ilaihirraji'un"... Itace kalmar da Jaafar ya
    iya fad'i. Ina kan ta farga sai ga hawaye na zuba
    tana girgiza mishi kai,mukulli Garba ya tambaya,
    kan cikin azama ya lalubo a aljihu ya bashi.
    Salman ya k'allo cikin tausayin kanshi, har yanzu
    hannu na ka tana k'ada kai tana kuka. "Shikenan
    kin zaunar mu Salma... Burin ki ya cika sai ki
    zuba ruwa a kasa ki sha.... Tuni ta kara fashewa
    da kuka. Fad'in "A kashe meter... Ne yasa yai
    cikin gidan da sauri. Ba ka ganin koh ina sai
    dusu-dusu dan hayaki. Da taimakon Maman
    Ummi ta bar kofar suka shiga daga cikin gida.
    Sai dai har yanzu kuka take baji ba gani. Yau
    tasan ta kad'e har ganyenta. Motar kashe wuta
    ce ta iso,da taimakon dak'yar wuta ta mutu.
    Ilahirin kitchen da bedroom ya kone ya laso
    parlour ta silin Allah ya t'sayarta. Fito wa tai
    bayan taji komai ya dan lafa ta leka gidan,sai ga
    nan Ja'afar din sun fito rike da barbadin
    _documents_ nasa a hannu. Kamar munafuka ta
    dan ra6a ta shigo kai duk'e tana jan hanci. Sai da
    yazo dai dai ita ya t'saya. Kanta kasa tana
    sharar hawaye,a hankali ya saki burbudin
    takaddun ya fice jiki duk yayi sanyi.
    **************************** Zaune suke a bak'in
    masallaci shi da Garba bayan komai ya lafa yana
    tausarshi,yan unguwa sai jajanta mishi suke suna
    tafiya. "Dan Allah ka'r ka ce zaka d'au
    mummunan mataki akan Salma, kai
    hakuri,ubangiji ya mayar ma da alkairin da ka
    rasa. Shiru Ja'afar d'in yai,zuciyar shi sai tafasa
    take,dan ma yana ta kok'arin neman kariya daga
    zugar shedan. Zuwa chan dai ya nesa, "Babban
    ni takaici na Garba Takaddu na ne,tun jiya ake
    _verification_ gobe ne namu,ni bana ta
    Salma,dan a bakin aurenta ta fita... "Ni ga nan
    d'akin waje zan iya maleji. Kafad'arshi Garban ya
    dafa,lalle kowa da jarabawar shi a rayuwa,shi
    kuma abokinshi ta mata Allah ya bashi. "Yanzu
    toh ya za ai?... Murmushi Ja'afar d'in yai wanda
    yafi kuka ciwo... "Ya k'wa zanyi Garba?.. Kana
    sane da gamnatin nan tamu, wa zai k'ar6i uziri
    na gobe?.. Shiru yai mishi,dan tabbas yasan bai
    da abin fad'a ma abokin. Gida suka koma,tana
    nan inda suka barta a durkushe ta tasa takaddun
    a gaba tana shesshekar kuka. Ja yai ya t'saya
    yana k'allonta, muryar ta har ta dashe. Abin
    haushi wai kuma zuciyarshi ta fara tausayinta.
    Da sauri ya d'auke kai daga k'allonta dan jin
    zuciya na ingiza shi yaje ya lallaso ta, Salma ce
    fa... Dake wa yai ya daure tukun yace "toh meye
    ne na kuka kuma Salma?..ki tashi kawai kije gida
    dan sharad'in dazu yana kan ki.... Da sauri ta
    dago ta k'alleshi, tuni taji kukan ya kafe,sai ido
    da ta kafe shi dashi, shaf ta manta wani sharad'i
    ne ma? Tuni ta tafi duniyar tuna abinda ya afku
    ka ta fita. Garba ne ya katse mata tunani da
    fad'in "haba dai dan Allah? Wannan sharad'in bai
    k'yautu a gun ka ba Ja'afar.. Aure ya fice wasa
    fa.. Ka janye sharad'in nan tun kan kowa ya ji ku
    koma auren ku.... Da sauri ta k'allo Garba,duk ta
    kasa ta6uka komai, Mey Garba yake nufi da su
    koma auren su? Yaushe Ja'afar ya sake ta?....
    Bai furta ba sai dai in yanzu.. Cikin muryar kuka
    tana ka'rkarwa tace "bai sake ni ba Garba, auren
    mu na nan... Koh yanzu ya furta?.. Banji ba
    Allah... Ni bai sake ni ba...bai sake ni ba.. Sai ta
    karasa tare da fashewa da wani kukan mai ban
    tausayi. Ido kawai suka zuba mata, tamkar
    zararriya haka take magana. Duk sai ta karya
    musu zuciya, barin gogan,har bai san ya je
    gareta ba,da zummar dago ta yaje ya lallashi
    abarshi,sai dai kamar wanda aka t'sayar ya
    d'auke hannunshi, baya ya koma yana rint'se
    ido... Tabbas yanzu saki ya gifta a tsakani,bai da
    _right_ na ta6ata,tabbas bai dashi. A hankali ya
    furta "Salma kin cuce mu... Kin fara dasa
    katanga a tsakanin mu... Ban san da abinda na
    rage ki ba Salma...ban sani ba, dazu a yadda
    nake jin zuciya ta,wallahi dan banzan doka naso
    na miki,Allah ya kareni da yin kuskure. Baya ya
    juya mata,kan ya k'allo Garba. "Dan Allah ka
    kaita gida gani nan zuwa... Waje yai ya barsu
    nan,Shikenan ta tabbata,ba makawa Ya Ja'afar
    ya sallama ta.. Ai tuni ta kara jiniyar
    kuka,dak'yar ta tashi sukai waje da Garban. Sai
    duba Yayan nata take koh zata ganshi. "Muje
    Salma,InshaAllah komai zai daidaita,.. Juyowa tai
    ta sadakar da yai nisa... Yana k'allon su har
    suka kule kan ya fito a inda ya 6oye a bayan
    bishiya. Harda goge y'ar k'walarshi... Salma kinyi
    aiki. By Feenat Ja'afar
    9/29/16, 9:06 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    19_"Toh a garin yaya haka ta faru? Fita kukai?...
    Tambayar da baba ya jeho musu kenan bayan
    Garba ya kawo ta ya dakko Jaafar shima.
    Kukanta kawai take,ita burinta ya kara maimaita
    sakin, kuma yaushe ya mata?. "Salma komai
    mukaddarine fa daga Allah,ba kuka zakiyi ba, kiyi
    adu'ar Allah maida muku alkairi kinji... Kai ta
    dago,ido duk yayi luhu-luhu, ta dubi Ja'afar,
    kanshi na kasa,cikin muryar kuka tace "Abba
    cewa yai fa ya sake ni... Wallahi ba dagangan na
    bari haka ta faru ba.... A zabure Mama tace "ya
    sake ki?.. Kai ta k'ada tana dan k'allon Abba da
    yai shiru yana k'allonta. "Ni dai banji lokacin da
    ya saken ba kuma.. Ta karasa da dan kukanta.
    Abban ta d'aure mai kai, chan ya k'allo Ja'afar,
    "Mey take fad'i ne Ja'afar?... Sam ban gane inda
    ta dosa ba.. Kai ya kara d'ukrawa,kan ya
    dago,mama in banda harara ba abinda take sakar
    mishi. Ya sani da dole su Abba suji. Cikin
    nut'suwa ya hau zayyanawa Abba halin da Salma
    ta t'sirar mishi,har zuwa kawo kararta gun Mama,
    kawo yau da abin ya faru.. Tsananin mamaki
    Abba kasa cewa komai yayi,wai Salman sa ce da
    wannan d'anyen aikin? Chan dai ya numfasa tare
    da fad'in "Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'un... Kuma
    kin fita d'in Salma?.. Baya ta fara ja tana k'ada
    kai, "Abba dan Allah kai hakuri,bazan kara ba...
    Murmushi Abban yai na takaici.. Ya ma rasa mey
    zai wa Salma ya ji dad'i.. Duka? Kai ya k'ada.
    "Ni meye nawa? Ba dai kin fanshi fita sama da
    aurenki ba?.. "Wannan shine sakin Salma...
    Tunda har kin fice bayan yace *A BAKIN
    AURENKI*.... Kai ta dago da sauri.. Saki kuma?
    Daga fad'in hakan?... Kawai sai ta sa musu kuka,
    "Dan Allah ya Ja'afar kai hakuri, Allah bazan kara
    ba,Abba kai hakuri... Cikin t'sawa yace "tashi ki
    bar wajen nan kamin nai miki lilis koh na huce...
    Kasa motsawa tai,ai da zafin nama Abba yai
    kanta da takalmi,Mama ta tare, amma duk da
    haka sai da mummuka mata. Dak'yar Ja'afar ya
    lallaso shi. "Kin wa kanki toh Salma,dan dole
    kizo ki bar gidana, wallahi ba zaki k'wanar min
    ba... "Haba wai Malam dan Allah.. Waye baya
    kuskure a rayu.... "Kimin shiru kema, dan duk
    laifinki ne,tunda kinsan irin shegantakar da take
    aikatawa, amma wai ki kasa sanar ni na d'au
    mataki.. Jan Salman tai d'aki tana bashi
    hakuri,dan sai ya iya had'awa da ita. Sai da ya
    gama sababinshi kamin Ja'afar ya hau bashi
    hakuri, "InshaAllah bazata kara ba Abba, nima na
    rasa abin yi ne shi yasa nai hakan.... "Ni fa
    banga lefinka ba Ja'afar, kamin dai dai.. Gaba
    nasan bazata kara ba. Shi dai kawai hakuri yake
    bama Abba. Abba ya tambaye shi kan saki nawa
    ne? Yace daya. Tashi yai yace ya jira shi,sai
    yace bari yaje gida shima ya d'au machine
    sannan ya sanar musu. D'aki Abban ya shiga
    bayan Ja'afar din ya fita. "Amma kin bani
    mamaki Allah Rabi... Ashe ba zaki zama mai
    g'yara wa ba sai dai kiyi shiru? T'sawan lokaci
    yaro yana hakuri da halin yarinya amma kina
    sane?... Shiru tai,sai da ya gama chake ta ta hau
    bashi hakuri. "Ke kuma tun yanzu har har kin
    kone tun kamin ki tafasa koh Salma?... Kai ta
    k'ada tana yai hakuri, "A'a, ni ai nawa mai sauki
    ne,koh dai ki g'yara halin ki,koh ki shiga hannu
    na... Bansan lokacin da kika sauya k'yak'yawar
    dabi'ar ki ba Salma?.. Sosai yai mata fad'a cikin
    zafi zafi kan ya kara da ta shirya,dan ya rantse
    bazata k'wanar mishi a gida ba... "Haba
    malam,ina zata toh?... Cikin fad'a yace "gidan
    mijinta... Koh da magana?.. Kai ta kada,kan tace
    "sakin fa?.. Sannan wane gida bayan ya kone?...
    "Eh a konan nan zata zauna akwai daki a waje
    yace da bai kone ba,sannan ki sani igiya d'aya
    babu a tsakanin ki da shi. "Ki gode Allah kin
    samu mai sanki,yau da wani ki kai wa haka sai
    ya tabbatar da ya miki shegen duka kan ya baki
    saki... Amma shi kok'ari yayi ma a take yace min
    ya mayarki. "Abu d'aya zan iya fad'a miki
    Salma... Wallahi, duk ranar da zaki maimaita
    haka,ki kuma k'waso kafa ki zo min gida sai na
    6a66alla kafarki... Baki sake Mama ke K'allonshi,
    ita kam yau kad'ai ta kara mugun tsoron
    Abba,tasan a yadda yau ya daketa tsaf zai iya
    6alla tan. By Feenat Ja'afar.
    Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 29
    Zeenat Yakubu
    tnx 1st 2 cmmnt
    Like 路 Reply 路 Report 路 Jul 29
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    19_"Toh a garin yaya haka ta faru? Fita kukai?...
    Tambayar da baba ya jeho musu kenan bayan
    Garba ya kawo ta ya dakko Jaafar shima.
    Kukanta kawai take,ita burinta ya kara maimaita
    sakin, kuma yaushe ya mata?. "Salma komai
    mukaddarine fa daga Allah,ba kuka zakiyi ba, kiyi
    adu'ar Allah maida muku alkairi kinji... Kai ta
    dago,ido duk yayi luhu-luhu, ta dubi Ja'afar,
    kanshi na kasa,cikin muryar kuka tace "Abba
    cewa yai fa ya sake ni... Wallahi ba dagangan na
    bari haka ta faru ba.... A zabure Mama tace "ya
    sake ki?.. Kai ta k'ada tana dan k'allon Abba da
    yai shiru yana k'allonta. "Ni dai banji lokacin da
    ya saken ba kuma.. Ta karasa da dan kukanta.
    Abban ta d'aure mai kai, chan ya k'allo Ja'afar,
    "Mey take fad'i ne Ja'afar?... Sam ban gane inda
    ta dosa ba.. Kai ya kara d'ukrawa,kan ya
    dago,mama in banda harara ba abinda take sakar
    mishi. Ya sani da dole su Abba suji. Cikin
    nut'suwa ya hau zayyanawa Abba halin da Salma
    ta t'sirar mishi,har zuwa kawo kararta gun Mama,
    kawo yau da abin ya faru.. Tsananin mamaki
    Abba kasa cewa komai yayi,wai Salman sa ce da
    wannan d'anyen aikin? Chan dai ya numfasa tare
    da fad'in "Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'un... Kuma
    kin fita d'in Salma?.. Baya ta fara ja tana k'ada
    kai, "Abba dan Allah kai hakuri,bazan kara ba...
    Murmushi Abban yai na takaici.. Ya ma rasa mey
    zai wa Salma ya ji dad'i.. Duka? Kai ya k'ada.
    "Ni meye nawa? Ba dai kin fanshi fita sama da
    aurenki ba?.. "Wannan shine sakin Salma...
    Tunda har kin fice bayan yace *A BAKIN
    AURENKI*.... Kai ta dago da sauri.. Saki kuma?
    Daga fad'in hakan?... Kawai sai ta sa musu kuka,
    "Dan Allah ya Ja'afar kai hakuri, Allah bazan kara
    ba,Abba kai hakuri... Cikin t'sawa yace "tashi ki
    bar wajen nan kamin nai miki lilis koh na huce...
    Kasa motsawa tai,ai da zafin nama Abba yai
    kanta da takalmi,Mama ta tare, amma duk da
    haka sai da mummuka mata. Dak'yar Ja'afar ya
    lallaso shi. "Kin wa kanki toh Salma,dan dole
    kizo ki bar gidana, wallahi ba zaki k'wanar min
    ba... "Haba wai Malam dan Allah.. Waye baya
    kuskure a rayu.... "Kimin shiru kema, dan duk
    laifinki ne,tunda kinsan irin shegantakar da take
    aikatawa, amma wai ki kasa sanar ni na d'au
    mataki.. Jan Salman tai d'aki tana bashi
    hakuri,dan sai ya iya had'awa da ita. Sai da ya
    gama sababinshi kamin Ja'afar ya hau bashi
    hakuri, "InshaAllah bazata kara ba Abba, nima na
    rasa abin yi ne shi yasa nai hakan.... "Ni fa
    banga lefinka ba Ja'afar, kamin dai dai.. Gaba
    nasan bazata kara ba. Shi dai kawai hakuri yake
    bama Abba. Abba ya tambaye shi kan saki nawa
    ne? Yace daya. Tashi yai yace ya jira shi,sai
    yace bari yaje gida shima ya d'au machine
    sannan ya sanar musu. D'aki Abban ya shiga
    bayan Ja'afar din ya fita. "Amma kin bani
    mamaki Allah Rabi... Ashe ba zaki zama mai
    g'yara wa ba sai dai kiyi shiru? T'sawan lokaci
    yaro yana hakuri da halin yarinya amma kina
    sane?... Shiru tai,sai da ya gama chake ta ta hau
    bashi hakuri. "Ke kuma tun yanzu har har kin
    kone tun kamin ki tafasa koh Salma?... Kai ta
    k'ada tana yai hakuri, "A'a, ni ai nawa mai sauki
    ne,koh dai ki g'yara halin ki,koh ki shiga hannu
    na... Bansan lokacin da kika sauya k'yak'yawar
    dabi'ar ki ba Salma?.. Sosai yai mata fad'a cikin
    zafi zafi kan ya kara da ta shirya,dan ya rantse
    bazata k'wanar mishi a gida ba... "Haba
    malam,ina zata toh?... Cikin fad'a yace "gidan
    mijinta... Koh da magana?.. Kai ta kada,kan tace
    "sakin fa?.. Sannan wane gida bayan ya kone?...
    "Eh a konan nan zata zauna akwai daki a waje
    yace da bai kone ba,sannan ki sani igiya d'aya
    babu a tsakanin ki da shi. "Ki gode Allah kin
    samu mai sanki,yau da wani ki kai wa haka sai
    ya tabbatar da ya miki shegen duka kan ya baki
    saki... Amma shi kok'ari yayi ma a take yace min
    ya mayarki. "Abu d'aya zan iya fad'a miki
    Salma... Wallahi, duk ranar da zaki maimaita
    haka,ki kuma k'waso kafa ki zo min gida sai na
    6a66alla kafarki... Baki sake Mama ke K'allonshi,
    ita kam yau kad'ai ta kara mugun tsoron
    Abba,tasan a yadda yau ya daketa tsaf zai iya
    6alla tan. By Feenat Ja'afar.
    Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 29
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 20_Koh
    da Ja'afar din yazo haka ya kara bashi hakuri kan
    suka d'au hanya. Zaune take a d'akin da ya rage
    musu,duk ta dawo kalar tausayi. Waya yake
    amma yana k'allon yadda ya takure kanta tana
    K'allonshi. D'anna wayar ya cigaba bayan ya
    gama, cikin nut'suwa ta hau bashi hakuri, kan
    Allah bazata kara ba. Sannan bazata kara fita ba
    izinin shi ba. Shiru yayi,hakan yasa ta fara kuka
    tana rantsuwa kan haka. Sauka yayi akan 1sittern
    dake a d'akin ita kad'ai sai karamar katifa da filo
    daya da ledar t'sakar d'aki. Yasan dan so yana
    ma Salma,sannan yana matukar ganin darajar
    Abba cikin idonshi, sannan yana mutunta
    soyayyar da ta mishi a da chan baya. "Salma kin
    d'aina so na yanzu sam,shi yasa ki ke ganin
    damata a yanzu... Ki duba kiga abinda yawan ki
    ya wanzar mana...nayi imani a garin saurin ki
    fita ne har kika manta wani abu a k'unne a
    kitchen... Ki duba irin kinjin magana ta abinda ya
    jawo... Salma takadduna sun kone kaf...sai
    guntu, sanin kanki gobe muna da _verification_
    da za'a gunar mana. "Ba wanda zan je ma hannu
    Rabbana ya k'alle ni... Kinga meyiwa na rasa
    aiki,dan zan shiga _miss call_... Kinga kin zaunar
    mu... Ba gida ba aiki.. Cikin kuka ta mat'so tana
    bashi hakuri, "kai hakuri banzan kara ba Allah..
    Murmushi yayi kamin ya janyota da sigar lallashi.
    "Ina sonki Salma,kisa a ranki komai zanyi zanyi
    ne _for your own good_... Bazan ta6a miki abu
    dan tuzarci ba... _cos I love you_... Kank'ameshi
    ta kara cikin jin dad'i... Tabbas tana son mijinta,
    zata jure komai dan 6acin rana irin wannan. Koh
    da yazo k'wanciya ita tana gefe yaga bata niyar
    k'wanciyar tunda ta fito a bayan gidan waje.
    Daga k'wancen ya mika mata hannu halamar
    tazo. Har wata kunyarshi ce ta da tazo mata
    yanzu. Da rarrafe ta isa gareshi,sai ya nuna
    mata kafad'arshi kamar kullum,nufunshi ta sa
    kanta. Da murmushi ta g'yara, kan cikin nut'suwa
    ta zame ta k'wanta. Duk kusan tare suka sau
    ajiyar zuciya, bata ta6a saba bacci a kafad'ar Ya
    Ja'afar ba... Haka shima bai ta6a sa6a bacci,ba
    tare da Salma na hakarkarinshi ba. A daren ta
    tabbatar mishi da lalle har yanzu tana son
    nashi,har ma tai kok'arin mantarshi wasu
    abubuwan. *Hmmm..Allah sa da gaske ne
    Salma*... *************************** "Haba dai?
    Yaushe?.. T'salle ta doka lokacin da ta sauke
    wayar a k'unnenta... "Ya Ja'afar.... Da sauri ya
    katseta da "Ummi ta haihu... Yana murmushi.
    Hannunshi ta kamo,sosai tana a farin ciki.
    "Yaushe zamu ganin baby?.. Murmushi yayi,kan
    ya k'alli agogo, shida da rabi,harda wasu y'an
    mintuna. "Yanzu kam dare kinga ya gabato...
    Gobe da safe kan ma an sallamota sai kije koh?..
    Kai ta k'ada tana wani tunani... Jin ya kai hannu
    cikinshi yasa ta dan murmusa.. Gira ya daga
    mata,kamin yace "saura mu koh?... Murmushi tai
    mishi ta k'ada kai. "Mun kusa ai...k'wantar da
    hankalin ka sarkin son yara... Dariya sukai,kan
    yace "sosai ina son su kam...in naje yaron Garba
    kamar nace su bamu aro... Kai ta k'ada, "lalle a
    gaishe ka.. Ni kam nafi son mu shekara kan na
    haihu da... Murmushi yai yana kada kai kawai.
    ~~~~~~~~~~~~~~~~~~ "MashaAllah, ganshi
    kamar dan larabawa... Ta g'yara mishi hular
    kanshi... Dagowa tai cikin wasa tana"um um,su
    Ummi an iya haihuwa... Shiru tai ganin yadda
    Ummin ta 6ata rai. "Mey akai kuma ki ke wani
    6ata rai ina magana?.. Baki ta ta6e,kan ta ja
    k'wanon namanta ta fara ci. A y'atsine tace "ya
    bazan bata rai ba?... Saboda t'sabar wulakanci
    tun jiya na haihu amma sai yau zaki wani zo kina
    nad'e taburmar kunya?... K'allonta take ba
    kiftawa, sam Ummi batta kunya.. Sai dai kawai
    ta basar. "Dadina dake Ummi baki bada uziri a
    koman ki.. Yanzu ina laifin kin haihu da magariba
    nazo da sassafen nan?... Baki ta ta6e kan ta
    had'iye naman bakinta. "Ki ce kinbi order mijinki
    dai Malama, amma bare nawa ne suka zo tun a
    jiyan?.. Karara tsoron mutumin yaci k'arfin ki
    k'wana biyu na fuskanta... Shiru tai dan bakin
    ciki, ba abinda ta t'sana irin a dinga cewa tana
    tsoron Ja'afar...K'wafa tai cikin ranta. Zuwan
    Aunty A'i ne yasa aka dawo mutunci kuma.
    Kullum tana gidan Ummi,duk dan gudun magana.
    Yau kam Ja'afar yace ta hakura gobe tunda aiki
    jibi kuma suna,yau masu g'yaran gida zasu zo.
    Ba tace toh ba,haka bata ce a'a ba. Sai dai duk
    ta sauya,tunaninta muddin yau take zuwa gidan
    Ummi,toh ba makawa sai sunce chaketa,hakan
    ya tabbata kenan ita mai tsoron Ja'afar ce.
    Tabbas lokaci yayi da zata nuna musu bata
    tsoron Ja'afar. Hakan yasa da k'warin g'wiwarta
    ta tashi ta bishi d'akin waje. Shiri yake yana son
    fita wajen ciciku cikun neman takaddun shi da ya
    kone. Yanayin da ya ganta ta dan kama kai
    yasan yau abin ya mot'so. Kawai sai ya kau da
    kai. Zama tai gefen gado tana k'allon shi ta gefe,
    "Haba Ya Ja'afar dan Allah... Yau daya kar kamin
    haka dan Allah, ka barni naje tunda an g'yara
    kitchen ga kuma d'aki muna dashi a waje bayan
    suna suyi aikin.... Ido kawai ya zuba mata,sai da
    ta kai Aya tukun yai magana. "Ke mey yau din
    zata miki in baki fita ba?.. Kullum fa tun
    haihuwar nan kina fita Salma,dan yau kad'ai nace
    ki hakura sai gobe shine ba zaki iya ba Salma?
    Fuska ta y'atsine, kan tace ita dai kawai ya barta
    ta fita toh. K'allonta yake,abu yai sauki yanzu
    tana son dawo da hali? "Son ranki za'a bi yanzu
    koh nawa Salma?... A gida na ban isa nace ga
    abinda za ai ba sai ace a'a?.. Meye haka kike
    son kawo wa kuma da ya wuce?.... Hawaye ta
    fara mishi,tabbas yau in bata fita ba,toh gobe fa
    sai dai ta toshe kunne. Haushi tai bala'in
    bashi,akan wannan shine harda kuka?.. Sam bai
    son abin da ya wuce a dawo dashi. Nan ta zaune
    mishi tana mishi kukan gardamar sai ya batta.
    Haka yanaji yana gani sai shi ya sauke ya barta
    yace ta shirya su je. Da murnarta ta shirya suka
    fita ya sauke ta. Sai dai shi sam baida walwala.
    Haka tai ta fita har ran suyar nama,washegari
    ma wai zata wanke gida,anan suka hau suka
    fad'o.. Ya ja ta ja,harda fad'in dama ance
    tsoronshi take ji. Ya rant'se da in har ta fita,toh
    zai maimaita mata abin ranar,wato ta fita a bakin
    aurenta. Tuni ta nut'su ta dawo hankalin ta. Tuni
    ya kashe bakin t'sanya,har ya fice ya barta tana
    kuka,harda dariyar mugunta... Ya k'wa gano lago
    ai. By Feenat Ja'afar.
    Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Jul 29
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    21_Ranar ta fita a Napep ta layin su Ja'afar taga
    wani kamar shi tare da wata, har zasu wuce ta
    gane Bintu ce,da sauri tace mai Napep ya t'saya.
    Sam a yadda suke ba kace ba masoya bane,dan
    sai wani sunne kai take kasa halamar kunya.
    Tuni zuciyarta ta hau tafasa,ba shiri tai wajen
    gadan-gadan,dai dai suyi sallama harda dago
    mishi hannu. Kan ta karasa har ya juyo itama ta
    tafi... Ganin yanayinta shima ya dan
    tsorata,amma sai ya maze. "A'a, har kin fito?..
    Harara ta sakar mishi kan ta k'allo Bintun da har
    tai mata nisa. "Ban sani ba... Ashe dama zance
    ka fito shine kace na hau adaidata koh?.. Kuma
    da Bintu?.. Har kana wani yage mata baki...
    Hannu ya kai kan bakinshi halamar tai shiru yana
    duba layin, "Haba Salma,a titi fa muke,kiyi hakuri
    ba abinda ki ke zata bane ba... Harara ta kara
    sakar mishi,kan ta farga har ido ya ciko da
    hawaye. Tabbas yau ya tabo jaraba... Dan sarai
    yasan Bintu kam sonshi take,kuma Salma ta
    sani. Akan kishiya k'wa, yasan sai Salma taki ci
    taki sha. Tuni ya hau lallami harda rantse rantse
    kamin ta yarda bayan anje gida. Wataran yakan
    yi tunanin koh Salma na da Aljanu,in ta tashi
    sauya hali tafard daya ne,sai dai in ya bud'e
    mata wuta su shirya. ~~~~~~~~~~ "Shiru ake
    jinki makociya,koh dan ziyarar yamman nan an
    daina zuwar mana sai jefi-jefi, koh mutumin har
    yau yana nan da kullen?... Baki ta dan ta6e,kan
    ta bawa maman Ummi amsa. "Ai sai abinda yai
    gaba, yanzu tunda akai abinnan na farko abu
    kadan sai ya kafan sharad'i kan in na t'sallaka a
    bakin aurena, ina gudun rabuwar mu,yanzu ma
    minti goma ya ban na dawo. Baki Maman Ummin
    ta ta6e, "lalle kina da aiki in dai mazan nan ne,
    saf zasu mayarka marar y'anci in bakai ma
    tufkar hanci ba,harda lokaci? Tab aiki.. Ga gobe
    sunan _nurse_ din layin chan (Maman
    Nuwaira),ke koh barka baki je ba, ke kinsan za'a
    watsa karya kiyi kok'ari ya barki muje. Kai ta
    k'ada, "Ai dole,dan wallahi baza ai bani ba,ko bai
    bari ba naje koh minti ashirin ne a wat'sa
    warishan nan dani. Hannu Maman Ummi ta bata
    suka tafa harda shewar su,ana haka Ummi tai
    sallama,kan tunda ta shiga Jafar yace tana nan
    ta fito,wai sai had'a rai yake,shi yasa ta bar
    mishi gidan, nan ta daura kan na Maman Ummi,
    Zuwa chan Maman ummin tace "Kiyi kok'ari hudu
    ki biyo min zuwa 5 dawo. Da wannan suka baje
    har ta wuce ka'idar Ja'afar. *Washegari*. "Wai
    dan Allah Salma na tambaye ki zaki ban amsa?
    Y'atsine fuska tai kan tace "ina ji.. "Shin dad'i ki
    ke ji in kin t'saya muna musayarya magana
    dake?.. "Mey yasa in na ce ki bar abu sai dai nai
    son ranki,amma ni ban isa ba? "Ita maijegon ta
    ta6a tako kafarta cikin gidan nan da sunan tazo
    gunki?.. Ki ban amsa? Baki ta saka,kan tace
    "oho,kana nufin gyaiyar sod'i zani kenan?.. Tunda
    ga areni muje biki koh?.. Kai ya kada, "Ke ki ka
    kira kanki haka,ba Ja'afar ba,abu daya na sani,ko
    na fita ba jimawa zanyi ba, saboda in ma kin
    fita,toh kisan inda dare ya miki... "Mey ka ke
    nufi? Kana nufin yau ma zaka ce a bakin auren
    nawa Ja'afar?.. Da sauri ya kada kai,
    "K'warai,tunda abinki naga na yanzu har so yake
    yafi na da, in har kam kin fitan,toh kisani,kin fita
    *A BAKIN AURENKI*... Sai ki zabi wanda ya fi
    miki, aure? Koh gidan suna?... Kofar ya bugo
    mata yai waje tare da barinta baki sake. "Eh lalle
    yau zan nuna ma tabbas ba tsoron ka nake ba
    Ja'afar... Wannan kurin bakin wallahi bazai
    hanani fita sunan ba,daga yau kalmar nan ta *A
    BAKIN AURENKI* tabar bakinka. Daki tai tana
    balbalin masifa ita kadai kamar yana k'allonta.
    Kaya ta fito dasu tana duba wanda zata sa,
    _lace_ din sunan Ummi ta dakko wani karamin
    _swiss_ da aka sashi siyanshi dan dole. Sunan na
    manya ne, dan haka sai da kure adaka. Ba koh
    shakku ta fice, yau tun dazu taji gidan su Maman
    Ummi t'sit kamar ruwa ya shanye su,halamar mai
    gidan yana nan kenan,amma tunda ta fara jiyo
    hayaniya tasan yai waje. Gidan suna kam ya
    kayatu, sun samu abinda ake so tuni aka baje a
    faranti ana ci ana kora wa gulmar wata. Kan ta
    farga har 5 da yan mintina. Haka kawai taji
    gabanta na fad'uwa hankalinta yayi gida. Tashi
    tai ana fad'in ta t'saya k'ulli ya kare a k'ulla
    mata tana a bawa Maman Ummi. Sauri take ta
    zubawa, dan da y'ar tazara a t'sakanin su.
    Adu'ar ta daya,Allah sa Ja'afar bai dawo ganin
    koh ta fitan ba. Ta rasa dalilin da ya sa
    hankalinta ya tashi,bayan ita ta zabi hakan.
    Lekawar da zatai shine taci ka'ro da Ja'afar suka
    had'a ido. *WAIWAYE*... ***************
    ************** Haka yai ta juyi har kusan k'arfe
    biyu. Washegari haka ta tashi sukuku, ga
    fargabar Abba yau zai dawo,ga wani mugun
    mak'on Ja'afar da yake taso mata. Kai in ma ba
    wai bata kula bane gani take zazzabi ne a jikinta.
    "Salma... Dagowa tayi ganin mama a kofa,da
    mamaki fal fuska ta karaso ciki. "Wai har yau
    kukan nan ki ke Salma?.. Mey yaron nan yai miki
    ne haka?.. Hannu ta kai kan fuskrta,sam ba
    tasan tana kuka ba, da sauri ta goge tana
    k'ak'alo murmushin dole. "Mama ina k'wana.. Kai
    kawai ta kada mata. "Haba Salma,kar fa ki rako
    mata duniyar nan...kar ki zamo mace mai
    kulafucin D'a namiji duk k'wa wulakancin da ya
    mata man... Ashe ni ina chan jiya nai baccin
    farin ciki da aka rabu lafiya ba rabo bare ya kawo
    cikas a zawarci ashe ke kina nan kina kukan an
    rabu? Haba Salma, karan nan ne fa ki ke da
    dama ta biyu,tunda har ya sallame ki. "Maza
    goge hawayenki ki biyoni daki yanzu. Kai ta
    kada,a gaskiya ta fara mamakin irin kiyayyar
    dasu mama suke ma Ja'afar, wato har ma godiya
    ake ta rabu da alakakai?... Allah yaga tafi jin
    haushin kanta sama da haushin Ja'afar, in ma
    taji haushin shi toh bai wuce yadda ya k'ulle
    mata gida ya kuma tafi koh ajikinshi. By Feenat
    Ja'afar.
    Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 29
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    22_"Toh wa ya jawo?... T'sam tai yayin da zuciya
    ta tambaye ta, "Ni ce... Tabbas ni najawo, amma
    ba laifi na bane. Kuka ta fashe dashi,tabbas anci
    k'arfinta,ta ko'ina an mata dabaibayi da huduba
    gur6atacciya. "Gashi na jawo wa kaina saki biyu
    ba tare da na samo kan ba(kan Ja'afar).. "Oh ni
    Salma.. Ina tunani na yake da har na aikata
    wannan wautar?.. Ina son da nake ikirarin ina ma
    Ja'afar?.. Ina ya je... "Salma... Mama ce ta
    kat'se mata tunanin gaskiya da kira. Hannu tasa
    ta share hawayen ta,ta daga kai tare da fitar da
    iska dan daidaita nut'suwar ta. "Na'am.. Ta amsa
    kan ta tashi tai waje. "Gani mama, Kan gado ta
    nuna mata kan tazo ta zauna. Ba musu ta
    karaso. Kafad'arta ta dafa kan ta numfasa, "Kina
    ji koh Salma? Kai ta daga mata. "Baban ki yau
    nasan zai dawo,tabbas ya rit'saki nasan zai cid'a
    ki ne a banza. "Yanzu abinda nake so kiyi
    shine,ki je gidan A'i,dan mijinta baya gari ya tafi
    sari,ki barni in na gama lalla6a shi sai ki
    dawo,dan karan nan kam sai dai ai wacce za ayi,
    amma aure kin gama... G'wara a chanja
    hannu,tunda wannan d'in ba fus, bare ass,sai dan
    banzan dacin rai ba koh gidan kai... Hawaye ne
    ya zubo mata,ba da ban suna matukar kama da
    Mama ba,da tayi shakkun akan haihuwar ta...
    Mama na da kamasho a ta6ar6arewar aurenta
    kashi 70 acikin dari... Tabbas uwa uwa ce,
    amma su kam tasu uwar sai g'yaran Allah..
    "Au,au,kuka ki ke? Dan nace baida gidan
    kanshi?.. Koh shi ya siya ya gina da gumin ajin?..
    Yarinya ki duba yadda ake harka,y'an uwanki na
    shiga ta alfarma amma ke kin zama y'ar k'allo..
    Ki farka a bacci Salma,dan rayuwar nan ta zo mu
    fafata ce. Kai ta k'ada tana goge ido,sai ta mike
    tai hanyar waje, "Bari na shirya zuwa gidan
    Aunty A'in, naga 10 tayi. Kai Maman ta daga
    harda washe baki, "Yauwa,ko ke fa.. Maza aje a
    shirya,ga nan abincinki a kitchen. Kai ta k'ada
    kan tai waje, da kallo Maman ta bita, ba abinda
    y'arta ya gaza a gareta,wa ma zai ce ta ta6a
    aure in ta fito da ita gari?.. Dole kud'in da ba taci
    ba da yanzu taci gun Salma. ***************
    ************** A k'wance take kan _3sittern_
    Aunty A'i,in banda ciwan kai ba abinda take,
    "Tashi ga maganin kisha... Kai ta dago,Aunty A'i
    rike da kofi da _paracetamol_. Bayan tasha ta
    g'yara zama,d'uk gidan bata jin da wanda bai
    ta6a kushe mata Ja'afar ba sai Abba da Aunty
    A'i. Hawaye ne ya zubo mata,kan kai duk'e tace
    "ban san mey Ya Ja'afar ya t'sarewa su Mama
    ba da sam basa kaunarshi... Yanzu ki duba Aunty
    A'i Mama yau tace murna take an sake ni..
    Harda fad'in g'wara da bamu samu rabo ba...
    Kuka ne yaci k'arfinta,tuni ta hau yi ba
    kakkautawa. Taso wa Aunty A'in tayi zuwa kusa
    da ita ta hau lallashi,chan ta numfasa itama
    harda hawaye ta fara fad'in "Kinyi wauta Salma
    matuka,samun irin Ja'afar a yanzu wallahi sai kin
    tona,irin halin da kika dinga karta mishi duk na
    samu gun Abba,kinsan nima ba wai Mama nayi
    dani bane sosai,dan ban fiya shiga irin shirgin
    nan ba. "A gantali har gida sukutum ki ka kona
    mishi Salma.. Naji ance ya kuma shiga cikin y'an
    _missed call_..Bana tunanin har yau ya gama
    tattare takaddun da ya rasa kuma duk a dalilinki
    fa,amma dai dai da rana daya bai ta6a hanaki ci
    koh sha ba?.. Duk da baki san ta ina yake samu
    ba. "Maimakon ki zama mace ta gari mai
    k'wantar mishi da hankali har ya manta bakin
    cikin da yake ciki na rasa aikinshi,a'a sai ma
    kara hura mishi wutar masifa ki ke a gida.
    "Salma kina da ilimi fa,kinsan d'ukkan hukunci a
    game da matar da take sa6a umarnin mijinta,
    bare ke da kusan kullum cikin shi kike?.. Ina ki
    ka bar islamiyar taki Salma?.. Da har kika bari
    rudin su Ummi da chan wasu jahilan makotan
    suke hure miki k'unne,wanda in zaki titsiye su ba
    mai iya rashin mutuncin da ki ke Salma.. "Nayi
    imani zaman cikin gidan ki ya fiye miki alkairi
    sama da zaga makota yawan gulma da ki ke..
    "Ya sanar ni shi sai a shafe wata nawa,baiga
    makotan naki na zirya gidan ki ba sai dai aiken
    bani taliya bani mai, shin sun fiki sanin ciwan
    kansu ne Salma? "K'wanaki haka har gida na
    samu yana fad'a kina fad'a, amma dana shiga nai
    miki fad'a, sai kika nunan wai maza sai da wuta..
    "Kan kiyi aure Salma ni nayi da shekara hudu, ba
    zaki fad'an halin maza ba,amma a lokacin na biki
    da murmushi ne kawai. "Ki dube ni nan Salma...
    Dago tai ido jajir hawaye na zuba. "Wallahi tunda
    nake akan fita unguwa ban ta6a sa'inasa da
    Abban Aslam ba,kar kara in naja,ya ja,hakura
    nake na barshi,wani sa'in sai kiga har ya
    fita,amma sai ya dawo yace in shirya ya sauke
    ni,ina fara'a za'a gama komai ba bacin rai, duk
    wanda zai fad'a miki ana tank'wasa namiji ta
    fad'a da bala'i wallahi karya yake miki,sai dai ma
    kullum yai ta baud'e ga uwa uba sane mishi da ki
    ke. "Zuciya nason d'ukkan mai k'yautata mata
    Salma,sannan a kullum tana kara nisa ga wanda
    ke munana mata... Ki gane wannan, tunda dama
    taki,shine ya koma miki ta hagu, ki fita a bakin
    aurenki Salma, tun da kuruciyar ki wai har kin
    zama bazawarar k'arfi da yaji? Ranar da kanshi
    Ja'afar din yazo gidan nan,akan irin yadda ba
    k'ya jin maganarshi,nai mishi alkawarin zanje har
    gida na miki fad'a sai gashi Allah ya kawo
    wannan. Sosai tai mamakin Aunty A'i,da yau ta
    zauna fed'e mata biri har wut'siya.. Tai imani duk
    maganganunta ba wanda ba ita ke da laifi ba
    tabbas. Wata muguwar nadama ce ta sakko
    mata,kuka kam ba kama hannun yaro, har sai da
    taji ba dad'i. Bataki koh yanzu ta nemi gafarar
    Ja'afar ba kan ya maidata aurenshi,tai alkawarin
    d'auwama acikin dakinta har sai yace Salma fito.
    Aiya Salma, Ja'afar baya tataki,yanzu ta Bintu
    yake.. By Feenat Ja'afar.
    Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 29
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    23_Zazzabi harda amai take,duk zatan Aunty A'i
    akan kukan da taki dainawa ne. Washegari ba
    zato ba t'sammani Aunty A'i ta t'sinkayi sallamar
    Abba a t'sakar gida. Lokacin dawowarta daga
    band'aki kenan ta gama zuba ma Salma ruwa a
    amai na tun jiya da yaki t'sayawa,sai dai tana jin
    Abba ne ta mike tare da yin waje da sauri.
    Hannu Aunty A'i ta d'aura aka,ganin zabga-
    zabgan bulalin da Abban ya shigo dasu gidan,
    fad'i yake "Ina take Aisha?.. Tuni idonta ya raina
    fata,fatan ta Salma taji ta buya. Cikin in'ina tace
    "Abba wa d'in?.. Hannu daya marar bulala ya
    nunota dashi, "Kinci gidan ku... "Bani hanya na
    wuce,yau mai rabani da Salma sai Allah a gidan
    nan.. Da k'arfi Aunty A'i tace ta gudu,hayaniyar
    ce ta fiddota a band'aki ta had'a uban zufa dan
    azabar amai, har bata danji sosai, lekawa tai ta
    labule jin an ambaci sunanta... Ido waje ta koma
    da baya tana neman ma6oya,tuni ta ware tai
    bayan kujera tana rufe baki da duk hannunta biyu
    jin Abba a parlourn. "Dan Allah Abba kai
    hakuri,wallahi bata da l... "Aisha,koh ki fito min
    da ita koh bulalinnan su kare a kanki... Ido Salma
    ta rint'se da sauri,kirjinta sai d'ukan tara tara
    yake. Sai dai mey? Kamshi turaren kayan Abba
    ne ta busu hancinta,take taji amai ya taho tai
    kokarin ta mat'se sai dai ta kasa,tuni k'ak'arin
    aman ya taho sai dai ciki ba komai. Bata zata ba
    sai jin magiyar Aunty A'i tai tana dan Allah yai
    hakuri... K'wak'waran mot'si batai ba taji saukar
    bulali tai ajiki ta ko'ina. Ihu take da iya guntun
    k'arfin daya rage mata tana Abba zan mutu,
    ina,kawai lafta mata yake,da Aunty A'i ta rike sai
    ya cika ya hau zuba mata wata. Makogaro ba
    ruwa,duk ya tafi a amai,tuni har muryarta ta
    dashe,sai k'ak'arin amai da take. Kamar an hullo
    mama sai ganinta sukai a kid'ime,ganin yadda
    yake jibgar Salman ta bala'in tsorata, da sauri tai
    waje dan kara kiran yayanshi Ganin Abba zai
    kisa,yasa da sauri Aunty A'i tai ma Salman rumfa
    tana yai hakuri cikin kuka,ganan Salma koh
    k'wakkaran mot'si batai,bai bi takanta ba ya hau
    zuba musu tare, "Abba ciki ne da ita,wallahi zai
    zube.... Chak ya t'saya da bulala a hannu sai
    zufa yake, yai dai dai da shigar Mama tai katari
    da zancen Aunty A'in. Bulala ya yarda yana
    haki,tamkar yasa kuka dan bakin ciki,tunda yake
    basshi da fadanshi amma bai ta6a sa hannu ya
    dakesu ba sai akan Salma,wannan shine karo na
    biyu gareta. So take tafi k'arfin kowa a ganin
    shi,toh shi bazata fi karfinshi ba. "Ba mai fin
    karfina a gidana ban maganin shi ba... Yau kin
    t'sira a dalilin zancen A'i,da na lahira ya fiki jin
    dad'i.. Duk da laifin nafi daura ma uwarku data
    zuba ido kuna abinda kuke so... "Mun shiga
    uku... Da sauri Maman tai kan Aunty A'i mai
    magana. Jijjiga salman take tana kira. "Salma!...
    Salma!!.. Mama bata mot'si wallahi... Tuni suka
    hau jijjigata Aunty A'i na kuka. "Shikenan Malam
    ka kashe min Y'a ka huta... Babu yadda banyi da
    kai ba akan kai hakuri kar kazo,kar kaje,ga nan
    irinta ka... "Ki rufe mana baki, koma meye ke
    kika jawo, ruwan k'anin Aslam ya gani a jarka da
    sauri kuma ya dakko wai su mat'sa agun,ido duk
    hawaye suka mat'sa. A hankali ya dagota tare da
    yayyafa mata, a hankali ta kawo numfashi sai dai
    ido a rufe. "K'unnen k'ashi gare ki ne Salma,shi
    yasa baza mu shirya ba sam sai kin g'yara hali.
    Kuka ta fara kad'an kadan lokacin da suke
    dagata, sosai ta lillisu,duk jiki ciwo. Wayar Aunty
    A'i,da Ja'afar suke magana wai yaji Abban su
    yace Mama ta bugo kan Abba zai kashe Salma...
    Cikin kuka tace "Kazo gidana suna nan. Duk ya
    kuma kid'ime, tabbas ba d'ukkan wasa yasan
    Abba yake ma Salma ba,tunda Aunty A'i take
    kuka. Garba ya kalla,"dan Allah kaini gidan Aisha
    yayar Salma. Da mamaki yake K'allonshi, "amma
    dai kasan yanzu _chairman_ zai zo yama signing
    koh?.. "In bazaka kaini ba na fita na hau abin
    hawa. Kafad'a ya daga, "a muje, ni meye nawa.
    Mijin Aunty A'in ya kira koh yana gidan,yace su
    shiga kawai,Abba ya sanarshi komai tun dazun.
    Abba ya fita lokacin da suka zo,mama ta tafi
    nemo abin hawa. Aunty A'in ce ta shiga
    dasu,ganin bulalin wajen duk sun kakkarye ji yai
    kamar yasa kuka,yanzu duk bulalin nan a jikin
    Salman sa ta kare? Jiki a sanyaye suka je
    parlourn,duk ta kudindina tana rawar sanyi,da
    sauri ya karasa gunta yana kira,tana jinshi ta
    kara rushewa da wani kukan. Hijabin ya yaye
    mata,yana ko'k'arin cicci6ota ya tuna da sakin
    dake t'sakanin su,sai ya zame hannu tare da
    zama. Bai san wani irin so yake ma Salma
    ba,wanda har yake rawar jiki akanta duk da
    abinda ta mishi, gashi har taja jiya ya bada kai
    gun Bintu bori ya hau. "Mey yasa Salma?.. Mey
    yasa ki ka zabar mana irin rayuwar nan?.. Gashi
    yanzu kin dasa min son kara aure koh na samu
    maslaha aciki... A zabure ta tashi,duk da yadda
    take jin jiki tana cije le6e dan azaba. "Mey kace
    Ya Ja'afar?.. Aure?.. Da sauri ya k'allo ta,sam bai
    tunanin zancen ba a ciki yai ba. Ganin bai bata
    amsa ba yasa ta yarda da abinda taji,hannu tasa
    duka biyu ta dafa kan ta zamo kasa tana cije
    baki,g'wiwa biyu ta durkusa duk tai kalar tausayi.
    "Ka rufamin asiri Ya Ja'afar dan Allah,wallahi, na
    rantse bazan kara ba..Dan Allah kar kamin
    kishiya.. Dan Allah, wallahi bana sonta.. Allah
    zan g'yara..nai alkawari,.. Ido ya rint'se, had'i da
    cije le6e,ba yau Salma ta fara mai magiya da
    rantsuwa kan ta d'aina ba,amma ba abinda ya
    sauya zani.. Yanzu komai ya kare musu,aure
    gareshi ya zama dole. By Feenat Ja'afar.
    Juma'@ Mubarak.
    9/29/16, 9:07 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 24-Kai
    ya kada tare da mikewa, "kiyi hakuri Salma.. A
    baya na baki d'ukkan wata dama taki kinyi watsi
    da ita.. K'arfi da yaji so ki ke ki mayarni wani
    iri,dame zanji Salma?.. Na fita waje na samo
    6acin rai,sannan na shigo gida nan ma wani
    6acin ran ne,maimakon a lallashe ni..A'a ni
    kullum ni nake lallashi. "Kiyi hakuri,Allah ya baki
    lafiya.. Garba ya k'allo yai mishi halamar su tafi.
    A hankali ta mike tana jin wata irin hajijiya na
    debarta. "Nasan ni na ja ma kaina komai Ya
    Jaafar... Ja yai ya t'saya, jin taci gaba yasa ya
    juyo. "Tabbas na chanchanci d'ukkan wani
    hukunci da zaka min in dai zaka yafe min.. Kasa
    tai da kai,tai matukar zama abin tausayi a
    gunshi,sai dai kawai ya kasa gane nadamar
    Salma a yau,dan ta saba, ga kafa sai ka'rkarwa
    take. "Amma dan Allah wa zaka aura?.. Ba dai
    Bintu ba?. A yadda ta t'sareshi da ido yasa ya
    kasa magana,sai ya kalli Garba,kafad'arshi ya
    daga mishi halamar ba ruwan shi. Sai da ta
    maimaita kan ya daga mata kai. Murmushi tai da
    yafi kuka ciwo,a hankali take neman juyawa wani
    kanta ya sara gami da ganin duhu. "Kar ki min
    fassara Salma,ba abinda ya had'ani da Bin... Luu
    ta fara halamun zata fad'i, cikin zafin nama yai
    taku daya ya taro ta. Gaba d'aya jikinta ya
    saki,ga wani irin zafi kamar garwashi. "Salma..
    Jijjiga ta ya fara,da sauri Aunty A'i ta shigo,sai
    ga Mama na fad'in ta taimaka su sa Salman a
    Napep gashi ta nemo.. "Mey zan gani haka... Da
    sauri suka juya ganin Mama da tai turus ganin
    yadda ya mammakale Salman,ita k'wa k'allonshi
    kawai take hawaye nabin gefen idonta. Garba ke
    mishi da hannu kan ya saki Salman amma kamar
    yana zigashi,sai kara naneta yake. Gaida Maman
    sukai da girmamawa tai banza dasu. Sababi
    Mama zata fara Aunty A'i ta jata sukai waje.
    Garba ne ya tsayarshi ganin yana neman cicci6ar
    Salman. "Kasan dai yanzu ba a mat'sayin
    matarka Salma take ba,kar ka nemo mana
    magana dan Allah.. Harara ya sakar mishi,kan
    cikin fusata yace "na mayarta toh.. Koh da
    magana? Kai ya k'ada mishi, kan ya bud'e mishi
    labule, "Dan Allah kaimu asibiti... "Auntyn mu..
    Aunty A'i ya k'wada ma kira, da sauri suka fito
    ita da Mama dake huci. "Asibiti zamu kaita, dan
    Allah Mama ki yi hakuri na kaita.. Harara ta
    sakar musu kamin tabi bayansu ta sallami mai
    Napep sai asibiti. Murna ta koma ciki,da d'ukkan
    hannu biyu mama ta dafe kai,jin rahoton likita
    kan tabbatar da cikin Salma,dan haushi ba tasan
    tai waje ba. Shikenan an 6ata mata shiri, ciki?..
    Kai amma an sha da ita, sam ta zata fad'in A'in
    ne dan a bar Salma. "Mama kiyi hakuri zata
    samu lafiya,bari naje na siyo allurori mu dawo.
    Kala bata ce musu ba, asalima ji tai kamar ta
    rufeshi da duka koh ta huce. A gun Garba ya
    k'ar6i kud'i,basu juma da tafiya ba sai ga Ummi
    da Aunty A'i sun zo,tuni k'wa ta ware tana
    surfawa Ja'afar Ummi na tayata. Kai Aunty A'i ta
    k'ada, fatan ta a kullum Allah ya ganar dasu
    Mama alkairin Ja'afar, alkairin da batajin koh su
    wanda suka auri masu halin suna musu. "Mama
    Salma fa matar Ja'afar ce har yanzun,don
    musulunci ya mallaka mishi,matukar batai idda
    ba,bare da kunne na naji yace ya mayarta
    wallahi, dan Allah Mama ki sassauta, in har da
    mey lefi aciki toh fa Salma ce.. "Ke dama ina
    kika ga kishin kai?.. Ai guntunki ta tsotsa, shi
    yasa sam kusan halin ku daya... Aure kuwa in dai
    ni nai nakudar Salma toh ya kare ya gama.. Ba
    ruwana da wani ya mayarta,sakaryan yaro
    kawai,sam bai da zuciya wallahi. Ummi ce ta
    amshe tana k'wafa. "Ai wallahi dad'i yake ji dan
    yaga Abba na jibgarta,dama garin d'ukan yaja ya
    rasa cikin ai da shi ya jiyo... "Ummi mey yasa ke
    sam baki da mutunci ne?.. Baki Ummin ta turo,
    "Ja'afar fa ba sa'anki bane,in bazaki g'yara ba
    toh kar ki 6ata... Salma ita ta chanchanci komai
    ba Ja'afar ba,gashi taja yace aure zai kara... A
    zabure Mama ta jiyo, "Aure?.. Shine ki ke kuma
    fad'a min ya mayarta?.. Kai ta k'ada, "eh lalle
    Ja'afar, toh k'wa zama da kishiya ba dai y'ata
    ba, karan nan zamu banje da Malam wallahi akan
    maganar komen nan,sam naki jinin yaron nan
    wallahi.. "Ni kam Mama bana ganin aibun Ja'a..
    "Kimin shiru,kar ki gani din,amma aure angama.
    ****************************** Yau k'wananta
    biyu aka sallame ta,fur Mama taki bawa Ja'afar
    fuska,daga ina wuni lafiya shikenan. Su Abban su
    Ja'afar harda y'an cikin gida sunzo sun jajanta
    abinda ya faru. Kowa ya bawa bangarenshi
    rashin gaskiya, take Baba yace ya mayarta. Kai
    duk'e yace ai tun ranar chan ya mayarta,nan ya
    ja mishi kunne kan sarar ki fita A BAKIN
    AURENKI. A gaban su Abba ya kara tasa zancen
    zai kara aure,cikin fusata Abbanshi yace "Ba mun
    gama maganar nan da kai tun jiya?.. Wane aure
    kuma bayan wannan da aka mayar? Kai yai kasa
    dashi yai shiru, murmushi Abban su Salma
    yayi,kamin yace "Kamin dai dai Ja'afar, fatana
    Allah yasa auren shi zai zaunar da Salma a
    dakinta ta rungumi ibada. Ja in ja sukai tai
    t'sakanin Abban Salma da Abban Ja'afar, dak'yar
    Abban Ja'afar ya yardewa Ja'afar kara aure. Ana
    watse wa koh gama jan mota basuyi ba Mama ta
    fara sababi,ita a fafur ba inda Salma zata,bata
    zauna da kishiya ba,saboda haka ba mai zama da
    ita a yaranta. Itade Salma bata um bata um-
    um,sai hawaye kadai ke zuba,ita kad'ai tasan ya
    zuciyarta take hautsina mata,ta faru ta
    kare,tunda har manya sun amshi magana.
    "Ja'afar? kishiya? Kuma da Bintu kawarta?.. Tab
    da matsala. By Feenat Ja'afar
    9/29/16, 9:10 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    24_Daaga sosai akai da Mama akan komawar
    Salma,sai da Abba ya bud'e mata uwata sosai
    kamin harda Yayanshi ta saki aka ta koma din.
    Ita kanta Salman yanzu ba kaunar komawar take
    ba sai ta mot'so mata ga laulayi. Ga Ja'afar
    tunda ya ji batun ciki ya kasa sukuni,kullum yana
    zaryar dubiya da leda. Shi dai bai mat'sa da sai
    ta dawo ba lokacin, dan g'yaran gida sosai yake
    wanda Ummanshi ta bashi ya zauna aciki. Har
    gida yau Abba yaje gun Abban sun kan lalle yau
    Jafar yazo ya dau Salma. Da dare k'wa ta koma
    dakinta. G'yaran nan gidan ya t'saya
    chak,sakamakon aikinshi da aka mayarshi aka
    bashi albashin da ya wuce shi,bai da mat'salar
    kud'i yanzu,auren shi kawai yasa a gaba. "Ina
    k'wana.. Cikin sanyin murya ta gaida shi kai
    duk'e, kai ya daga kamin yace "ya jiki?.. Shiru tai
    ba amsa. "Ki tashi ki zauna man.. Kai ta dago ta
    k'alleshi kamin ta kada mishi, "A'a magana nake
    son muyi da kai. Zama ya g'yara yana
    sauraranta. "Mey yasa ka ke son auren Bintu?..
    Da ido ta kafeshi tana jiran amsa. Murmushi yai
    kan yai baya kad'an harda d'aura kafa daya kan
    daya. "Saboda tana so na ne Salma.. Kai ta kada,
    ''kaima kana sonta?.. A bazata tambayar tazo
    mishi,ga takafeshi da ido hawaye taro a idonta.
    "Ki gane Salma, ba wai.. "Eh koh A'a?.. Amma
    nake son ji kawai. Ba koh shakku yace mata "eh..
    Amma.. Hannu ta daga mishi tana hawaye,
    "Barni haka dan Allah,amma kasan Bintu k'awata
    ce da koh?.. Ya zaka min haka? Kai ya kada
    harda dariya, "A sani na banta6a ganin Bintu a
    gidan ki ba,asalima... Sallamar Aunty A'i ce ta
    kat'se mishi maganarshi,sai ya tashi dan dan
    bud'e mata kofar,da kallo ta bishi tana mamakin
    kalamanshi,sai kawai ta k'ada kai ta mike tana
    goge ido. "Bissmillah mana Auntyn mu.. Yana
    gaba ta biyoshi a baya, sosai suke dasawa da
    Aisha,dan tasan abinda take sosai,shi yasa baya
    6oye mata komai. Bayan sun gaisa ya mike yana
    zai fita, kai kawai ta k'ada mishi,sai Aunty A'i ce
    tai mishi a dawo lafiya. Zama Aunty A'i ta g'yara
    tana ma Salman k'allon tuhuma. "Ashe Salma
    baki fara g'yara ba har yanzun?.. Da rashin
    fahimta ta k'allo ta tana hawaye, "Fita fa yayi
    jiyan nan dawowarki amma har kin fara nuna
    mishi baki sauya ba. "Aunty A'i ba abinda na
    mishi fa Allah.. Katseta tai da fad'in "Amma zai
    fita babu koh a dawo lafiya?.. Haba Salma,nan ki
    ka dinga rantsuwar kin shiryu, koh har kin leka
    makotar ne yau d'akko sabon darasi?.. Kuka ta
    sa mata tana girgiza kai, "Haba Aunty
    A'i,k'awata fa zai aura fa,taya bazanji zafinshi
    ba?.. Da mamaki tace "wacce kawar taki? Cikin
    kuka tace "Bintu,dalibar shi ce a Day school fa.
    Ita dai ta hanga bata gano wace Bintu bace a
    k'awayen,tasan sarai k'awayen Salma basu fi
    biyu ba wanda tasan su. "Wace Bintu kuma cikin
    k'awayen naki? Amma basan ta ba koh?.. Kai ta
    daga mata, "islamiya mukai tare fa.. "Mtsww,
    t'saki Aunty A'in tai tana k'auda kai, "har wata
    kawar islamiya K'awa ce?, bana jin ko hanyar
    gidan ku ta ta6a zuwa balle ta zama kawarki,
    koh ta halarci bikin ki?.. Kai ta kada mata tana
    goge hawaye. Cikin lallami ta fara lallashinta.
    "Kar fa ki bari tun kamin ta shigo taci galaba
    akanki Salma, yanzu ba lokacin t'sayawa kishi
    bane a gunki, lokacin g'yaran kuranki na baya ne
    Salma... Ki d'auka baki ma ta6a sanin wata Bintu
    ba rayuwa,dan ba gaminki da ita sam. "Ki kuma
    fidda zancen auren nan a ranki,dan koma meye
    ke ce sila Salma. Nasiha tai ta mata tana kuka
    har ta gamsu da bayaninta. Ta bata shawara
    masu k'yau, ta kuma d'auka. Da ya dawo ya ga
    chanji,sannan bata kara mishi maganar Bintu ba.
    Yau satin ta daya da dawo wa,amma banda
    Maman Abba ba wanda ya leko mata har Maman
    Ummin, Ga sai wani kama mata kai Ja'afar din
    yake bare tace zata leka,abu daya ta sani,shine
    ta daina zuwa gidan kowa sai in ta kama.
    Washegari har kofa ta rako shi zai fita tace zata
    leka gidan Maman Ummi.. Yana fita yace mata
    sai ta dawo kawai. Da k'allo ta bishi,sai ta ga
    kamar gat'se ya mata,dan haka ta koma ciki tai
    k'wanciyarta. Mukullin gidan da ake g'yara zai
    fitar musu dashi sai ya dawo. A k'wance ya
    sameta ido rufe a parlour,sai yai jim,ganin bata
    fita ba har ya dawo. "Har kin dawo ne?.. Kai ta
    girgiza mishi,sai yai d'aki yana tunaninta, haka ta
    saba mishi kan gaba ta fand'are mishi,shi dai
    yasan yai alkawarin mud'in ta tambaye shi fita
    ya d'aina hana ta,yasan duniya makaranta,da
    sannu zata gane abinda yake gujar mata. Koh da
    zai fita sai ya kara nanata mata kan taje kawai.
    Bai jima da fita ba ta fito,tana dan jin hayaniyar
    su kasa-kasa. Har zatai Sallama sai ta ja ta
    t'saya jin wata gulmar da suke. "Ai yanzu ya
    zamarta mai gadinshi, tunda ta dawo ba inda taje
    tana d'aka,koh duk sururin zai kara auren ne?..
    Tana jin Maman Ummi tace "oho mata,ba ita
    areni muje biki ba,mijina baya fad'a.. Muryar
    Maman Abba tajiyo tana fad'in ''ni tausayi ma
    take bani wallahi, ranar chan dana shiga duk ta
    rame tai baki,kana yaronka da kai an ma saki
    2.... Baya tai cikin sanda danjin wani na shirin
    fitowa. Gida ta koma ta cire hijab tai dabar a
    kujera, tun yaushe haka take faruwa da ita?..
    Ashe ita k'allon mara wayo suke mata acikinsu?..
    Kai ta daga sama, lalle ta gane mey Ja'afar yake
    nufi da mutunci yake nemar mata.. Yau ta gane
    ashe in an yi gulmar wani da kai yau gobe da kai
    za'a kafa ai taka. "Allah na gode maka daka sa
    na ji na kuma gani. Tabbas Ya Ja'afar babban
    gata yai mata. Toh a ina ma suka samu labarin
    za ai mata kishiya?..har dare tana neman amsa.
    Ranar har kukan bakin ciki tai na taraiyarta dasu
    Maman Ummi. Tuni ta tattare kowa ta wat'sar
    shi,duk da ba duka aka taru aka zama daya ba.
    Ranar Maman Waleeda da suke kira uwar tsoron
    miji ita ta zo mata harda nasiha har gida,matar
    da koh gidanta sai tai fita ashirin bata leka
    ba,kuma makociya ta kusa,har misali tai mata da
    Maman Ummi. "A kaf unguwar nan bana tunanin
    da matar da take cikin takura irin na Maman
    Ummi Salma, ke shaida ce,in kinji gidan yai shiru
    ba koh tarin yaro kasan uban na gida. Sannan in
    zai shekara ba taje ko'ina ba shine dai dai a
    wajenshi,duk fita in zatai satar hanya take tasan
    in ya fita da yamma sai dare,amma a gun kuri
    tafi kowa iya dadin magana,da ina cikin su,daga
    baya na gane taraiyyata baza tai dasu ba,sai na
    zabi zaman gidana ya fiye min alkairi sama da
    yawan gulma. "Ka'rkara in abu ya faru in leka a
    tsatssaye in dawo, dan Allah ki iya kafarki
    Salma,dan zasu kai ki su baro ne kawai. Kai ta
    k'ada mata, "Na gode Maman Waleeda,Allah bar
    zumunci,kuma InshaAllah naji bayanin ki,duk da
    mun kusa tashi a unguwar ma duka InshaAllah.
    Anan ta sanarta za ai mata kishiya,k'warai ta
    jajanta mata kan ta kara da y'an shawarwari,tun
    daga ranar mutunci da Maman Waleeda
    suke,kusan duk yamma tana turo mata su
    Waleeda taya fira,har lokacin tashinsu yazo.
    ***************************** Cikinta yana da
    wata biyar lokacin auren Ja'afar saura sati. Sam
    bazaka zata Salma bace, dan tamkar bai dameta
    ba haka tai a auren. Har ranar Ja'afar yana fad'in
    wai ta daina sonshi gaba daya,koh kishi bata yi
    zai kara aure,murmushi kawai ta masa,dan tsaf
    ta kula da rawar kan da yake k'wana biyu. "Ba
    k'ya shirye-shiyen komai gashi lokaci ya taho
    fa... Tamkar ya choka mata abu makogwaro taji
    wani iri,kawai sai ta sa mishi ido tana k'allo.
    Tabbas rawar kan Ja'afar karuwa take akan
    auran nan,banda haka wani irin tambaya ce
    wannan?... Shikam tunani yake yadda Salman ta
    g'yaru har kullum,a ganinahi halin ko'in kula da
    yake nuna mata ne akan fita. "In da hali zan fita
    kar6o wasu kayana unguwar Ummi. Kafad'a ya
    daga mata,kan yace "sai kin dawo... Yai waje.
    Baki sake ta bishi,tun bayan dawowarta ta kasa
    gane inda Ja'afar ya dosa,abu yake mata tamkar
    ya kosa da zaman ta a gidan. Gashi tun kamin
    amarya ta tare har ya sallamata,wai ko'ina nan
    gaba in zata kawai taje,dan yanzu bai son 6acin
    rana irinta da. Toh mey yake nufi? By Feenat
    Ja'afar.
    9/29/16, 9:11 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    26_Kowa bin kofar dakinta yai da kallo, yana
    murna ba'a rikicin mata biyu a gidanshi yau gashi
    an fara,dole ne tun wuri yai ma tufkar hanci. Har
    yayi dakin Salman sai ya t'saya, dole ne ya nuna
    mata kuranta, in da tai mishi fitsara ya k'yale toh
    yanzu bazai d'auka ba,dan ba ita kadai bace a
    gidan,kawai sai ya juya dakin Bintu. Kuka take
    yana ta fadanshi taki kulashi, chan kuma sai ya
    sassauto, "Ni tashin hankali ne bana so a gidana
    ne,tun wuri ma in zaku had'a kai ku had'a, dan
    ba mai chazan hawan jini. Kai ta dago tana mishi
    k'allon tuhuma, "Au shine dalilin da yasa ka fad'a
    wa matarka baka so na?.. Ni nace ina son ka
    koh?.. A haka za ai zaman lafiyan?.. "Ke kinga
    bana son iyayi,dawa nai wannan zancen?.. Da
    sauri cikin kuka tace "da matarka man,wato
    harda fad'a mata kwantai nayi nai ma tallan
    kaina.. "Ban san anyi maganar nan ba Malama,ki
    ma cire zargin ni na fad'a mata, bari na je zata
    fad'a min yaushe muka fara y'ar sharri da ita...
    Waje yayi zuwa dakin Salman. Kai Bintu ta k'ada,
    "ashe munafuka karya take dan ta had'ani fad'a
    da Miji,toh karyarki taci karya,Allah sa ya k'wada
    mata mari tukuicin sharri. Ita kam tanajin bud'e
    kofarshi ta mike tare kama k'ugu ta k'ank'ance
    ido. "Salma yaushe muka fara y'ar sharri dake a
    gidan nan?.. Yaushe nace miki Bintu ce tai min
    tallar kanta na aura?.. Harara ta sakar mishi da
    k'allon kar ka rainan hankali. "Ka nad'e taburmar
    kunyar ka man ta haka,wato kayi amarya shine
    ka zabi ka tuzartani agunta,karafkaf abinda ya
    faru ta fad'a mini,toh da ka fad'a mata saura
    igiya daya ta aurenka a kaina sai mey?.. Baki ya
    saka cike da mamaki,lalle ya shiga tarkon kaidi
    na mata, wato kowacce sharri take neman k'ulla
    mishi a gun y'ar uwarta ashe?.. Bai da tace wa,
    kawai sai ya juya zai fice, da sauri tace "a ka
    fita man,dan nayi imani bazaka karyata cewar ba
    kai ka fad'i ba... "Idan kuma habaici da iyayi
    kake neman matarka ta dinga min dan ka huce
    haushinka na da toh bissmillah,dai dai nake dana
    sa kafar wando daya da kowa a gidan nan
    wallahi.. Juyowa yai yana kallonta, sai tai d'aki
    ta barshi t'saye baki sake. Titi ya fice ko ya
    samu sa'ida, lalle yau ya jinjinawa sharrin
    mata,amma kaf yafi jin haushin Salma,dan sam
    yanzu ya fuskanci fitsararta tafi ta da yawa. Tun
    daga ranar ba jituwa t'sakanin matan, daya in
    Bintu ta fad'awa Salma sai ta fad'a mata
    dubu,daga karshe ta bige da kukan bakin ciki, har
    mai gidan yazo ta kit'sa mai karya da
    gaskiya,wani sai dai ya bata hakuri, dan a
    ganinshi yanzu Salma tafi karfinshi,dan da ya
    mata magana ita y'ar dika take,daga shi har
    amaryar zata chake tass, sai dai yai abinda zaiyi.
    Shi yasa shi kuma ya t'siri mata t'siya,in dai zata
    kona mishi rai,toh shi kuma zai ta biyewa Bintu
    suna ta mata feleke a t'sakar gida, daga karshe
    kam sai yaci nasara,dan haka zata shiga d'aki tai
    ta kukan bakin ciki,a nan zai ta mata dariyar
    keta. ***** Sallama taji kamar ta Maman Ummi
    da Maman Abba,lekawa tai ta window, sune
    kuwa, "munafukan Allah ta'ala kawai... Ta fada
    tana kokarin ta fito rai 6ace,dan tai imani duk
    abinda take fuskanta yanzu da sa hannun su
    aciki... Chak! Taja ta t'saya rike da labule a
    hannu ganin Bintu ta fito da gudu danjin sallamar
    su. "Sai yau Aunty Ladi zaki zo min? Har nayi
    fushi ai.. Baki sake Salma take k'allonsu,tana
    k'allon suna nuno kofar dakin da baki suna ma
    Bintun kuskus tai baya da sauri. Ido ta rint'se
    tare da cije le6e,lalle mutum mugun ice ne,yanzu
    ta gane inda Bintu ta samo duk wasu
    _information_ na zaman aure nata ba agun
    Ja'afar ba,ido ta bud'e, ta d'au alhakin Ja'afar,
    har rantsuwa yai mata amma taki yadda. Karshe
    har raba shimfida tai dashi akan maganar har sai
    da ya gamo ta da Aunty A'i aka shirya. Zama tai
    tana jiyo shewarsu a dakin Bintun. Har kullum
    bazata daina nadama akan taraiyarta dasu
    Maman Ummi ba,tasan duk fushin Ja'afar ne da
    t'sinuwar mala'iku ke bibbiyarta. Har hawayen
    bakin ciki tayi yau,tai kuma alkawarin daina
    sa6awa mijinta ko da taji haushin shi. T'sakar
    gida ta fito bayan ta g'yara fuskarta, tai sa'a
    kuwa sun fito zasu tafi suna ta dariya. Ganinta a
    t'sakar gidan yai bala'in saita nutsuwar su,a
    t'saye take k'yam tamkar wata soja ta had'e rai
    tam,ido cikin ido take k'allonsu,tuni suka hau
    inda-inda, "dama kina ciki?.. Sannun ku da gida..
    Harara ta sakar musu,ba shiri sukai hanyar
    waje,Bintu ce ta t'sayar su, "bari na raka ku
    hanya Aunty,ina zuwa na kira mai gida izinin fita.
    Duk tana k'allonsu,har tai ma Ja'afar waya wai
    za tai rakiya waje ya bata izinin fita. Bokiti ta
    zaburo da sauri tai hanyar fita,da sauri sukai
    waje sun zata kansu zata iyo,kawai sai ta ja
    t'saki ta shige band'aki. "A toh na zata koh rafka
    mana zatayi ai,g'wara muyi ta kai ta kai,dan
    wannan da gani zatai kishin hauka... Dariya suka
    sa tana jiyo su ta band'aki daga zauren sunki
    tafiya. Ruwanta na cika da ta tara ta bud'e
    band'akin a hankali tai zaure, basu nufa ba sai jin
    saukar ruwa sukai akansu har Bintun. Bokitin ta
    d'auka tai kansu dashi a sukwane, da ture ture
    suka fita waje da gudu. Tana haki ta leko kofar
    gidan ''Ashe karyar munafurci kuke, da ku t'saya
    na g'wada muku aikin mahaukaciya, shegu gadon
    na aiya,a haka zaki kare Maman Ummi wallahi,
    InshaAllah kema dubinki ta kusa cika. "Ke kuma
    yau mai rabani dake a gidan nan wallahi sai
    Allah, yau zaki ga karyar iskanci. Gida ta koma
    tana hakin daga ruwa bucket guda da tsohon
    ciki. A t'sakar gidan ta zauna tana maida
    numfashi a hankali, ta jima da zama kamin taji
    tafiyar Bintu cikin sand'a, kofar ta zubawa ido
    tana harara, kai ta leko dashi dan ganin koh
    Salman bata nan sai suka had'a ido. "Wallahi
    baki isa ki ce zaki hanani shiga ba, in gaske ne ki
    bari na shigo na shirya in fad'an ki ke nema dani
    ba hauka ba. Murmushi tai daga inda take, "Lalle
    kinyi kuskure in kina zatan zan iya had'a jiki da
    karya irin Bintu,haukar nake son sauke miki aka
    yau ai, gaba kin d'aina irin kuskuren nan ina zuba
    miki ido kawai,yau dole na fidda ki cikin gona ta.
    Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 31
    Feenat Ja'afar Novel's
    "Karya ki ke wallahi ki iya koyan hankali Salma,ai
    fad'a da makami tsoro ne,ki ajiye bokitin mu
    gabza da hannu in kin is... "Meye hakan ke kuma
    Bintu?.. Juyawa tai da sauri,tana ganin Ja'afar ta
    sau kukan munafurci harda kank'ame shi,wai
    Salma tace in ta shigo sai ta kashe ta da duka
    da bokiti bayan ta jika su ita da bakin da zata
    raka... Ciki yai gadan-gadan gun Salman,tana
    ganinshi ta mike t'saye rike da bokiti,bai
    watawataba kawai yai kanta da niyar mari tai
    baya. Kunci ta rike har tana halamar yin baya
    zata fad'i, "Kin haukace ne Salma ko mey?..
    Gidan ki ne da har zaki kafa dokar wa zai shiga
    ko ya fita?.. Cike da mamaki ke d'auke a
    fuskarta, ganin yadda ya rufe ido yake zazzaga
    mata bala'i harda yunkirin mari. "Ni zaka mara da
    akan waccan karyar Ya Ja'afar?.. A tuzare yace
    "eh wallahi, da da halin duka ma sai na
    miki,kuma daga yau kar in sake jin kin kamanta
    matata da sunan kare a gidan nan.. Kai ta k'ada,
    kan tai baya tana g'yara t'sayuwa tai d'aki. Code
    wear ta ciru, a masife ta fito tana mika mishi,
    "Amshi waya, yau in ka cika kaine Ja'afar ka
    dake a gidan nan sai nasan na ta6a maka y'ar
    g'wal dinka Ya Ja'afar, amma ni in naci sunan
    Salma,toh wallahi babu mai takani ya k'wana
    lafiya,zaman lafiyarta a gidan nan kawai ta fita
    harkata... "Bazata fita ba d'in, haba. Wannan
    wace irin masifa ce wai?.. Kullum ke kenan cikin
    dacin rai?.. Ba wanda yake t'sallake masifarki in
    ta motsa.. Haba Salma,yarinyar nan tun tana miki
    kawaici har sai kin kaita bango,koh tausayin
    yanayin da kike ciki ba k'ya yi?.. G'walo Bintun
    ta sakar mata tana a bayan Ja'afar. Kawai sai tai
    murmushi tai d'aki ta dakko hijabi da kud'i ta
    fito. Cikin sanyin murya tace "kamin izini zan fita
    Ya Ja'afar.. Harara ya sau mata!kan yace "Da in
    zaki fita ba kina gaban kanki ba?.. Wato ga
    shashasha yana magana dole ki fice,toh kije duk
    inda zaki ai kin saba... Dak'yar ta iya shanye
    kukan dake son subuce mata,ga Bintu sai dariya
    take mata a boye,da sauri ta zira hijab dinta tai
    waje. K'wafa yayi shima kamin yace Bintu ta
    shiga ciki yana zuwa. Waje yayi da sauri,har ta
    samu mai Napep ta shige tana hawaye, a tunzure
    yai gun mey Napep din, "Kar ka kuskura ka jata
    cikin Napep dinnan in kana son kekenka ya tsira..
    Sauketa tun wuri.. A masife ta rufe ido tana
    mishi balbalin bala'i kan bazata sauka ba din. Shi
    dai mai Napep duk ya tsorata,jin ta dawo kanshi
    yasa ba shiri ya tada Napep,magana yake mata
    amma ina,da sauri ya juya shima yai gun nashi
    machine din yabi bayanta. "Hajiya wannan binmu
    yake a baya fa,wallahi kar ya tafkan asara..
    Murya na rawa tace "Dan Allah ka kara gudu
    sabuwar gandu zaka kaini.. Kan ta karasa kukan
    har ya taho mata,kawai sai ta jingina kanta ta
    hau yi kamar ance mata Mama ta mutu. By
    Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:14 AM - Queen Safiyyert馃憫: *漏 Feenat Ja'afar*.
    25_Yau amarya ta taro gidan Ja'afar,suna chan
    d'aki yan d'anna kirjin Salma.
    Tai kuka yau harta gode Allah,tukun daga baya
    taje ta d'au wanka.
    Tabbas ba'a iya dake wa kishi,koya sai ya tona
    ka,dak'yar ta samu ta saita kanta kamin y'an
    kawo amarya suzo kawo amana.
    Kowa ya wat'se, daga ita sai amarya, kowa tana
    dakinta.
    Karadin Garba ta kiyo a parlourn ta,tuni taji
    gabanta ya sara, tabbas tasan tare suke da
    ango.
    A hankali ta yaye labule tana k'allon su har suka
    shiga dakin amarya had'i da parlour mai k'allon
    nata.
    Zama tai ido tuni ya ciko da k'walla, sai tai
    ko'k'arin had'iye wa.
    Tana jin Garba yana bazai shiga ba yaje tai
    tanadin ta6aryar duka, tana suka sa dariya harda
    tafawa.
    Kwafa tayi,wato ga mahaukaciya sabon kamu.
    Tana jin rufe kofar gidan tai sauri ta k'wanta ta
    rufe ido.
    Da sallama ya shigo parlourn, ba kowa sai
    kamshin turaren uwar gida y'ar Borno jikar
    Shuwa.
    Ko'ina yaji sabon abu,kamar itace amaryar, labule
    da kujeru purple da baki, su Mama anga ba sarki
    sai Allah,kawai sai aka fito da tsohuwar
    ajiya,baba ya cika aka sai mata kayan
    parlour,ragowar nata na da suka siyar,gado k'wa
    tace bazata siyawa wani gardi ba,harda kukan
    Salma.
    Sai ma kuma gashi ashe yana da niya,gado
    barawan Italian da katifa yai mata a kud'in da
    Ummanshi ta turo mai daga Zaria.
    D'akin ya shiga,nan ma shiru ba amsa,tai
    rigingine kamar mai bacci.
    K'allonta ya t'saya yana yi kamin ya ajiye ledar
    hannunshi,sosai cikin ya kara fito mishi da k'yan
    Salma warai.
    Tai k'yau cikin attamfa ruwan purple da
    pink,tasha k'walliya sosai gun Ummi,idon nan
    yasha (mascara/eyeliner).
    Da komai Salman sa ta fi Bintu sau dubu
    agunshi,sai dai ta nuna mata hasken fata.
    Hannu ya kai kan cikin yana shafawa a hankali,
    tana jinshi yana yan surutanshi ma cikin.
    Ajiyar zuciya ta yi,sai ya k'allo ta,a tunaninshi
    baccinta ne yai nisa.
    A tashi yai yana k'allonta,kan a hankali ya duk'o
    tare da nufin kai bak'inshi nata,tana jin hucinshi
    sai ta juyar da kai da sauri.
    Murmushi yayi kamin ya shafo kanta da suka sha
    yiriyirin kitso.
    "Asbha ta ga Salma.. Ki yafeni kinji...
    Bargon kusa da kafarta yaja ya lilli6eta,kamin ya
    kashe wutar dakin yai waje.
    Ido ta bude tana nanata maganar shi a zuciyarta,
    mey yake nufi da ki yafeni?..
    Saboda ya tafka miki t'siya mana.. Cewar wata
    zuciyar, le6e ta cije,yau gata a gidan Ya
    Ja'afar,akan gadon su,amma ba shi ciki,yau zasu
    fara raba matashin kafadar Ja'afar da wata
    chan.. Tana son Ja'afar, sai ma yanzu ta gano
    t'sant'sar son da take mishi,ji take kamar ta
    had'iyi zuciya ta mutu dan kishin mijinta,
    tuni tasau wani dan marayan kuka a
    hankali,kamar tace Ja'afar dawo.
    ****
    Ita k'wa amarya tuni ta mike ta fara zarya a
    d'aki, dan a idonta ya shiga bangaren Salma,tuni
    ta fara cika tana bat'sewa.
    Tana ko'k'arin fito wa a parlourn ya shigo,da
    sauri ta koma ciki har tana tuntu6e,duk ba tasan
    ya ganta ba.
    Ba laifi,tazo da tarikice dayawa,sam sai t'sarin
    na Salma yafi burgeshi,dan shi bai son tarkace a
    gida da sunan k'walliya,ga wani kala blue da pink
    na kayan labule da kujeru,sam bai mishi ba.
    "Ki fito da sallaya parlour.. Kawai sai yai waje
    dan yin alwala a band'aki.
    Assalatun farko ta farka,cike da mafarkin Ja'afar
    wai yana ta mata fara'a.
    Kasa tashi tai,tabbas da gaske yanzu tasan
    bakinshi kamar gonar audiga dan fara'a, tunda
    yai k'wanan d'akin amarya.
    Hakan ne yasa ko da gari ya waye taje kitchen
    ta d'aura abin kari,dan tun asuba taga text din
    Aunty A'i kan ta k'auda kishi tai musu kalacin da
    safe,dan Allah..
    Wannan Kalmar ce tasa ta shiga dan dole.
    T'saye take tana juye abincin a flaks,ba abinda
    ta tsana irin hada kitchen da band'aki da
    kishiya,harar bangaren kayan jeren amarya tai
    tana gunguni ciki-ciki,bata nufa ba taji shafo
    wuyanta ta baya.
    A zabure ta juya dan ganin waye. Murmushi yake
    mata kanar dai a mafarkinta,da sauri ta d'auke
    kai daga K'allonshi zuwa gefe.
    "Kamshi duk ya karad'e gidan nan K'anwata..
    Hannunta yake neman kamowa ta mat'sa tana
    "An tashi lafiya..
    K'allonta yake daga sama har kasa,tana sanye
    da rigar banci _sky blue_ nai filawa purple, sai ta
    d'aura zani da dank'wali akai, tai mishi k'yau
    sosai,ga dan kurcicin cikin ya fito yai d'as.
    "Ya gajiyar jiya?.. Na shiga kinyi bacci ban son
    tashinki.
    Yawu ta had'iya tare da fad'in "ummm.
    Fur taki k'allon fuskarshi balle ta fassara mata
    bakin ciki.
    Dan da ganin yadda ya fara mata zagwadin nan
    ta faru ta kare.
    "Ga abincin ku,zan wuce..
    Hannu yakai zai karbi natan tayi saurin janye wa
    ta wuce,kai ya k'ada bayan ya dawo daga
    k'allonta.
    Dakin amarya ya koma,tana kudindine cikin
    bargo, sai baccinta take narka abinta.
    Parlour ya dawo ya zauna,Salma nuna mishi halin
    ko in kula take tun satin biki, sam bata koh
    kishinshi,sabgar gabanta kawai take.
    K'wafa yai ya kada kai,dan ba karamin haushi
    hakan yake bashi ba.
    Motsinta yaji a t'sakar gida,ta window ya dago
    yana k'allonta zata wuce band'aki da bokiti da
    kwandon wanka,watoh daga shi har amaryar shi
    basu isheta ma kallo ba?.. Dan wai koh hanyar
    d'akin bata kalla ba,k'wafa yai kan yai waje gun
    band'akin ya t'saya kamar maigadinta.
    Har ta gama wanka yana t'saye,tana bud'e kofa
    sai ganin mutum tai a t'saye ya bake hanya,kai
    ta k'auda da nufin ta wuce ya riko bokitin,yaja ta
    taja,kawai sai ta sau mishi,k'wandon sabulun
    yake neman k'ar6a tai baya dashi.
    "Wanka zanyi man Salma.. Wani k'allon ta watsa
    mishi kan ta had'e rai,
    "Bana _sharing_ din soso.
    Baki sake yake k'allonta, cikin fusata yace "da
    da wanne muke yi?.. Kanta gefe tace "toh yanzu
    na sake t'sari...
    A tunzure yace
    "Wai Salma meye haka?.. Bana..
    "Kai Dear J,ga soso nan kai wankan.
    Juyawa sukai gun mai magana, Bintu ce daga ita
    sai y'ar yaloluwar rigar bacci ba koh zani balle
    dank'wali.
    T'saki Salma ta ja,kan tace ''Malam ban waje na
    wuce,tuni ya kara kuluwa, shi take ma tsakin?..
    Yai mata k'yau,kawai sai ya dungurar mata da
    bokitinta ya shige band'aki,da sauri Bintu tai
    kitchen ta d'akko mishi nata,koh ta kansu bata
    kara bi ba ta zari bokitin ta kara mai,a ranta tana
    "karamar y'ar iska kawai.
    Sam Salma taki dad'i, dan fur taki bawa kowa
    fuska a gidan,dan taga da mugun falli amaryar ta
    shigo mata.
    Har girkin amarya ya kare ya dawo ga Salma
    amma ba sauki.
    Zata gaidashi tai komai,amma ba magana
    duguwa, sai ma haushin sa dake kara ziyartar ta.
    Tuni ya kai kara gun Aunty A'i,wai Salma taki
    sake masa fuska.
    A ranar tai mata waya ta kare mata tass,tuni ta
    hau kuka,wai ai dan ita bata kishiya ne,bazata
    gane lamarin ba,ga kusan kullum Bintu na
    chakalarta tana kaucewa.
    Shiru Aunty A'in tayi,dole wannan ba zancen
    waya bane,
    "Ki bari zan zo koh zuwa gobe ne.
    Ranar girkin Bintu ne,yau tun safe take fallin
    fararo a t'sakar gida,sai ya6a mata haibaici take
    ita kad'ai kamar sabon kamu.
    Salman tana zaune kan taburma a kofar ta tana
    yanke farce.
    Harara ta sakar mata,kan taja t'saki,
    "Wawiya kawai..
    Shewa Bintun tayi harda guda.
    "Kece babbar wawiya wacce zaman gidanta ke
    mintsininta.. Ehee, naji komai ai,saki daya ya
    rage miki duk a dalilin gantali gardi.
    A masife ta tashi,sai dai nan da nan ta k'auda
    bacin rai dan ya6a ma Bintu magana dai-dai ita.
    "Ahaiyee,, naji,tunda banyi k'wantai a layi bare
    ina bi ina tallan kaina agun d'a namiji ba ehee, ke
    har kin isa ki ce kin san komai?. tunda dey ni ba
    matar tushe bace ba... Dan tuni akasan da matar
    tushe dai bata k'warjini... Karya uwar bin maza
    kawai...
    "Eh naji ki ce komai,igiya uku ce a kaina kinga na
    fiki matsayi a...
    "Ke... Bana son shashancin banza wallahi..
    Juyawa sukai danjin mai gidan yai shigar bazata.
    "Ihu har titi mutanan unguwa ana jinku sai kace
    wasu karnika?...
    Harara Salma ta sau mishi da t'sabar tuhuma a
    k'allonta.
    "A ni ba karya bace, dan har gidan mu ka samo
    ni..chan ka nemi karya tun wuri..
    Jiki ta kad'e tai dakinta ta barshi baki a sake.
    Ita kam Bintu lukwas tayi,tabbas Ja'afar kadai
    zai iya fad'a ma Salma cewa ita tace tana
    sonshi,da kuka tai d'aki dan bakin ciki.
    Itama haka take gun Salman,sosai taji zafin
    maganar Bintu,tasan kuma babu mai fad'a mata
    sai Ja'afar.
    Toh fa Ja'afar, ka shiga t'sakiya.
    By
    Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:16 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    26_Kowa bin kofar dakinta yai da kallo, yana
    murna ba'a rikicin mata biyu a gidanshi yau gashi
    an fara,dole ne tun wuri yai ma tufkar hanci. Har
    yayi dakin Salman sai ya t'saya, dole ne ya nuna
    mata kuranta, in da tai mishi fitsara ya k'yale toh
    yanzu bazai d'auka ba,dan ba ita kadai bace a
    gidan,kawai sai ya juya dakin Bintu. Kuka take
    yana ta fadanshi taki kulashi, chan kuma sai ya
    sassauto, "Ni tashin hankali ne bana so a gidana
    ne,tun wuri ma in zaku had'a kai ku had'a, dan
    ba mai chazan hawan jini. Kai ta dago tana mishi
    k'allon tuhuma, "Au shine dalilin da yasa ka fad'a
    wa matarka baka so na?.. Ni nace ina son ka
    koh?.. A haka za ai zaman lafiyan?.. "Ke kinga
    bana son iyayi,dawa nai wannan zancen?.. Da
    sauri cikin kuka tace "da matarka man,wato
    harda fad'a mata kwantai nayi nai ma tallan
    kaina.. "Ban san anyi maganar nan ba Malama,ki
    ma cire zargin ni na fad'a mata, bari na je zata
    fad'a min yaushe muka fara y'ar sharri da ita...
    Waje yayi zuwa dakin Salman. Kai Bintu ta k'ada,
    "ashe munafuka karya take dan ta had'ani fad'a
    da Miji,toh karyarki taci karya,Allah sa ya k'wada
    mata mari tukuicin sharri. Ita kam tanajin bud'e
    kofarshi ta mike tare kama k'ugu ta k'ank'ance
    ido. "Salma yaushe muka fara y'ar sharri dake a
    gidan nan?.. Yaushe nace miki Bintu ce tai min
    tallar kanta na aura?.. Harara ta sakar mishi da
    k'allon kar ka rainan hankali. "Ka nad'e taburmar
    kunyar ka man ta haka,wato kayi amarya shine
    ka zabi ka tuzartani agunta,karafkaf abinda ya
    faru ta fad'a mini,toh da ka fad'a mata saura
    igiya daya ta aurenka a kaina sai mey?.. Baki ya
    saka cike da mamaki,lalle ya shiga tarkon kaidi
    na mata, wato kowacce sharri take neman k'ulla
    mishi a gun y'ar uwarta ashe?.. Bai da tace wa,
    kawai sai ya juya zai fice, da sauri tace "a ka
    fita man,dan nayi imani bazaka karyata cewar ba
    kai ka fad'i ba... "Idan kuma habaici da iyayi
    kake neman matarka ta dinga min dan ka huce
    haushinka na da toh bissmillah,dai dai nake dana
    sa kafar wando daya da kowa a gidan nan
    wallahi.. Juyowa yai yana kallonta, sai tai d'aki
    ta barshi t'saye baki sake. Titi ya fice ko ya
    samu sa'ida, lalle yau ya jinjinawa sharrin
    mata,amma kaf yafi jin haushin Salma,dan sam
    yanzu ya fuskanci fitsararta tafi ta da yawa. Tun
    daga ranar ba jituwa t'sakanin matan, daya in
    Bintu ta fad'awa Salma sai ta fad'a mata
    dubu,daga karshe ta bige da kukan bakin ciki, har
    mai gidan yazo ta kit'sa mai karya da
    gaskiya,wani sai dai ya bata hakuri, dan a
    ganinshi yanzu Salma tafi karfinshi,dan da ya
    mata magana ita y'ar dika take,daga shi har
    amaryar zata chake tass, sai dai yai abinda zaiyi.
    Shi yasa shi kuma ya t'siri mata t'siya,in dai zata
    kona mishi rai,toh shi kuma zai ta biyewa Bintu
    suna ta mata feleke a t'sakar gida, daga karshe
    kam sai yaci nasara,dan haka zata shiga d'aki tai
    ta kukan bakin ciki,a nan zai ta mata dariyar
    keta. ***** Sallama taji kamar ta Maman Ummi
    da Maman Abba,lekawa tai ta window, sune
    kuwa, "munafukan Allah ta'ala kawai... Ta fada
    tana kokarin ta fito rai 6ace,dan tai imani duk
    abinda take fuskanta yanzu da sa hannun su
    aciki... Chak! Taja ta t'saya rike da labule a
    hannu ganin Bintu ta fito da gudu danjin sallamar
    su. "Sai yau Aunty Ladi zaki zo min? Har nayi
    fushi ai.. Baki sake Salma take k'allonsu,tana
    k'allon suna nuno kofar dakin da baki suna ma
    Bintun kuskus tai baya da sauri. Ido ta rint'se
    tare da cije le6e,lalle mutum mugun ice ne,yanzu
    ta gane inda Bintu ta samo duk wasu
    _information_ na zaman aure nata ba agun
    Ja'afar ba,ido ta bud'e, ta d'au alhakin Ja'afar,
    har rantsuwa yai mata amma taki yadda. Karshe
    har raba shimfida tai dashi akan maganar har sai
    da ya gamo ta da Aunty A'i aka shirya. Zama tai
    tana jiyo shewarsu a dakin Bintun. Har kullum
    bazata daina nadama akan taraiyarta dasu
    Maman Ummi ba,tasan duk fushin Ja'afar ne da
    t'sinuwar mala'iku ke bibbiyarta. Har hawayen
    bakin ciki tayi yau,tai kuma alkawarin daina
    sa6awa mijinta ko da taji haushin shi. T'sakar
    gida ta fito bayan ta g'yara fuskarta, tai sa'a
    kuwa sun fito zasu tafi suna ta dariya. Ganinta a
    t'sakar gidan yai bala'in saita nutsuwar su,a
    t'saye take k'yam tamkar wata soja ta had'e rai
    tam,ido cikin ido take k'allonsu,tuni suka hau
    inda-inda, "dama kina ciki?.. Sannun ku da gida..
    Harara ta sakar musu,ba shiri sukai hanyar
    waje,Bintu ce ta t'sayar su, "bari na raka ku
    hanya Aunty,ina zuwa na kira mai gida izinin fita.
    Duk tana k'allonsu,har tai ma Ja'afar waya wai
    za tai rakiya waje ya bata izinin fita. Bokiti ta
    zaburo da sauri tai hanyar fita,da sauri sukai
    waje sun zata kansu zata iyo,kawai sai ta ja
    t'saki ta shige band'aki. "A toh na zata koh rafka
    mana zatayi ai,g'wara muyi ta kai ta kai,dan
    wannan da gani zatai kishin hauka... Dariya suka
    sa tana jiyo su ta band'aki daga zauren sunki
    tafiya. Ruwanta na cika da ta tara ta bud'e
    band'akin a hankali tai zaure, basu nufa ba sai jin
    saukar ruwa sukai akansu har Bintun. Bokitin ta
    d'auka tai kansu dashi a sukwane, da ture ture
    suka fita waje da gudu. Tana haki ta leko kofar
    gidan ''Ashe karyar munafurci kuke, da ku t'saya
    na g'wada muku aikin mahaukaciya, shegu gadon
    na aiya,a haka zaki kare Maman Ummi wallahi,
    InshaAllah kema dubinki ta kusa cika. "Ke kuma
    yau mai rabani dake a gidan nan wallahi sai
    Allah, yau zaki ga karyar iskanci. Gida ta koma
    tana hakin daga ruwa bucket guda da tsohon
    ciki. A t'sakar gidan ta zauna tana maida
    numfashi a hankali, ta jima da zama kamin taji
    tafiyar Bintu cikin sand'a, kofar ta zubawa ido
    tana harara, kai ta leko dashi dan ganin koh
    Salman bata nan sai suka had'a ido. "Wallahi
    baki isa ki ce zaki hanani shiga ba, in gaske ne ki
    bari na shigo na shirya in fad'an ki ke nema dani
    ba hauka ba. Murmushi tai daga inda take, "Lalle
    kinyi kuskure in kina zatan zan iya had'a jiki da
    karya irin Bintu,haukar nake son sauke miki aka
    yau ai, gaba kin d'aina irin kuskuren nan ina zuba
    miki ido kawai,yau dole na fidda ki cikin gona ta.
    Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 31
    Feenat Ja'afar Novel's
    "Karya ki ke wallahi ki iya koyan hankali Salma,ai
    fad'a da makami tsoro ne,ki ajiye bokitin mu
    gabza da hannu in kin is... "Meye hakan ke kuma
    Bintu?.. Juyawa tai da sauri,tana ganin Ja'afar ta
    sau kukan munafurci harda kank'ame shi,wai
    Salma tace in ta shigo sai ta kashe ta da duka
    da bokiti bayan ta jika su ita da bakin da zata
    raka... Ciki yai gadan-gadan gun Salman,tana
    ganinshi ta mike t'saye rike da bokiti,bai
    watawataba kawai yai kanta da niyar mari tai
    baya. Kunci ta rike har tana halamar yin baya
    zata fad'i, "Kin haukace ne Salma ko mey?..
    Gidan ki ne da har zaki kafa dokar wa zai shiga
    ko ya fita?.. Cike da mamaki ke d'auke a
    fuskarta, ganin yadda ya rufe ido yake zazzaga
    mata bala'i harda yunkirin mari. "Ni zaka mara da
    akan waccan karyar Ya Ja'afar?.. A tuzare yace
    "eh wallahi, da da halin duka ma sai na
    miki,kuma daga yau kar in sake jin kin kamanta
    matata da sunan kare a gidan nan.. Kai ta k'ada,
    kan tai baya tana g'yara t'sayuwa tai d'aki. Code
    wear ta ciru, a masife ta fito tana mika mishi,
    "Amshi waya, yau in ka cika kaine Ja'afar ka
    dake a gidan nan sai nasan na ta6a maka y'ar
    g'wal dinka Ya Ja'afar, amma ni in naci sunan
    Salma,toh wallahi babu mai takani ya k'wana
    lafiya,zaman lafiyarta a gidan nan kawai ta fita
    harkata... "Bazata fita ba d'in, haba. Wannan
    wace irin masifa ce wai?.. Kullum ke kenan cikin
    dacin rai?.. Ba wanda yake t'sallake masifarki in
    ta motsa.. Haba Salma,yarinyar nan tun tana miki
    kawaici har sai kin kaita bango,koh tausayin
    yanayin da kike ciki ba k'ya yi?.. G'walo Bintun
    ta sakar mata tana a bayan Ja'afar. Kawai sai tai
    murmushi tai d'aki ta dakko hijabi da kud'i ta
    fito. Cikin sanyin murya tace "kamin izini zan fita
    Ya Ja'afar.. Harara ya sau mata!kan yace "Da in
    zaki fita ba kina gaban kanki ba?.. Wato ga
    shashasha yana magana dole ki fice,toh kije duk
    inda zaki ai kin saba... Dak'yar ta iya shanye
    kukan dake son subuce mata,ga Bintu sai dariya
    take mata a boye,da sauri ta zira hijab dinta tai
    waje. K'wafa yayi shima kamin yace Bintu ta
    shiga ciki yana zuwa. Waje yayi da sauri,har ta
    samu mai Napep ta shige tana hawaye, a tunzure
    yai gun mey Napep din, "Kar ka kuskura ka jata
    cikin Napep dinnan in kana son kekenka ya tsira..
    Sauketa tun wuri.. A masife ta rufe ido tana
    mishi balbalin bala'i kan bazata sauka ba din. Shi
    dai mai Napep duk ya tsorata,jin ta dawo kanshi
    yasa ba shiri ya tada Napep,magana yake mata
    amma ina,da sauri ya juya shima yai gun nashi
    machine din yabi bayanta. "Hajiya wannan binmu
    yake a baya fa,wallahi kar ya tafkan asara..
    Murya na rawa tace "Dan Allah ka kara gudu
    sabuwar gandu zaka kaini.. Kan ta karasa kukan
    har ya taho mata,kawai sai ta jingina kanta ta
    hau yi kamar ance mata Mama ta mutu. By
    Feenat Ja'afar.
    Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 31
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 27_Tun
    kan Napep ta t'saya ta mika mishi kud'in, da
    sauri ta shige gidan Aunty A'i fuska duk hawaye.
    "Toh kiyi min bayani man ba kuka ba
    Malama,mey aka mi... Wayan Aunty A'in ne ya
    hau ruri Aslam ya miko mata. A takaice ta k'alli
    Salman sai tai waje dan amsar wayar. Tana ji
    tana waya da Abban Aslam kan zata shigo da
    Ja'afar. "Dan Allah karki shigo dashi,wallahi ban
    san ganinshi,gwara in na huce da kaina zan
    koma. Baki sake take k'allonta hijab a hannu,
    "Ok,kina nufin yaji kika yi kenan?.. Shiru tai mata
    tana ci gaba da goge hawayenta. Bata kara bi ta
    kanta ba tai waje. Ba'a jima suka shigo tare,kai
    ta kautar gefe, tana jan hanci,ido yayi luhu-luhu
    dan kuka. Abinda ya faru ya t'sarawa Aunty A'in,
    tuni ganin duk ita ya d'aurawa lefi yasa ta hau
    musu bori ba shiri. Ido kawai Aunty A'i ta sa
    mata. "Auntyn mu kin gani koh? A gabanki ma
    kenan,wallahi na rasa rikicin Salma sam
    yanzu,abu kadan yanzu zata hau balbalin bala'i
    sai dai ni na bar mata. "Yanzu da banzo ba Allah
    kad'ai yasan mey zatai ma y'ar mutane,k'alli a
    halin da take fa,amma Salma taki k'wantar da
    hankalinta ai zaman lafiya.. "Ni fa kar ma ka
    zata kishi nake da kai koh kuma waccan amaryar
    taka,sam ba haka bane,ni mud'in za'a tada min
    hankali toh lalle na kowa zai tashi... _period_.
    Aunty A'i ya k'allo halamar tasa baki.
    Tambayarta take mey ya had'a su?.. Amma fur
    taki magana a gaban shi,har aka gama sulhu
    yace ta taso su koma tace sai dare. Da kai Aunty
    A'in tai mishi kawai kan ya k'yaleta. Ba musu ya
    tashi kan sai ya zo,yana fita ta mike tai kitchen.
    Tana cin abinci Aunty A'i na mata fad'a, kan ta
    d'aina fada Ja'afar na fada,dan ta fuskanci Bintu
    ta iya bariki. Nan ta fad'a mata ainashin abinda
    ya faru,harda irin habaici da sharrin da Bintun ke
    mata kullum. Baki ta ta6e. "Ni fa Aunty A'i Bintu
    bata gabana, abu daya na sani na tsani a gabana
    yana biye mata tana mishi abinda taga dama..
    Yana konan rai ne,shi yasa yake rasa kaina.
    Murmushi tai mata, "Lalle Salma kina so Bintu ta
    kai ki ta baro, kin kuma yi saken da kika bari
    kishiya har ta gano lagon ki,dole yai ta ganin
    bakin ki ke kadai,dan ke kadai ki ke iya daga
    jijiyoyin wuya agabanshi akanta,in sharri ma ta
    miki ki barta da Allah kawai,shi zai isar miki,kar
    ki manta igiya daya tai saura a t'sakanin ku da
    Ja'afar, kuma kince ta sani,toh wallahi ki sani
    ingiza mai kantu ruwa kawai zata miki,so take
    tai ta tunzuro ki har ki tafka kuskuren da za ai
    mai dika, kinga taci galaba kenan. "Gaba koh
    abinsu suke kina d'auke kanki a kansu, sannan
    abu in kinga zai ja ki fad'i wata magana
    musamman kan Ja'afar kiyi shiru kar ki tanka
    dan Allah Salma. "Ja'afar na sonki,kiyi amfani da
    hakan sai ki ci galaba kan Bintu.. Har ta gama
    mata fada tana ta nazarin abin,toh Allah yasa ta
    iya k'auda kan. Ita kwa Bintu murna fal rai,dan
    tana lekensu ta k'auran zauren, fatan ta Allah
    yasa yadda ya figi machine din nan in yaje kawai
    ya dankara mata saki. Shi yasa tun kan ya dawo
    taje ta t'sant'sar wanka ta hau kananan kaya,
    duk da ba ita ke dashi ba. Ita a ganinta an sau
    Salma an gama,.. K'warai ta gode da shawarar
    su Aunty Ladi ta waya da ta yau,tabbas da
    BARIKI kadai zata mallaki Ja'afar ba boka ba
    Malam. Sai dai har dare ba Ja'afar ba dalilin
    sa,kawai sai ta zata bai gama hucewa
    bane,tasan mutumin ak'wai saurin zuciya. Dirin
    machine dinshi taji,da sauri ta kara fesa turare
    ta haska touch light tai zauren da zummar taro
    shi yasha Bariki. Turus taja ta t'saya gabanta na
    fad'uwa, ganin ya mike yana fad'in ma Salma
    "Dafani man toh,ban san ki fad'i ne garin sauka.
    Da kamar kar ta kulashi,amma ganin hasken
    fitilar Bintu yasa ta hau shagwaba. "Toh ni kam
    tsoron sauka fa nake tunda cikin nan yai girma,in
    zaka iya ka sauke ni toh... Ta karasa da kalar
    tausayi. "Toh toh,amma ki kokarta,ki rikeni gam,
    koh ki bari na fara sauka... Kofar Bintu ta saka
    da sauri ta koma ciki dan bakin ciki. Tana jiyo su
    a t'sakar gida Salman na fad'in "Wash.. Allah Ya
    Ja'afar kafata rikewa take fa.. Tuni gogan ya hau
    rikicewa abinda aka jima ba'a mishi ba yau yake
    gani,bar zuciya da abinda take so. "T'saya na
    d'auke ki toh ai kina ma kok'ari.. Tana jiyo
    Salman na fad'in "kai Ya Ja'afar, anya zaka iya
    kuwa?.. Nayi nauyi fa yanzu. A zabure ta mike ta
    tana lekensu ta window ta cika tai ham. Dariya
    suke k'yak'yatawa kan yace"bari ki ga,nawa ki
    ke.. Da sauri ta sau labulen ganin ya k'wa daga
    Salman ya dauke kamar y'ar tsana suna dariya.
    Har d'aki ya dire ta suna nishad'i kamar ba su
    bane dazu an bar Bintu da kukan d'aki. Sai yanzu
    ya tuna ai koh sallama basuyi ba suka shigo.
    Murmushi tai mishi lokacin da yace bari yaje ya
    dawo. K'wafa tai tana kada kai, "kowa ya iya
    BARIKIN ai,in na baje tawa sai kin ji jiki Bintu.
    Yau da sauri-sauri yai ma Bintun sallama yana ta
    zumudin sun dinke da ta k'arfen. Kuka wiwi tai
    tayi bayan fitarshi. A gaban mudubi ya tarar ta
    tana g'yara gashi,kowa farin ciki fal ranshi,ta
    baya ya sakalo cikin yana shafawa harda sakar
    ajiyar zuciya. Murmushi tai mishi,tare da shafo
    siririn sajen shi ta bayan, sai ya k'wanto da
    kanshi wuyanta suna ma juna murmushi ta jikin
    mudubin. Yaushe rabon su kasance haka shi da
    Salman sa?.. Ga y'ar shagwa6ar nan yau yana
    shanta,duk sai ta mantarshi komai. A hankali ya
    rad'a mata a kunne "I love you... Murmushi tai
    kan ta juyo tana lumlumshe ido jin dad'in kalmar,
    lafewa tai jikinshi tana fad'in ''Me too.. Sosai
    yasha mamakin Salman shi yau,komai yi mishi
    take cikin kauna da kulawa, kamar farkon
    aurensu kamin komai ya wargaje. Hakan yasa
    washegari kowa fuskar nan kamar gonar audiga
    dan fara'a, amma banda Bintu Lol. By Feenat
    Ja'afar.
    9/29/16, 9:17 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 28_Tun
    daga ranar aka dinke da Salma da Ja'afar d'inta,
    sam ta d'aina sanya da abinta, shima abin nema
    ya samu,wai ! Matar falke ta haifi jaki. Kan kace
    k'wabo,tuni tsohuwar soyayya ta dawo d'anya,sai
    ya zama kamar kamar yanzu ma tafi yawa. A
    cikin wata guda duk sun sauya,takanas zaice su
    fito aje siyayyar kayan baby,fur Bintu take kin
    zuwa,sai suyi tafiyarsu a kafa suna tadin su,sai
    jiran EDD. Kwana biyu Bintu an tsiri zaman
    d'aki,sai ta kule ka rasa abinda take aciki ita
    daya. Ranar tana bacci da safe wajen k'arfe
    goma taji kwkwazon maigidan yana tayi ba
    kakkautawa. Tashi tai ta fito parlour. "Na fita ban
    karya ba,yanzu ma na dawo ashe baki tashi ba,
    bayan tun asubar fari kika fara wannan charting
    din danaki jini a rayuwa,na hana kin ki
    hanuwa,toh ina gaf da fasa wayarnan a gidan
    nan Allah. Baki ta ta6e tare da tashi a hankali
    tayi d'aki dan fita wanka. Tana kallo ta fito wai
    yai hakuri ta daura mishi indomie,koh ta kanta
    bai bi ba yai waje yana huci. Kamar jira take,da
    dan gudunta ta koma d'aki ta dane Facebook
    cikin group din su na KI G'YARA DA KANKI.
    Kusan duk anyi katari masu kishiya sun da yawa,
    nan zatai ta samun shawarwari mey kyau da
    marar k'yau,dak'yar ta tashi ta d'aura jalof ta
    koma. "Wato sai yanzu nake hangen maganar ka
    abokina, dan yanzu abinda Bintu take har yafi
    mai na gantali ciwo,in ta hau wannan Facebook
    din nata,sam bata ji bata gani,abinci a kone, in
    ma ta samu d'aurawa kenan,sallah a kure,bacci
    sai biyun dare,da asuba ta d'aura a inda ta
    tsaya,ga in ka shigo kaji tana dariya ita kad'ai,
    Allah zaka zata Bintu sabon kamu ce... Dariya ya
    fara mishi harda k'yak'yatawa,har ya fara
    k'uluwa,yasan haka zata biyo baya, amma shi
    yanzu shawara yake nema ya zai da sabon halin
    Bintu?. "In ka gama kai magana sai ka bani
    shawarar abin da zanyi. Dak'yar Garba ya takaita
    dariyar ya fara magana. "A lokacin chan baya ai
    bakaji zance na ba,dake idon ka a rufe yake,na
    sanarka baka san mey wani irin hali zaka jajubo
    ba,kace kai fa gaji ka gani sai Bintu.. "Malam ni
    shawara zaka bani,in babu zanyi gida. Dariya ya
    cigaba dayi,kawai sai ya zuciya yai gaba. "Ma
    had'u in ka gama,dan hankalina yai kan
    Salmatee. "Wash Allah bayana,Bintu!...Bintu!!..
    Tamkar ba kowa a gidan ka ke ji sai karar fankar
    sama dake kadawa a parlourn wacce bata hana
    gumi t'satsafo mata ba. Rarrafo wa tai zuwa
    kofa,iya karfinta ta kwalawa Bintun kira,ji take
    tamkar zata mutu dan azabar ciwo,tuni ta fara
    kuka tana ambatan Allah,tasan koh zata mutu
    Bintu bazata taimake ta ba,fatan ta Allah ya
    hankad'o mata Ja'afar koh wani ya ceceta.
    "Wayyo Ya Ja'afar, Innalillahi.. Bintu.. A razane
    ya karaso cikin gidan dan jin ta ambaci Bintu
    cikin kuka. "Subhanallah.. Salma.. Ina Bintun
    toh?.. Da sauri ta dago,tana ganinshi ta kara
    fashewa da kuka tana cije le6e. gaba daya ya
    tallafota yana aikin sannu sannu. Waya ya ciro
    dan neman Garba ya kaisu asibiti, tana ta ringing
    shiru.. Da rigarshi ya goge mata gomin dake
    tsatsafo mata, "Bari na ga koh bacci waccan
    take na taso ta. Hannunshi ta rike gam tana
    girgiza mai kai, Kanta ya shafa, "ki d'aure
    Salma,bari na kirata kinji. Dak'yar ta cika shi yai
    dakin Bintun, dan ji take yana tafiya zata mutu.
    Bata parlourn, sai ya bankad'a daki,tana mike a
    kan gado taja rabin bargo tana dariya kasa-kasa
    tana charting hankalinta yai gaba. A sukwane yai
    kanta,bai wata-wata ya sinketa da mari mai rai
    da lafiya,a gigice ta mike tare da dafe
    kunci,wayar ya warce, "Lalle haukar nan taki
    karuwa take Bintu,yanzu dama kina cikin gidan
    nan Salma take ta kakarin kiranki kamar zata
    mutu?.. "Toh ki biyoni yanzun nan waje, tana turo
    baki ta sakko kan gadon tana gunguni. Nishi take
    ta dafe d'ukkan hannunta a kasa, sannu yake
    mata da tausayawa,da harara Bintu ta bita da jin
    haushin akanta an mare ta. "Ka kira min Iya
    Shatu dan Allah Ya Ja'afar kar na mutu.. Bintu
    ya kallo dake maka musu harara, "Kizo ki
    kamamin ita na kira Iya Shatun, kamar bata so ta
    matso kusa,yana fita ta mat'sa tana jan
    tsuka,"aikin banza,dan kina wata shegiyar
    nakudarki akan hakan kika ja aka mare ni, wallahi
    za... "Eh dan Allah kazo yanzu mukaita asibiti..
    Shiru tai jin Ja'afar na kokarin shigowa tare da
    matsawa gun Salman da sauri zata ta6ata tana
    sannu. A hankali ta janye daga hannun Bintun tai
    dan ciki kad'an tana nishi, da sauri ya karaso
    dakin yana mata sannu. Nishi take iya karfinta
    sukaji sallamar Iya shatu,tana dubata tace ai
    haihuwa ce tazo gadan-gadan, ya basu waje, ya
    siyo reza da sauran abin bukata. Gam hannunta
    na cikin nashi,ji yake tana cikawa in ya tafi zata
    mutu. Kanta ya tallafo yana ta d'aure, iya shatu
    sai k'allon ikon Allah take. "Kai hakuri
    Jafaru,zata haihu lafiya dan ina jin kan D'a,
    yanzu bazata ji komai naka ba sai adu'a. Kai ya
    kada harda guntun hawayenshi yai waje,yana fita
    Bintu ta d'aura a bayanshi. Iya shatu tsuhuwar
    ingozoma ce mai ritaya, da guntun hand gulf din
    zuwa awunta ta karbi haihuwar Salman. Allah ya
    taimake tazo mata da sauki inji Iyan,sai shigowa
    yai shi da Garba yaji ihun jariri,baki wangale zai
    dakin iya shatu ta fito k'ar6ar reza. Ummanshi
    ya fara mawa albishir sai Aunty A'i,tuni ya fesa
    cikin gidan su,da ance mey ta samu? Sai yace
    bai gani ba. Har aka kintsa komai basu kara
    ganin keyar Bintu ba,sai da zasu asibiti ta fito,shi
    kam baiya ma ta ita. Suna fita su Aunty A'i suka
    zo da Ummi,lokacin Bintun na t'sakar gida tana
    yankar farce,ita dey Iya sai mamakin karfin hali
    irin na Bintu take. Sallama suke ta manna musu
    bajon hauka,tuni Ummi taja dogon t'saki, taki
    jinin Bintu a rayuwa. "Banza y'ar bakin ciki
    kawai,toh sai ki had'iyi zuciya ki mutu ai.. Hannu
    Aunty A'i ta daga mata halamar tai shiru,ita k'wa
    da harara tabi su har suka shige. Sun dawo an
    duba suna lafiya ita da babyn ta,Ja'afar baki har
    kusan k'unne dan murna,yana makale da yarshi.
    "Um,Baban baby ba koh dan karar nan ma ta
    manyan yayu.. Kai ya sosa yana ma Aunty A'in
    murmushi, ba dan yaso ba ya mika mata ita. Kan
    kace mey gida har ya cike da dangi yan barka da
    yan unguwa. Sai dare ta samu tasa hakarkarinta
    dan hutu. K'allon babyn take mey kama da
    Abbanta, gashi kadai da dan _beauty points_
    (dimples) tai gadonta. Murmushi tayi tana kai
    hannu kan kumatun babyn, Allah mai halitta.
    Murmushi yake musu yayin da ya shigo d'akin,
    sai ta daga kai ta k'alleshi, kai ta girgiza tana
    dan murmushi. Sallama ta uku yana musu kenan
    yana dawo wa,ta rasa wani irin kulafuci yake
    musu musamman babyn. Zama yayi yana shafo
    sumar babyn da farin ciki. "Oh ni kam,koh zaka je
    da ita in tai kuka sai ka kawo ta. Murmushi yayi
    yana kai baki kan dimple din babyn yana kissing.
    "Ba kinki barina na k'wana anan ba?.. Da kalar
    tausayi yace "yau dai daya naji dumin y'ata kinji?
    Sai ya marairaice fuska. Dariya ta dan mishi,kan
    tai magana ta jiyo Babah mai zamar mata tana
    ya fito zata zo ta k'wanta,taga sallamar bata
    karewa. Dariya suka sa kamin ya tashi yai waje.
    "Maza ki rika biye mishi ki debo ma kanki
    magana da kazamin goyo ai. Da rashin fahimta ta
    k'allota tana neman karin bayani. ***** ***** Yau
    suna,baby taci sunan Mama tun ran huduba
    amma ya 6oye mata. Sosai yau daya Ja'afar ya
    biya mama,harda mishi waya tana kwarara mishi
    godiya ba iyaka. Maijego tai ras abinta da Baby
    Miemien ta,sun fito sunyi k'yau sosai. By Feenat
    Ja'afar. Ai hakuri da wannan dan zani gidan
    Suna Salma.. Zuwa yamma in na dawo zakujini
    Lol..
    9/29/16, 9:17 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    29_Suna ya wat'se kalau,maijego tai
    goshi,ak'wati guda Mama ta mata na suna sai na
    baba,ga Umman Ja'afar nata daban da tazo
    suna,chan gidan su Ja'afar su ma sun mata
    karamci,sai son barka. Wankansu suke cikin
    g'yara na musamman da Mama ta zage yi ma
    y'arta, albarkacin Miemie mama ta sakko sosai.
    Shirya Miemie take tare da taimakon Ja'afar din
    suna ta nishad'in su yau za ai yawan arba'in. Ta
    chakare sosai kamar yau ne sunan ita da Miemie.
    Baya ta juya mishi yana goya mata ita, "D'aure
    ta dakyau,dan kinga machine zamu hau.. Kai ta
    kad'a tana murmushi, Sai da ya zaga ko'ina yaga
    yayi kan ya bata majanyi tana mishi dariya, "A'a
    toh in baki iya ba ni sai na goya abata kawai...
    Dariya tai kan tace "Da kwa kabar abin fad'i
    agari kuwa. Jakar ya d'au mata ta d'au mukulli
    sukai waje,shima yasha sabuwar shadda abinshi.
    Bintu na t'sakar gida tana d'anne-d'anne a wayar
    da dak'yar ya bata. Da harara ta bisu harda dan
    t'saki a hankali. "Toh mu zamu fita sarauniyar
    charting.. Sai kisa mana mukulli a gida dan
    gudun kar a dirko kina sana'ar taki koh.. Tuni ta
    kara k'uluwa kuwa,ita dai an mayarta borar karfi
    da yaji a cikin gida. Hannu Salman ta dago mata
    halamar sai sun dawo,da harara ta bisu har sukai
    waje. "Jishi kamar wani dan daudu rike da jakar
    mata. K'wafa tai tana tashi t'saye, "Ba dai kin
    fara fita ba?.. K'wanan nan zaki yabawa Aya
    zakinta wallahi. ** K'wana biyu yau tayi tana fita
    yawan arba'in, yau ne na uku,yau kuma aka tafka
    t'siya da maigidan,dan fur yace ba inda zata je.
    "Bazaki k'waso ma yarinya rana ba fa,kiyi hakuri
    kawai. Iya wuya Salma ta kawo dan takaici, tayi
    magiyar yaki kuma,kawai sai ta raya mata tunda
    dama taki bari ta koma hagu. "Amma gaskiya
    baka min daidai ba Abban Miemie in har ka
    hanani fita yau. "A ka'ida sati ake fita yawan
    arba'in fa,amma ni na yarda zanyi ukun shine har
    na gama shiri amma kace bazani ba... Gaskiya
    da sake. Gefe tai da kai tana kunkuni,tuni ta
    kular dashi shi zuciya kusa. "Toh ban hanaki ba
    kije d'in, amma ki ajiye min y'ata ki tafi ke kad'ai.
    Baki sake take k'allonshi,ganin yadda ya fidda
    waya yasha kunu ya barta. A zuciyarta tace "Eh
    lalle,da gani abin Ya Ja'afar yazo da wulakanci...
    "Kasan dai ba yadda za ai na tafi na bar Miemie
    a gida,dan Allah in wasa ka ke ka bari,dan kam
    nasa rai da fita yau.. A tunzure ya mike da niyar
    magana cikin masifa,sai yai shiru yana k'allonta.
    "Kiyi toh gaban kanki kawai.. Sai yai waje da
    zummar barin gidan ma dan haushi. Sai dai
    mey?.. T'saye yayi yana binta da k'allo galala,
    ganin yadda ta fara kame-kame dan ya kamata
    tana musu la6e ta window. "Ke kuma lafiya kike
    abu kamar marar gaskiya?.. Dakewa tayi tai
    ganin kamar bai ramfota ba. "Dama zuwa nayi
    ina son na leka nan na dawo ne... "Ba mai fita
    yau acikin gidan nan in dai ni ne mijin, wacce ban
    isa ba ta fita nagani.. A fusace ya fice yabar
    gidan,duk sai ta Salma tafi zafi. Ita kam Bintu
    dariya tasa harda shewa, "Yau karya ta kare,sai
    a za6a zaman gidan miji koh fita yawan gantali
    gard'i... Tana jiyota tai banza da ita tana
    hawayen bakin ciki. Waya ta d'auka ta kira Aunty
    A'i kan abinda Ya Ja'afar ya mata. "Salma kiyi
    biyayyar aurenki, dan Allah kiyi hakuri da fitar
    kawai. "K'wana biyu ai yayi ma,tunda kin zaga
    ko'ina ai har gidan su... "Aunty A'i ban fa wuni a
    gida ba kullum a ziyara muke wuni. "Ai duk fita
    kina zuwa,dan Allah kar ki dawo muku da hannun
    k'yauta baya man,kuna cikin zamanku abin
    sha'awa. Baki tai ta bata sai da ta tabbatar mata
    da ta hakura kamin sukai sallama. Haka tanaji
    tana gani ta hakura da fitar tai zamanta a d'aki.
    Koh abincin rana kin zuwa yai yaci a gidan sai
    gidan Garba yaje. Kawai zuciya ke raya mishi
    Salma ta fita,bazai so yaje gida yaga tabbas ta
    fitan ba,kawai sai yai zamanshi har yamma tukun
    ya koma gida. Dakin Bintu ya nufa har yanzu
    baida walwala sai ya tabbatar da Salma bata fita
    ba,yasan Bintu kat ce,bata t'sallaka doka akan
    fita,in yace A'a, toh ta hakura. Sannu da zuwa tai
    mishi tana fara'a, a ranshi yana aiyana da Salma
    ce yasan sai ta cika tai fa kan ta mishi sannu da
    zuwa duk akan ya hanata unguwa,amma kullum
    y'ar uwarta ko ajikinta. "Yau bayan fita ta Salma
    ta fita?.. Kai zata girgiza, sai tai saurin kwa6ar
    kanta, dole yadda tasa taga bakin ciki har yau
    itama ta gani. "Eh,bata jima da dawo wa ba
    ai,baka sani bane?.. Hannu ya daga mata,cike da
    jin haushi yace "ya isa ni,tambaya na miki kawai.
    Waje yayi tana binshi da g'walo, yana yin nisa ta
    tuntsire da dariyar mugunta. Kamin cikin sand'a
    tai waje jin ya zata kaya. Ba koh sallama ya
    shiga parlourn, ganan takalmin a gefen kofa
    wanda ta fitar zata sa dazu. Tana zaune tana
    _feeding_ din Miemie ya shigo yana binta da
    kallo,da fara'arta tai mishi sannu da zuwa.
    Kekam yayi yana k'allonta ba koh kiftawa, tabbas
    Salma ta fita,dan mud'in bata fita ba bazata tare
    shi da wannan fara'ar ba haka,yasan kayarshi.
    "Wato kin fita hankalinki ya kwanta koh?.. Ban
    isa ba ashe har yau halinki yana nan baki sauya
    ba koh Salma?.. Baki sake take K'allonshi da
    tsananin mamaki,sai d'aure ta yake da jijiyoyinta.
    Cikin nut'suwa tace "Ni fa ba inda naje tun fitar
    ka,dan Allah ka d'aina tun.. Malama ki amshi laifi
    kawai,kinsan nafi t'sanar musu sama da komai,
    koh kina nufin Bintu karya zata miki?. K'allon
    mamaki take mishi,a hankali ta maimaita
    "Bintu".. Yaki ma bari tai mishi bayani sai
    zazzaga mata yake kan bata maidashi abakin
    komai ba. Kawai sai ta sau mishi kuka,tama rasa
    abin fad'i,wai Bintu ce ta fad'a mishi,wato ita ba
    abin yarda bace sai kishiyarta indai kan fita ne.
    "Haka ki ke ai,da kukan rashin gaskiya
    Salma..sam bana son ki dawo mana da hannun
    agogo baya,ina ta murna komai ya wuce ashe
    albarkar ciki ne yasa ki zaman dole. Ganin
    kukanta na karuwa yasa ya fice ya koma d'akin
    Bintu. Har da bawa kura ajiyar nama,wai duk
    randa Salma ta fita dan Allah karta 6oye mishi.
    Tun daga ranar ya sauya mata,sam in ya shigo
    sai dai ya d'au ya'rshi ya fice,itama daga
    gaisuwa shikenan ta gama,dan a ganinta
    wulakanci ne wannan babba. Ga wani fi'ilin
    mutunci da Bintu ta koya da kissa,kullum faram
    faram take mata,harda gaisuwa in antashi. Ta
    d'au Miemie ta goya a bayanta in Baban ya
    d'akko ta. Ba karamin dad'i kwa Ja'afar din yake
    ji ba,dan yana karrama mai son Miemien shi,ita
    kam Salma nata ido,sai ta dukufa gun kai
    kukanta ga Allah. Dan tabbas tasan tai saken da
    har mijinta yai mata mummunan tambari. Bintu
    kuwa kullum rokon ta Allah duk wani sharrin da
    take nemanta dashi Allah ya mayar mata kanta.
    By Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:20 AM - Queen Safiyyert馃憫: [8/2, 2:29 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    30_Sai ya huce kamar sati ana mutunci da ta
    tambayi fita unguwa zai kicin-kicin,yace tai son
    ranta,haka zata hakura tanaji tana gani,in ya
    dawo kuma tasha fad'an da batasan laifi ba.
    Kawai Allah ya d'aura mata wani irin hakuri,daga
    Ja'afar din har Bintun ido tasa musu kawai.
    A haka har Miemie tai wata hudu Salma na
    zaman hakuri, musamman ga saurin fushin
    Ja'afar gareta,ga tai alkawarin daina kai kara gun
    kowa sai gurin Allah.
    Ana haka Maman Abba ta haihu.
    Ganin yau y'an mutuncin na kanshi yana zaune
    ya shagala da yiwa Miemie wasa tana wage
    mishi baki tana dariya.
    Da fara'arta ta zauna kusa dasu tana k'allonsu.
    "Abban Miemie...
    K'allota yayi tare fad'in yana jinta,cigaba yayi da
    wasan su.
    "Inda hali dan Allah zani barkar Maman Abba yau
    kwananta hud'u da haihu banje ba.
    Kai ya kad'a, "wace Maman Abba?..
    Da zumudin zai batta ta sanarshi makociyarta ta
    unguwar su ta da.
    Abinda yake ya t'sagaita yana k'allonta ba koh
    kiftawa.
    Tuni ya zata an rufe babin y'an tsohowar
    unguwar su a gidan,ashe har yanzu tana makale
    dasu.
    Bazai manta dasu ba,dan sune ummul aba'isin
    wargaza gidanshi.
    Kai ya girgiza mata,
    "Kiyi hakuri ba halin zuwa..
    Baki ta sake tana K'allonshi, a gaskiya bazata
    zuba ido tai ta zaman gida na y'anci ba,da takura
    gaskiya.
    Amma sai ta bishi da lallami.
    "Dan Allah ya Ja'afar ka barni naje,nima dana
    haihu fa sau biyu tazo min har suna uku,kaga ba
    dad'i ace ni koh sau d'aya banje ba barka ba sai
    suna.
    "Sunan ma ki fidda a ranki,dan inda mu'amular
    dana fi tsana,toh mu'amular ki da y'an unguwar
    chan ne,kin gane ai?.
    Kasa tai da kai,sosai take d'aure irin halin da Ya
    Ja'afar ya tsiro mata,yanzu da ta kara tambaya
    zai ce tai gaban kanta,hakan yasa tai shiru.
    Shi kuma yadda yaga batai gardama ba yasa yai
    tunanin zancen bai shige ta ba ne.
    Miemie ya ajiye kusa da ita ya bar mata d'akin.
    A hankali ta zame ta kwanta,sai ga hawaye ya
    zubo mata.
    Zaman gidan nan ya fara isar ta,hakurinta ya
    fara karewa.
    Tana ji yai ma Bintu sallama ya fice,kawai sai ta
    sau kuka a hankali marar sauti.
    Wato a dake ka a hanaka kuka?.
    ****
    Tun bayan fitarshi bayan ta gama kukanta
    Miemie ta fara,kukan har ya wuce kima, komai
    tayi taki shiru,kawai sai ta goyata tasa hijab akai
    suka fita t'sakar gida dan sanyin magriba.
    Bintun na t'sakar gida tana saita abin fad'i kan
    Ja'afar ya dawo tambayar Salma koh ta fita,dan
    komai a k'unnenta ya wakana.
    Jijjiga ta take tana yawo daga t'sakar gida zuwa
    zaure da ita,tasan Miemie ba mai rigima bace,
    tabbas da abinda ke damunta yau,yawan kukan ji
    take kamar itama tasa kukan koh taji sa'ida.
    Dak'yar ta samu tai shiru,sai ajiyar zuciya take
    halamar tai bacci.
    Buta ta d'auka ta shiga band'aki kenan sai gashi
    kamar an hulloshi gidan,fatanshi yau ya rit'sata
    garin satar fita.
    Bintu ya kalla wacce ke murmushin ganinshi,sai
    taunar cingam take tana kas-kas,kai da ganinta
    da yanayinta kaga na mai shirin kulla wani
    sharrin.
    "Sannu da zuwa..
    Kai ya daga mata, kamar kullum zai tambayi
    Salman sai yaji bud'e band'aki.
    A fusace ya kallo Bintu, "bayan fita ta Salma ta
    fita?.. Ki fad'an t'sakani da Allah.
    Kwai tayi kan ta fasa tare da yin kas dashi,
    "Eh ta fita,mey ya faru? Yanzun bud'e dakinta ta
    shiga band'aki ka shigo.
    Gadan-gadan Salma tayi kanta da butar data cika
    zatai alwala anjima,kansu farga ta rot'sa mata
    aka tana huci,bai isa ba ta rufeta da duka baji ba
    gani,fad'i take
    "Sharrin naki ya wuce bayan idona yanzu a
    gaban idona ma yi..
    Mari ya d'auketa dashi shima yana fad'in ta sake
    ta.
    A fusace tace bazata saka ba,ita kam tamkar
    wawiya ta bari Salman na jibgarta,ganin da gaske
    take yasa da sauri ya finciko Bintun tare da kara
    mata wani marin.
    Kunci ta rike tana K'allonshi, "ki sani na gaji da
    halinki a gidan nan, karan nan zan d'au
    mummunan mataki akanki wall...
    "Ka sallame ni in ka gaji dani Ja'afar.. Dan ni tuni
    na gaji da zaman gidan ka, ka sallame ni ka huta
    toh..
    "Haka ki ka ce?..
    A fusace tace "eh haka nace..
    Tuni shedan ya shiga cikin zuciyar
    kowa,musamman Ja'afar da ya rufe ido tamkar
    bashi ba.
    "Ki je gida sai na neme ki toh...
    Cikin kuka tace
    ''Ban isa zuwa musu ba sheda ba,dole ka bani
    sheda..
    Ba tare da jin komai ba mugu(shedan) yasa ya
    rufe ido.
    "Kije na sake ki toh..
    Chak! Taji kukan ya t'saya sai na Miemie data
    tashi dan hayaniya.
    Baki sake take k'allonshi fuska wanke da
    hawaye.
    "Ja'afar ka sakeni kace fa?.. Muryarta na
    ka'rkarwa ta tambaya.
    Da sauri ya bud'e ido ya dawo hankalinshi kanta.
    K'allon-k'allo suke ma juna cikin rashin sanin
    abin fad'a, musamman Ja'afar dashi ya furta.
    Ido ta rufe a hankali, sai ga hawayen da ya
    makale sun zubo.
    A hankali ta bud'e idon ta k'alli Bintu.
    "Allah ya biya ki da dai-dai abinda ki kamin
    Bintu.. Ki sani,sharri kare ne,ko yayi nisa zai
    dawo gun maishi..
    Jiki a sanyaye ta juya gun Ja'afar.
    "Shikenan abin nema ya same mu Ja'afar.. Aure
    ya kare a t'sakanin mu..igiya uku ka rusheta
    Ja'afar.. Ka rushe su..
    Hannu tasa ta share idonta.
    "Ba ka da bukatar na t'saya maka bayani yanzu
    kam,dan ka zuba katanga a t'sakanin mu.
    Cikin nut'suwa tai hanyar waje ba tare da ta koh
    waiwayi d'aki ba.
    Da k'allo ya bita, ilahirin jikinshi ka'rkarwa
    yake,ya kasa tattara kalma daya da zai ambata,
    har Salma ta 6ace wa ganinshi.
    'By
    Feenat Ja'afar.
    [8/2, 10:40 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    31_"Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'un.. Allahumma
    Ajurni fi Musibati,wakhluf li khayran minha...
    "Salma ki ce min ba gaskiya ki ke fad'a ba
    Salma?.. Dan Allah ki ce wasa ki ke..
    Murmushi take,wanda da zatai kukan zai fi mata
    alkairi, amma ta kasa,tun zuwanta gidan Aunty
    A'i ido ya kafe,tunani ya t'saya.. Dabara ta ka
    re,sai kallo da ido da murmushi da yafi kuka
    ciwo.
    Waya Aunty A'in ta d'auka dan kiran Ja'afar,
    tayuwu koh shi ya mata bayanin da zata gamsu
    tunda Salma ta zama kurma.
    "Ja'afar..
    "Bashi bane.. Tsam tayi dan tasan Bintu ce ta
    d'auka.
    Da karfin hali ta tambayi in yana kusa ta bashi
    man, t'saki tai mata kamin ta kashewar.
    Kasa tai da wayar tana mai tabbatar da kalaman
    Salma na aure babu,ya ka re.
    A hankali ta sakko ta t'suguna gaban Salman
    tare da dafa kafafunta.
    "Salma kimin magana ba shiru ba dan Allah.. A
    dunkule kika bani, dan Allah kiyi magana, shin da
    gaske ya sake ki cikon na ukun?..
    K'allon Aunty A'in take cikin ido,tabbas wannan
    kalmar ita ta 6acewa tunaninta.
    Kan ta ankara ta sau mata wiwi,baji ba gani.
    "Bintu ce... Wallahi itace.. Ban mishi komai
    ba..ya raba aurenmu.. Allah banyi komai ba
    karan nan Aunty A'i,ki yarda dani dan Allah, koh
    su Abba baza su yarda ba...
    Kamar karatun yara haka take had'a kalaman
    cikin kuka.
    Jiki a sanyaye Aunty A'in ta tashi tazo kusa da
    ita,sosai ta gane sambatu take,cike da tausayin
    y'ar uwartata ta rungumo ta, ta abu daya take
    gane gaskiyar Salma tun a yarinta, shine fad'in
    abin da batai ba cikin kuka.
    "Na yarda Salma,na yarda dake karan nan.. Ki
    bar kukan haka, Allahu yasa shi yafi zama muku
    alkairi.
    Ita dai kukanta take.
    Ina Ja'afar ya gano abinda Aunty A'i ta sani
    game da rayuwar Salma, da bai bawa CID na fitar
    ta ba, da ya fuskanci ta sauya tun sa'ilin da in
    yace ta fita take kuka,da ba ayi hakan ba.
    *******************
    "Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'una... Ja'afar mai ya
    kai ka wannan yanke d'anyen hukuncin kan ku?..
    Mey ya kai ka?.. Abinda ya faru yake sanar
    mishi,gaba daya ya rasa abin yi.
    "Shin ka tambayi ta fitan koh bata fitan ba?.. Koh
    har yanzu kai baka hango hankalin Salma ba ne..
    Kai ya k'ada mishi
    "Ba wannan ne karon farko ba,ni nasan Salma
    fiye da zaton ka..
    "Ka kuma yarda da Bintu fiye da yarda ka bawa
    Salma yarda koh ka ke nufi?..
    Murmushi yayi na takaici, "Ja'afar bakasan sharri
    irin na mata bane.. Da baka ba Bintu amanar
    aurenka sukutum ba Allah. Tayu ka tafka babban
    kuskure na fahimtar Salma karan nan.. Amma ka
    yi bincike, shine t'sarin Shari'a.. Ni na shiga gida.
    Da kallo yabi bayan Garban, duk maganar shi
    gaskiya ce,kuma ba daya daga ci da ya aiwatar
    kamin komai.
    Yau daya yaga fushin Garba karara kwance a
    fuska,tabbas haushin shi yake ji shima,kamar
    yadda shima yake jin haushin kanshi da kanshi.
    Jiki ba kwari ya tada machine yai gida.
    Dole ya tit'siye Bintu ta sanarshi gaskiya.
    Bata d'aki,ga nan wayarshi da ya manta da tata
    akan gado halamar tana sana'ar tata ta charting.
    A garin ya d'auki tashi ya danno screen na
    Bintun, haske ya baiyana halamar tana ma kan
    charting din tai wani waje.
    Kwanciya yayi da bayanshi jiki duk a
    sanyaye,bazai iya bawa wannan ranar suna ba.
    Ido ya kura ma wayar Bintun kirar _Techno_, zai
    so yau yaga mey ke debe hankalin ta zuwa
    Facebook.
    *Bintu U*.
    _"ke an saki shegiyar fa,ki tayani murna zan
    sakata in wataya_..
    *Shining star*:
    _"Kai matar nan baki da dama,a bani satar amsa
    dan yanzu na dawo makarantarki_..
    Da azama ya mike zaune dan ganin charting din.
    *Binta U*
    _"Hhhhh,tuggu dai kamar kullum nayi,sai dai na
    yau mai zafi ne,dan jiya an bani sa'a har gida,
    take ina fad'in ta fita ya d'anna mata saki,baiwar
    Allah harda dan guntun wa'azin ta ta min
    hhhhh_..
    *Shining star*
    _"ina ma zan iya irin wannan sharrin naki dana
    huta, sai dai tawa tasan takan duniya,ina mata
    take dawo min da abu na_..
    *BINTU U*
    _"ba gari daya muke ba,da wallahi taci karya,ni
    zan baki maganin y'ar banza_...
    "Ya Allah... Kai shafo cikin ranar jiki hawaye na
    zuba, da sauri ya d'anna _previous chat_
    Sai gata kamar an jehota da buta a hannu tana
    zare idano na munafukai.
    Sam bataji koh dirin machine dinshi ba,sai
    arbawa tai da takalmanshi.
    Da d'ukkan hannu biyu ya dafe kanshi yana
    hawaye,mey zai ma Bintu ya huce da bala'in da
    ta jawo mishi?..
    A hankali kalaman Salma ya dawo mishi,
    _"Allah ya biyaki da dai-dai abinda ki kamin
    Bintu..Ki sani,sharri kare ne,ko yayi nisa zai
    dawo gun maishi_...
    Gashi tun kan a kwana ya dawo ma Bintu bata
    shirya ba...
    "Ka dawo..yaushe ka shigo..ban banji shigowar
    ka ba..
    Da in'ina take maganar, ganin yadda hawaye ke
    diga a kafafunshi ga kuma wayarta a hannunshi
    tasan yau karya ta kare.
    Ido ya goge kamin cikin nut'suwa ya ajiye wayar
    kan gado ya k'allota.
    "Tabbas kinyi nasarar rabani da d'ukkan farin
    cikina Bintu.. Kinyi nasara,tanan kam nasan kin
    ma Salma fincinkau,dan ita bata sharri..
    "Na baki d'ukkan wata amana,ki mayarni
    shashasha.. Ki nunan yau abinda Salma take
    gudu a kishiya,"makirci"..
    "Amma ki sani,wallahi!,wallahi!!.wallahi!!!
    Uku,yadda kikai sanadin 6allewar aurenmu da
    Salma kinyi naki.
    "Kamin nan zaki ji jiki kamar yadda ki ka sa taji
    t'sawan zaman ku..
    Kan tai kwakwaran mot'si ya hard'o ta, ta ko'ina
    mari yake bata iya karfinshi tana ihun jama'a su
    ceceta..
    Sai da tabbatar ya taga wuta dan mari kamin
    yana haki ya nuno ta.
    "Kije kema,na yanke igiyar aurena dake kanki har
    guda uku... "Tun kan ki kwana maganar Salma ta
    kar6u gun Allah...
    Ihu ta saka tana bashi hakuri kan ta daina, "dan
    Allah karka sake ni...
    Hanyar waje yayi yana sa waya a aljihunshi.
    "Ki tabbatar baki kara awa d'aya cikin gidana
    ba,dan saki uku na furta.
    Waje yayi ya ja ya t'saya a zaure,tamkar wani
    yaro ya rushe da kuka mai tsanin ciwo..
    Yayi kuskuren da dak'yar ya g'yara shi cikin
    rayuwarshi.. Yayi kuskuren da ya bari Salma tai
    mishi nisa...
    Yayi kuskuren kin kar6ar shiryiwar Salman sa..
    Tabbas ya tafka babban kuskure a rayuwa.
    "Allah ya isa t'sakani na dake Bintu... Ubangiji
    yai ma Salma sakayya akanki daga yau har ranar
    sakamako... Allah ya isar mata cikin sauri..
    Ganin hakan ba mafita bace gareshi yasa ya
    d'akko waya hannu na ka'rkarwa zai nemo Garba
    yaga kiran Aunty A'i na dazu.
    Garban ya kira,dole ayi wacce za ai,Aurenshi da
    Salma mutuwa ce kadai zata raba.
    Da Allah ya had'ashi cikin muryar kuka kan yazo
    gidanshi yanzun nan..
    "Isha'i ake kira fa Ja'afar..
    "Dan Allah kazo,in bakazo ba komai zai iya
    faruwa...
    Ba'a fi minti goma ba yazo,fatattakar arziki yai
    ma Bintu ta bar gidan ya rufe ya fad'a mota.
    Da t'sananin mamaki yake k'allon abokin nashi, a
    iya abotarsu bai ta6a ganin koh da hawaye na
    Ja'afar ba bare kukanshi mai sauti irin haka.
    Dan Ja'afar namijin duniya ne,Jarumi, kuma
    jajirtacce, yasan komai ya sashi kuka ayau ba
    karami bane.
    "Gidan Aisha zaka kai ni yayar Salma..
    Baki sake yake k'allonshi,
    "Yayar Salma kuma?..
    Ido jajir ya kalloshi ba halamar wasa,dole ya tada
    mota suka d'au hanya.
    Waya yai mata kan ta fito yana kofar gida.
    "Malam mijina ya fita..kai hakuri.. Kit ta kashe
    wayarta,yau Aunty A'i ta d'au zafi ya sani,tabbas
    kuma Salma na gidan..
    Murfin motar ya bud'e a fusace ya fice Garba na
    kira.. Kofar a bud'e take,kawai ya tura ya shiga,
    nufinshi a d'aureshi bayan yaga Salman.
    "Salma!,, Salma!!.. A tunzure Aunty A'i ta fito a
    parlourn dan tsayarahi shiga mata parlour.
    Yadda taganshi bata isa hana shi ba ganin
    Salman, dan g'wiwa biyu ya zube gabanta tamkar
    yaga Salman.
    Hanya ta bashi ba musu,da zafin nama ya mike
    ya shiga parlourn, bata zata ba taga mutum a
    kanta,da sauri ta zabura ta mike tana kwad'a
    kiran Aunty A'i da sauri.
    Bata nufa ba taga mutum zube a gabanta kanshi
    a kasa.
    Ido ta rint'se tare da kawar da kanta,koh kadan
    bata son kara ganin Ja'afar a rayuwarta Abadan.
    Juyo wa tai da niyar surfa mishi ruwan bala'in da
    ba shiri zai bar gidan,sai dai mey?
    Da t'sananin mamaki take kallonshi tana k'allon
    Aunty A'i.
    Hawaye ke malala a idonshi kamar wanda ya
    rasa jin dad'in rayuwarshi,abin g'wanin ban
    tausayi.
    Ja'afar?.. Kuka ma?, a namey toh?.
    "Salma gani gabanki, a matsayin wanda ya tafka
    miki laifi cikin rashin sani,da kuma sharrin
    Bintu..Salma kiyi hakuri,wallahi _am really really
    sorry.. Kar ki barni dan Allah.. Zan tagaiyyara
    Salma.. Zan zauce.. sharrin Bintu ne,kuma itama
    ta amshi hukunci,dan na saketa kamar yadda ta
    jawo mana,
    _please_ Salma _forgive me_... Wallahi _I can't
    live without you anymore_,ki tausaya ma mijinki
    uban yaranki...
    Baya taja da sauri ganin yana kara kusantota.
    Da sauri Aunty A'i tai waje jin kuka zai kubce
    mata.. Dole haka zata kasance dasu Salma,ranar
    rabuwa, rabuwar da ba a da tabbacin za'a dawo
    ta.. Tabbas tausaya wa rayuwar su,dan a irin
    soyayyar nan ita ce ake kira *Mutu ka raba*..
    Gashi yanzu K'ADDARA ta raba masoyan biyu.
    By
    Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:24 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    32_Kuka take yanayi iya karfinsu, tabbas
    K'ADDARA ta rigayi fata, duk kuma yadda ka
    t'sara rayuwarka sai ka ga ba haka ya tafi
    ba,tabbas ta Allah itace daidai. Baya tai ta zube
    kan kujera da6ar.. Duk sunyi kuskure, kowa na da
    laifi,meyasa ma tace ya saketa?.. Mey yasa?..
    Le6e ta cije tana mai sa d'ukkan hannunta biyu
    zuwa fuskarta, kuka kam yau har sunji ba dad'i.
    A hankali ta dago tana K'allonshi ido yai luhu-
    luhu,duk ya marairaice mata hawaye na zuba, tafi
    tausayin kanta sama dashi, Kokarin magana take
    su Aunty A'i sukai sallama ita da maigidan da
    taima waya. Fuska Ja'afar yai saurin gogewa
    ganin yadda Abban Aslam ya sau baki yana
    kallonsu,bai tunanin abin ya kai haka ba, kuka a
    gaban mace da zubewa g'wiwa biyu?.. Lalle
    yasan abin babba ne. "Innalillahi Wa'ina
    Ilaihirraji'un... Itace kalmar shima da ya fad'i
    bayan yaji mai ke faruwa.. "Dole aje gida kowa
    ya samu labari,dan wannan ba abin a 6oye bane
    koh da za'a nemi sulhu,saki ya cike na uku abin
    yafi karfin zama anan Ayush.. Zamu tafi da
    Salman kai Ja'afar sai ku taho da abokin ka. Har
    kusan goman dare ana abu daya akan zancen
    saki. "Ka ce kayi saki,ita tace ya zama uku,
    sannan kana zancen ai sulhu koh? Kai ya daga
    da sauri, murmushi Abban yayi,abin yaso ma
    bashi dariya, "Wato Ja'afar... "Malam Umar
    wannan zancen ba zancen da za'ai wa sakwakwa
    bane,kan Ja'afar ya dawo. "Kai kuma in dan baka
    tashi mun wuce ba zan mugun sa6a maka
    yanzun nan.. "Kana hauka ne?.. A wane garin ka
    ta6a jin anyi saki d'ai daya har uku kuma ana
    neman sulhu?.. "Ai baka fara ganin komai ba
    Ja'afar, ba dai zuciya ba?.. Za ta sa ka dana
    sani, "Malam Umar ai hakuri bisa wannan
    K'ADDARAR da ta sakko mana,zamani ne yanzu
    muke ciki da yara basu dauki saki a bakin komai
    ba.. Tashi yayi yana bawa Abban Salman
    hannu,kan ya kallo Ja'afar,har yanzu sautin
    kukan su ke fita shi da Salman. "Muje koh?..
    Salma ya dago ya kalla da sunkuyar da kai,
    "Salma dan Allah ki basu hakuri kar su
    rabamu,kin san bazan iya rayuwa ba ke
    ba,Abadan Salma...Please. Kuka ta kara saka
    mai karfi, t'saki Abba yayi ya karkade riga yana
    nuno shi cikin fad'a. "Hauka kenan wannan, dan
    koh a musulunce Salma ta haramta a gare ka..ta
    haramta har abada,dan kai kam ka nuna mana
    bazaka ta6a iya rike aure ba, saki tamkar wasan
    yara? Itama waccan wai ka mata saki uku?.. Toh
    koh aure Salma tayi na fad'a maka ta haramta a
    gare ka har abada,kaje kaci zuciya. Da gudu
    Salman ta tashi tai d'aki tana kuka.. "Haba
    Alhaji, abin bai kai haka ba,kuskure ne kowa yana
    iya tafkawa a rayuwa.. Anji bai k'yauta ba,amma
    kar hakan yasa kai mishi baki,kai hakuri. "Hakuri
    shine ya biyo ni yanzun nan.. Wace iriyar
    haukace wannan kamar a jahiliya?.. Wani yai
    mishi sakin?.. Haka Ja'afar naji na gani yai waje
    yana waiwayen dakin da Salma ta shige yana
    hawaye. Tun daga ranar duk suka zama sakwa-
    sakwa, barin Ja'afar da baida kuzari,ga Abba ya
    sako shi gaba ta ko'ina.. Dan har gida iyaye
    Bintu suka zo sukai ma Abba rashin k'yauta wa
    akan yadda bayan saki uku sai da aka
    kumburawa ya'rsu fuska,harda ikirarin
    koto,dak'yar aka basu hakuri kan suka debe
    kayanta, ranar Abba yayi takaici har yaji ina ma
    da ya barma Umman shi Ja'afar,kila da baici
    karo da bacin ranshi ba. Sai dai yace kayan
    Salma koh sama da kasa zasu had'e ba mai diba,
    ashe ma in ya bari aka diba sun rabun kenan...
    Ja'afar mat'sala. Anyi ban baki, Abba yayi fad'an
    ya dawo lallashin amma Ja'afar ba sauki,kawai
    sai Abban Salma yace a rabu dashi,dole in ta
    tashi aure zai bari a diba da kanshi. Kullum ta
    Allah yana kan jelar gidan su Salma,a wata guda
    har kama ya sauya,ba aski,ba g'yaran fuska,ya
    zama tamkar zararre. Sosai Abba yake tausaya
    mishi,Mama kadai ke shafawa idonta toka ta
    hana ya ga Salman,sai dai a bashi Miemie, haka
    zai gaji har ya tafi,sai dai tai ta ganin text na ban
    hakuri,gobe ma zuciya zai dawo. ***************
    *************** Rayuwa irin ta kunci kam sun
    ganta a wata hudu da ta gabata. Salma ta
    saduda sosai akan Ja'afar,dan har yanzu shi
    yana kan bakar shi. Sam in ka ga Salma ta
    sauya,ta dawo shiru shiru sosai,kullum zaka
    same ta a daki,koh ta dukufa tunani, koh tana
    k'allon Miemie tana hawaye. "Salma... Gefe tayi
    da sauri da kanta tana goge hawayen jin
    maganar Mama akanta. Dole yau ta kawo
    karshen matsalar nan. Zama tayi a gefen gadon
    tana kare mata kallo. "Rayuwa fa kullum sauyi
    take Salma,amma banda taku, ni dai ban ta6a cin
    karo da kulafucin D'a namiji irin naki ba, wata
    hudu ba kwana hudu bane Salma.. "Lokaci yayi
    da za ki cigaba da rayuwarki ki manta da kashin
    Ja'afar.. Ki d'auka Rabon Miemie kawai ya had'a
    ku,ki manta da rayuwar da,dan ta wuce,ki
    fuskanci zahiri a rayuwar gaba Salma.. Fad'a
    Mama ke ta mata tana kuka, taya zata mance
    Ja'afar?.. Taya zata mance zaman su?..Soyayyar
    ta da Ja'afar had'i ne na Allah a ganinta ba wai
    wani rabon Miemie ba... In har Ja'afar na bata
    haushi bai wuce yadda ya dankara mata saki ba
    ba ji ba gani,amma bacin hakan,tabbas bata da
    sama da Ja'afar a zuciyarta kawo iyanzu..
    "Nasan da kin gama iddar ki sarai... Da sauri ta
    k'allo Mama da t'sananin mamaki, kai Maman ta
    kad'a mata. "Tunda ki ka zo gidan nan ina
    fuskance dake Salma,kin gama iddah tun wata
    uku da suka wuce. Kasa tai da kai tana goge
    hawaye,tasan Mama gaskiya ta fad'a, dan
    shayarwa bai hanata period ba.. "Nasan ma
    hakan ne Salma,yanzu abinda nake so dake
    shine, "Dole ki fara fita,dan saki ba takaba bace,
    bazai yu kiyi ta zama a gida ba kamar matar
    kulle,tun yanzu zaki fara fuskantar cigaban
    rayuwa,bana son musu koh taurin kai Salma a
    zuwan nan daga gunki, dole komai nace kiyi kiyi,
    kina jina koh?. Shikenan kuma,ta faru ta kare,wai
    an ma mai dami daya sata.. Shikenan ta shiga
    sahu,yanzu sai jiran bazawari.. Kuka ta sa mai
    sauti,yi take ba kakkautawa,har ta kular da
    Mama ta bar lallashi ta hau sababi. Dole kam in
    dai ta yadda da K'ADDARA ta maida komai ba
    komai bane.. Dole ta daina yaudarar
    zuciyarta,tana biya zancen Ja'afar a kullum akan
    tashi ce shi kad'ai.. Hannu tasa ta share
    hawayenta,kan ta g'yara zama. "Na shirya bin
    umarnin ki Mama matukar bai sa6a shari'a ba..
    Baki Maman ta washe, "Koh ke fa,yanzu naji
    batu,ko ke fa Salma. Kasa tai da kai tana
    murmushi, sosai taga farin cikin Mama.
    Washegari da dare bayan Abba ya dawo taje
    gunshi suna zaune da Mama,yai mamakin
    sauyawarta faradd daya,shima sai murmushi
    yake mata. "Abba.. Zama ya g'yara da murmushi
    ya amsa. "Abba makaranta nake son shiga
    dama... Da sauri Mama ta kallota, ji zata kwafsa
    musu kuma,wai makaranta? Baki ya washe dan
    murna. "Toh Salma,kinyi tunani mai k'yau, Allah
    yasa a shiga a sa'a. Kai kasa tace "Amin Abba...
    "Anjima ina son zan k'waso akwatina na a gidan
    Abban Miemie koh da y'ar makota ne.. Kai ya
    kad'a mata "A'a,ki bari zan ma shi Ja'afar din
    magana zai kawo miki har gida. Sosai sukai fira
    Mama na jinsu bata ce kala ba,tana shiga d'aki
    Maman ta bita. "Ya zaki min haka Salma?.. Wace
    makaranta kuma ana zaune lafiya?.. Shiru tai sai
    da ta gama kan tace ba abinda karatunta zai
    tsare mata,tai hakuri tasan zai mantar ta wasu
    abubuwan. Ba dan taso ba ta yarda. Ta gama da
    Mama, saura Ja'afar. By Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:25 AM - Queen Safiyyert馃憫: A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    33_Washegari Abba da kanshi ya samu Jafar din
    a shago,duk da yai jim,daga baya ya tuna da
    wannan ne damarshi na ganin Salma a yau dan
    tuna mata da alkawarin shi. Da yamma k'wa
    yasa Garba ya k'waso mata akwatinan ta da
    sauran sabbin kayanta marar dinki. Da sallama
    ya shigo gidan, ya k'wa taka babbar sa'a Mama
    bata nan. T'saye yayi ganin Salman t'saye a
    gaban famfo Miemie na mata kukan kunu tana
    dauraye murfin feedern. "Sam baki da jimirin
    yunwa Miemie,kimin hakuri yanzun zan... Itama
    shirun tai dan jin sallamarshi. Da dan rarrafe da
    tafiyar da batayi kwari ba ta nufi gun Abban da
    murna. Ganin Miemien ne yasa shi dawo da
    hankalinshi kanta,sama yai da ita kamar kullum
    suna dariya. A hankali ta rufe idonta tanajin
    zuciyarta na bugawa da sauri,kusan wata 2
    rabonta da ta sashi a idonta,jin takunshi na
    kusanto ta yasa ta juya da sauri tare da had'iye
    hawayenta. Ya sauya mata,duk ba g'yara, har
    wata kasumba ya had'a ta dole ta rashin g'yara
    fuska. Da t'sananin murnar ganinta ya karaso sai
    washe baki yake,da sauri tai baya ganin abinda
    yake shirin yi tai gun taburma ta d'akko,sai ya
    bita da kallo baki sake, tabbas Salma batai
    kewarshi kamar yadda ya mato a kewarta ba..
    Koh irin d'aukin nan na ganinshi t'sawan lokaci
    haka bata yi. Dan dukan da Miemie take mishi ne
    yasa ya kallo ta,da hannu take nuna mishi kan
    feedern dake hannun Salman. Kan taburmar ya
    nufa tare da zama,so yake sai ya fassara
    yanayin Salman,shi yasa yake ta k'allonta.
    Feedern ta mika wa Miemie tana dan satar
    kallonshi kan ta kau da kai tace "Ina wuni.. Shiru
    yai mata,sai ta dan kalloshi cikin ido,shima ita
    yake kallo,bazata iya kallon kwayar idonshi
    ba,zata chaza mata matsala,da sauri ta kara
    dauke kai tana maimaita gaisuwar. "Mey yasa
    kwana biyu ba k'ya d'aukan kira na Salma?.. Ba
    k'ya ban amsa koh na miki text?.. Gefe ta kara yi
    da kanta tana kallon wani waje, kan tace "Ban
    gani ba ne.. Da mamaki yake kallon yadda tai
    maganar cikin nuna ko'in kula. "Salma kin daina
    so na yanzu koh?.. Yadda yai maganar yasa jin
    wani iri da dan tausayinshi,da jihadi ta juyo ido
    cike da kwalla. "Ya Ja'afar, ya dace mu fuskanci
    zahiri fa yanzu,mu daina yaudarar kan mu dan
    komai ya afku..Dole nai aure ka sani,ban maka
    alkawarin zama ba aure ba,bazan maka alkawarin
    kin kula wani ba.. Yanzu haka karatu zan
    koma,ka d'auka rayuwar da ta shud'e a mafarki
    muka yi ta, yanzu mun farka... Dole akwai cigaba
    a rayuwa.. Kai hakuri, amma bani da alaka da
    daukan kiran ka yanzu,ka manta Salma dan
    Allah,mu fuskanci rayuwar gaba.. Kai ta kautar
    tana goge hawaye, shi kam k'allonta kawai yake
    ba koh kiftawa. "Ke nan kina nufin son da nake
    miki karya ne?... Soyayyar mu hasashe ce
    Salma?.. Zaman mu da rayuwar auren mu wasa
    ne?.. Kina nufin Miemie ma mafarki ce?... Da
    fusata yake tambayarta,kai kawai take girgiza
    mishi tana hawaye. "Ba haka nake nufi ba.. "Toh
    mey ki ke nufi?.. Shiru tai tana cigaba da kukan
    ta,sai ya kada kai cikin takaici. "Salma kin d'aina
    so na kam.. Girgiza mishi kai tai "Ina sonka Ya
    Ja'afar, har karshen rayuwata.. Abu daya nake
    son ka gane,yanzu komai ya sauya,alakar Mimi
    ce kawai ta rike mu... Ka cire son zuciya aciki,
    dan bazan iya haramtawa abinda Allah ya
    halasta min ba.. "Assalam Alaikum, wannan
    akwatunan fa a zau... Tsaye tai ba tare da
    karasawa ba, kai kasa ta amsawa Mama
    sallama,ciki Maman ta karaso,ya gaida ta kai
    kasa,duk shiru sukai ba mai magana, sai muzurai
    Mama take ma Salman kan ta shiga daga ciki.
    Jiki a sanyaye ta tashi ta shiga ciki,a hankali ta
    sa kanta a kan katifa tana hawaye. Ba dan yaso
    ba ya tashi yai fita,tare da shigo mata da
    akwatunan ta. Har zauren Mama ta bishi ta sa
    sakata tana sababi kan tai gun Salman. "Wai ke
    baki da hankali ne Salma?.. Meye had'inki da
    wannan da har zai shigo cikin gida ki bashi
    taburma, har ki zauna a gabanshi kina wannan
    shashancin cin?.. Mey fa rabawa(K'ADDARA) ta
    raba ku har abada. Shiru tayi har Maman ta
    gama tana ta kok'arin shanye kukanta, ta sani da
    koh tayi bayani Mama bazata gane inda ta dosa
    ba. "Kiyi hakuri bazan sake ba. Kai ta k'ada tuni
    har tai laushi. "Ina kuje miki yaudara irin ta D'a
    namiji ne Salma,gaba in kina mishi haka sai ai
    abin kunya. Shiru tai tanajin wa'azin Maman
    kawai. G'yale ne kusan kala 5 had'add'u,tana
    washe baki ta fito dasu daga leda. "Ki zabi na
    za6a ki darje,dan zawarcin ki sai yafi y'an
    matanci a komai Salma, gobe kayan k'walliya
    zasu zo dan na bawa Hajiya Jidda kud'in kayan
    g'yaran jiki,ga wata yayi nisa da komai kin samu
    akan lokaci.. InshaAllah sai mun cike gurbin da
    muka rasa.. Ni da zakiji shawarata ma da an
    yaye Miemie a satin nan a mikata ga gidan su
    chan ya karata... Da sauri ta dago tana kallon
    Mama, Kat'seta tai da fadin "Eh man,bashi yake
    ikirarin yana kawo shi ba?.. Toh zamu mayar
    mishi da abarshi kawai. Kai ta hau girgiza ma
    Maman,Allah yaga ba mai rabata da Miemie sai
    aure. "Mama Miemie fa karama ce,kawai tai
    saurin tashi ne,koh fa wata tara bata cika ba..
    Dan Allah kiyi hakuri,dan ba abinda zata t'sare
    min koh a makaranta. Harara ta aika mata, "Kina
    nufin da ita zakina fita?.. Kallonta take ta rasa
    amsar ba Maman. "Toh da sake wallahi, ba
    yadda za ai ina tufka kina bin bayana da
    warwara.. Zawarci da goyo?.. Toh da sake,dan
    ba mai gani ya kulaki alhalin kina sa6e da y'a.
    "Aikina fitarshi ta naga dama ce,in ma kince
    baza'a mayarta ba ni zan na miki renon,aje a
    dawo lafiya. Shiru tai tana jinta kawai. Washegari
    sai ga kayan k'walliya jibgi,su mascara, eye
    shadows,su sabulun g'yaran fata harda su man
    gashi,ga haddun man gyaran jiki,lalle Mama da
    gaske take. Shi kam tunda ya koma da yazo
    k'wanciya yake tuna dazu,lalle in Salma tasan
    wata toh bata san wata ba. Tazo k'wanciya taji
    karan wayanta,agogo ta duba, tasan ba mai mata
    haka sai mutum daya. Badan taso ba ta d'auka,
    sai dan jin dame yazo. "Naji kije makarantar,
    amma bisa sharad'i uku.. Baki ta bud'e cike da
    mamaki,wai koh ya manta bata karkashin ikon
    shi ne yanzun? Dan dai taji sharad'in tace tana ji.
    "Good. "Na daya kafarki toh kafar Miemie duk
    inda zaki shiga. "Na biyu ba zancen yaye sai
    Miemie ta cika shekara biyu kamin kiyi komai.
    "Na uku,fitar ki sai da nikaf da hijab,sannan ni
    zan sama miki mai kai ki a Napep ya d'akko ki in
    kin gama, dan ba ko wanne kato zai na d.. "Ka
    ga malam,ka bari ka fad'awa Miemie wannan
    dokar taka ba wai ni da nake Salma ba... Dan ba
    y'ar ka bace ni,ni nake da damar t'sara rayuwata
    yanzu ba kai ba. "Abu daya nasan na yarda zan
    iya shi,shima dan hakkin ka ne dole,shine yaye
    Miemie,zanyi yadda kace, sauran kuwa ba
    huruminka bane... Wayar yabi da kallo baki sake
    jin ta kashe kit.. Lalle Salma ba ta so zaman
    lafiya ba a garin nan, amma zata jidi mamakin
    shi. Dan shi tai mishi daidai ma da zata tafi
    makaranta. Tun daga ranar ya daina kiranta a
    ganinshi zata damu ta bashi hakuri ayi yadda
    yaso,sai dai ta daure ita. Ana haka ranar Abba
    yace ya batun makarantar da yace zai koma?..
    Kanshi t'saye yace ya ma Abban ai ya fasa. Nan
    ya bud'e mishi wuta kan bai isa ba,duk haukar da
    yake ranar ya samu labari gun Mama,dan har
    gida tace ai mishi t'sakani da Salma,sai dai yazo
    za'a bashi Miemie in dan ita ne. Sosai yaji
    haushi,yasan aikin Salma ne..shi yasa ya d'auke
    mata wuta,sai dai ya tura k'annenshi su dakko
    mishi Mimi
    Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Aug 4
    Feenat Ja'afar Novel's
    Su Salma an samu gurbi a school of hygiene,da
    shawarar baba ta cike ba Polly ba. Ranar da ta
    fara fita da personal zata kai takaddun ta. Ba
    yadda zaka ga Salma ka gane itace da lokacin
    tana budurwa, yanzu Salma ta daban ce,ta gaban
    goshin Mama, dan ta dage dole sai tayi kara'i da
    zawarci. Kwanar su Ja'afar ta shawo,tasan
    yanzu haka yana makaranta dan sha d'aya na
    safe. Sosai tai k'yau cikin doguwar riga ruwan
    kwai mai duwatsu,da g'yale karami ta nad'a
    fari,ta ritaya jaka karama mai (chain),ba wata
    k'walliya tayi ba ta azo aga,dan wannan ma
    Mama na t'saye tayi ta,ta kuma rantse ita da
    hijabi sai a sallah. Zai wuya kace ta ta6a aure
    har da rabon Miemie, dan yanzu ne take
    shekarunta na (22) a duniya. Kanta kasa take
    tafiyarta cikin nut'suwa, sai dai ji take duk ta
    tsargu,tamkar Ja'afar na kofar gida yana
    kallonta. Dak'yar ta kai kanta bakin kwalta tana
    sauke numfashi, ashe feeling take... "Kin k'yauta
    Salma kenan?... A razane ta juyo jin mai
    maganar.. Rai had'e yake kallonta tamkar bai
    ta6a dariya ba. Duk da ta tsorata da ganin
    yanayin da yake amma ta cije itama ta ci kunu.
    "Da nai mey fa? Rai 6ace yace "Ina Miemie?..
    Kai ta k'autar gefe,kan tace "Gida".. A fad'a
    fad'a yace "Wato bakiji abinda nace ba koh?..
    Kalli shigar ki,kamar wacce zata party,sam baza
    mu shirya dake ba in.. "Tafiya ne?.. Wani mai
    keke napep ya tambaya, kallo irin na baka isa ba
    tamai, kamin tace ma mey keken "Eh tafiya ne.
    Tana kokarin shiga tace "ba ruwanka da shiga
    ta,cos I know what i'm doing.. And ni ba y'arka
    bace, na fad'a ma ka rabu dani. Sam taki k'allon
    fuskarshi bare ta sare gun taka mishi burki. Baki
    sake yake binta da k'allo har mai napep yaja
    kamin ya samu k'warin ya tanka. By Feenat
    Ja'afar.
    9/29/16, 9:28 AM - Queen Safiyyert馃憫: [8/7, 11:03 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    34_Jingina tai a jikin Napep din tana sauke ajiyar
    zuciya.
    "Kai hakuri Ya Ja'afar, ya zama dole na koya ma
    nisa dani,kai hakuri,ina sonka wallahi..
    "Hajiya magana ne?..
    Kai ta dago jin mai Napep na tambaya, ashe
    maganarta ta fito fili.
    Ta gama komai Monday zata fara zuwa,kwarai
    taso ta yaye Miemie sai dai ba hali,dole tabi
    yadda uban y'ar ya t'sara.
    Shikam Ja'afar tun daga wannan ranar kullum
    zata makaranta sai yai mata maganar wani
    abu,koh yace k'walliya tayi yawa, koh yace
    uniform ya d'ame ta.
    Wani sa'in har ta wuce tana dariyar zariya irin ta
    Ja'afar, tabbas gani take ya zare.
    Shima kamar yadda Abba yace haka dole ya fara
    _processing_ dan tafiya masters a B.U.K,sai dai
    fur Abba yace garin zai bari,a Zaria zai yi,kar ya
    damu an ma kusa shirya masa komai ba koh
    kwandalar sa.
    Tamkar ya aza hannu aka ya kwala ihu yake ji
    ranar,yana nan ma ya ya k'are da Salma bare ya
    mata nisa?..
    Tafe suke ita da wata y'ar makarantar su da
    tazo zata rakata bakin kwalta, ta gama shirinta
    kenan zata gidan Aunty A'i sai fasawa tayi.
    Tai kyau,fatar sai shining take taji mai da
    sabulun Mama.
    "Allah ba wanda zai ce kin haifi Miemie sis
    Salma,kin ganki kuwa?..
    Murmushi tai ma kawar tata lokacin da take
    t'sayar mata da Napep.
    "Haka dai kuke cewa kullum.. Murmushi tai mata
    sukai sallama.
    Tana kula da wani mai mota yana ta kallonta ya
    t'saya siyan Apple.
    Kokarin tsallakawa yake ganin zata wuce da
    sauri,kai ta kada dan sarai tasan yau ma za'a
    tafka dirama irinta ranar chan da Ja'afar, dan
    tana kallon yadda yake maka mata harara a kofar
    gidan su suna zaune shi da Garba da wani,tasan
    darajar kawarta taci da yanzu ya taso bambami
    dan tasa g'yale a kafad'a, kai ta girgiza dan
    yanzu abin dariya yake bata ma...
    "Assalam Alaikum.. Waiga wa tayi jin an mata
    sallama.
    Da dan sakin fuska ta amsa tana mai cigaba da
    tafiya a nut'se.
    "Gunki nazo fa y'an mata dan Allah.
    Kai ta daga aikwa idon Ja'afar kyar kanta.
    Da murmushi ta juya badan taso ba sai dan
    yakice dan gudanta, duk da tasan baza a wanye
    lafiya ba.
    Tuni dad'i ya kama saurayin dan da har ya fara
    d'ari-d'arin mata magana,sai ya ga kamar matar
    manya ce.
    "In bazaki damu ba dan Allah ki ban numbern
    ki,wannan ne gani na biyu da na miki a layin nan
    yanzu ina sauri zan kira ki...
    Ta gefen ido ta sato k'allon Ja'afar ai kwa a
    suk'wane yake zuwa gun nasu.
    Da sauri ta karbi wayar mutumin da zummar sa
    mishi ya iso.
    Su dai su Garba ido ne nasu,dan abin Ja'afar ya
    daina bashi dariya yanzu tsoro yake bashi.
    "Bashi wayarshi ya kauce tun kan na
    dagargazata a gun nan..
    Banza tai dashi tana cigaba da latsa wayar
    karya,bata aune ba taji ya warce da karfi.
    "Karbi wayarka ka bar layin nan Malam, koh kaga
    tayi sa'ar tsayuwar ka?..
    Baki sake saurayi yake kallonshi,shi a tunanin shi
    koh yayanta ne ma,dan shima haka yake ma
    samarin k'annenshi baraza,dan haka bakin shi
    alaikum ya kar6a yana kallon Salman.
    Cike da tsiwa ta kallo Ja'afar din,
    "Malam wai ina ruwanka da samari na ne
    eyeee?..
    "Kimin shiru tukunna, kema zan dawo kanki ne ai.
    Da hannu ya nuna ma saurayin hanya halamar ya
    ware,ba daban yaga Ja'afar din ba na wasa bane
    ba da ba yadda za ai ya bar wannan
    sankaceciyar budurwar.
    Da sauri ganin zai tafi tace "Malam ina zaka
    ne?.. Kai ya kad'a mata yana murmushi kan ya
    kara gaba.
    A fusace ta nuno shi da hannunta
    "Wallahi Ya Ja'afar na gaji da wannan abin fa,dan
    wallahi na kusa kai karar ka gun Abba ya mana
    t'sakani,mey ruwanka dani wai?...
    Shiru tai tare da matsawa da sauri ganin ya mika
    hannu bayan gyalen ta.
    "Wai kai lafiya ka ke?.. Harara ya sau mata kan
    yace
    "Tun muna sheda juna ki daina sarar nan ta
    sauke g'yale a kafad'a Allah...
    "Bazan daina ba din, na fad'a ma bani ba kai,
    tunda kai har yanzu bakasan Annabi ya faku ba...
    Shiru tai ganin Garba.
    "Haba Salma,haba,a titi fa ku ke?.. Tunda kinsan
    halin kayanki sai ki gaba ki barshi ya karata, dan
    Allah ki daina biye mishi.
    Harara ya sakar ma Garban, "ina ruwan ka toh
    kai ma,kowa dai yasan da matata nake t'saye ba
    kowa ba..
    "Mtsww... T'saki taja rai 6ace, duk suka kallota..
    "Wallahi you are sick..
    "Ni matarka ce, amma fa a da, kai istigfari ma
    tun wuri,dan wallahi za kayi sa6o...
    "Kimin shiru fa Malama..dan kwanciyar hankalinki
    wallahi kibi abinda na ce kiyi,period..
    Shiru tai tana kallonshi,karfin hali sai gun
    Jafar,tabbas sai tayi da gasken gaske,dan
    abinshi gaba yske,shima Garban k'allonshin
    yake,abu dai kamar wasa yake gani yanzu zai
    zama babba.
    By
    Feenat Ja'afar.
    [8/7, 11:07 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    35_Drama sosai sukai kan ta wuce gida rai 6ace
    duk rai a dagule, dabarar ta ta kare kuma a akan
    Ja'afar, duk hanyar da zai zuciya ya daina kulata
    tabi ba nasara,tamkar ma zigi take mishi.
    "Mtsww... Taja t'saki,Tabbas so so ne,amma na
    Ja'afar son kai ne,dan shi yaja komai..
    "Ke kuma ke da wa kike t'saki haka?..
    Ba tare da ta dago ba tace "Ja'afar man.. Ya
    hanani sakat a unguwar n...
    Da sauri ta datse harshenta dan jin Mama fa ke
    tambaya,
    "Au har yau yana nan yana bibiyar taki koh?...
    Kai ta girgiza da sauri, zarar bunu..
    "A'a, ni nasan hanyar maganinshi,ki ban nan da
    gobe.
    Da sauri tace
    "A'a Mama ba komai bane fa,kiyi hakuri zai
    daina... Shiru tai ganin harar da take aiko mata.
    Tun daga ranar Mama ta zama y'ar rakiyar
    Salma hanya,sai ta tabbatar ta hau abin hawa
    zuwa makaranta zata juyo tana aika mishi
    harara,da tai na sati sai ya bar tare hanya kuma
    ya dawo waya.
    Ana haka shima admission nashi ya fito
    shima,tuni ya shiga kunci,dan yasan ya kusa yin
    nisa da Salma,hakan yana nufin komai zai iya
    faruwa.
    Ranar da yamma ana washegarin zai tafi yazo
    mata sallama duk da sunyi fad'a.
    Taimakonshi daya Mama bata nan ranar ma,dan
    yana ga ita kad'ai zata iya tsaida shi a yima
    Salma kashedi.
    Shigarshi zauren kenan sukai kicibis zata
    fito,harara ya sakar mata kan yaja ya t'saya.
    Fita take shirin yi ya ruko gyalenta da sauri har
    yana zamewa,don haka a fusace ta juyo da niyar
    balbaleshi ya marairaice mata fuska.
    "Saken g'yale toh.. Murmushi yake yaki saka, ''ka
    saken gyale koh na fuce... Da sauri ya cika yana
    tare kofar fitar.
    "Maganar fahimta nake so muyi dake,dan Allah ki
    t'saya..
    Hannu ta hard'e a kirji ta k'alleshi,itama zata so
    su fahimci juna.
    "Ina wuni toh,tunda har gaisuwa kin soke dani.
    Da kalar tausayi ya kara yana sukui da kai har
    taso yin dariya kamin ta gaishe shi.
    "Ina Miemie?.
    "Da Mama suka fita,kayi kai maganarka kan su
    dawo fa.
    Tsayuwa ya gyara tukun ya kira sunanta, rai sake
    ta amsa,fatan ta yasa zancen azziki zai mata ba
    wai shirme ba.
    "Salma".. A karo na biyu ya kara kiranta, bai jira
    amsarta ba ya cigaba,
    "Gobe zanje Zaria kan batun makaranta da zan
    fara, kima Allah Salma ki yi kamar ina nan dan
    Allah,banda kula tsagerun samarin nan wanda
    har yau basu mallaki hankalin kansu ba dan
    Allah.
    "In ma aure naso kiyi ina ga ni ya dace na baki
    mijin aura,bare a agendar mu bamuyi haka dake
    ba...
    T'sam tai tana kallonshi da halamun ya zare tana
    murmushi, amma zata bishi a haka a wanye
    lafiya.
    "Toh naji,zan kuma kiyaye,happy?..
    Kai ya kad'a da murmushi, "yauwa koh ke fa,dan
    Allah Salma ki riken alkawari nan..
    Kai ta kad'a tana taji ai.. Da haka suka rabu ya
    bata kayan zakin Miemie, murna fal ranshi suka
    rabu ranar.
    K'warai ta samu sakewa sosai bayan tafiyar
    shi,tuni ta kara bud'e shafin zawarci sabo,duk da
    kasan ranta tausayinshi take ji sosai.
    A wata daya tai samari biyu irin son Mama, barin
    Alhaji Usman Dan chanji.
    Kud'i sosai yake kar mata kamar ba gobe,
    albarka kwa kullum samunta take gun
    Mama,yace shi ba yaro bane,dan haka yana so ai
    auren cikin k'ank'anin lokaci.
    Ya sanar mata yana da mata daya da yara biyu
    kachal,aurenshi uku,sun rabu da biyu sai Hajiya
    ta k'arfen.
    Tunda suka rabu tazo gida tana tuna abu uku,
    tabbas a yanzu bata da ra'ayin auren mey
    mata,dan taga aya akan Bintu.
    Sannan bata son mutum mai irin kud'in Alhaji
    Usman sam a rayuwarta.
    Gwara ma Kamal dan shi matashi ne kamar su
    Ja'afar, kuma yafi kwanta mata a rai,gashi da
    saukin hali da saukin kud'i.
    "Oh ni y'an nan,ashe arziki ke binki Salma a
    rayuwa?..
    K'allon Maman take yadda take daga abubuwan
    da Alhaji ya bata,ita dey nata ido.
    "Bana jin koh lokacin y'an matancinku kun ta6a
    had'uwa da irin wannan, babbar harka ai tayi y'an
    nan...
    "Mama ni fa mutumin nan bai kwanta min ba
    sam Allah,gashi har ya fara maganar aure tun
    yanzu,ga yana da mata fa,ga ni sam irin kud'in
    nan baya...
    Baki sake Mama ke k'allonta,tuni ta tsayarta
    cikin fad'a.
    "Rufe baki ni sauraniyar y'an iya t'sari, ashe har
    yau kina nan da halin nan Salma? Arziki na binki
    kina zura da gudu?..
    "Ina ruwanki da matarshi?.. Koh a kanta zaki
    zauna?..
    Kai ta girgiza zatai magana ta dakatar ta.
    "Koh dai Salma hudubar yaron chan tai tasiri
    akanki?..
    Kai ta kad'a,
    "Allah Mama ba haka bane,ni ina tsoron kishiya
    ne,kinaji fa wai aurenshi uku suna rabuwa sai ita
    ke zama...
    "Sai mey toh?.. Kar ki bada mata mana Salma?..
    Baki sake take k'allon Maman,kamar ba ita ke
    fad'in ba mai zama da kishiya ba a yaranta tunda
    itama bata zauna ba,wace daga ce ba'aci ba
    lokacin auren Bintu da Ja'afar amma yanzu kud'i
    ya warware Mama?... Kat'seta tai,
    "Saboda haka komai yace ki ce toh, in ma ita ke
    fidda su toh ke zama daram,dan wannan ba
    gidan fita bane in an shiga...
    Hawaye ke zubar mata yayin da tazo k'wanciya
    tana tariyo zancen Mama, dole in dai tana son
    faranta mata wai ta ba wa Alhaji dama.
    Waya ta d'auka jin shigowar text message,tasan
    na Ja'afar ne.
    _"Salmatee,remember, a heart dat truly loves
    never loses hope..but always believes in d
    promise of love,no matter how long d time and
    how far d distance,at d right time,love will fine a
    way".._ ki rike alkawarin ki,love you..
    *Ja'afar*
    Kukanta ne ya karu sosai bayan ta gama
    karantawa, tabbas in ta cigaba da sauraran
    kalaman Ja'afar zasu sa ta karaya har ya ci
    galaba akanta..
    "Bani da kamar ka har kullum Ya Ja'afar, sonka
    gareni ba mai misaltuwa bane,amma kai kaja
    mana koma meye...
    Fuska ta goge sakamakon jin tahowar Mama da
    Miemie na kuka.
    Washegari kanta t'saye ta bawa Alhaji damar ya
    turo magabatanshi kawai koh ta huta da
    dawainiya da son Ja'afar.
    Sabon sim ta siya tasa a sabon wayar Alhaji da
    ya bata,a haka suka raka wata kusan biyu, duk
    da tai kewar text da kiran Ja'afar din.
    Shikam yana chan hankali tashe na rashin samun
    wayar Salma, ga Abba ya sanarshi kar ya sake
    ya dawo sai an nemeshi a makaranta,
    Duk da an sanarshi ana kawo Miemie gidansu ta
    yini.
    A jikinshi yaji abu na faruwa,duk sai yaji bai da
    nut'suwa sai ya je gida dan tabbatar da
    zarginshi.
    ***
    Tunda daga d'anno kanshi layin su Salman ya ja
    ya t'saya. T'saye take da dan murmushi a
    fuskarta, sanye cikin favorite dinshi riga da skirt
    na atamfa purple, tai kyau matuka gyalen nan a
    kafada,daga inda yake zai iya gano bakin
    gashinta a tufke ta chan kasan dankwalinta,
    tasha ado tamkar zata party.
    Wani abu ne yazo dai dai makogwaronshi ya
    tsaya,kishi...
    Bai san ya isa gun ba sai da yaji ana "lafiya?..
    Kallo shi yayi, duk sai yaji yau baida ma k'warin
    g'wiwar fad'a,Salman ya kalla,da sauri ta kawar
    da fuskarta gefe ta had'e rai.
    Sai ya dawo kan Alhajin,tsaf sai ya haifi
    Salma,sai t'sabar kud'i da jindadi da suka 6oye
    shekarunshi.
    Kallonshi yake tun daga sama har zuwa kafa, so
    yake ya gano ta inda ya fishi har Salma ke mishi
    murmushi haka. A zuciya yace
    "Babu... Sai dai kud'i kawai da sa kaya masu
    t'sada.
    "Kai fa,daga ina ba koh sallama?..
    Cike da haushi ya kallota, "baki sanarshi ko ni
    waye ba ne?.. Kan Alhaji ya dawo,ba shakku
    yace "matata ce ita,zaifi mana k'yau in ka daina
    zuwa gunta Alhaji.
    Murmushi yayi Alhajin,kan ya kallo Salman, "sai
    kinji ni kawai.. A takaice ya k'alli Ja'afar din,ba
    sai an fada mishi waye ba,halamu ya nuna
    tsohon mijinta ne,har zaga wa tai ta rufe mishi
    tana daga mishi hannu d'auke da murmushi, har
    ya kule tana daga mishi hannu kan ta d'au
    kayanta koh ta kanshi bata tai hanyar gida,da
    zafin nama.
    "Wato abinda ki ke kenan tun bayan tafiya ta
    shine yasa ki ka kashe waya? Salma mey yasa
    kike son ki 6ata min rai wai?.. Jibi fa shigar ki,ji
    gashi a waje,wace iriyar rayuwa ki ka za6a
    mana?
    Cike da fada tace
    "Wace iriyar ka za6arwa kanka dai Ja'afar.. Ya
    zaka zo kana fad'an wata iriyar magana mijin da
    zan aura?.. Karan nan bazan dau abinnan naka
    ba wallahi, aure zamuyi dashi nan da wata biyu...
    Sai kayi abinda zaka yi.
    By
    Feenat Ja'afar.
    [8/7, 11:07 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    36_Kan yai k'wak'waran mot'si ta shiga gida tare
    taru kofa harda sa sakata.
    Jiginna tai hawaye na neman zubo mata,daga
    yar bular dake jikin kofar ta leka waje,kofar gidan
    yake kallo jiki a sanyaye kamar yasa kuka,juyawa
    tayi hawayen dake makale mata ya zubo,dak'yar
    ta seta kanta ta shiga ciki rai cike da tausayin
    Ja'afar.
    Kusan kullum zai zo ba zuciya dan bata baki
    akan Alhaji tana mishi wulakanci,shi kam Alhajin
    har dariya yake bashi wani sa'in, dan baijin da
    abinda zai iya rabashi da Salma a dai dai lokacin
    nan,sai dai jin saki uku ne kawai sai ya bar jin
    komai,iyaka ma yai ta tusa ma Ja'afar din bakin
    ciki in ya gansu da kalamai ma Salman.
    Biki ya karato ga makaranta,amma haka duk
    week end daga Zaria zai zo kan batun Salma ta
    janye zancen bikin nan.
    Duk ya fita a hayyacinshi duk akan auren Salma.
    Da halamu ya fara hankalin daina zuwa gun
    Alhajin,sai dai in yazo ya tsaya chan gefe sai
    tazo shiga ya tare ta da magiya.
    Yau saura k'wana biyu biki, sai gashi shi da
    Garba,dawowarsu daga gidan g'yaran jiki kenan
    ita da Ummi.
    Turus ta ja ta t'saya ganin Ummi ta wuce ita ya
    tare mata hanya.
    "Ka ga yau bani da lokacin jin wannan
    mahaukatan zantukan naka,jibi iyanzu na d'aura
    aure, ya kamata kasan inda dare ya maka,
    sabuwar rayuwa zan fara,saboda haka kai yanzu
    ya rage ma,danni yanzu baka gabana...
    Kai ya kad'a mata,
    "Karan nan bazan hanaki aure ba Salma,sai dai
    ba da Alhaji ba.
    Baki sake take kallonshi, Garba ya nuna,
    "Garba zaki aura Salma,kimin wannan alfarmar.
    Kai ta dauke daga kallonshi ta k'alli Garban
    wanda shima ya cika da al'ajabin kan maganar
    Ja'afar.
    Sai ta girgiza kai da murmushin takaici.
    "Tanan kuma ka bullo min?.. Auren kisan wuta
    Ja'afar? Lalle kayi nisa ba zakaji kira ba.
    Bayab hannunta tasa tana goge hawayen idonta.
    "Wai ka zata ni din auren kisan wuta zanyi da
    wanda zan aura?.. Kai ta kara kadawa,
    "Kai kuskure toh,dan ni aure zanyi na tsakani da
    Allah,ba wai nayi na fito ba Ja'afar..
    "A'a Salma,ba haka ne nufi na ba.. Da muryar
    kuka ta tareshi,
    "Hakane man,haka kake nufi,wato ka kawo min
    abokin ka na aura bayan wani lokaci ya sake ni
    sai ka halartawa kanka ni koh?..
    Baki sake duk suke k'allonta,ganin yadda hawaye
    ke zubar mata.
    "Jahilcina bai kai nan ba Ja'afar, a bazan ta6a
    abinda ka ke so ba, a gareni yanzu k'allon Yaya
    nake ma,da kuma uban yarinyar dana haifa,
    bayan haka.. Kai ta girgiza, kan tace "you mean
    nothing to me a yanzu kam..
    Jin baice komai ba yasa taci gaba.
    "Banzaci haka daga gare ka ba Garba,a ganina in
    shi ya 6ata kai mey dawo dashi kan hanya ne,
    wallahi auren t'sakani da Allah zanyi, ku sani
    kuma auren so zanyi,wanda nake fatan mutu ka
    raba ne,dan Allah,dan kaunar ka da Allah ka bar
    bibiyata,dan Allah..
    Shiru tai dan ganin shima idonshi ya taru da
    hawaye,da sauri ta shige gida tana goge
    hawaye..
    Har ta shige yana binta da ido ba magana, sai
    hawayen da ya zubo mishi shar, da sauri yasa
    hannu ya share.
    Kafad'arshi Garba ya dafa, "kaji zancenta, tai
    mana fassara baibai,ya kamata kai hakuri ka bar
    kulata in har kana wa Allahn data had'a ka dashi.
    Kai ya daga, "InshaAllah..
    ~~~~
    Taro ne iya taro,taron shedar auren Salma da
    Alhaji Usman, daga inda yake t'saye a chan nesa
    da kofar gidan yana k'allon komai har aka shafa.
    Juyawa yai da jaka biyu hannunshi tare da sanya
    bakin glass dan 6oye sirrin dake idonshi.
    Yasan yanzu kam Salma ta mishi nisa.
    "Mama taki ta bud'e dakin fa,daga ina jiyo sautin
    kukanta Allah.
    Ta window Ummi ta leka,gata k'wance ta tasa
    tsohuwar wayarta a akan fuska tana razgar kuka,
    So ba karya bane Salma.
    By
    Feenat Ja'afar.
    [8/7, 11:08 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    37_Har aka kai amarya gidanta bata bar kuka
    ba,dayawa sun zata kukan na Mama ta cire
    Miemie ne, dan basa ji koh auren farkonta tayi
    haka.
    Kowa ya wat'se sai ita kad'ai, ko'ina take kallo a
    dirare, gida ne iya gida,tun bata fita ba ta
    zaga,yau gata a gidan da ba Ja'afar, ba kuma
    Miemie,tuni ido ya cika da kwallar tuna baya.
    Anya tai ma Ja'afar adalci kuwa?.. Anya bata ci
    amanar so ba kuwa?.. Ta sani da takai Ja'afar
    bango,hakan yasa bai kara waiwayarta ba,ta
    yuwu yai zuciya... Ido ta goge da sauri jin motsin
    za'a bud'e d'akin.
    Ango ne yasha babbar bunjima da rike da leda,
    bakin nan har kusan kunne,jan mayafinta ta kara
    yi ta rufe fuska.
    "Amarya! Amarya!!.. Ba k'ya laifi wai koh kin
    kashe dan maigida koh?..
    Murmushi ta k'akalo mishi, zama yayi a gefenta
    tare da ajiye ledar a gefen bedside, bata aune ba
    taji ya yaye mata g'yale yana kallon fuskarta.
    Alwala yace ta d'auro suyi nafila,dan wai
    agareshi babbar kyauta ce ita daga Rabba.
    Sun gabatar da duk wani al'ada,sai dai har ango
    ya d'ane gado amarya tana t'saye a gaban
    madubi
    sai sininiki take,gabanta sai mugun fad'uwa yake
    tamkar wacce tai auren fari.
    Murmushi yayi da kanshi ya taso ya karaso har
    gaban madubin tare da kamo hannunta.
    "Muje ki kwanta haka dare nayi sosai..
    Kamar yarinya ya kwantar ta gefen shi yana kallo
    da murmushi.
    Salon ya sauya,tuni ta fara digar da hawaye,shi
    kadai yake kid'anshi yana rawarshi,sai dan sautin
    kukanta dake fita kad'an-kadan,wanda a gareshi
    tamkar zigi take mishi.
    Kai ta juya ta kallo Alhajin dake bacci
    hankalinshi k'wance,abu uku sun hanata bacci,na
    farko kukan zamanta ta wani ba Ja'afar ba,na
    biyu tunawa da Miemie, na uku minsharin Alhaji..
    Har gari ya waye bacci sai jefi-jefi-jefi ke
    dibanta,sam taki jinin minshari kusa da ita,tsaf
    yake hanata bacci.
    Shikam da farin ciki ya tashi irin na sabbin
    ango,ita kam da ido kawai take binshi.
    Tara sai ga yaron uwargida ya kawo abinci,da
    fara'a ya gaida ta,kanshi ta shafo kan tace ya
    sunan shi?
    "Sunana Ja'afar".... Kallonshi take da mamakin
    jin sunanshi, koh dai bataji dakyau bane?...
    Kat'seta yai da fad'in
    "K'anwata kuma Nabila,Umman mu tace sai
    anjima zamu shigo kar mu tashe ki a bacci.
    Murmushi tai mishi yace ya tafi.. "Ja'afar...
    Ido ta rint'se jin maigidan ya kira sunan,ba shiri
    ta d'au abincin tai kitchen.
    Bayan sun gama komai yace suje bangaren uwar
    gida zai magana dasu.
    Batai zatan da kishiyoyi masu kaunar kishiyar su
    ta ra6e su sama da matar Alhaji ba,sosai tai
    mata bazata,tun tana d'ari-d'ari har ta saki jiki da
    ita da yaranta, musamman Ja'afar..
    Yau Miemie ce tazo mata,sai murna take taga
    Auntyn ta.
    Duk babyn ta rame,yaye bai amsheta ba.
    ''Miemie, ga nan Abdul yazo ku tafi gun Mama
    koh?...
    Kafad'a ta make halamar taki tana neman kuka,
    "Yi hakuri gobe zanje gida mu taho koh?..
    Kuka ta saka mata baji ba gani, sai mak'e
    kafad'a take tana ita "um-um.
    Sai ta sallami Abdullahi kan gobe yazo ya d'auke
    ta, har ya jima da tafiya Miemie bata bar kuka
    ba.
    Sai um-um kawai take fad'i, suna haka Alhaji ya
    shigo,duk yai kicin-kicin da fuska, cikin fad'a-
    fad'a yace ta lallasheta man,shi baison hayaniya
    bare ta yaro...
    Baki sake take kallonshi,kaya ya ajiye ya juya ya
    fice harda dan tsakinshi,toh mey yake nufi?...
    Y'arta ta d'auka ta sa6a a baya sukai kitchen
    tana fad'in tai shiru ba inda zata toh,kan aje
    ko'ina sai ga nan Miemie harda dariya tana bata
    labarin Mama cikin gwaranci.
    Har dare ba Alhaji ba duriyarshi,abinci ma sai
    Ja'afar ya turo ya d'auka.
    Suna k'wance Miemie sai k'allonta take,gani take
    kamar guduwa zata yi ta barta.
    Kanta ta shafo tana mata murmushi,
    "Yi baccinki my Miemie, ina nan fa tare da ke
    kinji?.
    Kai ta daga mata tana k'allonta.
    "Antee...
    Kai ta dago kan tace
    "Na'am Miemie nah...
    "Abba...
    Tsam tai tana k'allon Miemien,Abba? Ta nanata a
    ranta.
    Murmushin dole ta k'akalo tana fad'in Abba yana
    nan Miemie,bata aune ba taji ta kara fad'in
    Abba...
    Hawayen da take makalewa ne suka zubo
    mata,da halama yanzu Miemie ce matsalar
    ta,dan zata dawo mata da hannun agogo baya.
    Da dabara ta d'auke hankalinta daga tunanin
    Abban ta hau lalla6ata har tai bacci.
    Photocopyn Ja'afar ce Miemie,barin yanzu data
    kara girma, tunani take koh dai Ja'afar har yanzu
    baya zuwa gida, laifinta ya shafi Miemie?
    Dan tasan sai Miemie ta kwana biyu bata ganshi
    ba take nemanshi haka.
    Tana nan har maigidan ya shigo,sai wani k'allo
    yake aikama Miemie wanda ta kasa fassara shi.
    Tun daga ranar ya zamana in dai Miemie zata
    zo,toh fa zata rasa gane kan maigidan, ta rasa
    dalili, musamman in tai la'akari da hadithn
    hausawa na Duk mai son uwa toh yaso d'iyanta.
    Ranar har ta kasa d'aurewa tai mishi magana,
    amsar da ya bata ta jima tana sata hawaye.
    Ga Miemie da kulafuci bare tace kar a sake kawo
    ta,asalima duk randa tazo fara'arta karuwa take.
    Sa6anin in tazo mata,data gane sai take d'akko
    ta duk randa bata da girki su k'wana, ranar da
    maigidan yake da ita su wuni ai rabuwar kuka
    har uwar.
    Allah yaga Miemie kadai take gani taji sanyi a
    ranta.
    Ranar suna fira a bangaren uwar gida take mata
    korafi kan halin maigidan akan Miemie.
    Murmushi tayi kamin tace
    "Sai kinyi hakuri da halin Alhaji Salma,ba tone-
    tone ba,a'a kawai dai ya kamata ki sani, Alhaji
    sam baya son yara,musamman hayaniyar
    su,hakan yasa ya d'aurawa kansa kin haihuwar
    k'arfi da yaji, nayi ta zaman takaicin halin nan na
    Alhaji har t'sawan shekara bakwai,a lokacin aka
    tada kayar baya kan sai ya kara aure tunda ni
    sun zuba ido shiru.
    "Hanna ta shigo itama ta shekara biyu shiru, ni
    dai nasan kusan kullum yakan tasa ni da Hanna
    dan shan maganin daukan ciki.
    Ana nan ranar wata kawar Hanna tazo suna
    jajanta ko dai matsalar gun mijin ce,toh a ranar
    dai asirin Alhaji ya tonu,dan kawar Hanna taga
    magani tace na hana d'aukar ciki ne.
    "Ranar muka mishi tawaye har Hanna,in takaice
    miki yace shi bai shirya haihuwa ba yanzun,anan
    sukai baram-baram da Hanna ya bata takardar
    ta.
    "Haka sauran mata biyun kowa tazo zai fad'a
    mata ra'ayinshi, da taga bazata iya ba zata fice,
    duk kuwa da tarin arzikin shi,a lokacin muna da
    shekara kusan sha uku da aure,koh mai zaiyi na
    daina shan magani, hakurina ya kare,nan na kai
    kara gun Hajiyarshi.
    "Ya saduda muka haifi Ja'afar, yace daga nan ta
    isa haka,wai incigaba shan magani,a gabanshi
    zanyi kamar nasha, daya kauce zan zubar.
    Koh shekara Ja'afar bai ba na samu cikin
    Nabila,cikin da a kullum sai naga tasku gun
    Alhaji,gar da gar zai nuna bai kaunar su,barin in
    Ja'afar na kuka,haka nai ta hakuri har na haifi
    Nabila.
    "Yanzu kam magani sai dai shi yai tasha,amma
    banda ni,kinga Nabila har ta shiga shekara ta
    biyar.
    Tsam tai tana tunani bayan kammala bata labarin
    waye Alhaji, ita ba kullen ne yafi damunta ba
    sama da rashin son haihuwa..
    A kalla yanzu ta doshi wata na biyar a gidan nan
    amma ba bayani,sam bata kawo wani abin
    ba,ashe wannan ne dalili?..
    Bazata iya tuna ranar fitarta ta karshe a gidan
    nan ba,tun kwa bayan aure sau daya taje gida sai
    dai aukin waya koh azo mata, lalle duniya labari.
    "Zaman hakuri kawai zamuyi Salma,sai adu'ar
    shirya in da rabon zai gane, amma shawarata
    gareki ki rike y'arki, dan kar kiyi sakiyar da babu
    ruwa tun kina yarinyar ki dake,shi ba ruwanshi.
    Kai ta kad'a mata,Allah sarki Ja'afar, ta tuno
    lokacin data fara period tana kukan samun ciki
    yana murna.
    Ta tuno da abinda yace mata
    "Allah sa Miemie ta samu k'ani a kusan nan...
    Ta tuna data hau bori ya hau lallashinta,
    harda alkawarin shi zai mata reno in bata shirya
    ba...
    "Ba kuka zakiyi ba Salma,muyi ta adu'a.
    Hannu takai fuskarta, ashe kuka take bata sani
    ba.
    By
    Feenat Ja'afar.
    [8/7, 11:08 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
    AURANKI*
    *漏 Feenat Ja'afar*.
    38_Ranar sakwa-sakwa ta yini tana tuna halin
    Alhaji, bai da mugun hali koh daya sai na bakin
    kulle da kin yara,bayan nan baza tace ga mugun
    halinshi ba.
    Zataso sanin wane hali Ja'afar yake ciki a
    yanzu,dan tabbas tasan ya zuciya da ita,tunda
    gashi ance koh wajen Miemie baya zuwa sai
    aike?..
    "Mey nai kenan?.. Mey nayi ni Salma?.. Mey yasa
    ban iya jure zama ba aure ba a rayuwa kamar
    yadda yaso muyi..mey yasa?..
    Juyi tayi tana hawaye,
    Kila rabon Miemie kadai take dashi a
    duniya,tasan kuma aure dai ana yinshi ne dan
    abu biyu,samun zuri'a na daga ciki, gashi ita
    anan ana son a haramta mata.
    Tabbas d'aukar y'arta shine babban mafita a
    game da yadda take jin son ta haihuwa a yanzi..
    Wayarta ce tai ruri, a hankali ta goge hawayenta
    ta tashi,
    "Billy" taga a rubuce.
    Da sauri ta saita kanta kamin ta daga.
    "Sarauniyar kirki kina gida ne?...
    Dariya ta danyi kan tace tana nan..
    "Toh ina kofar gidan ki yanzu haka.
    Da sauri ta tashi dan g'yara fuska tana fadin gata
    nan zuwa.
    Sai da ta tabbatar da ba mai gane tai kuka kamin
    ta fita kofa shigo da Billy.
    "Matar nan kinganki kuwa?.. Kin zama big
    madam da gaske fa.
    Murmushi tayi tana kar6an Ilham.
    "Kai Billy banda fa sharri..
    Dariya tai tana "ba wani sharri, koh dai mun
    karu?.. Miemie tayi k'ani?
    Shiru tayi tana murmushin iya le6e.
    Bayan sun gaisa take ce mata ai daga wajen
    Miemie suke,tai ta kukan zata zo tana jin tace
    gun Auntyn ta zata.
    Murmushi tai tai kasa da kai,Allah sarki Mimi.
    "Yau Miemie aka kaima ziyara kenan?.. Murmushi
    Billy tai kan tace "ai duk sati sau biyu Abban
    Ahmad (Garba) ke zuwa dan dubo ma Abban
    Miemie lafiyarta.
    "Shine yau muka je tare,Miemie akwai
    wayo,kusan wata shida amma bata manta
    Abbanta ba,tana jin muryarshi a waya ta fara
    murna..
    Shiru tai tana nazari,ba dai ace tun tafiyar
    Ja'afar ya zuciya ya bar garin nan ba?..
    "Ja'afar kanar wasa,kinga wata shida muke nema
    yaki waiwayo mu,sai kulafucin a dubo mishi
    gudan jininshi... "Rayuwa kenan fa,kana naka
    Allah na nashi,in kai hakuri sai ka ga na Allahn
    ne dai dai a gare ka.
    "Amma Abban Miemie namijin duniya ne,mai
    ra'ayin kanshi,tunda ya jima haka nasan alhinin
    aurenki ne bai sake shi ba.
    Shiru tai tana jinta,a hankali ta fara jin nadamar
    wulakancin data kartawa Ja'afar, Abban y'arta.
    Yau Billy ta kawo fitina,dan har ta tafi bata da
    sukuni,har sai da ta tiki kuka son ranta taji
    dad'i,yanzu burinta Miemien ta dawo gare ta.
    Koh da maigidan yazo yaga yanayinta yasan
    tasha kuka,da ya tambaye ta sai tace Miemie
    take son gani ta d'akko ta.
    Anan ya tada mata bori,har sai da tai da na sanin
    maganar Miemie.
    Ba abinda yafi kona mata rai sama da yadda
    tanaji tana gani yai mata haramiyar
    makaranta,sannan Mama ta goya mishi baya,abu
    goma da ashirin sun had'e mata.
    Adaddafe akai shekara, lokacin tuni ta jima da
    d'akko y'arta,dan bazata iya da rashinta ba a irin
    yanayin da take na son yaran nan.
    Sai sai wani abu,fur Miemie taki jinin Alhaji, ko
    abu take in zai kwan dubu yana ta bari bazata
    koh k'alleshi ba,asalima har wani kumbura baki
    take in ta ganshi,Salma tai magana tasa mata
    kuka,ga bala'in Alhaji na wai yarinya tun kan ta
    girma ta rainashi shi da gidanshi, har harara wai
    take mishi...
    A tunaninta kamar Miemie wane harara ta sani
    bare wai kumbura mishi baki?.. Amma dan a
    zauna lafiya yasa kullum take kwa6ar ta.
    A gaban kowa har su Nabila zatai wasa harda
    k'yak'yatawa, amma fa koh a nan bangaren taci
    ka'ro da Alhaji zata d'unkume,tamkar ba ita
    ba,shima kwa da harara zai bita, wani sa'in harda
    t'saki..
    By
    Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:33 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    39_"Aunty A'i na rasa yadda zanyi ne,yadda yake
    nuna t'sanar Miemie karara yafi damuna,abu
    kadan tayi sai ya hantara,t'sawa, ga kullum yai
    ta surutun wai tana hararar shi,koh fa wai turo
    mishi baki,nawa take fisabilillahi?... "Allah bansan
    haka agolanci yake sai gun Miemie. Murmushi
    tayi "bari muga,ke dai sa ido... ta kallo Miemie
    dake chan gefe tana mota da motar wasa. Da
    k'arfi Aunty A'in tace "ke Miemie... Rai had'e,
    itama ta dago tare da 6ata rai tana kumbura ma
    Aunty A'in baki. Sai Aunty A'in tai mata
    murmushi tare da mika mata hannu, "zo Miemie
    naga kitso, waya miki?.. Kafad'a ta make
    halamar bazata zo ba kenan. Cikin wasa Aunty
    A'in tace "haba Miemie ta,zo zan baki sweet fa..
    Da sauri ta taso har tana dariya ta d'are ta tana
    kiran sweet. Baki sake Salma take k'allonta,Allah
    yaga banda yau ta gani da idonta bazata yarda
    Miemie zatai haka ba. Gira ta daga ma Salman
    halamar ta gani ai. Miemien na fita tace "Ikon
    Allah Aunty A'i, ashe dai gaske ne Miemie na
    mishi hakan. Kai ta kad'a, ''amma in ya mata irin
    yadda na mata,kila koh wasa take yana mata
    ne,yaro kamar Miemie dan lallabi ne,shi yasa tun
    farko banso kin karbi yarinyar nan ba
    Salma,gudun irin matsalar nan.. Ba magiyar da
    Abbanta bai min ba shima a waya kan baison
    ya'rshi ta zama agola, Gashi in bakiyi wasa ba
    shi kenan ta gama raina miki miji. Cike da
    damuwa tace "Nikam ta rufan asiri karta kashen
    aure Allah.. Dariya Aunty A'i tayi,lalle ma
    Salma,wai karta kashe mata aure? "Haba dai ke
    kuma,sai kace wata babba,kawai dai ita tata
    salon fad'an ne haka,amma zata daina. Ajiyar
    zuciya ta sau,kan tace "Bazaki gane ba Aunty
    A'i,wallahi in Abban su Nabila zai kwana yana
    cewa Miemie bari koh kallonshi bata yi,wannan
    nasan tana dashi,shi kuma sai ya kule,baya duba
    yarintarta,sai ma ki ga ya hauni da sababi. "Toh
    ki dinga sata misali kai mishi abu haka,kina kuma
    kula d yanayinta in yana mata magana,sai kina
    sata a hanya. Har magriba suna abu
    daya,matsalar gida Alhaji har ta tafi. Washegari a
    ita ke da shi,tun wuri ta shirya Miemie ta d'auke
    duk kayan 6arna duk dan a zauna lafiya.
    Chankula chankoto take mata tana dariya,ta
    sunkuya tana mata "aci ladan gabe" tana dan
    mata duka yai sallama. Kallo daya ya musu ya
    d'auke kai, dagowa Miemie tayi,in ba idonta ke
    mata gezau ba kamar harara ma ta mishi,tuni ta
    gintse fuska ta daina dariya. Ya salam, Miemie
    tai nisa a tsanar Abban su Nabila. Yake tai kan
    ta tashi dan binshi d'aki, "Miemie tashi muje gun
    Abba koh?... Kafad'a ta mak'e tana turo baki, sai
    tai kamar bata gani ba ta kinkime ta,a ranta tana
    fad'in "sai nayi da gaske a kanki Miemie. Ihu ta
    fara tana zazzamewa,a dole ita bazata je ba,jin
    suna iyowa dakin yasa da sauri yace "Kar ki
    shigo min kina min wannan kukan dama.. Chak
    ta tsaya tare sauke ta,kafadar ta kara makewa
    tana kallon Salman,sai ma ta fita tayi bangaren
    su Ja'afar. Kai ta dafe tana mai mamaki ita
    kam,Miemie,toh mey take so da ita?. *DAN
    KUKA...* ************************** Dube yake
    zai k'alli news amma baiga d'ayan remote ba, ga
    Salman ta shiga wanka, Kamar ance diba hannun
    Miemie dake chan gefen corridor tana wasa sai
    ga shi kuwa,yau shine motar ta ma. Da zafin
    nama ya tashi ya nufi gunta.. "Jiyinnnn" take
    dashi cikin tsawa yace "Wannan ne abin yin
    motar?.. Dagowa tai tana t'sareshi da ido cikin
    had'e rai, "Bani nan ni labarai zai wuce ni
    sarauniyar 6arna. Kafad'a ta mak'e mishi tare da
    yi da remote din bayanta tana zunguro mishi da
    baki. Cikin zafin nama ya dagota, dai-dai fitowar
    Salma dan jin fad'anshi, binta yake daga zaunen
    tana matsawa taki bashi,kawai sai ya fizgota da
    niyar kwata ta tun karfi, kai cikin fushi ta kwada
    remote din a kasa tana kuma mishi ihun kukan ya
    hanata wasa.. Dagashi har Salman suka bi
    remote din da kallo wanda kowanne part yai
    nashi gun battery ya cire. Da sauri Salman ta
    karaso ta kwada mata mari,sauke ta yai kasa
    yana sababin ai wai ita tasa ta raina mutane yai
    waje,k'allon da baiyi ba kenan ya fice. Harara ta
    kwada mata kan ta kamo kunnenta ta murde
    tana kuka, "Baki isa ki chazan matsala ba ja'irar
    nan,wato bakin hali ki ke son kowa koh?. Kashen
    aure zakiyi ne?.. Kullum baza'a aji kanmu da
    mijina ba sai akanki?.. Cikata tai tare da dan
    rangwashenta, "Toh baki isa ba,dole kizo ki koma
    gurin Mama koh dangin Abbanki da zama... Bata
    karasa ba Miemie ta fad'i tana burburwar fad'in
    taki,ita bazata ba. Ido kawai ta sa mata,kan tai
    kwafa tai d'aki,da gudu itama ta bita tana kukan
    bazata ba Salman ta rufe kofarta ta batta da
    bugun "Antee,Antee bata cho. Anan tai ta
    mitarta tanaji daga dakin tana "Ai sai kinje...
    Tuni ta kara jiniya, kuka harda shudewa amma
    tai burus da ita tana kwalliyarta. Zuwa chan taji
    shiru,sai tai murmushi, Miemie matsala. Fito wa
    tai dan ganin koh fita tayi,sai ta ganta kwance
    bakin kofa sai sauke ajiyar zuciya take tai bacci.
    Sunkuyawa tai ta leka,ido har ya kumbura, duk
    sai ta bata tausayi,batasan lokacin da ta d'akko
    abarta ba,batajin tunda Miemie take ta ta6a
    dukanta haka tai kuka. Kwantar ta tai a gado
    tana goge mata fuska da tissue,baki ta kai
    fuskarta, "am sorry kinji... kamar ta sa kukan
    itama,Miemie taurin kai toh,Alhaji hancini,ya
    suke so tayi da ranta ne? By Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:34 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    40_Washegari bayan la'asar tace mishi zata
    maida Miemie gidan Mama dan Allah ya batta
    taje daga nan sai tai barkar Ummi data haihu
    cikin dare. Da har zai hana,ganin kayan Miemie a
    akwati yasa bai gardama ba ya batta,kwarai
    tasha mamaki,dan rabonta da fita har ta
    manta,amma dake wacce bai kauna za'a mayar
    ya batta. "Ga driver in kin gama ya kaiku,kar
    kuma ki dad'e.. Kai ta daga tace ta gode.
    Rayuwa kenan,da ya batta ma taji dad'i,koh ba
    komai zata leka gida yau. Gidan Ummi suka fara
    zuwa,sai ta6e baki take tana korafin yadda ta
    zama matar k'ulle. "Aure sama da shekara
    wannan ne zuwanki na biyu gidana,wannan wace
    iriyar rayuwa ce,mutum sai shegen kullen t'siya..
    Tana jinta tai shiru,tana tunanin hali irin na dan
    Adam,mai wuyar gane hali,lokacin Ja'afar mai
    barinta fita haka ta gurza,yanzu kuma ta had'u
    da dai dai kowa,ga kud'i ga cima, amma ba fita
    ba haihuwa.. Zaman lafiya wai yafi zama Dan
    Sarki. Ita kanta Miemie murna take sun fita
    yau,sai dai suna zuwa gidan Mama taji Salman
    na maganar zamanta ta d'ane cinyarta ta riketa
    tam. Ban6are ta Mama take ajikinta tana ihun
    kiran Aunty,ita kuka Salma kuka, ga magriba ta
    sawo kai. Suna haka Abba ya shigo, duk ta rike
    gyalen Salma kam tana ihu. Dak'yar ta fizge tai
    hanyar fita da gudu tana kuka. "Subhanallah... Ta
    shid'e fa wannan... Chak ta tsaya jin daina kuka
    Miemien,da sauri ta juyo taga Abba na jijjiga ta.
    Ba shiri tai gun dai dai Miemien ta kawo wuta ta
    kar6e ta. Kuka na fitar hankali take tana bata
    hakuri, ''Ni bansan mey yarinyar nan zata tsare
    miki ba in ta zauna achan gunki ba,kullum sai da
    kuka koh jinya za'a rabu?.. Ki bar y'arki a kusa
    dake man tunda ita mai kulafuci ce... Kai ta
    daga tana share ma Miemien hawaye tana tai
    shiru toh.. Dole tana ji tana gani ta koma da
    Miemie, dan yau fir taki yadda tunda ta d'andana
    zama da ita. Kanta take shafawa,ita kam ta
    tasata gaba tana ta kallo ba koh kiftawa. A
    hankali tace "Miemie.. Idonta a kan Salman tace
    "Uhmm. Kwanto wa tai a gefenta tana g'yara
    mata kwanciya, kamar wata babba ta fara mata
    fad'an ta zama mai ji dan Allah. "Ban san
    matsala Miemie, ki rufan asiri ki daina halin nan
    naki na kumbura ma mijina baki,kinji?.. Kai ta
    daga mata kamar gaske. Sai tai murmushi tai
    kan tace ta taso suje suyi girki a kitchen. Shikam
    Alhaji da murnar yau Miemie ta tafi ya shigo
    gida,shi kanshi ya rasa mey yarinyar ta tsare
    mishi a gidan,duba ga su Ja'afar na gidan. Sai
    dai tun daga bud'e kofar parlourn farin cikin ya
    kau. Dariyar Miemie ya fara cin karo yana
    shigowa ta kitchen,dan haka da sababi ya isa.
    "Mey ya zaunarki har bayan magriba baki dawo
    ba?... Mey kuma ya dawo da wannan? Duk ido
    suka zuba mishi,mai hali kuwa Miemie tuni ta
    chunno baki gaba tana mishi wani irin kallo jin ya
    fara sababin nashi. "Wallahi har kusan suma tayi
    dan kuka yau,tausayi ta bani shine na dawo da
    ita,kai hakuri duk ita tasa muka kai magriba.
    K'allon Miemien yayi da kamar harara kamin ya
    kad'a kai dan takaici ya fice. Ajiyar zuciya ta
    saka,ta tsalake rijiya da baya da k'yar,kan ta
    dawo kan Miemie ita tuni har ta cigaba da
    sabgarta. Sai dai ana zuwa kwanciya yace daga
    yau Miemie zata bar kwana dakin su,koh ta koma
    kasa. Ya ta iya,dan a zauna lafiya ta sauke
    Miemie kasan,dan ba yadda za ai ta luluka
    yarinya chan wani waje ita tana wata jahar,a
    ganintq Miemie nawa take. ******* Fur yanzu ta
    daina ganin fuska gun Alhaji, in ya shigo ba
    wanda ya isheshi kallo,asalima ya daina zama
    bangarenta sai cin abinci koh bacci. Yau dai ta
    d'au damarar fara koyawa Miemie sabo da Alhaji.
    "Abba ki ne kinji Miemie nah?.. Ki dinga mishi
    oyoyo kina mishi dariya kinji?, banda
    harara,banda turo baki,kina ji na? Shiru tai tana
    binta da kallo kawai,chan sai ta yak'e mata
    hakori. Cikin farin ciki Salman tace "yauwa,koh
    ke fa,be a good girl ba? kai ta daga mata tana
    dariya. Alhaji yai wanka ya shirya yaje parlour
    yana duba abu a system nashi su kuma suna
    daki gun shirya Miemie. Daga parlourn ya kwada
    ma Salma kira wai ta fito mishi da agogon shi na
    kan mirrior. Murmushi tai ta k'alli Miemie,tasha
    parking da ribbon sanye da gown ja da baka iya
    g'wiwa, dake fara ce sai tai mata k'yau sosai.
    Agogon ta d'akko ta kamo hannun Miemie, "Kai
    ma Abba a maza yana parlour,ki nutsu dan Allah
    kinji Miemie nah.. Kai ta daga tana dariya ta
    karbi agogo tai parlour. Bayanta ta biyo dan
    ganin ya zata kaya, daga yau ne zata fara koya
    musu kusanci da juna shi da Miemie. A dunkume
    ta isa gunshi yana duba abu a laptop, mika mishi
    tayi ba koh magana, sai ya dago ganin itace,tai
    mishi kyau sosai,ga sai kamshi take,ba abinda ta
    bari na babanta a ganin shi har dacin ran,in baxai
    manta ba yanzu ne zata shiga shekara uku,amma
    duk ta tara dacin rai wai da fitsara. Kai ya
    d'auke ya cigaba da abinda yake, Salma har ta
    fara murna ganin bai mata dan halin ba yau. Ita
    kwa Miemie sai ta ajiye agogo kan hannun kujera
    ta juya tsautsayi agogo ya fad'o kasan tiles sai
    glass din ya fashe. Da azama ya juya,ganin
    agogon akasa a fashe Miemie ta juya ta mike ya
    fara sababi. "Duk wani mugun hali irin na ubanta
    yarinyar nan ta iya,agogon nawa zaki saka da
    gangan ki fasa min?.. Waje Salma ta fito ganin
    ya yo kan Miemien a sukwane, duk tana k'allon
    abinda ya faru. Kumatun Miemien ya ja tare da
    kai mata rangwashi akai yana sababi,tuni ta hau
    kuka jin zafin abin,da sauri Salman ta karaso dan
    bashi hakuri. "Shegiyar yarinya kawai,kin san
    kud'in agogon da kika fasa kuwa?.. Ja Salman tai
    ta tsaya tare da rintse ido. Ga ihun Miemie tana
    kiran Aunty,ga sai zagin y'arta yake harda
    sheganta mata ita? "Alhaji.. Cikin fusata ta kira
    shi tare da bud'e, Rai 6ace shima ya dago da
    niyar huce haushin shi kanta ta rigashi. "A
    gaskiya ka daina sheganta min yarinya, dan da
    ubanta gaskiya,haka kawai, ina fa kallo tana mika
    maka ka d'auke kai,ta ajiye ya fad'o kasa,toh
    meye lefinta aciki har irin wannan zagi?.. A'a toh
    gaskiya... Kai ta kawar ranta 6ace. Cika Miemien
    yayi yana kallonta, wannan ne karo na farko da
    ya fara ganin fitsarar Salma,shi zatai wa tsawa
    akan Miemie? By Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:37 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 41_Da
    gudu ta karasa tana kama hannun
    Salman,d'aukarta tayi a ta sa6a a baya, "Yi shiru
    kinji.. Muje daki... "Kar ki kuskura ki shigar min
    d'aki da wannan yarinyar.. Chak taja ta tsaya
    tare da juyowa tana kallonshi. "Kema kar ki
    shigar min d'aki,ni zakiyi wa rashin mutunci kan
    y'arki?.. Toh baki isa ba,dan ba ayi macen da ta
    isa daga min murya ba ki sani. Cikin karfin hali
    tace "Toh mey ka ke nufi da hakan?.. Daga fad'in
    gaskiya?.. Haba Alhaji,Kullum ina fuskantar
    yadda ka ke tsagwamar yarinyar nan,shi yasa
    sam bata shiri da kai ai... "Ba wani nan,bakin
    halin yarki dai irin na tsohon mijinki dai,da kuma
    shegen taurin kanta irin nashi,koh kin zata na
    manta da waye shi zamanin neman aurenki? Da
    sauri ta tare mai numfashi harda sauke Miemie
    kasa da sauri, "Ba ruwan Ja'afar cikin maganar
    nan tamu,zai fi kyau in ka daina sakoshi
    ciki..kuma na fad'a maka y'ata bata da wani
    mugun hali,sai dai naka mugun halin rashin son
    yara, da kuma.. Shiru tai tare da ja da baya ganin
    ya zaburo kanta, "wallahi kar ma ka soma,dan ba
    yadda za ai in zuba ido kullum kana aibanta min
    yarinya wallahi, nawa Miemie take? Amma k'arfi
    da yaji so ake ta iya dan hali.. "Salma ni nake
    fad'a kina fad'a?.. Ashe baki da mutunci?.. Kai
    ta kad'a tare da juyar da kai, "Nikwa nake da
    mutunci tunda a cikin gidan ubana ka auro ni
    kuma... "Subhanallah,haba ku k'wa.. Juyawa tayi
    taga Maman su Nabila na shigowa dakin. "Tun
    ina shanya nake jiyo ihun Miemie da naku,bai
    dace ba Allah,kuna abu a gaban yarinya.. "Ba
    ruwanki cikin zancen nan,in ba so ki ke ya taso
    da kwantaccen naki ba ke ma.. Shiru taja
    bakinta tayi tuni idonta ya fara zubar da kwalla,
    ya cigaba "Yara nawa ma basa gabana bare ta
    wani, saboda haka akan yaro ba mai sani ciwan
    hawan jini,dole yau ki mayarta gun ubanta,koh ki
    san nayi da ita. Cikin kuka tace "Bazan iya
    rabuwa da y'ata ba,kai hakuri raina ne ya 6aci..
    Malalacin murmushi yayi,kan yace "Daga baya
    kenan,amma dole ki za6a zaman dani koh da
    yarinyar ki... Maman Ja'afar ta kallo da itama ke
    hawaye tana kallonta,sai ta cije le6e da takaici.
    Juyawa tayi ta d'au Miemie, kan ta kalloshi ido
    na fidda kwalla. "Ni kam na kasance daga masu
    taya annabinmu kishin Al'ummar shi,dan haka ina
    son haihuwa,bi ma'ana zan iya rayuwa da Miemie
    kad'ai mud'in Annabin mu zai alfahari dani...
    Cikin zafin rai yace "Kimin hausar da zan gane
    Malama ni.. "Annabinmu yace kuyi aure dan ku
    hayaiyafa,domin go6e kiyama nai alfahari daku..
    Kayi aure,amma baka fatan tara zuri'a, hakan
    yana nufin kana tarjiya a bisa umarnin manzon
    Allah.. A tunzure yai yo kanta, "Kimin shiru
    fitsararriyar kawai,koh yayarki bata isa ja ina ja
    ba wallahi, dole ne yau ki za6i d'aya.. Cigaba tai
    da batun ta ido rufe, "Nai ma biyayya ta t'sawan
    shekara guda ina bin yadda kaso,toh ka sani ni
    Sunnah na dauki aurena,kuma zan cikashi ne ta
    hanyar tara zuri'a, dan zanyi alfarhari idan na
    kasance a daya daga wanda Annabi zai alfari da
    ita... Mari ya de6eta dashi jiki na 6ari,da sauri ta
    dafe gun tare da bud'e ido,kuka Miemie tasa
    ganin an daki Auntyn ta, "Mutuniyar banza
    kawai,ni zaki mayar jahili?.. Murmushi tayi kan ta
    kad'a kai. "A'a,dan kuwa kafi jahili,danshi dama
    bai sani ba bare take,kai kuwa ka sani amma
    kana taya shedan rawa,dan baka kaunar.. Shiru
    tayi ganin zai kara mata wani,da sauri ta rintse
    ido tana hawaye,jin shiru bataji saukar mari ba
    yasa ta bud'e ido. Hannunshi rike a hannun
    Maman su Ja'afar, "Lalle lokaci yayi da ya
    kamata in tanka maka Alhaji,lokaci yayi da zan
    daina bin umarnin ka ina 6ata.. Ashe har alfahari
    ka ke cewar yaranka ma basa gabanka?.. Jiran
    amsa take tana kallonshi, da borin kunya yace
    "Cika min hannu... Ba musu ta cika, Salma ya
    nuno "Ke kuma ki tafi gidan ku,na sake ki saki
    daya,na koyan hankali,in kin koyo kofa a bud'e
    take ki dawo.. Ido ta rintse gabanta na fad'uwa,
    wai ya saketa?.. Daga fad'in gaskiya. Kan
    Maman su Ja'afar ya dawo, "Wato zuwan
    fitsararriyar yarinyar nan ta sa kin fara sauya hali
    Halima koh.. Kai ta daga da sauri.. "Kwarai
    kwa,dan yanzu na gane kuskuren dana tafka a
    zaman baya da nayi da kai, nima ina son zuri'a,
    ina son su Ja'afar sama da komai yanzu,kuma
    zanso wanda duk yake son su,zan kuma yi fad'a
    da duk mai kinsu, aciki kuwa harda kai usman...
    Baki ya saka yana mata k'allon mamaki
    "Usman?.. Babbar magana.. Halima yau ke kike
    kama sunana ba ma Abban Ja'afar bare Alhaji?..
    Shiru tayi tana kallonshi,sai sababi yake daga
    karshe itama yace taje sai ya nemeta. T'saki
    sukai mai lokaci daya ita da Salma,duk da kallo
    ya bisu Salma tai d'aki. "Ai nima ka sallame ni
    kawai,dan bazan zauna da mutumin dake
    kyankyamin zuri'a ba,dole yau na barka,Allah ya
    yafen baya,amma yanzu kam ta kau,ka sake ni
    nima kawai... "Bazan saki ba,amma dole ki fuce
    min a gida,dan ba mai sa min hawan jini... Kuka
    Salman take tana jiyo sababin da Alhajin ke yi..
    Hannu Miemie ta kai tana girgiza mata kai itama
    tana kukan,gaba daya ta rungumo y'arta tana
    kuka mai cin rai,ita kuma haka Allah yayi ta
    marar sa'a a zaman aure,gashi yau a dalilinta
    auren shekara sama da ashirin na neman
    tsinkewa bayan ta t'sinke nata. By Feenat
    Ja'afar.
    9/29/16, 9:39 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    42_Jugum Abba yai bayan jin bayanin Aunty
    A'i,ita dai Salma sai kuka take,dan tasan yau
    kam sai ta Allah,fad'a kam sai dai ta toshe
    kunnenta. Amma da mamakinta sai ji tai ya
    sauke ajiyar zuciya tare da fadin "Allah ya
    kyauta toh,dama tun farko ni mutumin nan ba
    wai ya mun ba ne. "Yadda naga kowa na yinshi a
    gidan musamman Babar taku yasa nabi yarima
    nasha kid'a, sai fatan Allah yasa haka shi yafi
    alkairi.. Mama ce ta riga kowa saurin fad'in
    "Amin,ni nasan naso shi,amma daga baya sam
    mutumin ya fice min akai,dan daga gani ba wai
    zaiyi wani mutunci bane,ga dankaran kulle,yanzu
    kuma an kara da rashin son haihuwa.. Dame
    yarinya zata ji?.. Kallon mamaki suke ma Maman
    musamman Salma, yau mama ke fad'in aibun
    Alhaji da bakinta?... Lalle abu ya 6aci. Da dare
    suna kwance ta tasa Miemie a gaba tana
    kallo,itama ido ta sa mata, tunaninta zancenta ya
    tabbata. A dalilin Miemie aure ya 6alle..
    Murmushi tai kan ta gyara kwanciya. "Miemie..
    Kai ta daga tare da fad'in "Uhmm.. Sai ta
    mirgino kusanta tai rub da ciki "Kina murna
    kuwa?.. Baki ta yage mata ba dan ta fahimci
    nufin Auntyn ba. Sai ta kad'a kai,ta rasa wane
    irin nishad'i ke shigarta da yamman nan zuwa
    daren yanzu.. "A k'ya kam yi murna,wato kin
    rabu da alakakai koh? Kai ta daga mata tana
    dariya.. Itama tana dariya ta fara mata chakulkuli
    su na k'yak'yata dariya har su Abba dake waje
    suna jiyo su. Mama ya kallo,itama shi take kallo,
    "kina jin mutananki koh?.. Kamar yau take
    Sallah.. Murmushi tai tana sadda kai kasa, sai ya
    girgiza kai yana tuna wani abu. ****** Tun daga
    wannan lokacin hankalinta ya koma kan
    makaranta, babban bakin cikinta bai wuce yadda
    Alhaji yai burus da maganarta ba,a ganinta in har
    da mutunci koh Abbanta ya samu da zancen..
    Gashi a kalla yanzu ta kusa cinye kwanakin iddar
    ta. Duk suna waya da Maman su Nabila tace
    yana zuwar musu,sai dai ita baya samun ganinta.
    "Aunty!.. Aunty!!.. Da dan gudunta ta shigo gidan
    tana k'wada mata kira rike da leda tana ja,bakin
    nan har kusan kunnen Miemie. Kamar a mafarki
    taji kira ana ta6ata,a hankali ta bud'e ido dan
    bata jima ba da bacci ya debeta sakamakon
    ciwan period da take. "Uhmm Miemie.. Ya akai?..
    Ledar hannunta ta hau bud'e mata tana mata
    magana duk a hard'e dan murna. Riguna ne y'an
    kanti masu kyau da tsada da takalma, sai teddy
    guda biyu da y'ar tsana mai feeder a baki. A
    zabure ta mike tana duben Miemien,tasan ba mai
    irin ma wa y'arta tsarabar nan sai Abbanta,yawu
    ta had'iye kamin tace "Miemie,ina kika samo
    kaya haka?.. Dagowa tayi kamin tace "Abba ne...
    Tsam tai tana kallon irin farin cikin da Miemien
    take,wato in zai shekara bata ganshi ba tasan
    Abbanta. K'allota tayi tana mata yake ganin
    yadda take cire feedern a bakin y'ar t'sanar tana
    fad'in Inya.. Inya. Da sauri ta tashi tare da zarar
    gyale tai waje. A kalla zataso ganinshi koh dan
    ganin yadda yake a t'sawan shekara guda da
    d'auri. Sai dai har ta gama leke bata koh hango
    mai kamar Ja'afar fa sai sawun mota. Zaure ta
    koma tana lumshe ido tare da dafe kirjinta. Babu
    makawa Ja'afar ya shigo zauren nan.. Dan ga
    nan kamshin turarenshi ciki tana iya shakarshi.
    Jiki a sanyaye ta juya ta koma cikin gida, a chan
    d'akin Mama ta jiyo karad'in Miemie na ba ma
    maman labari tana dariya. Da murmushi ta samu
    ta dan dosana tana kallonsu kamar ta sa kuka.
    "Na fuskanci yarinyar nan in dai tai arangma da
    Abbanta tana kwanan murna, haka kwanaki
    dak'yar na ban6areta jikinshi ashe bata manta shi
    ba tana kuka,shima harda y'ar kwalarshi yana
    daga mata hannu... Ido ta kurawa Maman ba koh
    kiftawa.. Ba dai Mama na nufin Ja'afar yana
    zuwa garin nan ba kuma har gidan nan?... Mama
    ce ta kat'se mata tunani da fad'in "Ban tunanin
    yaron nan koh a hanya ya ganni zai gaidani ba
    sam bayan aurenki, duba ga yadda na rika mishi
    fatattakar arziki.. Zuwan shi biyu gidan nan ashe
    makaranta ya koma kinji.. Murmushi tai Maman
    da iyakar shi le6e tare da daga kai. Tuni ta
    zurfafa tunani,har bata jin mey Mama da Miemie
    ke fad'a,kan ta farga har idonta ya cika da
    kwalla,da sauri ta juyar da kai tare da goge wa
    kamin su gani. Sakkowa tai tana taya Miemie
    rad'awa teddy suna suna dariya. Kallonsu kawai
    Mama take tana wani tunani, kai ta kad'a kamin
    ta tashi ta basu gu dan tasan Abba yana gaf da
    zuwa. Washegari da yamma tana kokarin shiga
    wanka akai mata sallama. Hijab ta zira harda
    shafa powder da zumudin Ja'afar ne ma,kila ya
    samu labarin tana gida. Turus tayi tare da
    chunno baki kamar Miemie ganin Alhaji da
    abokinshi. Baki ya washe mata yana fad'in ta
    karaso man kusa... Murmushin mugunta tai kan
    ta kalloshi "Dan bani minti biyar na fito a gida...
    Kai ya daga yana mata murmushi, ashe bazai yi
    wahalar shawo kan Salma ba kamar Halima.
    Ruwan da ta zuba na wanka ta d'auka da wani a
    buta dan tsarkake kai in tai wankan t'sarki. Tana
    yi tana murmushi har ta gama. D'aki ta shiga ta
    tsane kanta da towel kan ta dan shirya a
    gaggauce ta fita. Yadda take murmushi ne yasa
    Mama tambayar waye yazo, a tunaninta koh
    Ja'afar ne,tana cewa Alhaji ne ta 6ata rai. "Ki dai
    kama kanki ki saiwa kanki mutunci,dan sam
    mutumin ba nagari bane,kinjini ai? Kai ta kad'a
    tana murmushi, lalle Mama, yau Alhajin guda?..
    Sai ta kad'a kai, "adu'a bata fad'uwa kasa banza.
    Bayan sun gaisa yake zungurar abokin nashi
    sarkin iya t'sari, duk tana jinsu tana murmushi
    dan feleke harda tambayar Miemie,sai da suka
    gama tass tana jinsu tana kad'a kai. "Ai yanzu na
    fita sahun matarka Alhaji,sai dai kabi sahun
    zawarawa na..dan nayi iddah ni... Fuska ya
    g'imtse yana kallonta, "haba kar muyi haka dake
    man,ina fa lissafi,yau watanki biyu da kwana uku
    rabonki da gida na, kinga ai bakiyi wata uku bare
    ace kinyi iddah koh ba haka ba abokina? Kai ya
    jijjiga yana fad'in "kwarai kuwa,dan haka muka
    sani a al'adan ce. Kai ta kad'a tana murmushin
    takaici, wato ga babyn roba,a hular a lokacin da
    akaso a d'auka a randa aka ga dama.. 6aro-6aro
    tai mishi dalla-dalla kan ita ai duk bayan sati uku
    take period, kuma ya sani sai dai ya take. A fafur
    yace shi baisan zance ba,kawai ya maida ta
    dakinta. Juyawa tai ta koma gida,tana ji sai
    kwad'a mata kira yake tai mishi banza. Da farin
    ciki ta shiga har baya misaltuwa, dan da yanzu
    dabarar yin wanka ba tazo mata ba da tuni
    ansha da ita an gama. "Ba dai ya maidaki ba
    naga kina murna tun yanzu Salma?.. Yanzu ke
    bazakiyi kishin kanki ba har kin bada kai daga
    fita bori ya hau?.. Ina laifin ya samo Abbanki da
    maganar in dai da mutunci aciki... "Au dariya ma
    na baki koh Salma?.. Ga shash.. "Mama ni fa ba
    aure a t'sakanin mu da Alhaji yanzu,dan tau nai
    iddah ta.... Baki sake take kallonta,dariya tasa ta
    bata labari,sai ga Mama na tikar dariya. "Lalle
    yarinyar nan da wayo ki ke,kwarai kinyi dabara,
    dan sam mutumin ya sane min, dan ban fad'a
    miki bane,ba'a fi sati da dawowarki gida ba muka
    had'u da dan talikinnan,d'auke kai yai kamar bai
    ganni ba fa,bayan sarai mun had'a ido.. "Shi yasa
    yaron nan Ja'afar nake ganin kimarshi har
    kullum,dan koh bayan rabuwarku yana daraja
    mu,musamman zai sa azo har gida abokinshi yai
    mana goma ta arziki in sun d'au Miemie... Shiru
    tayi tana sauraran maganar Mama, wai Ja'afar
    take ma ya6o haka da kirari?.. Farin cikinta a yau
    bai misaltuwa,ina Miemie na nan ta rad'a mata
    itama suyi tare,tasan dai duk inda take yanzu
    tana neman gida,dan tun dazu tai mata kwalliya
    da kayan Abbanta kaninshi yazo ya d'auke ta.
    Murmushi tai tana jijjiga kai. Lalle ne *Duniya
    Labari ce* By Feenat Ja'afar. feenat-jafar.my
    wapblog.com
    Feenat Jaafar's Mobile Blog
    feenat-jafar.mywapblog.com
    Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Aug 9
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    43_Waya yake d'annawa a nitse yana duba sakon
    waya kamar bayaso,kamili ne,da hasken
    shi,sajenshi a yanzu shine sirrin 6oye kyanshi na
    ainashi, sanye cikin kananan kaya da glass
    manne a idonshi,da gani yana ji da ajinshi a dai-
    dai lokacin nan,dan miskili ne yanzu na karfi da
    yaji. A yanzu ne yake tsone idon y'an mata
    musamman na jami'a, dan ya iya t'sare kai da
    tsare gida. Rayuwarshi ta sauya,dan ya dawo
    ainashin halaiyar shi ta da,koma yafi da din,
    Ja'afar kenan,namijin duniya. Dago kai yayi yana
    duba yanayin garin da yadda kowanne shago
    suke hadahadarsu,sai ya sauke kai kan Abdull
    mai tahowa dauke da baby a kafad'a tana ta
    washe baki tun kan ta karaso. Tuni fara'a ta
    maye g'urbin rashin walwalar shi,kashe wayar
    yayi tare da ajiye ta gefe dan tarar gudan
    jininshi,duk Abba dake gefe kad'an yana kallo.
    "Abbaaa... Miemien ta fad'a lokacin da yake
    k'ar6ar ta,murmushi yayi mata tare da shafo
    fuskarta "Na'am Miemien Abba.. Sai ta washe
    baki. Ciro changi ya mika ma Abdull, "Kan
    magriba kazo ka maidata kaji?... Kai ya kad'a
    tare da amsa yayi godiya. Zama yayi tare da
    d'aura ta cinyarshi, Tasha kwalliya da rigar da ya
    yo mata tsaraba cotton ja da pink,kan nan kamar
    an mata shampoo sai kyalli yake yasha ribbons..
    Hannu yakai kan dan beauty point nata ya latsa
    sai ta sa mishi dariya. A hankali shima yayi har
    hakorinshi suka baiyana. Tashi yayi zuwa gun
    Abba dan mishi sallama,kai ya kad'a Miemie na
    mishi bye-bye tana dariya. Kamar kullum nai yai
    ta yawo da ita suka sai ice cream suka nufi
    gidan Garba nan suka yada zangon su. Miemien
    Garban ya kallo yadda take tsalle kan Abban nata
    shikam sai murmushi yake mata. "Abokina ina so
    yau dai daya ka saurare batu na,sama da wata
    hud'u dana fara ma magana zaka ce a'a kai baka
    so.. Kallonshi yake jin inda yake neman dosa,tuni
    ya fara sauya kama. Ba tare da yabi ta kanshi ba
    Garban yaci gaba "Salma fa au... Cikin t'sananin
    fushi ya rufe ido tare da daga mishi hannu. "Dan
    Allah ka d'aina dawo min da hannun agogo
    baya,ina a cikin farina yanzu,banson jin sunan
    wata Salma chan.. Gefe yayi da kai yana
    chunkune fuska,kai Garban ya kad'a kan yai y'ar
    dariya, "Karyar banza kenan,yanzu da zance
    Salma tana gida an sakota da nasan ba wanda
    zai farin ciki a yau,kaine fa.. Baki sake yake
    kallonshi, "kana sanin abinda zaka fad'a man
    malam.. Matar mutanace fa yanzun. Murmushi
    yayi yana mishi k'allon bakasan komai. "Toh
    auren Salma ya rabu tun wata hud'u da ya
    wuce,sai ka kurbi ruwan sanyi ka huce.. Baki
    sake yake kallonshi ba koh kiftawa. Baya Garban
    yayi da kai yana shafa ha6a tare da daga mishi
    gira,ya dan jima a kame kamin ya d'auke tare da
    wayance wa. "Wannan bazai sauya komai ba
    kama ji da wai,dan ban manta abinda ta dirka
    min ba a baya.. Kama d'aina wata dariya..
    Kafad'a Garban ya make,kan yace "Daga baya
    kenan kuma,chan ta matse ma,dan nasan yau sai
    kafi kowa farin ciki a garin nan,karyar kawai.
    Tashi yayi yana daukan Miemie tare da hararar
    shi, "Kanka ake ji,ni nayi kaga tafiya ta.. Dariya
    yai kan ya mike dan sauke su, "Kaima an kusa
    jin naka soon. Harara ya sakar mishi kan suka
    fice yana ta mishi t'siya. ***** "Mama zan tafi,a
    min adu'a Allah yasa kar na samu mat'sala
    kamar yadda principal yace.. "Amin kam, in Allah
    ya taimaka zasu karbi uzirin.. Kai ta kad'a, ''Amin
    toh, na tafi kan wannan ta farka. Da sauri ta fice
    ganin zatai latti. Allah yasota tana zuwa wata
    Napep zata tashi ta d'au wani da dan sauri ta
    t'sayar ta shiga ba tare da ta dubi na ciki ba.
    "Dan Allah ka taimaka school of... Shiru tai jin
    wani kamshi da ya bigeta,turaren da koh ajikin
    wani taji,toh mutum daya ke zuwa ranta. A
    hankali ta waiwaya dan ganin waye masanyin
    turaren. K'yam tayi tana kallonshi da murmushi
    ba koh kiftawa, shima hakan take,kan da sauri ya
    d'auke kai kamar ma bai ganeta ba yake nufi..
    Dad'i ne..koh farin ciki a ranta a safiyar yau..
    *Ja'afar* Wannan shine yaushe gamo. Kokarin
    mishi magana take yace da mai Napep ya t'saya.
    Ba musu yaja ya t'saya, da mamakinta taga yana
    kokarin sauka a Napep d'in, da sauri mai napep
    yace "Kazo gaba toh. Ba tare da ya kalle yace
    "Kai hakuri,bana shiga keke da mata... Gaba yai
    ya batta baki sake.. Kuturu,wa ya ga turnuku...
    Ji tai tamkar ta d'aura hannu a ka ta kurma
    ihu,wai ita Ja'afar zai haka?. By Feenat Ja'afar.
    9/29/16, 9:44 AM - Queen Safiyyert馃憫: Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
    45_Washegari kowa da farin ciki ya tashi kamar
    ma ance an shirya. Yau tana son ta koma
    Salmanta ta da ne. Yau shima yana son komawa
    Ja'afar d'inshi na Salmateen shi,dan haka tun
    wuri yaje yai g'yaran fuska,ya rage sumar kai,tuni
    ya hasko kamar zamanin angoncinshi da Salma.
    Gun Garba yaje yasha kwalliya kamar wani sabon
    ango. "Ya mutumina nayi kyau kuwa?鈥� banda
    shakiyanci pls. Daga sama har kasa yake
    kallonshi,yai kokakarin 6oye dariyar shi. "Kayi
    man,ina zuwa haka da sanyin yammacin nan
    haka?.. Da zumudi yace "gun Salmatee hayatee
    man. Da rashin fahimta yace mishi "wace haka?..
    Harara ya sau mishi tare da fad'in "Ban sani ba,
    kaima ramawa zaka yin?.. Dan Allah ni taso
    muje.. Kai Garban ya juyar yana fad'in "ba inda
    zani bansan mace ba, haka kawai, Da zumudi
    yace "Salma ta fa,kar kace baka gane ba mana
    mun dinke.. Kunu yasha yace "ban gane
    ba,yaushe aka dinke?.. Koh ka manta
    kalamanka?.. Lallami ya fara yana kasa da
    kai,tuni Garban ya ware yana dillika mishi dariyar
    mugunta. Shi dai yau bata tashi yake ba,burinshi
    kawai su isa ga Salman shi. Yau d'aya ta zauna
    zaman kwalliya duk da bata da tabbas din
    ganinshi,har Mama na mata t'siyar ina zuwa?.
    Murmushi kawai tayi ta ciro wani arnan purple
    swiss tana kallo, shafashi tai tana tunano colorn
    da Ja'afar yafi kauna ya gani ajikinta. Riga da
    zani ne single, dinkin yai mata kyau tsam ya
    kama jikinta, da gaske yau ta fito a Salmanta.
    Tana daga d'aki ta jiyo yaro yazo wai Salma
    tazo,tana jin Mama na fad'in inji wa?.. Bataji
    amsar yaron ba taji Mama tace kace tana zuwa.
    G'yale ta rufa fari da ratsin flower purple tana
    k'allon kanta a mudubi,ina ma Ya Ja'afar ne
    man... "Ki fito ana kiranki a waje Ja'afar yanzu...
    6ata rai tayi tana gunguni, "Ja'afar kuma
    Mama?.. Ni fa ba danshi zan fita ba fa.. Harara
    ta sakar mata,kan ta juya tana fad'in
    "magulmaciyar kawai,ni zakiyiwa alaye?.. Da gani
    shigar Ja'afar daban take gunki ai... Dariya ta
    kunshe kan ta kara k'allon kanta a madubi ta
    fita. Suna tsaye sun rike hannun Miemie da suka
    dakko chan gidan su jaafar suna mata y'ar dage
    tana dariya. Murmushi ta tsaya yi musu da
    sallamarta. Ido ya zira mata,yayinda itama take
    kallon sauyawarshi a yau kadai kamar sabon
    ango. Murmushi ya sakar mata yana daga mata
    hannu halamun tayi k'yau, da sauri ta d'auke kai
    a kallonshi tana cinkune fuska. Kai ya kad'a yana
    murmushi, karya kuma ai ta kare, tunda har
    shigarshi an mishi. Ha6a Garba yake shafawa
    yana kallon wani fulakon karya gun Salma da
    Ja'afar. "Kaganta ni dai ya kamata nayi fushi
    bisa abinda ta dibga min,amma kaga an dakeni
    an hanani kuka... Harara ta sau mishi,kan ta kau
    da kai, "lefinka ai dayawa,bar tunatune kawai.
    Kai Garba ya kad'a,kan ya kallo Salman. "Salma..
    Kalloshi tai,bata tunani ta ta6a ganin Garba ya
    zama serious haka, hakan yasa ta bashi
    hankalinta gaba daya. "Nasan nima har yanzu
    kina ganin baki na sakamakon zuwanmu na
    karshe gunki. Rantsuwa ya mata,kan yace
    "Ja'afar baizo ranar gunki da neman auren kisa
    wuta ba sam,asalima yazo ne danya sadaukar
    miki da farin cikinshi gare ki sakamakon sanin
    waye Alhaji Usman.. Kai ta dago tana kallonshi.
    Sai ya kad'a mata kai, Ja'afar din ta kalla,shima
    itan yake kallo. Yacigaba, "yana son ki samu
    farin ciki ne Salma,wanda yasan a gidan Alhaji
    dak'yar ki sameshi,dan kaf halin Alhaji ba wanda
    ba'a karanto mana ba,hakan yasa ya gwammaci
    ya baki ni,duk nai imani sai ya fi mishi ciwo
    sama da auranki a waje.. Ya kallo Ja'afar da
    murmushi, "nasan abuna. Murmushi sukai ma
    juna,tabbas hakane,dan da Garba ya auri
    Salma,da yana gani bashi ba sake ganinshi bare
    hulda da gidanshi. "Dan haka banajin da wanda
    ya kai Ja'afar son farin cikin ki,ki d'aure ki bawa
    abokina second chance a zamanku kamar yadda
    bukaci haka. Nan yai ta musu fad'an rayuwa sai
    y'ar hakuri ce,da sanya tsoron Allah a
    lamari,gashi sunji dad'in tawakallin tunda suna
    fatan in Allah yaso su maida aurensu. Kan Garba
    ya tafi sai da ya tabbatar kowa ya yafe. Zaure
    suka koma ta sa musu taburma. Kallonta yake
    suna ma juna murmishin so cikin kauna. Sai wani
    dan sinke kai take halamar kunya. Hatta Miemie
    ta gane iyayen sun dinke, sai kallonsu take tana
    murmushi. "Assalam Alaikum.. Kai suka
    dago,Ja'afar ya amsa. "Aunty Salma wai ana
    kiranki a waje.. Kallon Ja'afar d'in tayi, Shima ita
    yake kallo,sai yai mata murmushi. "Tashi muje
    naga wane tsageren ne wannan... Miemie ya
    d'auka itama ta tashi tana murmushi suka fita.
    Alhaji ne yasha gayu da babar riga da wata
    katuwar mota yana murmushin ganinta. Fuska ya
    tsuke ganin fitowar Miemie da Abbanta suna
    wasan su. Tana ganin Alhaji Miemie ta g'imtse
    fuska,murmushi Ja'afar ya mata tare da shafo
    fuskarta suka karasa. Hannu ya bashi dan su
    gaisa Alhaji ya juyar da fuska gefe. "Gunki nazo
    fa. Kallonshi tayi tana murmushi, "toh
    Alhaji,gamu ai.. Da halamar tambaya ya k'alleta.
    "Ban gane ga ku ba?.. Kina nufin dashi zan
    ganki?.. Ja'afar d'in ta kallo tare da Miemie dake
    kallon Alhajin duk rai had'e daga shi har y'ar.
    Murmushi tayi tare da matsawa kusansu suka
    jeru mishi a gaba. "Alhaji, kai hakuri, kai
    hakuri,ka daina zuwa,InshaAllah aurenmu zamu
    mayar da Abban Miemie.. Ka d'auka zaman mu
    yazo karsh.. ka d'auka rabuwar aure na da kai da
    auran duk had'i ne na Allah... Ja'afar ta kalla tai
    mai murmushi tare da shafo fuskar Miemie. "Kai
    hakuri na na zauna da iyalina, ka yarda sune
    farin cikina, ni ce tasu,kai hakuri pls... Kai ya
    kad'a,tare da kallonsu,duk daga gani suna a farin
    ciki.. Tabbas yasan yai sake,gashi ya tashi a
    tutar babu,ba Halima ba Salma,ba su Nabila ba
    Miemie... Wa zai gane a jiya yayi nadama?.. Ya
    zasu gane yasan dad'in jin motsin D'a kusanshi a
    yanzu?.. Wa zai gane ya hakura yanzu kam yana
    son zuri'a?.. Murmushi yayi yana d'auke kai,kila
    haduwarshi da Salma sanadin shiryuwarshi
    ne,koh yanzu ya gode Allah. Kai ya kad'a tare da
    masu fatan alkairi, k'warai tai mamakin jin harda
    mata godiya a bisa gaskiya da take tsage mata.
    Hannu ya mikawa Miemie fuska d'auke da
    murmushi. Kafad'a ta mak'e tare da lafewa a
    kafad'ar Abbanta. Mota ya shiga tare da fitowa
    da leda cike da shopping na chocolate da ice
    cream.. Alawa daya ya fito dashi tare da fad'in
    "Zan baki sweet fa,zo mu gaisa mana Miemie..
    Salma ta kalla kamar mai jiran umarninta.
    Murmushi tai mata tare da daga mata kai,abin
    kai sai taje ba musu,yau sai ga Miemie harda ma
    Alhaji dariya. Da zai tafi hannu ta daga mishi
    tana mishi bye-bye tana dariya. Duk sai Alhajin
    ya bata tausayi Alhajin,har Ja'afar na daga mata
    gira halamar tambaya. Marairaicewa tayi tare da
    shagwa6e fuska. "Y'arka ta rabani da Alhajina
    shikenan kunji dad'i.. Harara ya sakar mata
    kamin yace "toh bishi, Allah yai ma y'ata albarka
    yarinya mai kishin Abbanta koh? Kai ta daga
    mishi tana dariya,da murna ya shillata sama ya
    chafe suna dariya. Gwalo yai ma Salman,sai
    Miemie ma ta hau mata,tuni ta fara chunno
    musu baki suna cikin shagwa6a. By Feenat
    Ja'afar.
    Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Aug 11
    Feenat Ja'afar Novel's
    *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 46_Ba
    sauran jira,dan karara suke nuna ma fitsara a
    gidan Mama, su Ja'afar abin nema ya samu,ba
    guntun fulako,ba shiri ta bama Abba shawarar ayi
    a mayar da auren nan. Wata daya aka sa suka
    sha biki kamar ba gobe.. Nan take jin labarin
    auren Bintu a gidan mai mata uku,tana chan ta
    zama bora. Su Maman Abba duk sun halarci bikin
    nata,nan take tsurkuta mata labarin Maman
    Ummi kan ranar ta fita gantali miji ya
    dawo,bayan ta dawo yace ta nemi inda dare ya
    mata,karshe dai akai saki. Murmushi tayi,tasan
    Allah ba azzalumin sarki bane,dole yadda taga
    tasku Maman Ummi tagani itama. Jingina yayi a
    jikin bango yana kare mata kallo,fuska rufe ruf da
    g'yale,murmushi yayi dan tunawa da daren
    farkonsu a wanchan gidan. Karasawa yayi tare
    da g'yaran murya kad'an yana leka fuskarta.
    Zama yayi tare da sauke ajiyar zuciya. A hankali
    ya kai hannunshi tare da daga mayafin da ta rufe
    fuskar. Tsam yayi yana kallonta ido cikin ido,tuni
    ya marairaice mata fuska,kuka fa?.. Hannu yasa
    yana share mata wani na zubowa,duka ya hayo
    gadon tare da janyota yana shafo bayanta
    halamun tai shiru. Sai da tai shiru kan ya dago
    kanta. Ido suka zuba ma juna ba koh kiftawa.
    Chan ya nisa cikin murya kamar mai jin bacci
    yace "Kin tuna kalaman da na ta6a turo miki na
    karshe cikin text message dina kuwa?.. Tunowa
    ta fara,sai yai murmushi tare da zamewa kan
    katifa da ita a kafad'arshi. Ajiyar zuciya suka
    sauke tare da kamo y'atsunta. "Na ce miki _" a
    heart dat truly loves never loses hope..but
    always believes in d promise of love,no matter
    how long d time and how far d distance,at d right
    time,love will fine a way".._ "Hope kin yarda da
    maganar ba wai soki burutsu Masoyinki bane?.
    Kai ta daga mishi halamar ta yadda,tunda ga nan
    K'ADDARAR wani zama ya kara had'a su waje
    daya. Yau kam ya gama gasa mata jiki da
    d'anyun kalaman da ya tanadesu kawai da
    Salmanshi,fatanshi Allah ya kare sa6ani a
    tsakani. Washegari da t'sant'sar farin ciki suka
    tashi,suna kitchen had'a break fast sai nannan
    yake da ita. Tashin Miemie suka ji tana kiran
    Aunty cikin kuka taga sabon waje. Ganin iyayen
    waje daya ita kanta sai binsu take da kallo,
    mot'si kad'an ta kallesu,kamar wacce bata so su
    rabu da juna suyi rayuwarsu tare. ********** Yau
    ziyara aka fito ta sallah ita dasu Ummi, Sun zaga
    duk inda ta tambaya saura gida 1 taga sun
    karkata zasu shiga gidan kawunsu wanda jiya
    sunje. Ja tai ta tsaya tare da ce musu su shiga
    su fito dan yau bata tambayi nan ba. Murmushi
    Aunty A'i tai tare da kad'a kai,a lalle kullum
    Salma hankali na kara zuwar mata. Tuni Ummi
    kam tai gaba tana t'saki. Tana nan tsaye
    kawunsu ya fito a gidan,bayan sun gaisa yace
    mata ya bata shiga ba ga y'an uwanta suna ciki?
    Kai a kasa tace "Abba ban tambayi nan ba
    ne,dan jiya munzo yini. Murmushi yayi na jin
    dad'i, "hakane kinyi tunani mai kyau,Allah ya miki
    albarka. Kai ta kara kasa kamin ta amsa. Kud'i
    ya ciro daga aljihu ya kirga dubu ya bata,dan
    sosai Salma tana wa mutane bazata,yana
    matukar son mutum mai gyara kuranshi. "Sannu
    da jira uwar y'an ka'ida... Juyawa tayi daga
    kallon wani a mota sun tsaya da Kawunsu da ya
    wuce yanzu,sai dai kan ta tantance su Ummi sun
    fito. Murmushi ta mata tare da basar da zancen
    suna tafiya. "Wannan ai wahala ce,ace duk inda
    zan shiga sai miji ya ban izinin shiga?.. Kai ta
    girgiza, "gaskiya da sake.. Hararar da Aunty A'i
    ta mata ne yasa tai shiru. Kallo Ummin tayi da
    murmushi, a irin hudubar nan a baya suka
    dilmiyarta,ita kwa yanzu a shirye take da yima
    Ja'afar biyayya matukar bazata sa6a Allah ba.
    Har akaje gida nan ma Ummin ta hau zaiyyanawa
    Mama halin da Salma ta tsiro, tuni Mama tai
    mata kacha-kacha,Ummi harda kukan takaici
    ranar. Da dare yazo ya dauke su,sai taga a motar
    Garba da kamar ta ganshi dazun. Taga anje gida
    yana kokarin rufe mota da abin rufa sai ta kasa
    d'aurewa ta tambayi nan zata kwana? Murmushi
    ya mata tare da bud'e gida. Sai da akazo
    kwanciya yake sanarta ai shine albishir din dazun
    da yace sai sun zo gida. "Ya sai sabuwa ne,sai
    mukai cinikin wannan dashi tawan, munyi abin
    hawa. Murna tai ba kadan ba tana k'allon
    mukullin motar. Ido ya zuba mata yana kallo ba
    koh kiftawa. Baki ta kai kan idon tare da hurewa.
    "Salma.. Hankalinta ta bashi tana murza
    yatsunshi cikin nata. "Daga yau na yard'e miki
    koh ba idona ki taka ko'ina u r free... "Dazun
    naga komai Salma,ina horn bakiji bane,kin sani
    farin ciki dazun kinsa naji ni din na isa gun
    matata.. Duk inda ta tambaya nan zata jefa
    kafarta. "Sai ganan kuma kawu shima ya labarta
    min yadda kuka yi sai murnar wai kin san ya
    kamata yake.. "Nagode sosai,yau har kawu
    yasan ni mai fad'a aji ne a gidanshi.. Murmushi
    tayi tana kara ruk'unk'umo shi. Ta gode Allah da
    yasa ta gyara dabi'ar ta maras kyau ta maye mai
    kyau. Fatanta duk wata mace mai irin halinta ta
    daina,dan ita taga misali akanta. Dan a yanzu
    rayuwarta ta fi mata dad'i da kwanciyar hankali,
    ta gane yanzu kulle ma wasu matan ke ja ma
    kansu, tana fatan kowacce mace ta guji fita a
    bisa sharad'in *A BAKIN AURENKI* da suke
    yi,dan gudun haifar da saki irin nata mai
    gabadaya. Alhamdulillah.. Nan na kawo karshen
    littafin A BAKIN AURENKI.. Ina rokon Allah
    kuskuren da nayi ya gafarta min. Da fatan
    darasin ciki ya isar masu halin Salma za kuma su
    gyara,Allahu ya datarmu aikin kwarai a
    gidajenmu. Gareku dubin masoyan Feenat
    Novel's, na gode kwarai da kaunar ku
    gareni,Feenat na son duk mai sonta, dama wanda
    bai yinta.. Luv you all. Sai kun sake jina a sabon
    littafi mai sunan... *RABO IN YA RAT'SE*...
    Nafisa Bashir Tanko, (Feenat Ja'afar) ke muku
    fatan saduwa da alkairi.

    @BABA MONO HAXOR 



    No comments:

    Post a Comment


Pages